Auren Huce Haushi Book 1 Complete Hausa Novels By Maman Fatima
Reading file: AUREN HUCE HAUSHI BOOK COMPLETE DOCUMENT BY MAMAN FATIMA.txt
Chapter 17 of 34
Page 28
____Hankalin Zahra be kwanta ba sai da taji Yana maida numfashi a hankali alamun barcin ya dauke shi ajiyar zuciya ta sauke da farko Bata yarda ba da yace barci zasuyi Saida ta gani da gasken yayi barcin.
Kokarin zame kanta da yayi Mata pillow da gefen kafadarsa tayi, a cikin barcin ya kara janyo ta jikinsa yana gyara Mata kwanciyar amman idonsa dai a rufe, shiru tayi lif a jikinsa Dan Bata son ya farka su hada ido ai da kunya amma taga alama shi bashi da ita misqalazarratin idan wani ne ai zuwa yanzu Basu wani sababa yanda abun yazo musu a hagunce, ko dan shifa yana ikirarin ya santa batun yanzu ba to a Ina?Kuma waye shi?daga Ina yake? Waye sameer a zahiri shi yaron sameer ne ita Kuma a bad'ini shi yake bashi directive abin da daure Kai Kuma yace ya manta garinsu da komai nasa Amma a gurinta yana fada Mata ya tuno kakarsa har da 'yar tsamar da sukeyi.
Tunani barkatai ta dunga yi har barci yayi awon gaba da ita, karfe hudu da rabi na Asuba alarm din daya saita ya tashe su kusan lokaci daya suka farka har lokacin tana jikin shi, shiru tayi Bata nuna ta tashi ba, so take ya wuce toilet.
Addu'ar tashi daga barci yayi a hankali ya zare ta daga jikinsa kura Mata Ido yayi a cikin dimligh din dakin face dinta sai glowing takeyi ko Ina a jikin fresh sai wani sansanyan kanshi ke fita daga jikinta wanda har ya zauna a jikinta Dan duk jikinsa kamshin yakeyi, light kiss ya Bata a kumatu ya gyara Mata rufar saboda sanyin AC ga sanyin Asuba. Duk abinda yake tana jinsa bakam tayi Dan ji tayi wani irin nauyinsa ya rufeta Wai wane irin barci ne tayi har yayi sabgar rabata da rigarta amman Wai Bata sani ba, Jin karar ruwa yasa tayi saurin tashi ta janyo rigarta tana cuno Baki.
"Haka kawai duk a kalleka waya sani ma ko Abu ya saka a cikin Apple din Dana Sha shike Nan na Kama barcin asara sai yanda yayi Dani" da sauri ta ida janye blanket din tana duba jikinta Jin ba wani bakon Abu yasa taji sanyi a cikin ranta, sai Kuma abun ya Bata dariya, Jin ze fito yasa ta koma ta kwanta jallabiya ya zura ya saka tashi ka fiye naci, ya dauki tasbasha (counter( ya matso kusa da ita Dan guntun ruwan alwala na fuskarsa ya yarfa Mata kadan a fuskar ta.
"Ki tashi kiyi alwala an kusa tada sallah nasan idonki biyu tun lokacin Dana tashi".
Ya fada Yana nufar kofa zuwa masallacin cikin hotel din.
Tashi tayi ta nufi toilet din a gurguje tayi wanka ta daro alwala lokacin data fito har an idar da sallar, lotion din data gani ta shafa ta bude jakar duk wani abun da zata bukata ya sako a ciki ita mamaki take to a Ina ya Sami kayan ita dai ba nata ya dauka ba, hatta bra ma size dinta ce doguwar Riga ta cire daga leda ta saka baka Mai aikin stone, hijab ta saka ta tada sallah.
Har ta gama azkar Bai shigo ba sai gurin shida da rabi ya shigo directly inda take ya nufa.
"Barka da Asuba".
Zahra ta fada tana sadda Kai kasa, shiru yayi kamar Bai jita ba sake maiamaitawa tayi.
"Taso kiga yanda ake gaida Dear ba irin wannan local gaisuwar ba"
Sunne Kai tayi tana Dan murmushi, tsugunawa yayin daf da ita yana kallon 'yan yatsun Hannunta sumul sumul dasu kamar Bata aikin komai da Hannun, dagota yayi gaba dayan ta ya mannata a jikinsa "ji nakeyi kamar kada nayi tafiyar nan ko Kuma na daukeki mu tafi, idan na tuna zanyi nesa dake wlh wani irin rauni ne yake kamani naji kamar idan bana Nan wani Abu ze faru".
