Trending Hausa Novels

Auren Huce Haushi Book 1 Complete Hausa Novels By Maman Fatima

Reading file: AUREN HUCE HAUSHI BOOK COMPLETE DOCUMENT BY MAMAN FATIMA.txt

Chapter 11 of 34

PAGE SEVENTEEN (17)

_________ Karfe biyar mai kyau motar da Alhaji Jafar ya tuko da kansa daga shi sai Zahra a ciki daga bayansa Kuma Abdul Hakeem ne a wata motar ya biyo Abban nasu bisa umarninsa,suka dira kofar gate din gidan Zahra,sau biyu Abban yayi horn Mai gadin ya leko da yaga Alhaji ne da kansa tunda daman ya San Alhajin farin sani yayi sauri ya bude kofar suka shigo gaba daya, da sauri Mai gadin ya karaso Yana budewa Alhajin kofa Yana gaishe shi yayin da Abdul Hakeem ya budewa Zahra ta fito suka zagaya Gurin da Abban yake, Abdul Hakeem suka gaisa da Mai gadin sannan Abban ya Kama hannun Zahrar ya nufi kofar main falon da ita, tasha farar laffaya Mai adon kananan flowers pink, jikinta kamar an Mata barin turare sai tashin kamshi take Mai Dadi. A bakin kofa suka Hadu da Mahmud din ya nufo kofar da sauri Dan Yana bedroom dinsa yaji shigowarsu tun bayan anyi la'asar Baba malam yace Alhajin yace ya same shi a can gidansa da yamma za'a kawo Masa iyalinsa.
Matsawa Mahmud din yayi daga bakin kofar Yana yiwa Abban sannu da zuwa sannan ya mikawa Abdul Hakeem hannu suka gaisa, kan kujera Abban ya zaunar da Zahra sannan ya umarci Mahmud daya zauna kusa da ita shi Kuma ya zauna a kujerar dake kallonsu, Abdul Hakeem Shima ya zauna, sai falon ya dauki shiru, gyaran murya Abban yayi kafin yace "Abdul Hakeem yi Mana addu'a' bayan yayi doguwar addu'a sun shafa Abban yace "To Mahmud ga matarka nan na kawo maka bani na baka ita ba Allah ne ya baka ni nawa idawa ce, gata Nan amanace a gurinka kada ka zalunce ta duk inda yanayin rayuwa ya kaiku na baka ita ne saboda na yaba da nagartarka na Dade Ina monitoring dinka ban tabaji ko ganin abun ashsha ba a tare da kai, kullum addu'ata Allah ya bani ikon sauke nauyin marainiyar Allah dake hannuna, kuma Alhamdulillahi na sauke gata nan marainiya ce Bata da uwa Bata da uba ba wa ba kani ita kenan iyayenta duka suka rasu suka barta, kada ka zalunce ta Dan girman Allah ka tausaya Mata saboda Mai rauni ce, ka zamar Mata uwa uba abokin Shawara kuyi dariya tare kuyi kuka tare ka jibinci lamarinta gwargwadon iyawarka. Ina Kuma Kara gode maka bisa share min hawayena da kayi baka watsamin kasa a ido ba lokacin Dana baka aurenta, na gode kwarai Allah ya saka maka da Alkhairi ya yaye maka damuwarka ya kawo maka mafita a bisa lamuranka".
Suka amsa da "Amin"
Sannan yaci gaba da fadin "ke Kuma Uwata ga mijinki nan kiyi Masa biyayya abisa abinda Bai sabawa Allah ba, ki girmamawa shi ki kiyaye bacin ransa ki kiyayie mutuncinsa da rike Masa sirrinsa kindaraja mas iyayensa da 'yan uwansa lokacin da Allah ya hukunta ku hadu dasu,nkiji tsoron Allah a cikin zamanta kewarku ki saka hannu ki Barbi duk abinda ya biyo bayan aurenki dashi Mai Dadi ko sabanin hakan. Dan Allah ki kwantar da hankalinki kiyi hakuri da abinda Allah ya hukunta a kanki komai Kika gani rubutacce ne daga Allah sai dai mu 'yan adam mu karasa shi, Amma tun ran gini tun ran Zane dama haka kaddarar take, ko shi mijin naki idan yayi nazari zega wata kila wannan kaddarar auren ce ta rabo shi da asalin inda yake, to Dan haka kowa ya rike tasa kaddarar wata Rana sai labari komai na duniya Yana da iyaka ikon Allah ne kawai bashi da karshe, Allah yayi muku Albarka ya kauda fitina a tsakaninku ya tabbatar da Alkhairi a cikin rayuwar aurenku, Mahmud sai anyi hakuri da Mata su masu rauni ne kwarai da gaske".
Tunda Abba ya Fara magana yaji kamar ya dauko wani gaigimemen dutse ya Dora Masa aka.
Cikin ladabin da baisan Yana dashi ba ya furta "in Sha Allah Abba ba wata damuwa Kuma amana na karba na rike Allah ya bani ikon saukewa nike da godiya Allah ya saka da Alkhairi ya Kara Nissan kwanaki masu Albarka"
"To Masha Allah, Abdul kayi Mana addu'a mu tafi kada almuru tayi Mana a nan, Uwata ki daina kukan Nan haka bana sonsa kiyi hakuri kowa da haka ya girma Allah yayi Miki Albarka, ga makullin motarki wadda mukazo da ita takice na sai miki, kudin dayar ta wajen Abbie suna gurin Alhaji muttaka tunda aka sayar da ita nace ya juya Miki kudin zuwa lokacin da za'a bukaci wata motar Dan haka in Sha Allah cikin sati Mai zuwa za'a kawo Miki dayar ma".
Suka tashi suka fita Mahmud yayi musu rakiya har gurin mota Saida suka tafi sannan ya dawo ciki, a inda ya bar zahrar anan ya sameta ta kwantar da kanta a kan cinyoyinta tana kuka Mai tsuma zuciya a hankali ya zauna kusa da ita yasa hannu ya dago kanta daga jikin cinyoyinta idanunta a rufe sai tsiyayara da ruwan hawaye suke. Ba zato ba tsammani kawai taji ya sakata a girjinsa ya kwantar da kanta ya saka hankici Yana share Mata hawaye, daya hannun Kuma Yana tapping din bayanta kamar yanda ake yiwa yaro idan ana so yayi shiru Yana kuka, jikinta gaba daya ya dauki rawa ta taso da niyyar zare jikinta Dan wani Abu takeji duk ilahirin jikinta Amma Dan bawan Allan nan yayi kememe yaki sakinta ba arziki ta hadiye kukanta, sai sauke ajiyar zuciya kawai ba kakkautawa saida ya tabbatar ta Samu dan nutsuwa sannan ya saketa Yana fadin " sorry Baby ki daina kuka bana son kuka Sam koda kuwa na karamin yaro ne".
Hannunta ya Kama ya mikar da ita ya nufi daya daga cikin bedrooms dinta guda biyu da suke mallakinta, Saida ya zaunar da ita a gefen makeken gadon sannan ya juya ya nufi kofa Yana fadin " it's time for prayer"
Ya fice Yana ja mata kofa.

