Romantic Hausa Novels

Matar Shege 1 Complete Hausa Novel

Reading file: MATAR SHEGE (1).txt

Chapter 21 of 21

Page 21

*BUY DATA FROM THE AFFORDABLE PRICE*

*I selling MTN data with this cheap price*

*MTN DATA PACKAGE*
500MB@===200
1GB@=====300
2GB@=====600
3GB@====900
5GB@====1,500
10GB@===2,600
15GB@===3850
20GB@===5000
40GB@===9900
Dial *460*260# to check Data balance.
*Validity 1 month*

*Airtel,9mobile and Glo* *also available.*
*Subscription for DStv gotv star time electric pay bills* *Whatsapp OR
Call 08066268951*

Na tashi zaune ina sake kallon sak'on da d'umbin mamaki,lallai Habib ya na son wargaza min shirina,aikuwa yanzu ne zan d'aura d'amarar zabga masa madarar rashin mutunci,don wallahi ba zai sani na yi wahalar banza akan Salim ba,na kira shi bai d'auka ba,sai sak'on da ya sake turo min me d'auke da kalamar _"I love you "_. Ban samu bacci ba a daren har sai da na samawa kaina mafitar da ta dace.

Washegari da sassafe na tafi gidan su Ummi,na samu dai yau ta kula ni,ta yi ta min nasiha a tsanake,na tambaye ta Kawu Sabi'u,ta ce ya na d'akinsa ba ya jin dad'i,ta ce jiya ma shi ya yi ta tausar Kawu Ummaru,don cewa ya yi sai ya zaneni,na yi farinciki kuwa don dama wurin sa na zo,na ce mata zan shiga na duba shi.

Ina fitowa tsakar gidan na ga Kawu Ummaru ya na shirin fita,ya zabga min wata kafirar harara,na sunkuyar da kai na gaishe shi,bai amsa ba sai k'wafa da ya yi ya fice,na tab'e baki ina bin bayansa da harara sannan na yi sallama a d'akin da Kawu Sabi'u ya ke.

Ya amsa,ya min izinin shiga,na shiga da sallama kaina a k'asa,ko fuskata ba na son ya gani,saboda nauyin zancen da na zo masa da shi, kamar amarya haka na nemi wuri na rakub'e,ina sake jawo hijjabina,na gaishe sa na yi masa ya jiki,ya amsa,na yi shiru na d'an lokaci kafin na ce" Kawu dama wata magana ce nake son yi maka"

Ya ce"to Zinatu,ina jinki".

Na ce"dama akan zancen aurenmu da Habib ne".

Ya ce"to,wani abun ne kuma ya taso? Ba an ce ya yarda zai aureki a hakan ba?"

Na ce"e,amma ni Kawu wallahi na fi son na auri shi Salim d'in".

Ya ce"meyasa?"

Na yi kalar tausayi na ce"wallahi Kawu ni ina tsoron wulak'ancin da zai biyo baya,wannan abun da ya faru k'addara ce,kuma ni a yanda nake gani Habibu zai aureni ne kawai saboda mugunta,wallahi yanzu ba so na ya ke ba...".

Sai na ga ya had'e rai,ya ce"shi ya fad'a miki yanzu ya daina son ki?" Na girgiza kai,alamar a'a.

Ya ce"to kul! Na sake jin haka daga bakinki,babban rufin asirinki shi ne ki auri Habibu,don kuwa shi ne kawai zai iya zama da ke ba tare da wata tsangwama ba,saboda irin yanda ya ke son ki,kuma ke ma sai bayan auren za ki fahimci abin da ake fad'a miki".

"Ba za ku gane ba!" Na fad'a a zuciyata.Wani takaici ya rufeni,nan take kuma wata dabarar ta fad'o min,wadda nake kyautata zaton ita ce ma babbar mafita,amma ni da na tsaya duhun kai ban aiwatar ba.

Na tashi na fita daga d'akin,ina jin takaicin su na rashin fahimtata,sallama na yi wa Ummi,na tafi,kai tsaye bakin titi na yi,na siyi sabon sim na saka a wayata,na yi gida.

Ina zuwa k'ofar gida na tadda motar Salim ta na k'ok'arin tsayawa a k'ofar gidanmu.Na ji irin abinda na ke ji idan na gan shi a y'an kwanakin nan,tsayawa na yi har ya daidaita fakin ya fito,mu ka tsaya muna kallon kallo na tsawon minti biyu kafin na k'arasa inda yake,na gaishe shi ina sunne kai,ya amsa fuska babu yabo babu fallasa,sannan ya mik'o min y'ar jakar da take hannunsa ya ce"congratulation Mrs Muhammad Salim!".

Na karb'a ina mamakin maganar sa,tun kafin na bud'e jakar ya shige mota ya bar unguwar. Na shiga gida,har ina tuntub'e saboda sauri,ina shiga d'aki na bud'e jakar,wani abu ya caki zuciyata ganin abin da yake ciki,invitation ne me kyaun gaske,d'auke da sunana da na shi,na duba date d'in na ga kwanaki biyar ya rage aurenmu.