Ya fada cikin muryar karaya da gaske a 'yan kwanakin Nan Yana Jin wani Abu daya fi na da a tare dashi.
Cikin 'yar siririyar muryarta tace "ba komai kaje kawai Allah Yana tare damu ba abun da ze faru sai abinda ya hukunta a kaina, Allah ya bada nasara yasa a Dace, kawai dai Dan Allah kayi min wata alfarma kafin ka tafi".
Hijabin ya zare a hankali daga kanta ya Dora a Kan bed side kafin ya zaunar da ita a jikinsa as usual.
"Fadi wace bukata gareki".
Dan shiru tayi kamar bazatayi magana ba.
Oya fell free with me, kiyi magana Mana kinsan eight thirty nake so na wuce".
"Daman so nake na ringa zuwa Dr.sulaimanu Adamu college of Hygiene inda nayi service na ringa yin lectures ko sau biyu ne a sati".
Wani kallo yayi Mata na Amma Baki da lissafi.
"Ni matata da yawon aiki? Gaskiya A'a! Wannan bukatar Bata karbu ba, me kikeci na baka na Zuba indai aiki ne wlh sai kin gaji da yinsa, tashi daga jikina kin wani samu cinya kin dane,kada na makara nayi missing flight mu tsuguna duk dan burin bawa ya rushe".
"Yanzu Allah bazaka Bari na rinka Zuwa ba".
Ta fada a marairaice.
"Kinsan Allah wlh Zan hadaki da zayyan Dan nasan Yana daf da shigowa garin Nan ya juya min dake can kauye gurin Hajiya Inna ko banza kin tuka mata tuwon dawa kin mata shara, kinga ita gaba ta kaita balarabiya na mata aikatau ita kuwa bakar fata Kinga sai mu Dora a media muma 9ja munci gaba ana zuwa daga middle East ana Mana aikatau".
Ya karasa fada Yana Jan Dan tsinin Karan hancinta.
Tana kokarin magana wayarsa dake Kan bedside ta dauki wani kidan larabawa Mai dadi.
"Dauko min wayata Dan tsabar na Zama mijin ......, Gashi Nan ringtone din ma kidan kune na saka". Wayar ta dauko, Zayyan ta gani kwalalo idanu tayi Ashe da gaske yake da yace Shi wannan din zezo yanzu ko waye shi kuma "oho" ta fada a zuciyarta.
Wayar ta Mika masa.
"Ka karaso?" Abinda taji ya fada kenan Bata San me yace Masa ba taji yace "ok, ka shigo ciki akwai securities a kofa zasu zasu rakoka gurin da Zan ganka".
Ya kashe Kiran Yana nufar kofa, ki shirya kafin na dawo yanzu zamu wuce".
Yayi Gaga abinsa ya barta da Baki a sake "ikon Allah shi Kuma ko waye yake bada umarni cikin dare ya wayi gari da abinda ya bukata tasan ko waye daga nesa yake Dan jiya tanaji Yana fadin kada a biyo ta jos a biyo ta kano, ita duk ya Gama Dame Mata lissafi wlh.
******
A hankali yake tafiyar cikin nutsuwa Amma da gani kasan tafiyar ta ingarman namiji ce, tunda ya doso gurin Zayyan ya kafe shi da ido, take ya shiga jinjina lamarin ogan nasa wato ana zaton wuta a maqera said gata a masaqa, waze tab'a tunanin sa a irin nan yayi masifar bada kafa.
Bai Farga ya kureshi da ido ba Saida yazo daf dashi, "sorry sir" ya fada Yana sadda kai, baiyi magana ba ya mika Masa hannu wannan d'abi'ar sa ce baka Masa irin gaisawar Nan sai dai kuyi musabihwa. "Barka da Asuba ya Hanya?".
"Alhamdulillahi."
Ya fada sai da Mahmud ya zauna kafin Zayyan Shima ya koma ya zauna.
Kamar bazece komai ba gurin ya dauki shiru.
Saida yaja fasali sannan yace. "I hope ba Wanda ka fadawa munyi waya ga Kuma inda zaka sameni?"
Kai ya girgaiza "ko daya oga ba Wanda yasan inda na tafi kawai nace musu zanje gida ne na samu Kiran gaggawa".
