Complete Hausa Novels

Tantiriya A Gidan Yari Part 3 Complete Hausa Novel

Reading file: Tantiriya_A_Gidan_Yari_Part_3_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 1 of 20

[2/13, 7:56 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫
A GIDAN YARI

BOOK 3
~TAIMAKO~

1-5

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA GARE KI
AIDA MAMAN TASNIM

PAGE NAKI NE
MRS CHIEF

*ZINARIYAR MACE⚡*
*Wai shin 'yar'uwa menene matsalarki? zubewar nono, ko kuma rashin kwankwason juyawa a falo maigida ya shiririce ya manta da tibi da matan tictok, menene matsalarki ne? rashin ni'ima ko kuma mugun sanyin da ya yi miki katutu, shin rashin taushin fata ne ko kuma kuraje da tabbani, ko bala'in ramar da ta addabeki kuma babu rashin ci ba rashin sha a gidan auranki, gwaigwayewar gashi ce matsalarki ko kuma kaushi da faso na tafin kafa da bushewar fata, kina bukatar fatarki ta yi glowing kalarki ta fita kuraje su mutu, ko kuma kina bukatar azababbun turaruka da humra tare da turarukan wuta. Na san dai kuna da yawa matan da tumbi ya yi musu karan tsaye ina nufin ya katse muku hanzarin yi wa maigida gwalli da muskuce-muskuce a falo😃 Nesa fa ta zo kusa AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE sun tanadar muku da nau'in magungunan da suke magance kowace irin matsala da izinin Allah. Babban burinmu shine sha'ani na aure ya inganta a samu daidaito. Muna da.*
Na gyaran nono.
Na sanyi.
Dilka tare da hadin sabulu.
Duk Wani nau'in maganin mata.
Humra turarukan wuta perfumes, original miski tahra 3in1, ciccibi budurwar kaza. Had'addun supplement irin wad'anda ba su da matsala. Maganin Sliming wato narka tumbi. Abubuwan da muke sayarwa suna da yawa, kuma babu asarar dukiya. Muna garin kano kuma muna tura kayanmu kowane gari fad'in Najeria da Nijar har ma da kasashemn ketare. Kai tsaye a tuntu'bemu ta lambobin wayarmu domin karin bayani.
*08089965176*
*07084653262*

Washe gari Khadija wato Mero komawa tayi ta cikin dakin da take kokarin lallai sai ta fasa shi,tana zuwa taji sheshekar kukansa ta bangaren dakin da yake,yau taji wani a kusa da shi tayi mamaki Jin ana bashi hakuri,Yana cewa itace wacce zan aura shike nan ta rasu ta barni,Ido Mero ta zaro tare da dafe kirji da hannu biyu tace dama Yana da wacce zai aura ma ashe,ta rasu Kuma to Allah yaji kanta idan tamu tazo Allah yasa mu cika da Imani" shine yake wannan kukan kamar wani mace sabo da soyayya,shi yasa in ba dole ba me za ayi da me kudi Abu kadan Kuka ba juriyar wahala,talaka kuwa ba ruwansa ya Saba da kaddara iri iri,kasa hakuri tayi da karfi tace to a gobarar ta Kone?Wanda suke cikin dakinsa sun zaci Aljana ce tsoro ya kama su Dan su iya tsayin rayuwarsu basu taba Jin maganar wani ta bayan dakin wani ba bare mace ma.

Matashin magana yayi yace ae gobarar har da ita ta Kone,Mero tace sai ka daga Murya banji baaaaa.......tsaki ya ja da gajiyawa yace da karfi da ita gobarar ta Kone,Mero tace Allah yaji kanta tayi Mutuwar shahada,su dai mazan tashi suka yi suka fice basu yarda da mutum yake magana ba.
Khadija taci gaba da magana ka gama kukan ne? banza ya mata,kyale shi tayi taci gaba bula katangarta yau dai taci nasara ta bula Inda ya tsage yatsu biyu zasu iya shiga,idonta Daya ta manna a jiki ta leka taga dakin gashi nan dai wai a haka VIP ne,tace wani abin sai gidan yari.

