Trending Hausa Novels

Auren Huce Haushi Book 1 Complete Hausa Novels By Maman Fatima

Reading file: AUREN HUCE HAUSHI BOOK COMPLETE DOCUMENT BY MAMAN FATIMA.txt

Chapter 14 of 34

Page 25
📖🖋️

________Dariya ya kama harda hawaye abinda bata taba gani ba.
Sororo tayi tana kallonsa, ita bataga wani abin dariya ba a maganarta, hannu ya Mika ya karbi wayar kunnawa yayi ya Mika mata Yana kashe Mata ido tare da d'age gira.
"Kina son kisan inda nake samun mahaukanta kudaden Nan ne?".
Kai ta gyada Masa.
"Good ki Bari sai ranar da Kika Zama ni na zama ke na mallaki kayana, a ranar nayi Miki Alkawarin sanin komai nawa na duniyar Nan, Idan Kuma yanzu you are ready za'a taimaki Dan Malam a lullubeshi da bargon ni'ima to? yanzu kuwa kisha labari har wanda Baki nema bama zan fad'a Miki, tunda ke inda nake samun kudi kawai Kika bukata baki son sanin waye ni?daga Ina nake?meya kawoni garinku? Gasu nan rab'ab'a da yawa, to ki rubuta ki aje har abada ni Mahmud bazan tab'a ciyar dake ko shayar dake ko wani Abu na jindadin rayuwa da haramun ba, duk abinda na Baki ki tabbata da gumin halalina na nema, kinga wannan wayar da kudina na saka na saya Miki,wato kina tsoron kada na Sato kayan mutane na kawo Miki ko?"
Kai shiga gigizawa.
"Ni ba cewa nayi kayi sata ba, gani nayi kana ta abubuwan da sai Mai wadata ne ze iya yinsu Kai Kuma Naga...." Sai kuma tayi shiru tana kallonsa.
"Oya continue Mana,kinyi shiru wato Kinga bana aikin komai ko?".
Shirun tayi Bata Kara cewa komai ba.
"Tashi ni ki bani abinda zanci idan na biye Miki da wannan yarintar taki sai yunwa tayi min illah kisa a Fara gulmarki ace kina barina da yunwa, ganshi kin sani azumin da Babu lada".
"Ba Kaine kayi zuciya ba ka tafi kabar abincin"

Ta fada a shagwabe.
"Ki tashi ki bani kada lissafin ya canza fa"
Ya fada yana matsowa jikinta sosai, da sauri ta Mike ta nufi dining inda ta jera abinci.
Table mat ta shimfida a Kan carpet din sannan ta dauko abincin ta aje.
Plate biyu ta dauko dayan ya janye.
"Ki Zuba Mana a plate daya ya Isa ai Kuma indai Ina gida plate din mu daya tunda Kika yimin horon yunwa yau daga Wasa Dan kawai kewar Hajiya ta ta kamani shine Kika horani duk ranar dana kaiki gabanta saina fada Mata tasan irin zaman da zatayi dake, ni Dan gata ne a gurinta bana laifi zakiga yanda take sona".
"Ko?" Ta fada tana zuba abincin a plate, Dan tura Masa plate din tayi kusa dashi "Gashi Nan ni bana Jin yunwa".