Sai ta dauki kusan minti biyar kafin ta Samu kuzarin warware Laffayar dake nannade a jikinta, doguwar rigar material ce a jikinta anyi Mata dinkin fitted gown tayi Mata kyau sosai kofar data gani ta nufa tasan toilet ne, lokacin data shiga abin ya girgizata irin kayan amfanin data gani a ciki ita ba bakuwar abin bace tasan ba kananan kudin aka narkar ba a cikinsa, abin ya Bata mamaki sosai sai dai wa zata tambaya? ta Jima a ciki kafin ta dauro alwala ta dawo dakin.
Ido ta ringa wurgawa ko zata ga sallaya tunda ita dai bakuwa ce a dakin can gefen sofa taga wani stool kamar coffee table da sallayun akai ta shimfida ta Fara sallah.
Tana cikin sallah ne taji kamar karar door bell kamar sau biyu, Saida ta idar ta tashi ta fito har lokacin tana share hawaye jefi- jefi, gurin kofar ta karasa ta bude Sajida da Hameeda da Mujiba ta gani ai batasa lokacin data fada jikin Sajida ba tana dakin kuka Mai tsuma zuciya.
Ciki suka shigo Sajida na fadin "haba bestie wallahi Dana San har yanzu baki daina kukan Nan ba da bazamu biyo bayanki ba, haba Ashe bazaki karbi kaddara yanda tazo Miki ba? ki Kuma godewa Allah a kowane Hali Kika Samu kanki, bake Kika halicci kanki ba ballantana ki tsarawa kanki yanda Zaki rayu, kin taho kina kuka duk kin dagawa Ammah hankali itama, kin kyau kenan? haba kiyi hakuri Dan Allah ki share hawayenki wallahi nasan yanzu zuciyar masu binki da mugun nufi tana can kamar zata fashe Dan ba haka suka soba duk da bansa daga Ina matsalarki take ba, ai kodan makiya kin kwantar da hankalinki ki rungumi mijinki ki ba mara d'a kunya, Amma kin tsaya kina wani Abu kamar wata karamar yarinya"
Tayi tsaki tana kallon zahrar da tayi kozai kozai ido ya kode Mata abinka da farin mutum.
Suma su Hameedar ban baki suka dunga yi Mata, da kyar ta hadiye kukan ta kallesu tana fadin "wallahi bazaku Gane bane ni kadai nasan me nakeji, komai ya kwance min Sam duniyar bata mun dadi".
"Hakurin dai zakiyi ki Kuma yawaita addu'a in sha Allah komai ze wuce kamar ba'ayi ba, muda muke son next year by now mu dawo suna".
Sajida ta fada tana murmushi.
Wani kallo zahrar tayi Mata ta juya kanta gefe tana fadar "Allah ya kiyaye min wata haihuwa can".
Mujiba ce ta kwashe da dariya tana fadar "A'a Banda cika Baki dai 'yan Mata Nan da labari yasha banban zamu tsinceki kina faman 'yan amaye amaye, lokacin ne Zaki gane Baki da wayo ko ba wata haihuwa can ba?".
Zumburo Baki tayi tana fadin "sai kiyi Kuma haka kawai Zaki jaza min, wani ciki ko dadin fada ma Babu".
Saima zahrar ta zame ta kwanta, tana jinsu suna ta faman zolayar ta har aka Kira sallar insha'i a Nan sukayi sallah kafin su shiga Kara gyara Mata Fallon da Kara masa freshner da turaren wuta Hameeda ta Kara karfin A C a falon ta gyara cutains din, bedroom din data fito suka shiga Mujiba bakinta ya kasa shiru tunda dai suka Samu zahrar ta daina 'yan koke koken sai ta balle da santin gidan Dan bayan sun idar da sallar ba inda Bata shiga ba ta leka can ta shiga can bedroom din Mahmud ne kawai Bata shiga ba tunda a rufe yake, fada take "wallahi zahra ki Kara godewa Allah, irin wannan haduwa haka wallahi ko makiyi Saida yaki fada Amma dai duk wani gata kin same shi sai dai fatan zaman lafiya kawai".
Ita dai Zahra ba baka sai kunne.Dan ita kadai tasan abinda ke Kai komo a zuciyar ta, su inda suka dosa daban ita inda ta dosa daban, ko tayi musu bayani ba ganewa zasuyi ba, domin su duka ba wadda ta tab'a shiga irin gararin data shiga, rayuwa Rumi rumi saika Gama sakankancewa da mutum Rana tsaka Abu ya lalace, uwa uba ganin da tayiwa Musbahu ba karamin famu yayi Mata ba, saboda da ta cire shi daga ranta kwata kwata ta hakura, Amma tana ganinsa komai ya rikice Mata da tana zargin kamar da niyya mamansa tayi haka saboda ya taba fada mata Maman nasa taso ya auri 'yar Yayarta shi Kuma ya ringa sharewa ana haka ne Allah ya had'a shi da zahrar abinda ya kawo karshen wancan dambarwar kenan. Amman tasowar mamansa da 'yan uwanta dashi kanshi takanas ta kano har Azaren don bada hakuri da neman gyara idan lamarin Mai gyaruwa ne, sosai abin ya tashi hankalinta, wata sabuwar soyayyar sa ce ta sake bijiro Mata idan tana tuna yanda yaci buri a irin wannan ranar da za'a kawo Masa ita a matsayin matarsa ta sunna halalinsa, irin abinda yake fadin ya tanadar Mata ita a wancen lokacin idan Yana fada kamar zata nitse kasa dan kunya Amma shi ko a jikinsa.
Wasu sabbin hawayene suka zubo Mata masu zafi tana ayyana shike nan komai ta Zama tarihi, ga inda kaddara ta kawo ta gurin da ba'asan darajarta ba ko alama sai aukin taba Mata jiki da yake Wanda ta fashimci hakan tun haduwarsu ta farko, ba kunya ya wani saka hannu ya rungumota Wama ya sani ko Dan duniya ne aka hadata dashi, tunda ance ba Wanda yasan asalin sa kuma tasan yanda yake din nan ko bashi da sisi mata zasu ringa kawo Masa rida tunda sun ganshi smart dashi.
Wani tsaki tayi tana ayyana to Ina ruwanki da wani smartness dinsa.
Mahmud Bai dawo gidan ba sai bayan sallar insha'i ganin takalma yasan akwai baki cikin gidan baya raba daya biyu 'yan uwanta ne ko kawaye, dakinsa ya wuce yayi wanka ya canza kaya ya fito falo, bai shiga dakinta ba daga inda yake yana jiyo mganganun bak'in, ita dai baiji tata maganarta ba Sam Zama yayi yana daddana wayar hannunsa.
Acan Kuma dakin Zahra Ya Abdul Hakeem ne ya Kira wayar Sajida Yana fada Mata su fito su tafi ya dawo daman lokacin daya basu kenan bayan sallar insha'i lokacin daya kawo su.
Sun fito falone suna zolayar Zahra Basu kula da mutum ba sai da suka sauko daga steps din da ze sada ka da corridor din bedrooms din suka ganshi a zaune Yana ta faman Danna waya, kallo daya Zahra tayi Masa ta kauda Kai haka kawai taji gabanta ya fadi, ta rasa wace irin masiface wannan.
Kansa ya dago yana amsa gaisuwar su Sajidar Yana fadin "har zaku koma ne?".
Hameeda ce tayi farat tace "To ba dole mu tafi ba yallabai tunda angon yaki zuwa ya sayi bakin amaryarsa ba Yana ganin Mai araha ce bai Sha wahalar komai ba aka bashi ita".
Ba Zahra da aka ciwa fuska a fakaice ba hatta Sajida da Mujiba Saida sukaji kamar kasa ta nutsa dasu a gurin Dan kunya, gaba daya suka zubawa Hameeda ido har shi uban gayyar, wani abune Wanda Zahra Bata taba tunanin Hameeda zatayi Mata ba, dan wannan cin fuska ne qarara bako kawaici a cikin maganar ko kad'an. Zahra kasa gaba ko baya tayi ta tsaya a gurin kawai, su sajida ma rasa ta cewa sukayi shi kuwa uban gayyar wayar dake hannunsa ya aje Yana kallon Hameeda direct kafin yace " waya fada Miki Mai araha ce bakiji sunanta ba? Zahra fa kinsa ma'anar sunan kuwa? tauraruwa fa a cikin taurari a gurinki take Mai araha Amma ni a gurina tafi zinari daraja, bari na baku indai abin sayen Baki ne in dai shi ne abinda ke shaida Kima da darajar mace a irin wannan ranar gurin kawayenta, ina zuwa". Ya fada Yana mikiwa ya nufi hanyar bedrooms dinsu, tunda ya wuce zahra ta juya da sauri ta nufi daki Bata yi musu ko sallama ba.

Bai jima da shiga ba ya fito da wata katuwar leda da Kuma envelope guda uku a hannunsa. Yana zuwa directly Hameeda ya nufa ya Mika Mata ledar da envelope daya sannan ya baiwa Sajida da Mujiba Suma dai dai Yana fadar "ga kayan sayen bakin Nan a cikin wannan envelope din Kuma kunsha ruwa a hanya".
Ba kunya Hameeda tace yanzu naji magana ai shi tuwon girma miyarsa Nama mun gode".
Taja katuwar ledar tayi gaba abinta mujiba ma tabi bayanta har suka fita Sajida Bata motsa ba ita kollon ikon Allah take akan Mahmud Wai wannan shine Almajirin da ake ta yayatawa a aurawa Zahra har Hajiya Mama na yiwa Abba magiyar kada ya Fara wanna danyan aikin tab wallahi da sake ita tafa abinda ta gani ga tare dashi ai da hasashe ne take yanzu be taga zahiri. Ganin sun fita yasa sajidar aje Masa envelope dinsa a gefen shi tana fadin "kabar abinka na gode, ni fatana ka rike min bestie da mutunci da amana yafi ka bani duk abinda ka mallaka, bansan Kai ko waye ba Amma jikina Yana bani kana boye wani Abu tun lokacin Danazo gidan nan da Kuma irin kayan danaga an kawowa bestie nasan Kai ba kaskantanccen mutum bane, Ina hadaka da girman Allah kada ka bautulcewa Iyayenta da suka baka ita kaji tausayinta marainiya ce, Dan Allah nasan duk inda ka fito ba karamin guri bane ka Zama garkuwarta ka zamar Mata bangon da zata jingina taji dadi duk rintsi. Dan Allah ka Bata kulawa Zahra 'yar gata ce kaddara ce ta zaunar da ita a kasar nan da Kuma kawaicin kakanninta suka hakura suka barwa Ammah ita, Dan Allah ga amana Nima na baka kamar yanda iyayenta suka baka kaji tsoron Allah a cikin zamantakewar ka da ita na San Nan gaba zaka samu zabinka ko Kuma tuntuni kana dashi Dan Allah kada ka wulakanta ta.. na rokeka ka Zama adalin shugaba a gurinta idan kaji yanda rayuwa ta dunga jujjuyata zaka tausaya Mata matuka, Dan Allah badan niba...."
Da tayi gaba ta nufi kofa Bata taji me ze fada ba domin hawayene suka ciko Mata idonta idan tace zataci gaba da magana kuka zata fasa masa ne. A bakin kofa sukayi kicibus da Mujiba wadda ta dawo kiranta ganin shirun ya yi yawa.

✨✨
✨✨
AUREN HUCE HAUSHI

✨✨
✨✨

💎PAGE EIGHTEEN💎

STORY

AND

WRITTEN

BY

MAMAN FATIMAH.

_________ Bayan wucewar Sajida Mahmud ya Dade Bai tashi ba, kwarai yarinyar ta burge shi matuka, da gaske take son Zahra domin furucin da yarinyar can tayi yayi touching dinta sosai, lallai ya tabbatar son da take yiwa Zahra bana Wasa bane shi tun lokacin da Magaji ya fada masa ta baro syprus Dan kawai ta halarci bikin zahrar ya jinjina Mata duk da suna hutu Amma yasan irin wadannan daliban ba kowane hutu suke zuwa gida ba sai dai idan iyayen sun sunci sun tada Kai.
Envelope din data aje masa ya kalla yayi wani killer smile ya zurata a aljihun Wando Yana Kara wani murmushin Wanda shi kadai ya barwa kansa sani.
Yaso ya shiga dakinta sai ya share kawai Dan yasa baya raba daya biyu kuka take Dan da gaske koshi baiji dadin furucin da akayi Mata ba Kai tsaye bako rusunawa a ciki.
Lokacin da Abdul Hakeem ya Parker motar a parking lot na gidan Sajida ce ta farkon ficewa daga motar zuciyar ta na Mata wani zafi Dan da gaske idan ta tsaya zata shatawa Hameeda rashin mutunci ne na karshe Wanda zata Dade Bata manta ba, dan da gaske an shirya ne kawai dan a tozarta Zahra a gabanta mijinta, shi yasa kenan lokacin da zasu ltafi ta shiga part din Mama Kiran Hameedar akan ta fito suje, taji Salma na fadin saura Kuma ki kasa fada ki dawo Mama ta tumurmushi banza, ita Sam Bata kawo komai ba kawai dai ta dauka wani abune can tsakaninsu saida hakan ta faru ta Gane me ake nufi da waceccen maganar. Tana jin Mujiba na kwala mata Kira lokacin data nufi karamin gate wanda ze sada ta da cikin gidan, batabi ta Kanta ba tayi wucewarta ciki ta kyalesu.
Koda ta shigo part din Ammah directly bedroom din da suka kwana ta wuce tana yiwa su Aunty Hasana sannu har ta shiga ta fito tana fadin "Aunty Dan Allah idan su Hameeda sun shigo kice su raba kayan su biyu kwai Banda ni". Ta koma da sauri Dan tana jiyo maganar su a kusa alamar Nan suka nufo.