Maman Wahida tana gidan yari yanzu Kam ta Saba ta zama Yar gari harkar gabanta take yi,iyalanta suna yawan zuwa dubata bata da matsala a vip take zaune,masu hali basa fadawa matsala,bata shiga harkar kowa indai ba a vip kake ba to tasan baka da gata ko kulaka baza tayi ba.
Mero bata San Maman su Wahida kanwar Mima bace tana dai ganinta kamar su daya da Mummy sai ta dinga mamaki, yau dai gaza hakuri tayi ta nufi wajenta da take zaune tana hutawa abinta.
Mero tana zuwa tayi Sallama sanye take cikin riga da skirt na wani tsohon Leshi Wanda suma Azima me kwana ba wando ce ta bata su Ganinta cikin tsumma,Mero tace Ina yini,Maman Wahida da kyar ta dago ta Kalli Mero Khadija Shekeke tace ya aka yi? Dan ma kin samu na gaishe ki ,na saki ki gaishe ni? Khadija tace na kwace gaisuwa ta ba Ina yini ba,dama kama kike da wata Mummyn Spark,da sauri ta Kalli Mero tace a Ina kika sansu kanwata ce uwar mu Daya uban mu daya,Khadija tace da Mima,da Rafeeq,Misam duk ba wanda ban sani ba a cikinsu,Sai lokacin tace zauna,Khadija tace uhm da kika ji nasan Yan uwanki to ni ba me kudi bace shara da wanke wanke nayi a gidan Mummyn Spark,Kuma rannan Spark yazo wajena.

Maman Wahida tace Spark din yazo wajenki? Mero tace ai shi bashi da matsala shi yake bani kudi da komai,amma ni Ina a matsayin kamar uwarsa ya kasa zuwa mu gaisa,Mero tace laifi kika Masa watakil ai ku halinku sai addua kwana Nan Yar uwarki zata zo ku hadu ku zauna kuyi ta zumunci,Mummyn Spark kwana nan zaki ganta a gidan nan,Maman Wahida tace ubanwa ta kashe ke karki jawo mana masifa a dangi,Azima ce ta fito tana rangwada tace Khadija yau baza kije sakar bane? zanje mana muje to,Khadija ta mike tabi Azima suka wuce Mero tace ke Azima karatun Nan da kyar nake ganewa kin San ni dakikiya ce gwara ma na addini Ashe haka ake wankan tsarki,na dade Ina haukata ban sani ba,ai sai jiya na koya,Azima ta dinga dariya tace gaskiya Jahila ce Khadija,Mero tace ta karshe ma, Gani da suna me dadi me asali amma ban gaji me Sunan ba gaskiya iyayena sun cutar Dani yanzu a gidan yari nake wayewa Kai duniya,ni Kuma a gidan yari nake Ilimi Ina wani zama Yar birni,Azima tace gashi Nan kin koma Yar birni na gyaraki tsaf,rashin kunyar ne har yau baki fara gogewa ba Dan Allah kiyi ki koya ki karasa cika sharudanki na gidan yari,ni kin ganni idan na fita a gidan yari duk Wanda ya aureni ya aurarwa kansa tsiya shi yasa bama na so na fita ni karshe ace nayi aure Kuma ni ba Wanda ya isa ya sani ko ya hanani.

Mero tace uhm Azima ke kam ai baza ki fita bama sai kaddara tunda laifinki ba sharri a cikin,Azima tace thank God nayi nadama ni wlh na Saba da zaman gidan nan ko gida na koma ma bazan ji dadi ba,Mero tace gashi mun hadu wai Azima kin San su Chika da Beauty,Azima tayi dariya tace daina tuna min su,ke gidan da kike aiki baki yi dace ba wlh wasu Yan aikin suna dace acan suke samun Ilimi amma suka barki a Jahilarki Khadija,Mero tace su ai Yan boko ne da karatun Boko suke aiki na addinin suna da shi dai dai gwargwado amma sun manta ma kudi da duniya yasa sun manta ma da wani Ilimin addini bare su koyawa wani,sannan duk talaka baida daraja a wajen su ta ya zasu koya Maka Abu suka San ma me kake ciki bare wacce nake gidanta a cikinsu itace ma tafi kowa lalacewa.