"Good, na kiraka ne zaka zauna gidan da wife Dina take zanyi tafiya, Wanda na saka gadin Naga alamar gaskiya Bata isheshi ba, ko Kuma ze iya komai saboda kudi, zan turo maka pictures na wasu Mata koda Wasa kada kabar kafarsu ta shigar min gida shi yasa na taso ka da tsohon dare ".
Zayyan jin magwnar yayi wani banbarakwai "wife Kuma? To ta ina Hakan ta faru? mutumin da ake tunanin baya kasa sai Kuma ya ganshi a nan Yana wata irin rayuwa hankalinsa kwance, ga abubuwan tambaya Amma ba Halin yinta.
"To in Sha Allah baza'a samu matsala ba".
"Yanzu zaka shiga cikin Ibrahim ze nuna maka dakin da zaka huta daga Nan zuwa sha daya Binyaminu ze shigo kuje gidan".
Ya fada Yana mikewa.
Da kallo zayyan ya bishi har ya b'acewa ganinsa, ajiyar zuciya ya sauke Yana jinjina Lamarin ogan nasu wato duk yanda kasan Shi idan yayi wata bada Qafar saika rasa gane wace alkiblar ya kalla. "Wife Dina". Yanda yayi maganar kasan ba wasa cikin Yana wannan tunanin Ibrahim ya karaso Bai sani ba.
Da azama ya shiga falon a zaune ya sameta da luggage dinsa a kusa da ita tayi rolling da Veil din rigar sai tayi masa wani irin kyau, a slow ya karasa inda take zaune ya saka hannu ya dagota tsaye ya sumbaci saman goshinta.
"Nayi Miki irin gaisawar ku, Ina key din lokaci Yana ja kada da gaske nayi sakaci kija Mana, muna lallabawa, kin hakura da Zuwa makarantar naji Baki ce komai ba?"
"Bani da say, sai yanda kace haka za'ayi".
"Nace A'a! in dai Ina raye da lafiya ta bazaki nemi komai ki rasa ba Koda kuwa faskare zanyi to zanyi na samu abinda zankula dake".ya fada Yana daukar luggage din ita Kuma ta nufi kan fridge inda ya ajiye key din jiya.
A jere suke tafiya sunyi wani irin dacewa wadda dole idan ka kallesu ka qara suna kokarin fita daga reception su Zayyan suna kokarin shiga, Mahmud ya kalla da jakar matafiya a hannu Yana rike da Hannun Zahra,.
"Kam bala'i"
Yaji Bakinsa ya subuce ya fada Yana matsawa baya Kamar yanda Ibrahim yayi.
"A sauka lfy" Ibrahim din ya fada shi kuwa Zayyan kamar an saka makulli an datse Masa baki.
"Ka bashi key din dakin ka biyoni mota Zan baka sako".
Ya fada Yana duban Ibrahim, mota Zahra ta shige ta barsu suna tattaunawa kafin ya shigo ya tada motar ya nufi get din fita har yabar harabar hotel din, Zayyan na lekensa ta window sai dai yasan idan yayi magqnar Nan da wani kwabarsa ce zatayi ruwa daya fesa labari, oga da rije jikar mace uwa uba yana tukata da kansa Kai wannan abin surprised da yawa yake"Ga bikin zuwa ne babu zani.
Tafiya yake da hanzari Dan ma safiya ce sosai titin ba yawan jama'a cikin Kan kanin lokaci suka shigo unguwar, Horn ya danna da karfi da gudu Mai gadin yazo ya bude yana fadin "barka da zuwa!"
Da gudu ya Koma ya dauko sakon dasu mama suka kawo jiya Yana fadin "barka da Asuba yallabai gashi jiya bayan futarku su Hajiya Babba sukazo suka bada a ajewa Hajiya".
Ya fad'a Yana risinawa Yana mikawa Mahmud ledar.
Saida ya karewa shi da ledar kallo, sannan ya hade gabas da yamma yace ka rika idan kana so, Kuma
Ka hade kayanka in anjima kadan binyaminu ze zo da Wanda ze canjeka aikin Nan adalci daya nayi maka ban koreka ba zaka koma share-sharen makarantar Yara kawai".
Jiki na tsuma Mai gadi ya durgusa Yana fadin "Yallabai me nayi haka da zafi Dan Allah kayi hakuri wlh baza'a qara ba ka rufa min asiri".