"Ashe zan Miki dura wlh, sai kinci kuji min yarinya da kinibibi Wai so kike da karfi sai kin koya min surutu ne? Kin iya kalato abin magana da wani bakinki chut".
Ya fada yana shafo pink din lips dinta.
Taci Amman ba wani na kirki ba da gaske abinci Bai dameta ba barta dai da 'yan ciye-ciye.
Bayan sun gama ne ta kwshe kayan ta gyara gurin duk Yana kallonta komai tayi kyau yake mata gata ba wata babba ba sai dai akwai Sama da kasa masha Allah.
Lokacin data gama ne ya yafito ta da hannu,a hankali ta nufo shi kamar me counting steps sai rausaya take, wani yawu ya hadiye, Dan risinawa tayi a gabansa duka hannuwanta ya kamo ya zaunar da it kusa dashi.
"Zaki rakani unguwa?"
Ya fada Yana zame Mata veil din da tayi rolling gashinta ne ya bayyana biki sidik dashi sai walqiya yake yasha gyara ga kamshin hair spray Yana tashi.
"Eh zani Bari naje na shirya".
ta fada Tana kokarin zare jikinta daga nasa. Duka hannuwansa yasa ya riko kugunta ya hade ta da jikinsa.
"Ina zaki?wane irin Shiri zakiyi kinsan inda zamu ne kike sauri?".
Lakwas tayi a jikinsa da karfi da yaji so yake ya Saba mata da Zama a jikinsa gashi baya ko Jin jauyin taba Mata jikin sai dai idan Bai soba.
"Bazaki tambayi inda zamu ba, kina Neman sake canza Kaya".
"Nasan gida zamuje Mana".
"Ai kece gidan, kinaji da so nake muje gidan da gaske mu roki alfarmar a bamu aron me aiki daya Wadda zata zauna min dake kafin na dawo".
"Kafin ka dawo? Ina zakuje?".
"Au Ashe ban fada Miki ba, aikin NGOS din Nan ne ya taso suka gayyace mu zuwa meeting da zasuyi a UK Kinga ai bazan zauna ba da dollars ko stalling founds suke biyan mu, idan Allah yasa na samu da Dan auki Kinga na Kara jarina tunda Naga Nima Ina sha'awar siyar da materials har munyi magana da Abba yace ze bani rumfa daya a Muda lawal market na gwada ko ina da nasibi a cikin sana'ar, sannan Habib ma munyi magana zamu Fara siyar da spare parts na motoci a nan Muda lawal market din dai".
"Allah ya bada sa'a, Kuma idan ka tafi sai yaushe zaka dawo? Ko kaima shike Nan abinda yake faruwa Dani ze faru a kanka kaima, kada ka tafi ka barni Dan Allah tunda nasan ba Sona kake ba baka ni akayi sadaka, Dan Allah ka taimaka ka kaini Jordan tunda Ina kudin flight kawai ka taimaka ka fitar Dani daga kasar da sunan Kai zaka tafi dani, bana son Ammah ta qara shiga cikin damuwa a kaina wlh Batasan tashin hankali ba Sai Dana isa aure Kullum idan kaga Ammah a cikin tashin hankali to a kan lamarina ne ni Kuma yanzu bana fatan na qara ganinta cikin bacin rai ta dalilina, kaje ka fada musu zaka tafi Dani ko Kano ne ka Kaini na zauna gidan su bestie kafin na samu visa, nagaji da Kasar nan wlh Ina da gata Amma sai walagigi rayuwa ta takeyi anan Dan Allah kayi min wannan alfarmar Koda ita kadai zakayi min ta karshe a zamana da Kai".
Ta kifa kanta a jikin kafad'arsa ta saki wani kuka Mai tsuma zuciya.
Bai hanata ba ya dai Kara matseta a jikinsa Yana shafa bayanta yasan abin Yana cin zuciyarta ne bata rasa komai ba amma an dabaibaye Mata Jin dadin rayuwa kamar yanda Baba malam ya fada masa. Sai da tayi Mai isarta ya dago kanta daga jikin kafadar tasa.
"Kiyi hakuri kowa da irin tasa jarabawar ke taki a haka tazo, Kuma waya fad'a Miki zan tafi na barki bazan dawo ba? Waye kuma yace Miki bana sonki? Kinsan tun tsawon lokacin da nake dakon soyayyarki kuwa? Tun Baki san meye son bama yarinya share hawayen ki Mahmud naki ne har abada, dole kije Jordan ke me gida sukutum a can.Amma yanzu kiyi hakuri nema zani idan Kuma na zauna bakya son tafiyar saina fasa Sameer yayi komai kawai nace madam ta Hana".
"Kaje kawai idan baka dawo ba nasan abinda zanyi".
"Keh! kina da hankali kuwa me zakiyi wlh zan turaki gurin Hajiya Inna duk da ban shirya zuwa yanzu ba kawai ki Kira min ruwa, zaman Allah nakeyi zamanki nakeyi badan ke ba Dana Dade da barin garin Nan".
" Ni Kuma?"
"Off course"
Ya fada da karfin gwiwa.
"As how?"
Share ta yayi kamar bai jita ba.
"Tashi ki rakani kada dare yayi, dauko Mana key din motarki na dana kada na tafi ban Sanya albarka ba, ki canza shiga kada a kalle min kayana" fada Yana mikar da ita daga jikinsa.
Duk kin haye min cinya kinsa sai ciwo take min".
Ya fada Yana Mata wani smile.
Bata kula shi ba tayi gaba abinta duk zuciyarta ba Dadi sannan tana jujjuya maganganunsa a zuciyarta, kinsan tun lokacin da nake sonki? Danke nake zaune a garin Nan gasu Nan dai da yawa.
Saida ta sakarwa Kanta ruwa sannan ta shirya agurguje ta saka wata Riga da siket na atamfa super dinkin ya zauna das a jikinta ta saka mayafin da yayi matching da atamfar ba tayi amfani da turaren kaya ba body mist kawai tayi amfani dasu a jikinta kusan kala uku, sai ya bada wani sansanyan kanshi Mai dadi. Tana gyara gyalen ya shigo dakin tsayawa tayi tana kallonsa shida yace unguwa zata raka shi sai gashi da Riga armless da wandon ta farare tas na kamfanin Adidas sai taga kwata kwata ya canza Mata ya koma irin 'ya'yan hutu din Nan na gaske wadanda Jin Dadi ya gama ratsa su yayi wani irin fresh da shi.
Matsowa yayi kusa da ita Yana Dan watsa hannu irin dai na isassun yaran. Mayafin ya kama ya ida rufa Mata a kanta.
"Kallon fa na menene? Kona canza Miki ne?".
Kai ta girgiza Masa.
"Baba son body language fa ki bude Baki kiyi min magana".
Yana janyo ta jikinsa.
"A'a kawai dai da naji kace unguwa zan rakaka kuma na ganka da......"
Sai tayi shiru.
"Karasa Mana sai Kika ganni da shigar nigas ko?"
Shirun dai tayi.
"Idan Ina tare da iyalin dole na sake, kema da nace ki canza ai na Shan iska nake nufi ba Wai irin wannan ba, zo muje ki canza yawon Shan iska zamu ki min hira ki bani labarin ki tunda ke bakya bukatar nawa ki bani happiness a wannan Daren yanda duk inda nake na rinqa Tino da abubuwan su zamar min kamar kina kusa Dani".
"Ni dai Dan Allah ka barni haka muje kawai"
"Dauko key din to muje dare nayi Kuma Ina son ganin Baba malam da Abban mu, ko ba namu bane?"
Ya fada Yana kallon ta, an samu cigaba, tunda ko banza tunda ya mamnatse ta take iya kallon idanunsa ba kamar da ba da Bata yarda ta kalleshi.
"Namu ne". Ta fada a hankali, badan Yana very closer to her ba da ba lallai yaji me take fada ba.
"Oya let's go".
Ya fada Yana nufar kofa, saida ya kashe electronics na gidan sannan suka fito Yana time da karamar luggage a hannunsa,Kati ya curo daga cikin wallet dinsa ya saka a kofar ya rufe, daga nesa Mai gadi ya hangesu sun nufi parking lot din gidan inda motar daya take ajiye, a ransa yake fadar "duk inda wannan Dan ya fito Dan mafita ne ba irin yaran Nan bane lalatattu kamar yanda aketa surutun abun masu kushe da ganin rashin kyautatawar su Alhaji nayi masu gani kyautatawar nayi".
Yana can Yana tunani Bai ankara ba yaji Karan Horn alamun har sun karaso Yana can Yana nashi zarafin.
Da gudu ya tashi Yana fadin Ayi hakuri nayi zurfi gurin tunani ne, a dawo lfy Allah ya tsare".
Horn ya yi Masa suka fice daga gidan.
Suna barin gidan sun hau babban titi sosai motar su mama ta doso kofar gidan. Dan saida suka hada turaren wutar ya kammala aka zabga Masa turarika masu mahaukatan kanshi da mazubai Wanda dole yayi attracting mutum.
Daga Dan besa direban ya tsaya Mama da Asabe suka fito Asabe na rike da ledar Mai tambarin gurin Saida turarukan wutar dasu humra suka nufi gate din gidan, Asabe CE tayi knocking ta 'yar karamar kofar jikin gate din ya leko ya gane Mama tunda ya jima a unguwar sai dai ita ba lallai yasan shi ba.
Da sauri ya bude kofar Yana fadin. "Hajiya kune haka barka da zuwa ina wuninku".
Ta rusuna ya gaishe su.
'yar dariya Mamar tayi tare da amsawa kafin tace masa.
"Munzo Kara duba Zahra ne tunda tazo ban samu mun shigo ba sai yau"
Cikin nuna girmamawa malam Sani yace. "wallahi kuma anyi sabani yanzu ba dadewa suka fita da Mai gidan da kun lura ma inaga kunyi kiliya dasu a lokacin da zaku shigo su Kuma sun fita".
Turus sukayi wannan ta kalli wannan.
"Ina suka fita daga kawo yarinya ko sati Bata rufa ba?" Ta fada da alamun bacin rain a maganar ta ta.
"Wlh nima ban Sani ba tunda ba hurumina bane sanin hakan ba, sai dai ko Zaki Kira ta a waya idan basuyi nisa ba sai su dawo".
Mama Bata taba danasanin rashin karbar number zahrar ba irin yau.
"Ba komai ga sako Nan ka aje mata idan Allah ya kaimu gobe Asabe zata dawo tayi Mata bayaninsa"