Na fad'a katifata ina yin siririyar dariyar farinciki,can kuma na rungume katin na fara hawaye.

Na jima a haka,sannan na zabura kamar an tsikare ni,na d'auki wayata na saka sabon sim d'in,na nemo lambar mahaifiyar Habib,sai dai duk rashin kunyata sai na ji ba zan iya aiwatar da abin da na yi niyya ba,na yi shiru ina nazari,kafin na d'auki jakar invitation d'in na fice daga gidan.

Kai tsaye wurin da na san zan samu Anas na yi,na yi sa'a kuwa ya na nan,sai na ja shi gefe,bayan mun gaisa na yi tsara masa duk abin da ya faru tun daga farko har k'arshe, sannan na fad'a masa abin da na ke so ya yi min yanzu.

Tunda na fara jawabi ya ke jinjina kai,ina kai aya ya ce"lallai Zinatu ke ma fa babban kai ce".

Ya d'ora"yanzu da gaske wannan gayen ne zai aureki?"

Na yi wani murmushi na ce"har ka ga invitation ai ya raba tantama".

Ya gyad'a kai ya ce"kawo wayas!".

Na mik'a masa wayata bayan na kira lambar mahaifiyar Habibu,bugu biyu ta d'auka Anas ya k'aro k'arar wayar ta yanda har na ke iya jin muryarta

Bayan ya gaishe ta ta tambaye shi me magana,ya yi gyaran murya ya ce"abokin Habibu ne".

Ta ce"to ya aka yi? Ai Habibun ma yau bai fita ba,ba ya jin dad'i ".

Anas ya ce" kin san kuwa Zinatu ce dalilin rashin lafiyarsa?"

Ta ce"kamar ya?"

Nan fa ya kwashe k'arya da gaskiyar da muka had'a ya zayyane mata tsaf,tun kafin ya kammala take jero salati da sallallami,sannan ta yi masa godiya,ya katse kiran ya mik'o min wayar,na yi masa godiya sosai ba shi invitation d'in har da na samarin unguwa,na koma gida,zuciyata fal da farinciki.

Ashe na yi wani kuskuren ban sani ba,za ku ji nan gaba...

Ban jima da komawa ba,yaro ya shigo wai ana sallama da ni,duk a zato na Habib ne,amma ina fita na yi saranda ganin Junaina tsaye a kusa da motarta

Na ji wani kishi ya rufe ni,na had'e rai na k'arasa inda take na ce"lafiya dai ko".

"Ita ce ta kawo ni" Ta fad'a,sannan ta zuge jakarta ta fito da wani envelope ta mik'o min.

Na kalle shi a k'yamace ina tab'e baki na ce"wannan kuma fa?"

Ta ce"me ki ke jin tsoro? Tunda har ki ka samu nasarar sace zuciyar Salim ai kin cika jaruma,ba na jin akwai abin da kanki ba zai iya d'auka ba".

Na karb'a,ina yi mata kallon daidai nake da ke.

Ta na k'ok'arin shiga mota ta ce"wancen tsohon layin nawa fa ya daina tafiya,idan ki ka buk'aci gani na sai dai ki zo wurin sana'ata".

Ba ta jira cewa ta ba ta shige mota ta tafi,na shiga gida,ina auna maganganunta,to uban me zai sa na nemi ganinta? "Mahaukaciya!" Na furta ina k'ok'arin bud'ewa,don ta lik'e da gam

"Innalillahi wa inna ilaihi ra'jiun!" Na furta ina fito da duka idanuna waje,wani tashin hankali me bugar da zuciya ya rikito min,ganin abin da ya ke ciki.

Jagwab! Na zube a wurin,ina dafe k'irjina,ba dan na san ba ni da ciwon zuciya ba da zan ce yanzu tashi zai yi,to ta yaya?

Gaskiyar Junaina,dole na neme ta!.

*LAST FREE PAGES*

KADA KU MANTA ZINATU TA CE TAYI KUSKUREN RASHIN GANIN SHAYE-SHAYEN SALIM A MATSAYIN MATSALA!

KUN SAN WACE IRIN ILLA SU NAZIFI SUKA YI MATA?

KUN SAN WANE IRIN KUSKURE TA YI,NA FADAWA ANAS SIRRINTA?

KUN SAN ABINDA JUNAINA TA KAWO MATA?🙆🏻‍♀️

Duka wannan amsoshin suna wurina,kudai ku biyo ni don jin yanda za ta kaya,na tabbatar ba za ku yi kukan kud'in ku ba, don yanzu aka fara wasan.

Ku dai ku hanzarta,don babu jira,gobe za mu d'ora💃

*ME SON CIGABAN SA 200 NE KACAL!*

_KATIN MTN, NA 200 TA WANNAN LAMBAR_
08028966015

MASU TUROWA TA ACCOUNT ZA KU TURO TA NAN
HADIZA ABDALLAH ZENETH BANK
2217944522

SAI KU TURO SHAIDAR BIYA TA NAN
08028966015

Y'AN Niger za ku turo katin Airtel 300f ta wannan lambar
08028966015

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.