Tun shigar Zahra bedroom din Nan ta kwanta rub da ciki take risgar kuka Kamar ba gobe, Hameeda ta Bata mamaki Bata taba zaton irin wannan ranar ba a tsaknainta da Hameeda cewa take ko kowa ya nuna Mata naqi a bangaren Mama ita kadai zata tsaya a bayanta duk runtsi duk wuya saboda a baya ba Mai cin fuskar ta a dakin Mama makukar tana gurin Koda kuwa mamar ce, Amma yau Hameeda da bakinta Kuma a gaban idonta take fadar magana irin wannan, to meya canzata daga Hameedar data sani Mai sonta da kaunar ta da Bata kariya da kulawa a kowane janibi. Saida tayi Mai isarta har ta baiwa uku lada, sannan ta hakurkurta da Kanta ta tashi zaune. Kanta taji ya Sara Mata a hankali ta furta "Alhamdulillahi ala kulli halin. Allah na gode Maka duk abinda kayi nufi a gareni na karba ka bani ikon cinye jarabawar Nan dan isar Annabi Muhammad s.a.w.w".
Hannu tasa ta dafe Kanta dake matukar Sara Mata, wannan wace irin rana ce a gareta? ranar da duk wasu masoya keda tarin burika a Kanta Amma ita ranar ta ta farko ta kasance ranar cin fuska daga inda Bata taba zato ba, ba tarairaya duk burin da suka dade sunaci na irin wanna ranar ya tashi a banza. "Astagafirullah Ubangiji ka yafe min zunubina daya janyo min irin wannan rayuwar Mai tarin qalubale a cikinta".
Ajiyar zuciya ta sauke tana Kara dafe Kanta da gaske jinsa take Kamar ze rabe gida biyu, ba zato ba tsammani taji an bude kofa Bata daga Kai taga ko waye ba dan kamshinsa kadai ya Isa ya fada Mata Mai shigowar, Kuma ma waye ze shigo haka Kai tsaye a irin wannan lokacin, sallama yayi Mata Amma Allah baisa ta amsa Masa a fill ba ta dai amsa a zuciyar ta.

Takowa yayi a hankali har zuwa inda take zaune, har lokacin Kuma Bata daga Kai ta dube shi ba farar ledar dake hannunsa ya aje kusa da ita ba tare daya tanka Mata ba ya juya ya nufi kofa yana juya baya ta dago da sauri ta kalli bayansa kananan Kaya ne a jikinsa sabanin dazu da yake sanye da wani lallausan yadi fari tas da hula, sai taga Kamar yafi kyau yanzu akan dazun, kananun kayan sunfi karbarsa akan manyan da yake sakawa, hannun daya saka ya Kama handle din kofar idonta ya Kai taga hannun wani fresh dashi Kamar Mai rayuwa a kasashen sanyi. Ganin Kamar ze juyo ne yasa tayi saurin kauda Kanta Dan kada ya kamata da wadannan idanun nasa tana kallonsa. Kofar tabi da kallo bayan ya fice a hankali ta sauke ajiyar zuciya da gaske fa mutumin Nan yana Mata wani irin kwarjini, ga wani tsare gida naba gaira ba dalili da yake saiya karta Abu ya wani maze Yana Shan kamshi.
Karan bude kofar ne ya dawo da ita daga tunanin data shiga na wucin gadi, kusa da ita ya zauna daf da daf dan ji tayi Kamar numfashi daya suke sharing dashi, a hanakli yasa hannu ya dago fuskarta data Kama idon ta rufe, a zuciyar ta tace "na bani ni Fatima shi Kuma kome faskar Nan tawa tayi Masa? shi dai ya taba jikina kawai ya sani, muryar shi ta jiyo cikin deep voice yana fadin "Pls open your eyes and look at me mana".
Kai ta shiga girgiza Masa alamar a'a.
Shi abin nata ma mamaki yake bashi, a ranar da suka samu wannan arangamar da ita soron gidan Baba malam yaga ta rufe idanu ya dauka ko tsabar razanar zata fadi ne. Amman sai yaga abin na neman ya Zamar Mata jiki indai zata ganshi to kuwa sai ta rutse idanu Kamar taga wani abun tsoro, a haka zasu rayu da ita ai baze yuwu ba gaskiya dole yayi wani abun daze cire koma meye yake haddasa Mata hakan a tare dashi.
"Ok Ashe zamu kwana a haka kenan tunda bazaki bude idanun ba, ko Kuma wallahi na shayar dake mamaki yazun nan".
Shiru tayi Masa kirjinta Yana fat, fat da sauri kusancin yayi yawa duk ya kanainaye ta.
Batayi zato ko tsammani ba taji harshensa akan fata idonta Yana lasa yana busa mata iskar bakinsa kamshin Lister mint mouthwash Yana dukan fuskarta ciki Shirin fita hayyaci tayi baya da sauri ta fada kan gadon da baya idanun nata tar akan fuskarsa da yana mata wani Yana Mata wani kallon kasa - kasa nan da Nan taji tsikar jikinta tana tashi sai hawaye zurrr...
"Why! meyasa? Ai da sai ki barni na kwashe abinda yake hanawa kina kallon nawa Mana, oya tashi abinci zakici bazaki kwanta da yunwa ba kisa na Fara karya Alkawarin dana daukar Iyayena na kula dake,dan kowa amanarki yake bani da jaddadda min na rikeki da amana da gaskiya cikinsu harda bestien mu kuwa".
Ya fada a kasalance Yana kashe Mata ido.
Sai Kuma ya dan zamo kadan ya dauko plate Wanda ita Sam Bata San lokacin daya ajesu a gefenta ba, ledar ya bude wani kamshi ne ya doki hancinta Mai shegen Dadi kaza ce wani irin gashi akayi Mata Kamar na tsire da vegetables a ciki ya juye Yana fadin.
"Oya tashi kici kafin ki kwanta kinsan yunwar dare tana kawo ciwon ulcer,kada ta kamaki ace Ina barinki da yunwa ni d'an malam gara na Kara kiwataki duk wanda ya ganki ace Masha Allah! Kamar ba matar Almajirin Baba malam ba".
Ya fada da alamar zolaya a karshen maganar tasa. Itafa Yana Bata mamaki wallahi zata iya rantsewa idan aka saka Masa hannu a Baki baze ciza ba amma dubi yanda ya wani zage yana magana Kamar bashi ba.
Ganin da gaske zata Bata Masa lokacin shi Kuma Yana da abinyi da yawa yasa ya matsa sosai kusa da ita ganin Yana nema Kara mannata a jikinsa yasa tayi saurin tashi zauna tana kikkibta idanu tana kallonsa. Da hannu ya nuna Mata plate din, cikin Rashi kuzari a maganar tata tace Masa "na koshi bazan iyaci ba kaina ciwo yake".
Ta fada murya a shagwabe ga daman tasha kukanta.
Sai yaji ta Kara bashi tausayi abun ne yayi Mata goma da ashirin.
Cikin sigar lallashi yace.
"To kici ko kadan ne saina kawo Miki magani kisha kinji"
Ya fada yana Kara nuna Mata plate din da idonsa, kadan taci duk a takure shi har mamaki take bashi a yanda yake ganinta ai ta wuce ace tana jin irin wannan kunyar ko tsoron irin haka, tunda da gani wayayya ce ta ajin karshe, ga Kuma yanda ta ringa ta'ammali da samari kala kala, a yanda yaji labari fa sau uku ana fasa aurenta Wanda ba Wanda yasan dalilin hakan, yasan kawai rainin hankaline irin na Mata, yanda zamanin ya Zama abinda ya Zama Amma dai ai gaskiya zatayi halinta komai daren dadewa.
Ba laifi ta danci tace masa ta koshi tana kokarin fitar da kwalla. A zuciya yayi yana jinjina saurin kukanta Kamar wata 'yar goye Sam yaga kuka ba wani wahala yake Mata ba, tana kuka tun abun kukan Bai Samu ba to idan ya samu yaya za'ayi kenan?.
Kwashe kayan yayi ya fita dasu Bai jima ba ya dawo da p.c.m tablet a hannunsa da ruwa marar sanyi, farm fresh yogurt ya Fara zuba Mata ta karba Tasha sosai dan tana sonta sosai lokacin tana Jos har kamfanin take zuwa ta sawo musu, tayi Mata Dadi sosai sanyin moderate ba Mai cutarwa ba.
Saida ya tabbatar da tadan samu relief kafin yace Mata.
"Ki tashi ki canza kayan jikinki ki kwanta idan kikayi barci kan ze daina ciwon, in Sha Allah, Kuma na fada Miki tun kina Asibiti ki rage damuwa Bata maganin komai sai Karin matsala Amma idan Kika hakura komai Mai wucewa ne Zaki sameni fiye da yadda Kika tsammmata kiyi hakuri komai da Kika gani hukuncin Allah ne ba Wanda ya Isa ya canza idan Ina tunani akan kaina na duba yanda connection din ya faru nasa ba Wanda ya Isa ya tsara haka sai Allah Dan haka ki Barbi abinda ya Baki Koda bakya so kinda ance wani hanin ga Allah baiwa ne tunda gashi ya Baki Dan malami sukutum ai tsakaninki da Allah sai godiya". Ya fada Yana kafeta da idanunsa masu sakata ladabin dole.
Kai kawai ta gyada Masa, ba baka sai kunne, mikewa yayi da cup da robar farm fresh din a hannunsa ya nufi kofa a hankali ya juya very lockly suka hada ido kashe Mata ido daya yayi Yana Dan murmushi Wanda Batasan Kona menene ba, sannan yace Mata "good night".
Yaja kofar wasu sabbin hawayene taji Kuma ita harga Allah bada niyya ba jinsu kawai tayi hakika tana tausayin kanta, da gaskiyar masu iya magana da suke cewa cusa Kai ba kwarjini yawa ne yau ta gani ganin idonta Wai ita Amarya ce wadda zayati kwanan farko a gidan miji.
"Ya illahiy!!! Wannan wace irin ranace haka? Yanzu da Musba.... Astagafirullah".
Ta fada da sauri tasan tunanin wani irin haka haramun ne da aure a kanta.
Ta jima a gurin tana sakawa da kwancewa Amma dai duk inda ta juya amsar daya ce aikin Gama ya riga ya gama sai hakuri da zubawa ikon Allah ido Dan shine alimil gaibi.