Ta fada tana kallon Asaben, Wadda ledar ke Hannunta, da sauri ta mikawa Mai gadin tana fadar "in Sha Allah zan shigo Amma a fada Mata".
"In Sha Allah za'ayi fada kin gaida gida".
Ya juya da ledar a hannunsa, want abu Asabe ta radawa Mama a kunne tayi saurin tsayawa tana duban kofar da Mai gadin ke kokarin turowa.
"Malam Bismillah".
Ta fada Tana komawa tare da dauko Abu a cikin Jakarta.
Dawowa yayi Yana Dan sadda kai, kudin da Bata San ko nawa bane Mika masa.
"Ga wannan ba yawa Dan Allah a tabbata sakon ya shiga Hannunta komai dare"
"In Sha Allah Hajiya da shi zata shiga ciki, Allah ya Kara sutura na gode madallah".
Ya fada Yana qara gyara rikon ledar da kyau.
"Hajiya ta haka akeyi Nan gaba ko wani aikin kike bukata da gudu zeyi Miki kinsan su bugun Abuja ba bayanin da basa ganewa in dai kina ungo to zance ya Kare Abu sai dai in Baki nema ba, ai Nima goben da sako zan taho Masa Naga alamar kamar zeyi son abin duniya jifa yanda yayi caraf ya karbe kudin daman kamar jira yake.
Dariya sukayi gaba daya harda tab'awa, suka nufi motar data kawo su.

