Complete Hausa Novels

Bakin Rijiya Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Bakin_Rijiya_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 14 of 44

    A parlor zaune hafsat take a kujera me mazaunin mutum biyu,se shaam dake zaune a me mazaunin mutum d'aya,dak'yar ya iya bud'e bakinshi yace

"Hafsat ya jikinki"

"Naji sauqi Alhamdulillah"

"Akace kina nemana?" sadda kanta tayi qasa "Yaya dama zancen komawa nane gidanka,dan Allah kayi hakuri abubuwan dasuka faru wlhy ko mutuwan khaleefa ba laifina bane lokacin sa ne yayi" murmushi yayi yace

"Haba hafsat,kewai bakya fahimtar abubuwane? Ban soki nakuma zauna dakeba sanda kike mutum me lapiya,se yanzu dakika zama nakashashiya,na dade da fad'a miki sam bakin rijiya ba wurin wasan makaho bane saura miki yaushe ki gama iddah,idan ma banyi kuskure ba aiba idda a kanki,saboda haka kiyi hakuri ki kalli dahir ni bazan taba dawo dake gidana ba,ina miki ao irinna yan uwantaka matsayinki na kanwata amma bawai zancen aure ba" dukda bata gani amma hakan be hanata duban inda take jiyo sautin muryanshiba tace tana kuka

"Yanzu yaa shaam idan kai dakake dan uwana ka gujeni akan inada matsala waye aduniya ze aureni? Kaine sanadin lalacewar rayuwata,ka b'atamun duk wani abu danake taqama dashi,bani ga karatuna babu labarin future na,banida d'a ko d'aya a duniya da wanne kakeso inji?" murmushi ya kuma yi

"Hafsat wlhy kinji na rantse bazan tab'a iya zaman aure dakeba,ke ni idan ma kinamun wannan maganar haushi kike bani wlhy,kimun magana kanki tsaye indai zaki bani matsayin yayanki to zakiga gata na haduwa,amma zancen aurennan yarabu kenan har abada,idn bakida wani abun fada zan wuce"......sanda ta d'anyi shiru sannan tace

" Nayi dana sanin saninka arayuwa,nayi danasanin kasancewarka d'an uwa na jini agareni,nayi danasanin aurenka,nakuma yi danasanin aurenka,nayi danasanin kasantuwar zuciyata tawa ina ma ace canje aka mun bisa kuskure dana roqa a sauyamun da tawan sabida na kaucewa wannan wahalalliyar soyayyar,daga rana me kama da yau inaso ka nemo biro da takarda kakuma rubuta ka ajiye cewar ni hafsat nakashashiya nafita arayuwarka na har abada,na yanke duk wata alaqa dake tsakanina dakai, harta zamanka d'an uwana,ko a hanya ka ganni karka nuna sanayya tsakanina dake,bana buqatarka arayuwata ka sani ayau d'innan wlhy na tsaneka tsana mafi munin tunani,bazan hana zuciyana haukanta na sanka ba amma zan iya haramtawa rayuwata koda gaisawa dakai koda hakan yana nufin zan rasa ilahirin rayuwata kuwa tunda ai ka gama nak'asani meya ragemun,nice nan yaa shaam zan tabbatar maka da cewar bakin rijiya sam ba wurin wasan makaho bane" Yad'anyi mintuna biyu bece komai ba secan ya nisa yace "Hafsat me kuma ya kawo maganar tsana anan nifa d'an uwankine" miqewa tayi ta soma doddogara sandarta tana neman hanyar waje,kasancrwar tasan tsarin gida. Yasanya tayi amfani da basirar ta ta nufi cikin gidan zuwa dakinsu.....duk wannan zantutuukan nasu akan kunnen abba haris tausayinta me tsananin gaske ya rufe shi,daganan ya qudiri niyyar nemawa hafsat lapiya kota halin qaqa koda kuwa dukkanin abinda ya mallaka ze qare.....

    Hafsat tama kasa kuka,gaba d'aya wani mummunan yanayi takeji a zuciyarta game da shaam,tabbas yau tafara jin yana fice mata arai cikin qanqanin lokaci,wayantane ya soma ringing tashiga lalubarta tana kamowa dama wurin sazata amsa kira baze mata wuyaba ya sanya ta d'aga ta kara a kunne

"Assalamu Alaikum" shine tajiyo am fad'a a d'ayan b'angaren tun kafin tayi magana,cikin sanyin murya tace

"Amun wa Alaikassalam,barka da wuni"

"Hafsat ya gida ya kuma jikinki?" "Da sauqi Alhamdulillah" ta bashi amsa "Sunana Dr.sayyeed Hameed Ali uncle d'inki" Murmushitayi tamkar yana gabanta sannan tace "Ayya Uncle say ya aiki yakuma kwana biyu?"