Tunda Mahmud ya shiga nasa bedroom din ya kasa samun nutsuwa Banda yayi namijin kokari ya kauda kansa da lallai sai ya rage zafi gaskiya idan yayi haka baimata adalci ba. Dan shi a nasa bangaren kamai ya gama zamar Masa daidai, saidai ita uwar gayyar batasan wainar da yake toyawa ba dan idan da abinda shi Kuma Bai lamunta ba yayi Mata dole yafison komai Daren dadewa taso shi da muradin kanta yafi son ya koyar da ita yanda zata soshi fiye da kowane da namiji data taba so a rayuwarta, ba Kuma ya son tasan koshi waye bama ita ba kowa ma dake tare dashi a nan, yafi son ya Gina kanshi a gurinta a wannan matsayin na yanzu.
Wanka yayi ya saka pyjamas dinsa farare sol nasu laushi, yana jinsa cikin watan irin nutsuwa, maimakon ya kwanta sai ya dauko laptop dinsa ya dosa aiki sai gurin biyu da kwata ya ture computer din ya tashi ya nufi kofa ya fita dakinta ya nufa dakin zahrar yana zuwa yana turawa yaji kofar a bude Kuma dakin da haske yayi zaton ko barci ne ya dauketa tabar wutar Mai haske a kunne. Yana turawa ya ganta akan sallaya tayi sujuda Amma shashhshekar kuka take Allah kadai yasan abinda take roko tsakaninta da mahalicci ya jima a tsaye kafin yaja Mata kofar ya fita jikinsa a matukar sanyaye dan ba karamin qima ta kara a idonsa ba ya Kuma Kara godewa Allah da yayi Masa kyauta da wannan yarinyar yasan Allah sami'uddu'ai ne yasha raba dare Yana rokon Allah ya bashi mace ma'abociyar addini, sai gashi a inda Bai taba zato ba Dan gaskiya Bai taba kallonta a wata mujahida ba yafi Mata zaton bokon ya rinjayi bangaren islamar ta.
Koda ya koma shima Bai kwanta ba Saida yayi nafilfili sannan ya kwanta da tunani kala-kala a zuciya.
Hudu da minti arba'in ya farka ka'idarsa kenan ta tashi sallar Asuba, wanka yayi ya saka jallabiya milk colour ya bude kofa har ze wuce sai yaga Bai Dace ba gara ta tasheta ta.
Sanda ya tura kofar har ta Fara raka'atanul fajri ta Riga ta tashi, lallai ya jinnina Mata gurin ibada sai yaji ya qara samun wata nutsuwa a tare da ita da sauri yaja Mata kofar ya nufi falon jin za'a tada sallah.l

✨✨
✨✨

🔷AUREN HUCE HAUSHI 🔷

✨✨
✨✨

MAMAN FATIMAH

💎 PAGE NINETEEN 💎 (19)

AssalamuAlaikum warahamatullahita'ala wabarakatuhu.
Ina mika sakon jaje gan Alummar maiduguri bisa ibtila'in daya samesu na karyewar Alo dam, Allah ya jikan wadanda suka rigamu gidan gaskiya Wanda Kuma suke gida da Asibiti Allah ya basu lafiya, abinda aka rasa na dukiya Allah mayar musu da ninkin abinda suka rasa.

_______________Mahmud tunda aka idar da sallah Bai shigo gidan ba sai kusan karfe shida da rabi, ya Dan jima da Mai gadi kafin ya shiga ciki dakin Zahra ya nufa a kwance ya sameta akan sallaya da gani batasan lokacin da barci ya dauketaba yasan kusan kwanan zaune tayi, a hankali ya matsa daf da ita Yana karewa fuskarta kallo idanunta sun dan tasa alamun kukan da tasha da Kuma rashin barci, wayarta ce a gabanta a kunne tsugunawa yayi ya dauka Qur'an ya gani tana karantawa barcin yayi gaba da ita, baiyi tunanin tashin taba kada ya katse Mata barcinta.

Kan stool na madubi ya zauna da wayar a hannunsa Yana dubawa haka nan yaji Yana son ya shiga ya duba received calls da missed calls nata, a hankali ya ringa bi Yana dubawa yawanci kawayenta ne sai Kuma Ummee da ya gani har ze aje sai yaga Kamar number din guyn da zata aura Dan lokacin daya tafi da wayarta ya canza mata wayar da sim card din a Nan ya haddace number din tasa sai Kuma yanzu daya ga Kiran jiya dai dai lokacin suka bar gurin Baba malam, Nan da Nan yaji ransa ya sosu duk da Kiran daga gurinsa ne ba daga gareta ba.
Tashi yayi tsam yabar dakin da wayar a hannunsa shima kwanciyar yayi, can cikin barci yaji alamun ana Danna door bell da kyar ya tashi ya nufi kofa, Musaddiq ne da Faruq din Aunty Hasana suke kawo break fast cikin ladabi suka gaishe dashi ya amsa yana Basu hanya suka shigo da basket din dake hannun Musaddiq ya Dora akan dining table.
Musaddiq ne ya juya ya nufi kofa yayin da Faruq yayi tsaye, har Musaddiq yakai kofar fita daga falon ya juyo Yana fadin "Faruq me kake jira ne ka tsaya? kasan driver Yana jiranmu fa"..
"Taya zamu tafi bamu gaishe da Aunty Zahra ba?".
Mahmud ne yace "Faruq Auntyn barci take sai dai zuwa anjima sai ku dawo kaji".

***
Cikin damuwa da matsanancin tashin hankali Mama ta tashi, tunda garin Allah ya waye ta tasa kayan da Hameeda ta shigo dasu jiya a leda da envelope din kudin da mijin Zahra ya Basu a gaba ko bakasan kayan kwalliyar Mata ba kaga wadan Nan kasan ba Karabiti bane ga uwa uba kudin daya lafta musu ita abin har ya Fara Bata tsoro, dan a zahiri kowa yasan fakiri ne wanda Bai ajeba bai bada ajiya ba amma a badini abubuwan da yakeyi suna da ban mamaki.
Wayar ta ta dauko tayi dealing din wata number ba'a Dade ba aka daga Bata koyi sallama ba ta Fara magana "Asabe kome kike kizo anjima da matsala babba komai Yana neman ya dagule fa kizo kiga abinda wancan tsintacciyar magen ya baiwa su Hameeda jiya harda fadin magana dan Hameeda ta fadin maganganun danace ta fada wallahi Ina kokonto akan lamarin yaron nan Dan jiya da dare Dana Kira malam na BANDE cewa yayi Wai mun kuskure wani abu shi yasa har Alhajin ya iya daura mata auren Kuma yayi duk iya yinsa ya kasa ganin komai akan mijin nata sai wani haske kawai yake gani".
Daga can taji magansr mamar ta amsa da "hakane ba damuwa sai kinzo din ta aje wayar tana jan karamin tsaki ta tashi ta shiga toilet.

A bangaren Ammah kuwa bayan Sajida da zulai sun Gama aikin break fast din da aka Kai gidan zahra, sajidar wanka tayi ta Shirya kafin ta fito falo su karya, bayan sun Gama ne ta kalli Ammah tana fadin "Ammah in Sha Allah yau an tafi gida Ina son na wuce school ne daman na jira ne saina raka Zahra gidanta tun last week muka Fara lactures".
Ta fada a ladabce.