"Iya Alfarmar kenan bana korar ma'aikaci sai lefinsa ya Kai uku to Kai daya kayi ba tare da kasan laifi bane shi yasa nayi maka uzuri bazan rabaka da rufin asirinka ba dauki kaje yanzu Zan fito". Jiki ba kwari ya dauki ledar ya juya Yana ta faman tunanin ta ina ya kuskuro yallabai jiya lafiya kalau suka rabu yau Kuma ya tashi da canjin gurin aiki da Allah ma ya dube shi da Rahama daba Kora bace days shiga uku.
Suna shiga Mahmud yayi bed room dinsa ita Kuma ta nufi kitchen ta Fara hada abu marar wahala coffee ta dafa Masa sai sandwich kawai tayi shaf-shaf a tray ta Dora direct bedroom dinsa ta nufa ya fito daga wanka Yana goge jikinsa a ranta tace shi baya mura any time wanka kamar dangin kwadi.
Sallamar ta ya amsa Yana aje towel din dake hannunsa.
"Ke! Me kikayi daga zuwan mu ba dai abinci bane ko? Ni bana cin komai a irin wannan lokacin".
Langabe Kai tayi tana dubansa kasa-kasa har Zuwa lokacin wani nauyinsa takeji. Yana ankare da ita.
"Coffee ne fa da sandwich nayi maka Dan Allah kada ka tafi da yunwa,alhalin gani a tare da Kai ai da naji kunya daga zuwa ka nemi abinci a kanon".
"Inye ashe dai ana son mamudan?".
Ya fada yana nufar inda ya aje kayan da ze saka kananun Kaya ne na kamfanin Armani ya saka bako kunya ya cire rigar wankan ya tsaya daga shi sai boxer short, da sauri ta runtse idonta Dan Bata zata zeyi irin wannan abunba Yana kallonta ya basar yaci gaba da shiryawarsa, Zama yayi Kan sofa Yana umartarta ta kawo masa coffee din nan duka ta dauko ta aje gefensa ya dauka Yana sipping Yana kallonta tana Wasa da gefen veil dinta da ya sauko, sandwich din daya yaci ya yaji ya isheshi Shima Dan kada ya watsa mata kasa a ido ne, amma Sam baya iya cin komai a irin wannan lokacin.
"Zauna muyi magana" ya fada Yana dubanta,.gefen sofar tayi niyyar Zama ya tikota "Kinga gurin zamanki Nan ya dorata inda ya Saba..
"Zan tafi Baki San cikakken asalina ba, Zan fada Miki saboda sha'anin Rai da rayuwa kona dawo ko ba na dawo ba, Ni haifaffan garin sokoto ne iyayena duka biyun sunan Nan ni dangatan iyayena ne da kakata Hajiya Inna, suna Sona yanda Baki zato yanayin rayuwa ne ya kawoni nan, duk family na ba Wanda na fadawa labarinki sai kakata ta sanki a hoto tasan wasu labaranki, kota Allah ta kasance wannan dana Kira ya zauna yayi min gadinki sunansa zayyan na fada Masa ke matata ce ze sadaki da Family na, Dan Allah kiyi min Alkawarin duk rintsi bazaki juya min Bata ba, ki rike min aurena da Kima da daraja, idan Allah yasa na dawo Zan fada Miki koni waye da duk abinda ya shafeni na rayuwata Daman taki na sani ba sai kin fada min ba,
duk abinda kike bukata ki duba waccen lokar akwai kudi a ciki bangaren abinci Kuma nabar komai a Hannun Habib, ga Kuma kudin da Sameer ya Baki ban Baki ba". Ya aje mata su a akan cinyar ta.
Jin tayi shiru yasa ya dago fuakarta da hannunsa,kukan Zuci take ba wani sound sai dai hawaye"subhanallahi kuka dai? Kona fasa tafiyar nan kawai tunda Naga hankalinki yaki kwanciya da ita"
"Ba komai kaje kawai naji Kanata nanata maganar in baka dawo ba na sani ko idan ka tafi bazaka dawon ba".
Lakuce Mata Baki yayi "ai kece bazan dawo din ba, wannan ya shafa cikinta sai kin ajiye Mana babies a ciki idan naki dawowa aini nayiwa kaina, ki kwantar da hankalin ki nema zani ki min addu'ar samun nasara".
✨✨✨
✨✨✨
AUREN HUCE HAUSHI
Strory
&
Written
By
Maman Fateemah
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.