"Alhamdulillah hafsat,dama Number din abban ki damuke da afile nayi tankira baya zuwa gashi kuma emagency case ne ya taso,shiya sanya nace barin nemeki ko zaki had'ani dashi"

"Babu damuwa uncle say barin je ingaya mishi seya duba last call nawa ya kiraka,amma sekayi hakuri ni kadaice adakin khairii batanan,idan tashigo seta rakani gun abban" sosai ta bashi tausayi yace "Babu damuwa hafsat,nagode sosai"
"nima nagode sosau uncle say Allah ya saka ma da alkhairi" har ranshi yaji dadin adu'arta lokaci d'aya ya tuna da matarsa margayiya data tafi ta barshi da tsananin kewa,itace take yawan masa adu'a irin wannan tun bayan mutuwar mahaifiyarsa......
  
   Office Abba yaje ya sameshi,bayan sunyi magana awaya,da suka gaisa Dr.sayyeed ya tattara nutsuwarsa gun Abba sannan ya gyara zaman gilashin idonsa yace da Abba

"yallab'ai Allah shine ya dasamun tsananin tausayin hafsat wanda tunda nake ban taba jin tausayin patient kwatankwacin yanda naji akan hafsat ba,musamman yanda na kula da karacin shekarunta, da farko dai ni haifaffen qasar India ne amma kuma d'an asalin Nigeria,mahaifina likitane kwararre wanda gaba d'aya acn yake aiki acanne ya had'u da mahaifiyata datake Ba'indiya kasancewarta musulma gaba da baya ya sanya basusha wahala iyayensu suka aminta dasuyi aurensu, acan aka haifeni kuma acan nayi karatu na gaba daya,bayan mahaifiyata ta rasune mahaifina ya dawo ainahin qasarsa wato nan Nigeria a kuma birnin sokoto,inada qanne na mata guda biyu suna gidansu mahaifiyata dake Babban birnin indiya wato Goa acan suke karatunsu,ni kadaine nabiyo mahaifina nayi aurena anan har Allah ya karb'i ran matata a wurin haihuwa......Dalilin daya sanya na baka tarihin rayuwata shine sabida inaso kaje kayi bincike kaji koda zaka da abinda zan fad'a maka yanzu,dukda yake dakai nakesan muyi tafiyar idan ma hakan ta kama" Dukda yake Dr.say yayi magana me harshe damo amma abba be katse shiba yace "Ina jinka sayyeed"

"Mahaifina ya mallaki qatotuwar asibiti tashi ta kanshi a k'asar india inda kusan garuruwa hudu a fadin qasar zaka tarar akwai branches nata,zan baka komai sekayi browsing ka gani,akwai wani qwararren likita dake aiki a asibitin na mahaifina wanda shararre ne a b'angaren k'walwa shine nayi waya dashi sabida al'amarin hafsat yana damuna a bakin shi naji cewa inshaa Allah indai tanada rabon gani a duniya Allah ze bashi ikon mata aiki kuma fitowar farko ta warke sabida badashi aka haifeta ba, dama nikuma zanje india gun yan uwana dakuma kula da asibitin ta mahaifina shine nake sha'awar zuwa tare dakai da hafsat idan bakuda damuwa,nidai ayanda nake tausayin hafsat bana san ko sisin ku har jirgi ma nine nan zan dauki nauyi amincewarku kawai nake buqata dakuma uwa uba adu'arku" sosai Abba haris yaji dad'in wannan zancen yace "wannan ai babban ci gaba ne sayyeed,kuma zancen yadda tun yaushe aina yarda zancen kuma wai kyauta duk bata taso ba nine nan zan biya komai har zancen tafiyar ma,kuma wlhy na gode nagode maka sayyeed Allah ubangiji ya albarkaci rayuwarka ya sanya haske acikinta yakuma d'aukaka,Allah ya jib'anci lamuranka ya baka wata matar ta gari ya ilmantar da bayanka yakuma tallafi bayanka sayyewd" godiya sayyeed din tun kafin abba yabar asibitin yafara processing visa batare da sanin kowaba.......

     Ranar wata juma'a hafsat na kwance ta rufe idonta acewarta ba amfanin bud'asu wayanta ya soma ringing janyowa tayi ta kara a kunenta bayan ta d'aga,jin muryanshi kad'ai ya sanar mata waye me kiran cikin shagwaban dabata masan tana dashiba tace "Uncle say se yanzu,ni baran ma kula kaba Allah kuwan" murmushi yayi tamkar tana gabanshi

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.