"To Babu laifi hakan Allah yayi Albarka, sai Magaji ko Malam Bala wani ya Kai ki mun gode madallah, kunyi sallama da mutuniyar tun jiya kenan!" Ta tambaye ta.
Kai ta girgaiza tana fadar "A'a sai anjima zan shiga muyi sallamar".
___

Zahra Bata tashi ba sai wurin takwas da rabi tayi Mika gami da salati tana Kara ware idanu tana kallon dakin da alama kamar ma ta manta inda take Sai a hankali ta dawo cikin nutsuwarta "ya Salam".
Ta furta hankali tana ware sexy eyes dinta, wallahi Sam ta Manta da waifa a dakin gidan aurenta take ba a dakin Ammah ba, tashi tayi zaune kan sallayar tana Kara kallon Kanta har lokacin hijabin da tayi sallar ne a jikinta.
Toilet ta shiga duk jikinta ya Mata wani irin nauyi Sam Bata jin dadin jikin nata ruwa Mai dumi ta hada ta shige ciki tayi kwance tana shakar kamshin turen wanka data zuba ta jima sosai a cikin ruwan kafin tayi wanka ta fito sabon towel ta dauko mai kalar purple Babba ta daura ta fito gurin mirror taje lotion ta dauko ta shafa a jikinta, tashi tayi ta nufi gurin wata jaka kayan gyarab gashinta ta dauko, zuwa tayi ta zubesu yanzu da a gida ne da Ammah ce zata gyara Mata tsab ta hade shi guri daya, tana kiciniyar daureshi taji alamun bude kofa da sauri ta kalli gurin, Mahmud ne cikin shigar kananan Kaya yayi wani irin fitinannan kyau, hannunsa ya nade a kirji ya jingina da kofar ya zuba Mata idon dake figitata, shi be shigo ba shi be koma ba ya kafeta da idanunsa.
Tunda suka hada ido dashi tayi saurin sunkuyar da Kanta jikinta na wata irin rawa duk ji tayi ta rasa yanda zatayi daga ita sai towel din Nan a jikinta, gashin ta saki ya bazu har gadon bayanta ta matse hannunta a kijinta, sun Kai kamar minti uku a haka Yana Kare Mata kallo son ransa a cikin zuciyar sa Yana tsarkake sunayen Allah da yayi Masa kyautar bazata da wannan kyakykyawar halittar dake gabansa a matsayin matarsa ta sunna halaliyarsa wadda ba wani shamaki a tsakanin su.
Cikin takunsa Mai Cike da karsashi Amma a nutse, ya doso inda take tsaye Yana zuwa ba zato ba tsammani taji ya saka hannu Yana tattaro gashin daya bazu a kafadarta yana fadar "Bari na gyara Miki tunda Naga yana neman gagararki".
Bata iya ce Masa komai sai jikinta daya cigaba da tsuma, tsab ya hade ya saka ribom din daya gani a kusa mayukan gashin brush comb ya saka ya Kara gyara shi sannan yayi baya a hankali ya zauna akan sofa Yana fadar "ki shirya kizo muje ki bamu break fast gashi can Ammah ta aiko tun wurin 7:30 su Musaddiq suka kawo".
Bata amsa ba Kuma ta dago kalle shi ba, d'an gunguni ta fara kasa kasa "kawai ka zauna mun a daki kana kalleni kaki fita a gabanka kake son na saka kayan ko me?".
Yana kallonta gefen ido tana magana a ciki baya raba daya biyu yasan complain take akan zamansa. Tashi yayi Yana fadin "idan kin Gama kiyi min magana Ina aiki ne".
Ya juya ya fice.
Wata ajiyar zuciya ta sauke tana fadar "innalillahi ni Fatima Naga ta kaina Wai shi wannan waye shi? Nifa wallahi lamarinsa sun fara bani tsoro gaskiya" ta fada tana cuno Baki, sai Kuma tayi sauri har towel din jikinta na neman faduwa key ta sawa kofar, a gurguje ta saka doguwar rigar lace peach colour Mai touching din flowers green Bata daura Dan kwalin kayan ba saita rufa gyale green,Sam batayi wani make up ba powder kawai ta shafa sai lips glow turarenta ta fesa ta nufi kofa ta bude ta fice tsaye tayi a cikin corridor din saita rasa a wane bedroom din yake.
Ta jima a tsaye tana saka yanda zata tunkari dakinsa Kai tsaye, cikin yin shahada ta nufi inda take zaton nan ne bedroom din nasa a hankali ta murda handle din ta tura kamar wadda za'a cewa ket ta ruga, wani sanyi da kamshin turensa Dana freshner ya shiga hancinta dakin ba wadataccen haske duk curtains din windows a sake suke can kan sofa ta hango shi da laptop a gefen sa yana ta faman daddanabawa tsaye tayi ita Bata shiga ba ita Bata koma ba, yana kallonta ta gefen ido Amma sai ya basar kamar bai ganta ba.
"Assalamu Alaikum".
Ta fada a darare, Bai kalleta ba Amma ya amsa sallamar.
Dan Jim tayi kafin tayi karfin halin cewa "na gama shiryawar".
Kansa ya dago ya kafeta da idanunsa da yake razanata dasu kafin yace "idan bazaki shigo kije kawai an fada min Ina cinye mutane ne da Kika tsaye a nan".
Dan cuno Baki tayi ta saki handle din ta shigo a nutse Amma fa Babu nutsuwa Kota sisin kwabo a zuciyarta ta ayyana "waya sani ko mayen ne tunda abune a duhu".
A tsakiyar dakin ta zauna an carpet Kanta na kallon tace Masa "barka da Asuba".
Shiru yayi kamar Bai jiba Saida ya Mula dan kansa yace "Lafiya ya kwanan bakunta I hope ba wani damuwa ko?".
Kai ta gyada masa alamar eh.
Yace "good Bari na karasa wani dan aiki muje muyi break ko?"
Ya fada Yana kallonta.
Ganin tayi shiru yasa yaci gaba da aikinsa ita Kuma tana zaune duk sanyin dakinsa ya Mata yawa, tana son sanyi amma sai taji na dakin yana neman ya sakata rawar jiki.
Baifi minti biyar ba ya rufe laptop din ya Miki, gurin da take zaune ya nufo yana zuwa ya Dan tsuguna kusa da ita Yana fadin "taso muje kada nabar 'yar amanata da yunwa na amsa query a gurin su bestie ko?"
Ya fada Yana murmushi.
Hannunta ya kama ya dagota tsaye suna shakar numfashin juna Amma ita kanta yana duban kasa, dayan Hannun yasa ya dago fuskarta as usual yanda ya saba.
Ajiyar zuciya ta sauke a hankali Amma bata rufe idon ba kamar yanda ya hanata a jiya Bata manta ba amma ta kauda Kai gefe dan da gaske Bata iya had a ido dashi.
Dan kwanto da ita yayi jikinsa Yana juyo da fuskarta yana fadin.
"Wallahi kada ki rusa min budget dina kisa na kwashe kunyar nan daga idanunki tun banyi niyya ba matukar zakici gaba da irin wannan dabi'ar".
Das das girjinta ya kara bugawa akan wadda yake, tana fadin "oh ni Zahra tawa ta sameni shi Wai wane iri ne haka? sai yayi ta sakin magana ko kunya babu".
Saida ya matsa mata taci abincin kirki bayan sun Gama ne suka dawo parlor suka zauna Sam Babu sabo ko kalilan a tsakaninsu kallo ya kunna a Nile sat ya kamo super support suna kwallo live.
Ganin ita ba wani gane kan ball din take ba yasa ta Mike zata koma daki ta kira Sajida taji ya maganar tafiyar Dan tun jiya da Abba yace a jiya zata tafi gidanta sajidar tace itama sai gida ta.
Takunta biyu taji ya janyo ta ta fada jikinsa ba Shiri ta zaro ido waje hura kata iskar bakinsa yayi a fuskarta dalilin yasa ta rufe idonta kenan a hankali yace "Ina Zaki ki barni a zaune alhalin saboda na tayaki Zama yasa naki fita ko ina".
✨✨
✨✨

AUREN HUCE HAUSHI

✨✨
✨✨

💎 PAGE TWENTY 💎(20)

_______"ya Salam". Zahra ta fada a hankali jin yanda yake hura mata iskar bakinsa a fuskarta, yasa hannuwansa duka biyun ya tallabo fuskarta yana kallon face din very cute da ita, shifa baya gajiya da kallonta komai nata burgeshi yake yi Dan bakinta ya kalli 'yan kyawawan lips din ta pink, gdy yake yiwa buwayi Gagara misali daya mallaka masa ita a lokacin da bai taba zato ba, tunda ya kafeta da ido Bata yarda sun hada ido ba, ba Kuma tayi gigin dogowa ba.
Qaran da door bell din tayi shiya kawo karshen 'yar tutsiyen da yayi Mata wani soft kiss ya yiwa gefen wuyanta Wanda har Sai da ta zabura tana fadin "wayyo Allah!".
A shagwabe ta janye jikinta daga rikon da yayi mata, shi Kuma ya tashi ya nufi kofa, Bata jira taga waye ba tayi wuf ta nufi ciki jikinta kamar mazari.
Tana shiga ta zube a gado tana fitar da numfashi da sauri da sauri kamar wadda tasha gudu, jin alamun bude kofar yasa tayi saurin duba gurin Sajida ta gani tsaye ta tsura Mata ido tana Mata wani kallo cikin mutukar tsantsar farin ciki zahrar ta taso tana fadin "haba bestie kin wani tsareni da ido kina min kallon qurillah irin wannan ko Kinga wani abu a jikina ne?".
Ta qarasa fada tana karasowa kusa da ita 'yar madaidaiciyar ledar hannunta tana fadar "Wai meye Kika wani yi shiru kina kallona ne Dan Allah talk to me Mana pls".
Biyo bayan zahrar tayi har gefen gadon kafin ta samu kuzarin fadin "Bestie Kinganki kuwa just one day Amma har kin Fara canzawa, Fadi min meye sirrin gaskiya, na tafi jiya da zulumin ki a Raina yau kuma nazo na sameki haka kin wani Kara Zama fresh dake".
"Bestie tsakanin mu harda 'yar zolaya zakice Wai na Kara zama fresh?"
Zama tayi gefen zahrar tana fadin "wallahi I am serious kin canza a idona gaskiya Kinga ai dole na fada ko?".
"To shikenan kin fada bazan hanaki ba, wai da gasken yau Zaki wuce?"
Kai ta gyada Mana kafin tace "In Sha Allah meya rage kuma ai gara naje na fuskanci karatun ko tunda na samu nutsuwa kin shigo gidan ki. Alhamdulillahi, ga sauran abubuwanki na wajen Baffan rimi kici baga da amfani dasu dazuma munyi waya da safe yace na bawa Ammah abinda ya Aiko dai ya Kara jardada Mata na a fada Miki kada wani ya kawo Miki abu kici Kuma yace a tura a karbo Miki sako Nan da sati daya".
Dan langabar da Kai tayi tana Kara ganin kimar Sajida ta dauki matsalar nan tata bada wasa ba.
Godiya sosai Zahra ta yiwa Sajida akan abinda suke mata, sun Dade sajidar na yiwa Zahra nasiha akan ta rike aurenta da kyau ita bataga wani abun ashsha ba gurin Mahmud idan. Nan da Nan idon Zahra ya kawo ruwa ta shiga sharewa da hannunta tana fadar "wallahi bestie na rasa dalilin da yasa nake jin wani abu a tare dashi tun ranar Dana Fara ganin shi naji abun ko kallonsa fa nayi sai naji gabana Yana faduwa heart beat Dina Yana karuwa, kinsan ma inda matsalar take?"
Kai sajidar ta girgaiza tana fadar "sai kin fada".
"Kinsan haduwar mu ta farko rungumeni fa yayi a cikin jirjinsa tsam kamar.wata baby amman Kamar an dinke min Baki na kasa ko fada Masa magana ne saima wani azababben kwarjini da yayi min harda fadar na ringa kula kada nayi musu asara'.
Ai Sajida Bata San lokacin da wata dariya ta kubce Mata ba tana fadar.
"Babbar magana kice da wata tsumammiya a tsakani ku tun tuni har kika dauki alhakina gurin hanani kwanciyar hankali tun jiya Allah barci ma ban samu na kirki ba Ina zulumin abinda kaje yazo, Dan ba kowa bane za'a aje masa mace kamar ke ya iya kauda Kai gaskiya"
Wani duba zahrar tayi Mata tana fadin "ban Gane ba me kike nufi da maganganunki?.