Azima tace itace Danta yake auren Naila Inye lallai Naila tayi prison mijinta yayi prison ga uwarsa zata yi prison su uku rigis duk prison sai kace gado,Dariya suka yi Mero tace gashi nima daga zuwa aiki gidan na fado Ina tsoron Naila karta haifo Dan Birsina,karasawa suka yi Inda ake koya musu sakar,Azima ta wuce bangaren nata ta kayan Sanyi ita kuwa Mero bangaren mificin sarakuna irin na fadar sarki masu kyau da tsada su ta iya,tayi mugun iya saka su tunda tazo ta koya,gashi in sun saka baza a basu kyauta ba sai dai ka siya in kana da kudi,Mero sai da ta siyi biyu wai sai ta yi kyauta.

Bangaren su Malam Jilani suna zaune Dan Indo ya shugo idonsa jajir yace kai akaramakallas gaba dayan ku Jiya Mafarkin Jamilu nayi ya dawo gidan nan,Malam Garzali ya tuntsire da dariya yace wai Dan Allah baza ka manta da Jamilu ba,tayi aure ance tuni,Dan Indo ya jawo tarkacen kayan Naila data bari ya kalle su,ya daga wani katon bujen wandon ta ya furta Allah sarki duniya yanzu wannan Jamilu ta saka shi,Malam Jilani Yana boye dariyarsa yace Matar wani ce dai yanzu,haramun kake aikatawa,Dan Indo yace Allah ya tsinewa yaron nan Spark,zuwansa ba alheri bane ya cuceni,yanda nake Son Jamilu na tabbata baya sonta haka,duk sanda na sake ganinsa a gidan yari ko ziyara yazo sai ya yabawa Aya zakinta,Malam Jilani suna ta dariya,Dan Indo ya sake Jin Haushin su yace ai kune manyan munafukai dama karya kuke Kun San macece shi yasa kuka riketa a dakinku,Kuna fakewa da karatu Yan iskan banza Yan iskan wofi,Malam Sharu yace mu mene namu a ciki yaro dai Jamilu da hannunka kayi Masa hanya ya bar gidan Nan sabo da haka laifinka ne,mu karatun mu muke da addua,ai ba karatun Allah kuke ba ya ja tsaki ya fice.

Schola ne ya tare Dan Indo yace ya akayi ne Dan Maza? Dan Indo yace jiya mafarki nayi Jamilu ya dawo gidan nan,Schola yace wai Jamilu Terror? yace ae,dariya Schola ya dinga yi yace tab sai akace Maka gaskiya ne sannu waliyyi to Kai da Jamilu har Abada tana can tana ta Shan madarar Nido yanzu haka ma an samu Rabo ka samawa kanka lafiya ka hakura,Kaga ni na tafi wajen kawata Khadija nasan anjima kadan zata bayyana a Jikin katanga mu Sha hira Ina dalili ka likewa mace daya,Jamilu ai ya zama old version,ga new Version latest Khadija Ina laifi kana Jin Muryar mace ma a'a mu munyi can" ya wuce yana rangwada.