******

Tafiya suke yi Yana rike da Hannunta da nasa dayan, dayan Kuma Yana tuki cikin kwarewa lokaci lokaci Yana Dan matse hannun, ganin sun dauki hanyar barin garin yasa Zahra ta Dan dube shi.
"Wai Ina zamu ne?".
"Siyar dake zanyi, kinji yanda nake samun makudan kudina cikin sauki, duk garin da naje haka nakeyi na duba kyakykyawar mace na aura idan an sake Dani sai nabi dare na gudu nabar garin daman ba Wanda yasan daga inda na fito, bare ke yanda Allah ya surantaki da sura ai ke sai nafi samun alheri a jikinki".
Ya fada Yana wani daure fuska.
Zuruzuru Zahra tayi ganin fuskarsa ba annuri ko misqala zarratin Nan da Nan jikinta ya dauki rawa, duk sanyin ACn dake motar Saida gumi ya rufeta, kallonsa ta Karayi still dai fuskar kamar bai taba fara'a ba a duniya.
Jikinta tsumar ya karayi kamar ana kada Mata gangi, cikin sarkewar murya ta Fara magana bakinta Yana rawa.
Me nayi maka zaka cutar Dani?".
Rage gudun motar yayi cikin duhu, a hankali ya tssyar da motar, Zahra rufe idonta tayi take hawaye suka wanke mata kumatu.

✨✨
✨

AUREN HUCE HAUSHI

Maman Fateemah

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.