Wata dariyar tayi tana fadin "A'a ba mefa nake nufi kawai dai...... "
Sai tayi shiru.
Wani zancen ta dauko Tana fadin "Zahra ki tsaya ki nutsu a gidan aurenki ki gyale kowa duk wanda ze raina Miki miji kada ki amince ko waye kuwa Koda ni da nake Miki wannan maganar, Kuma game da Hameeda ki kula sosai Dan a jiya ta nuna Miki jiya ba yau bace, jini kuma yafi ruwa kauri, Koda ta dawo tana neman Kara shiga jikin ki da wata manufar tazo, Dan Allah kiba marada kunya duk yanda ake son ganin lapses dinki kada ki bada damar hakan".
In Sha Allah zan kula nagode Bestie Allah yabar zumunci. Zahra ta fada
"Ameen" sajidar na ta fada, suna cikin hira akayi knocking din kofar ba'a bude ba Zahra ce Mike tana fadin "ina zuwa, tana kokarin yafa gyale ta rufe gashinta Sajida ta warce ta aje gefen ta tana fadin "haba ke kamar matar liman a daki na da Bata ja ba tayi gaba saboda an Kara buga kofar, budewa tayi Mahmud ta gani Yana tsaye ya canza kaya ya saka Riga da wando na wani yadi light brown dinkin buda yana baza kanshi sa na ibada.
Matsawa tayi daga jikin kyauren ganin alamar shigowa zeyi Amma fa Saida yadan shafi fuskarta kadan sannan ya ida ahigewa ciki, tsaye tayi tana binsa da ido tana ayyana "Wai meye ne yake faman shafa mata fuska har a gaban mutane ko kunya bayaji tasan wlh sarai Sajida ta gani sai dai ta basar kawai gashi ta wani rike mata gyale ta wani barta tsurarta".
Direct gurin mirror ya nufa ya zauna a Kan stool, Yana fadin "Bestien mu zuwa nayi muyi sallama naji Abdul Hakeem yana maganar Zaki wuce yau ko".
Ya fada Yana murmushi, itama murmushin tayi masa tana fadar.
",In Sha Allah yau sai kano tunda Allah ya cika min burina Zahra ta shigo gidanta fine".
"To mun gode kwarai Allah ya saka da Alkhairi sai munzo visiting idan madam zata dauki nauyin zuwan mu Kinga Nima sai Naga duniya ko madam?" Ya zubawa Zahra narkakkun idanunsa Yana Mata wani kallon qasa qasa.
Shiru Zahra tayi tana yafa gyaren a kanta, Sajida ce tace "gaskiya Kam haka za'ayi".
Tashi yayi ya Dan tako kadan zuwa gaban Zahra kamar ze hadeta da jikinsa da sauri tayi baya tana turo Baki yi yayi kamar Bai gani ba, envelope ya Mika mata Yana fadin ki Bata sskonta ne na jiya data Bari nayi niyya bazan canza ba sai dai idan bataso ta bayar, nizan shiga gurin su malam".
A hankali tace "an gode madallah a dawo lfy".

"Amin to bestie sai munzo ko".
Bai jira abinda zata ce ba yayi ficewarsa.
Ajiyar zuciya Zahra ta sauke tana Zama kusa da Sajida Mika Mata envelope din tayi tana fadin "yaushe ya Baki kikace bakya so?".

"Jiya Mana lokacin da zamu tafi sanda wannan jikar marokan ta zubar da darajarta ta rokeshi, yanzu Dan Allah me Hameeda ke nema? wane irin rufin asiri ne Allah Bai mata ba. Amma ta lalace gurin roko? shi yasa na aje masa kudin sa nayi gaba kayan ma nace bana so su rike".
Dan murmushi Zahra tayi tana fadin "Saji danger wato halin na Nan ko? To nidai gashi nan tunda a gaban ki ya bayar saiki karba".
"Bude mu gani to"
Sajidar ta fada.
Stalling founds ne na ingila musu yawa a ciki kallon kallo sukayiwa juna kafin Sajida tace wallahi bestie akwai kukus a shinkafa zakice na fada Miki, Wai kuwa kin tsaya kin Kare guyn nan kallo kuwa?". Kinga ya Miki Kama da Wanda baida abinyi ko wanda ya tashi a cikin rashin wadataccen ilimi da mugu? Dubi muhallin daya ajeki, ance malam ya bashi gidan sai kungiyar da yakewa aiki sukayi renovation din gidan ki kiyasta nawa yaci gurin aikin kinsan da an kashe abinda yafi kudin ginin duk yi Masa akayi? Ki tuna Nan fa ba garinsu bane ance bako ne kuma yaki fadin garinsu anyi magana ance yace ya manta komai sai a hankali idan ya tuna hankali ze yarda da hakan? Kuma kina tunanin Abba ze daukeki ya bashi ba tare da yasan wani Abu a tare dashi ba? Kiyi nazarin abin Mana ni dai ina fada Miki kibi komai a hankali kuma yanda na fashimci wani Abu a maganar da Kika fada min kinfa kamu da son guyn Nan tun sanda kuka hadu ba tare da kin sani ba, Kuma Shima Naga yanda yake shige Miki ko kunya ta Bai jiba kinsan sai a hankali kawai kwanan Nan labarin ze sauya irinsu basayi da wasa fa".
Ta garasa fada tana dariya kasa-kasa.
Suna cikin tattaunawa Kira ya shigo wayar sajida "Ya Abdul Hakeem ne" ta fadawa Zahra kafin ta daga.
"To"
Kawai tace ta kashe Kiran tana fadin.

"To bestie ya Abdul Hakeem Yana jirana Wai a she shine ze Kaini nifa daya fada na dauka da Wasa yake lokacin da Ammah tace Magaji ko Malam Bala dureba zasu kaini sai kawai yace su Bari Shima Yana son yaje kanon Sai ya tafi Dani".
Dariya Zahra tayi tana fadin "idan tayi wari munji batun, yanzu ba fa Naga Ya Abdul Hakeem Yana dama dama dake ba bai fada min ba Amma zakice na fada Miki Ina ga target dinsa kenan yau yake son ya yad'a manufarsa shi yasa yayi Riga malam masallaci yace Wai daman kanon zaya".
Kin magana sajidar tayi sai murmushi kawai. Zahra tace "bestie ko dai komai ma ya kankama ne ban sani ba Ina shirme?".
Kafin sajidar ta Bata amsa wani Kiran ya shigo da sauri ta dauki jakarta tana fadin "To bestie sai gani na gaba Allah ya bada zaman lafiya ya kade fitina, sai anyi ta hakuri kafin komai ya dai daita ki kwantar da hankalin ki zakiji dadin Zama dashi in Sha Allah".
Har gate ta rakata babbar ledar dake hannunta ta Mika mata tana Mata addu'ar sauka lfy. Amsa tayi tana Mata godiya ta bude gate din ta fita, ya Abdul Hakeem Zahra ta gani a mota a zaune cikin mamaki tace.
"Ya Abdul Hakeem daman kana Nan waje Amma baka shigo ba?".
Fitowa yayi ya karaso gurinsu Zahrar ta gaishe shi, sannan ta juya ta koma ciki duk zuciyarta ba Dadi Kamar ta Hana sajidar tafiya amma ba hali.

*********

Mahmud Yana fitowa direct Famfon shanu ya nufa tunda lifan din Habib a gurinsa ya kwana, tun jiya daya karba da yamma Bai koma unguwar ba.
Lokacin daya karasa yayi arba da motar Sameer wani murmushi yayi Yana fadin. "magulmaci kawai".
Kafin ya shiga Saida suka dinga gaisawa da jama'a anata Allah sanya Alkhairi, Binya ya tambaya Ina Habib yace yaje Kai wani sako da malam ya tura shi ya Kai gidan sarki.
Gurin Malam din ya shiga shi dasu Sameer ya samu suna magana da malam din Yana shigowa da sallama mlm din yace.
"Yauwa Dan halak yanzu nake cewa bazaka jima ba zaka shigo, mutanen ku ne sukazo da wasu ayyuka gasu nan dai zasuyi maka bayani. Ya wajen iyalin naka!?"