Wata Majalisar ce guda suke kafata a wajen sabo da Mero tana zuwa ta Jikin wajen suna Jin Muryar mace,Mero da Azima suka zo ta wajen Mero ta kwala da karfi Salamu Alaykum harda rige rigen amsawa,Goje yace Kai Muryar mace duniya ce wannan yarinya Allah ya mata albarka tana kwantar min da zuciya tana sani nishadi,rabon da naji Muryar mace tun Jamilu Tantiriya tana nan,Mero tace Kai Yan Maza har naji warin ku na gardawa ta nan,irin na ubanki cewar wani me Suna Balarebe,Mero tace Ubana Yana can Babata ta takura Masa shine ka zage shi ai abin yayi Masa yawa Allah ya isa,Ina ma zaki iya shugowa gidan nan bangaren mu,Mero tana dariya tace uban me zan muku in na shugo,Schola yace madarar Nido za a Baki iri iri harda me bulkodi ahayye ni dai Allah ya tsare ni neman Yar uwata mace,Mero da Azima suna ta dariya,Azima tace wayyo gashi bana kwana da wando,Goje yace ku jefa ni ciki Dan Allah,I love you a jefa ni ciki,Hanif ne yazo wucewa ta wajen yaji suna ta ihu da dariya,da izzarsa ya dan tsaya yaji Muryar Khadija ta daki dodon kunnensa tana cewa a gidanmu ga shimfidita ga Kaza taka kyankyasar 'ya'yanta a kauye,ni fa a birni na koyi tsafta a gidanmu sai mu gama wanke wanke mu wanke kafar mu da soson wanken Kwanon,su Goje suna ta dariya sabo da Fadi ba atambayeka ba din da Mero ke yi kullum sai ta fada musu abinda suke yi a gidansu na kauye.

Balarabe yace tab Allah yasa bakwa abincin siyarwa,Mero tace cab ai kuwa wallahi muna yi awara da Koko,tsohon dankwalina babata ta dauka da shi take tace gasarar Koko da awara,har skert dinta na ciki mun taba amfani da shi,Schola yace wayyo kunya ku matsa na boye kaina ni Schola Ina zan sa kaina Yar uwa tana ta bankada,Goje yace to ke Khadija baki da kanne ne? Me kace bana ji sai kayi da karfi,da karfi yace Baki da kanne? Mero tace daga ni sai kanina Yana kauye wani Dan banza shashasha nake ganinsa yanzu Kuma a haka sai kaji watarana wata har kasa bacci zata yi a kansa Allah ya kiyaye wacce taso kanina Muneer tayi asara,Azima tace ke muje dalla lokacin makaranta Kinga ke kike koyon Addini muje ko Kya samu ki daina wannan iskancin zancen naki,Dan Allah karku tafi cewar Muler muna Jin dadin mu kamar mu rungume ku,Mero tace wayyo Dan ma Baku ganni ba,Goje yace Allah? tace Allah da kunji a cike muke kamar ana bamu kaji,Goje har da dafe Kai yace Kuma fa da gaske ne Yana magana da sauran mazan,Hanif kallon su yayi kawai wani takaici ma ya kamashi mene abin dadi a nan,yace gaskiya ku Baku San ma mene abin dadi ba,Goje yace Kai ai sabon zuwa ne baka wani Dade ba shi yasa kake fadar haka da ragowar turirin mata a jikinka ka shugo bai gama barin jikinka ba shi yasa,ka kyale mu Muji dadin mu,Hanif yace Goodluck,Yana kudu Dan uwarka Yana Niger Delter, Goodluck ma ya sauka daga mulki karewa cewar Schola Yana ta faman cakaki,yace tun yaushe nake binka Ina naci Ina sonka ka zama budurwa ta kaki yarda wai Kai me tsafta shine yanzu zaka zo ka takura mana, Kai kudin naka ma ba kyauta kake ba, tunda kazo gidan Nan sai girman Kai sisinka ba Wanda ya taba ci,Hanif yace Allah ya kiyaye irinka Dan neman takashi yaci kudina,taka dai da alama baza tayi haske ba tunda dai ba irin mugun farin nan bane Kai ato farar takashi sai Spark,dariya Hanif yayi yace ko waye wannan Spark din oho da an tashi gori da shi ake kwatance.

Sai dare Mero ta gama surutunta zuwa dare ta koma dakin da bama a shiga Inda ta fasa,Hanif an kawo Masa take away hadadde da nama Yana ci Yana ta jira yaji muryarta sabo da da ta Saba zuwa Yana Jin surutunta Yana samu Dan sauki a ransa,sallama tayi ya amsa da kyar,tace me kake ci ne? yace nama,masu kudi Allah ya Kara budi,Ameen ya furta yace ba waje da na San miki,tace ga kafa dinga sako min Yan siri iri ta wajen zanci haka,yace to ya mike ko wanne Yankan nama sai ya raba shi gida uku ko hudu sannan ya samu ya Dan turowa Mero kamar wata tururuwa ta karbe ta cinye Kuma.