Dan sosa kansa yayi Yana Dan sadda shi qasa yace "Lafiya kalau tace a gaisheka" .
"Masha Allah. Allah yayi Albarka"
Gurin su Sameer ya juya suka gaisa, kafin suka fita zuwa inda suke meeting.
Stepdown training zasuyi da school base management committee Basu tunda tsarinsu ya koma sun bin tsarin makarantun government ne sai kuma officially da suka gayyaci Mahmud zuwa gurin taron da zasuyi a Lagos nan da kwanaki biyar masu zuwa. Bayan Gama taron Sameer ya dauki Mahmud a mota suka fita hotel din suka nufa a hanya Sameer ya kalli Mahmud Yana fadin "yallabai meye labari naga text dinka komai an sawo zuwa anjima motar zata karaso amma sai nake ganin kamar kayi tafiyar nan da ita tunda zaka jima a can Kuma kaga duka kwanan ta nawa zaka tafin baka ganin abin ze iya Zama na surutu ko ace ma guduwa kayi amma dai ya kake gani?".
Dan Jim yayi kafin yace.
Tafiya da ita ba shine solution ba na dauketa na kaita Ina ko Kuma nace Mata wanene ni Nan nace Lagos zani can Kuma taga sabanin hakan ya kake tunani ka tuna fa she's educated, zatayi saurin gane komai ni kuma nafi son na Gina soyayya ta a zuciyarta ba tare da tasan who I am ba, I hope you understand?".
Kai ya gyada Masa alamar eh.
Sun Dade suna tsaya yanda program din ze kasance da abinda za'a batar da abinda za'a kashe a makarantar zuwa lokacin da zasu dawo suna cikin aikin direban daya dauko kayan ya Kira Sameer ya fada Masa ya shigo Azaren ya fada Masa inda yake tattara komai sukayi suka wuce gurin da direban yake, Sameer din ne ya shiga gaba direban na binsa a baya har zuwa gidan Mahmud din.
Mai gadi ya taya direban sauke kayan, kayan abinci ne da sauran tarkacen girki hatta nama da kifi daga can aka kawo kayane masu matukar yawa.
Ciki Mahmud din ya shiga tararwa ya yi tayi Baki har su zulai da sahura, a tsaitsaye suka gaisa yayi gaba zuwa bedroom dinsa.
Ganin idon su zilan yasa zahra mikewa tabi bayansa dai dai lokacin Kuma Yara suka Fara shigon kayan masarufin da aka kawo, ganin zahrar Bata Nan yasa su sahura shiga dasu store din kayan abincin suka hada da wanda Abba yasa suka kawo dazu da kayan gara su gireba dasu dublan da alkaki.
Sunyi mamakin yanda yara ke shigo da kayan abincin basu Kara Shan mamaki ba Saida aka Fara shigo dasu Nama da kifi ga drinks Nan ko ba'a fada ba Wai ance ido ba mudu ba amma yasan kima sun San kayan na manyan kudi ne, ko wacce da magana a bakinta Amma bata furta ba.
Zahrar na shiga corridorn ta waske zuwa nata dakin.

✨✨
✨✨

AUREN HUCE HAUSHI

✨✨
✨✨

💎 PAGE TWENTY ONE 💎 (21)

...............…... Sai da su zulai suka gyara Mata komai yanda ya kamata sannan suka gyara parlourn,lokacin da Mahmud ya fito bedroom dinta ya nufa baiyi wani knocking ba ya tura kofar a gaban gado ya ganta ta cire bedsheet din ta zubo da pillows din da alama wani Abu take nema sallama yayi mata cikin muryarsa Mai nutsuwa yana kallon ta, cikin takunsa na cikakken namiji ya karaso Yana tambayarta "lfy me kike nema ne haka Kika birkita gurin haka?".
Jiki sanyaye tace Masa "wayata nake nema tun safe banganta".
Dan matsowa yayi kamar ze tayata dubawar Yana fadin "Kuma tun safe Baki ganta ba Kuma Baki nema ba sai yanzu, to su waye suka shigo dakin ne?".
"Shiru tayi kawai tunda tasan daga ita sai sajida ne a dakin Kuma tun bayan tafiyar ta ko Baki ne 'yan ganin daki Bata ahigo dasu Nan Dan gani take yaushe za'a dinga shigo da jama'a har dakin barcin mutum su dai dayan tunda ba a ciki take ba.
Dagowa tayi ta Dan kalli gefen shi da gani wanka yayi ya canza kananun Kaya tana mamakin sa ita tunda take ganinsa Bata taba ganinsa da shiga irin wannan ba Kullum manyan kaya ne Amma daga jiya zuwa yau ya zamar Mata wani daban, Sam ba wancen bane take gani.
Kamar ze wuce ta bayanta sai Jin Hannun Mutum tayi ya zagayo ta cikinta ya manna bayanta a kirjinsa ya kwanto da kansa dai dai saitin kunnenta iska yadan hura Mata kadan tare da hucin numfashinsa kafin yace.
"Ki daina wahalar da kanki tana gurina tun safe na dauka, nayi mamakin da baki nemeta ba sai yanzu? Na cire sim din saboda Naga wani sakarai ya kiraki da number din to nasan ze iya bibiyarki tunda naga bashi da taushidi ko kankani Bai hakura ba da hukuncin Allah so yake da karfi saiya kwato abinda ya kubce masa".
Kasa ko kwakwkwaran motsi tayi sanda yake jero Mata maganganun. Amma jin ya Kira Musbahu da sakarai marar taushidi yasa taji Zuciyarta ta wani baci, idan beji tausayinsa na abinda ya faru ba ai baze Masa bita da kullin irin wannan maganar ba, shida ya tsunci dami a kala har ya samu bakin magana irin haka. Nan da Nan taji ta samu wani courage wanda Bata San tana da shi ba, cikin muna bacin rai ta fara kokowar raba jikinta da nasa tana fadin.
"Wallahi Musbahu ba sakarai bane, ba Kuma marar tauhidi bane,dan ya biyo abinda yake halalinsa amma kasan dai Banda qaddara ba abinda ze rabani dashi, dashi muka tsara planning na rayuwarmu Amma lokaci daya ka rusa Mana budget din mu ka yarda da aurena da aka baka Kuma wallahi tunda nake dashi bai ko taba rike ko hannuna ba, amma Kai kuwa fa ranar Dana fara ganinka a duniya dame ka Fara min bada rugumata ba?" Kai kenan baka da aikin yi sai tabawa mutane jiki ......
Bata karasa fadar abinda tayi niyya ba taji ya hade bakinsa da nata cikin zafin nama Yana ladabtar da bakin nata da harshensa, dayan hannun Kuma yayi Mata wani irin riko bana Wasa ba dayan Kuma yana yawo dashi a ilahirin jikinta cikin wani irin sarrafawa Mai zafi.
Wata irin tsuma jikinta ya kama ga hawaye kamar na lalataccen famfo sai zuba suke ba bakin kuka sai mutsu mutsu take Amma ko a jikinsa wajen sau uku ana Kiran wayarsa tana tsinkewa, yayi biris da Kiran Kumar baya ji, sai da ya tabbatar da ya ladabtar da ita yanda yake so ya saketa, kan bed ta fada tana shashhshekar kuka hannunta daya yana Kan lebenta dake Mata zafi haka ma kirjinta zafi yake Mata ga gaban rigar ya farke Mata ita.

Kafarsa daya ya doro Kan gadon dayar tana kasa ya Fara fadar maganarsa hankali kwance kamar bashi bane ya Gama yamutsa Mata jam'iyya yanzu ba cikin mugunta.
"Wallahi na Kara Jin wannan sunan a bakinki ko magana makamanciyar irinta saina shayar dake ruwan mamakina, an fada Miki ni lusari ne da har Zaki tasani gaba kina fada min rubbish ne? an rusa muku budget din sai kuyi duk abinda zakuyi, an fada Miki Nima son abin nakeyi ne? da har Zaki tsaya kina min rashin kunya akan wannan lusarin Mai karairaya kamar mace,ke yanzu wannan har wani namijin arziki ne da ze iya dake? wallahi da kinyi tsautsayin aurensa da kin Gane Baki da wayo, idan Kika Kara gigin fada min magana makamanciyar irinta zan Baki mamaki wallahi, , har kike wani zakewa kina fadawa mutane magana, kice tak akansa billahil Azeem sai kin Raina kanki a dakin Nan saina banbance Miki tsakanin namiji da muna maza".
Yayi tsaki ya juya abinsa cikin takunsa na ingarman namiji ya fice daga dakin zuciyarsa kamar zatayi bombing.
A yanda su zulai sukaga ya fito Saida abin ya Basu tsoro kallon kallo suka shiga yiwa juna, sahura ce tace.
"Zulai bakiga yanda Mai gidan nan ya fito bane? Allah yasa ba mutuniyar taki bace ta taboshi Kinga ai ba haka ya shiga ba".
Zama zilan tayi tana fadin "waya sani sahura muna Nan tare dake, nifa shi yasa nace ba zanzo ba yau amman Ammah ta matsa akan sai nazo na Gane mata lafiyar ta,tun safe wayarta idan an Kira Bata shiga".
"To Kinga kuwa dole ki dubota ki gani ko Lafiya ya fito a haka kofa a dawo lfyr mu bai amsa Mana ba".
Jiki ba kwari zulai ta nufi bedroom din Zahra ganin zilan ta shige cikin corridor sahura ta Ciro wayarta Nokia ta Kira Mama. Ba bata lokaci ta dauka kamar jira takeyi ta shiga labarta mata abinda ta gani tun daga kan kayan da suka Zuba store har fitowar Mai gidan yayi da alamun bacin Rai a tare dashi, to kawai sahurar ke fada alamun wani Abu mamar take fad'a Mata sannan sukayi sallama.
Sai da ya fice harabar gidan ya Ciro wayar daga aljihun wandonsa ganin Sameer ne yasa ya Maida wayar ya nufi inda Sameer din yake zaune cikin mota, Bai Masa magana ba, zagaya yayi ya shiga motar yana fadin "let's go"
Ganin yanayin daya fito ya hana Sameer din korafin barinsa a waje baice ya shigo ba, dan kwantar da kujera Mahmud din yayi ya kwanta yasa hannu ya dafe kansa da gaske Sara Masa yakeyi lokaci lokaci Yana Dan Jan tsaki, Sameer dai be tanka Masa ba yasan a kusa yake, sai da sukayi nisa da gidan Sameer din ya Dan juyo yana tambayar.
"Ina muka nufa yanzu nifa na gaji ga yunwa Ina ji kace muzo gida muci abinci Kuma ka watsar dani a mota inaga ma sai da ka rage zafi ni in Nan Ina hamma ka shanyani".
Ya fada Yana Maida hankalinsa a titi.
Tsakin ya Kara yi Yana dagowa daga kishingidar da yayi Yana duban Sameer din "Allah ya shiryeka ka dauka kowa ma irinka ne Wanda baya iya kauda Kai a Kan Mata? Muje can hotel din kayi order abinci kaci tunda bani na gayyato ka ba cewa nayi ka dorowa mota kayan Kai Kuma sai gurin jibi kazo, to bansan wane kinibibin ya kawo ka ba ka bar yarinyar mutane da ciki kana gantali".
Ya karasa maganar Yana hararar Sameer din.
Dariya yayi Yana "fad'in easy man bani na kar zomon ba rataya aka bani, waya fada maka lamarin su da sauki? bakaji abinda Abbanta ya fada maka ba? ai da yace sai ana hakurin da gaske ne Zama dasu Saida hakuri".
Wani sakaran kallo Mahmud din ya aikawa Sameer da shi.
"Ka wani zaqe kana ta zuba wani Abu nace maka tayi min ne? da kaketa faman fadin maganganu haka tsabar saka ido kawai, gobe ka tattara ka koma inda ka fito tunda ba gayyato ka nayi ba da zaka dameni da kananun maganganu zan shigo da kaina kanon ba ai ba bakuwa ta bace ba".
Ya fad'a da gaske Yana Bata rai.
Shiru Sameer din yayi ganin da gasken koma Nene yayi touching dinsa sosai.
Suna shiga harabar hotel din kafin Sameer ya Gama parking a parking lot Mahmud ya bude ya fice abinsa Yana picking din wayarsa da aka Kira.

******Tunda zulai ta doshi kofar bedroom din Zahra take jiyo Kamar shashhshekar kuka, hannunta har rawa yake gurin bude kofar Dan ba maganar knocking, rubda ciki ta sameta tana faman shashhshekar da sauri ta mayar da kofar ta rufe ta karasa gurin zahrar da sauri tana Fadin.
"Subhanallahi uwar dakina me zan gani haka me kikayi masa? Dukanki yayi? Dan Allah kiyi magana Kona Kira Aunty Hasana ne sai ki fad'a mata ko na Kira Miki Ammah".
Kai ta girgaiza mata alamun a'a, "to ki fad'a min ko zan iya yi Miki wani abun Mana".
Saida kukan ya lafa Mata sannan ta yunkura ta tashi zaune ido zulai ta zuba Mata ita ba yarinya bace kallo daya tayi Mata tasan da wata a kasa ganin yanda take a yamutsa ga labbanta sunyi jajir abinka ga farin Mutum ga gashin kanta duk gyaran ya turje. Zama tayi kusa da ita sai a lokacin taga gaban rigarta a yage Hannun bra dinta guda a tsinke.
Kai kawai zulai ta dafa tana Fadin "mezan gani haka ni zulaihatu! Haba Zahra'u me yayi zafi haka ai sai kisa ya illataki a banza, gardama kika yi Masa yayi Miki haka?"
Cikin shashhshekar kuka tace "A'a maganar Musbahu yake min shine ya Fadi Abu marar Dadi a kansa shine kawai Dan na mayar Masa da amsa Nima yayi min haka". Ta karasa fad'a tana kuka.

Kasake zilai tayi tana duban zahrar kafin tace
"Haba Zahra'u da wayonki da hankalin ki Zaki rinka irin wannan abun har yaushe Zaki ringa maganar wani namiji a gaban mijinki har kiyi ikirarin fad'a Masa magana marar Dadi akan shi ai yayi Miki kadan wallahi idan wani ne yau basai gobe ba saiyayi Miki kaca-kaca yanda ko sunansa ba Zaki Kara fad'a a gabansa ba, kada ki kuskura ki Kara irin haka Zaki ragewa kanki kima da daraja a idonsa, duka yaushe akayi daren da shashshawa zata Bata,Ina cewa jiya aka kawo ki amma ace an Fara da haka kinga abin baiyi kyau ba ko kadan, yanzu ki tashi ki shiga kiyi wanka da ruwan dumi zanje na cewa sahura kina wanka ne, mu tafi kawai tunda nasan halinta Abu kadan zata fara yaya tashi tunda nasan badan Allah ta biyoni ba dan Saida na fito harabar gidan ta biyoni.
Sallam zulan tayi Mata Tana Kara tausarta akan ta ringa tauna irin maganar da zata ringa fada masa.

Cikin karfin Hali ta Mike ta nufi toilet da gaske ya tsumama mata jiki ta jima a toilet din tana kuka maganganunsa sun Mata ciwo matuka har wani gori yake Mata Shima ba sonta yake ba, to an fada masa ita son nasa take har yake wani Mata wulakanci, ita ta rasa a Ina ta kuskuro ne take haduwa da fitintinu daga wannan sai wancan? "Astagafirullah".
Ta fada a zuciyarta, alwala ta dauro ta fito ba wani kwalliyar azo a gani tayi ba duk ranta a cunkushe ga 'yar wayar da zata debe mata kewa ma ya dauke, a ranta tace "mugu kawai wani sumumu kasam dashi Kamar na Allah Nan kuwa dan duniya ne Mai lasisi".
Tana cikin saka kaya taji karan bell alamun Baki a gurguje ta ida yafe gyalen rigar ta dan fesa turare tayi gaba.

*****
Sai Bayan sallar magriba su zilai suka karasa gida dai dai lokacin Magaji ya fito da manya warmers a hannunsa sai Autan Ammah da basket a hannunsa Shima, zasu kaiwa zahra abincin dare.
Suna shiga zilai ta wuce part din Ammah ta fada Mata sun dawo ita Kuma sahura ta nufi nasu bangaren sai da zulan ta shige part din sannan sahura tayi wuf ta shige sashen Mama.
Salma kawai ta samu a falon tana kallon series na India ko arzikin amsa sallamar sahurar Bata samu ba sai wani kallon banza tayi mata tana Fadin "lafiya Kika wani shigo afujajun haka?".
Kafin sahura ta samu zarafin Bata amsa Mama ta fito daga bedroom din ta tana Fadin Kamar maganar sahura nakeji?"
Cikin azarbabi tace "nice Mama mun dawo".
Ta fada tana Zama a kasa kan carpet.
Cikin kwarewa da munafurci ta shiga korawa mamar bayanin abinda ta gani harta Kara da cewa.
"Anya Mama yaron Nan kuwa Babu abinda yake boyewa kin ganshi kuwa? Gaskiya wallahi baiyi kama da fakiri Mai neman abincin yau da gobe ba, kayan abincin da muka zuba a store din wallahi ni wani abin ma ban taba gani ba hatta madara wannan manyan gwangwwnaye sunfi ashirin Nama kuwa na kaji kawai sun Kai hamsin Banda na rago Banda na shanu Banda kifi Allah Mama Saida muka cika freezer din cikin kitchen din ga lemuka da ruwa Kamar banza ga......
Bata Bari ta garasa ba ta daga mata hannu "bar shi kawai jeki zan nemeki".
Mikewa tayi tana Fadin "a huta lafiya Bari naje nayi sallah naji ana Kiran insha'i". Ta fice.
Tunda ta fita Mama ke jijjiga Kai tana kwafa, Sam hankalin salma na can gurin kallon ta Bata damu da abinda su mamar suke ba, Saida mamar ta Kira sunanta sannan hankalinta ya dawo Kan mamar tasowa bayi ta dawo kusa da ita tana fadin.
"Mana menene Naga kamar ranki a bace,?".
Tsaki tayi tana fadin.
"Anya Abbanku da Asma'u ba ninkeni sukayi a baibai ba kan auren yarinyar Nan? ni daman tunda naga daga b'angaren Asma'u da 'ya'yan ta da 'yan uwa ba wata turjiya nasan da abinda suka taka bakiji labarin da sahura tazo min Rashi ba?".
Kai salmar ta girgaiza alamar bataji ba, Nan Mamar ta shiga fad'a mata abinda sahurar ta fada Mata, Nan da Nan hankalin salma ya tashi ta shiga fadar "ai laifinki ne Mama Nan nazo na fada Miki naga wani inaso a gurin Baba Malam Kika dinga zagina duk yanda naso ki fashimceni shi ba irin wanda kike tunani bane ni naga abinda na gani Amma Kika shafawa idanunki toka kikaki saurarena ai gashi nan duk fafutukar ki ta tashi a banza ko yanda kika fada min gidan yake ai kinsan da wata a kasa".
Ta fad'a tana share hawaye, Nan da nan hankalin Mamar ya Kara tashi idanunta sukayi jajur, cikin kaushin murya ta Fara fadar.
"Ni za'a yiwa haka wallahi sai dai kowa ya rasa Dan wannan auren sunansa matacce dole ya saketa ko baya kaunar Allah ai indai Ina raye yarinyar Nan sai dai kyanta ya Kare a banza ba dai tayi aure inda zata huta ba ita da hutu sai dai tayi nata gaji da aiki, duk wani haske na rayuwarta saina dusashe shi Bari ma ki gani".
Ta yunkura ta Miki ta nufi bed room dinta tana lalubar wayarta.
Ayi hakuri ba editing Naga kwanaki wata na fadar kada a karanta rubutun ba kyau.



AUREN HUCE HAUSHI



Story
&
Written
By

Maman Fatimah.

Godiya da yabo sun tabbata ga Allah s.w.a, salati da daukaka da Amincin su tabbata ga shugaban mu Annabi MUHAMMAD s.a.w.w.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.