Naila ce ta fito tana rike da mara tana Nishi ta samu Spark a palon sama Yana kallo tace wash Allah Baby wayyo marata,zan mutu ta durkushe a wajen tana murkususu,a firgice Spark ya mike ya rike Naila yace me ya faru? Yanzu naji ciwon mutuwa ne wannan, Spark ya rude ya dauketa da sauri sauri suka tafi asibiti,Naila tana kuka tana bige bige a mota da kyar ma ya iya driving.
Suna zuwa aka karbeta aka fara bata agaji,sai da aka Dade Sannan mace Likita ta fito ta samu Spark hankali a tashe Yana jiran amsa meke faruwa.

Likita tace Sir Alhmdllh taji sauki amma kayi hakuri ciki ta samu baifi 4weeks ba Kuma ya zube,Spark yace ke likita ance bari yafi nakuda azaba kalau matata take? Indai matata kalau take shike nan Dan ciki taje gobe ma nayi sabo,dariya ya bawa likitar tace kalau take yace to Alhmdllh nan da jibi ma zan mata sabo Inshaallah,yanzu me ake bukata? Likita tace ai tafi karfin Pad sai dai pampers babba ake siyawa matan da suka haihu ko bari,Spark yace ban gane ba nufinki yanzu Jinin jikinta zubewa yake baku da hankali kuka ce kalau take,Likita tace ya gama fita cikin amma ai dole zata danyi jini kafin a samu ya dauke a hankali duk abinda ya dace anyi,Spark yace nifa shi yasa bana son matter din Nan ta ciki-ciki,ya fita yaje ya siyo abinda tace ya kawo mata,ta bawa nurse Dake asibitin kudi ne ko ba Yar jinya akwai masu yi.

Naila jikinta ta gyara ta shirya ya kawo mata wasu kayan ta canja ta fito kamar ba ita ba fes,waccen kayan Kuma data cire sabo da wadata sai tace ban taho da me wanke min ba ni na bar miki ko ki zubar,sai da ta fito Spark yace Ina kayan da kika cire? Ni wlh bazan iya wankewa ba na barwa nurse in bata so ta zubar.

Spark yace kut kayan da nake so nace dinkin Yana miki kyau yau fa ni nace ki saka su shine kika bayar wlh ba Yar iskar da zata saka,Naila tace sun baci fa sosai,yace ma wanke,sabo da baki San zafin nema ba in siya miki Abu me tsada kice a zubar kin San nawa ce atamfar? Kudin banza gareni,Naila kuka ta fara Dan kar a karbi kaya tasan halinsa ba kunyar uban kowa yake ji ba,kaina Yana ciwo kana ta min fada,Spark ba yanda ya iya yace sorry muje amma indai naga Nurse din nan sai na kalleta tunda ta sa min kaya ta shiga uku kurwata baza ta kyaleta ba,Naila tace ka kalleta Kuma? Tace kwarai ai asibitin nan sun shiga uku sun dinga ganina kenan,juyawa Naila tayi ciki da sauri tace Nurse kiyi hakuri ki bani kayana mijina yace bai yarda ba,Nurse tace ba komai gasu ma an zuba su a Leda in kinje gida Kya wanke,Naila ta karba ta koma mota a boot ya saka ledar kayan suka tafi gidan da magungunanta,suna zuwa gida ya bawa me aiki yace a wanke su tas in anyi normal da hannu a zuba su a washing machine tace to tana ta yiwa Naila sannu gata babba dama tasan komai

Tana gamawa ta hadawa Naila ruwan wanka ta gasa jikinta tayi wanka sosai tare da gyara kanta sannan tazo tayi kwalliya cikin wata fitted gown ta Leshi brown,abinci taci ta koshi Sannan ta Sha magani ta kwanta ta hau kiran waya Hello Ana gaisawa zata ce wlh bari nayi yanzu amma da sauki Alhmdllh mun dawo gida, kowa sai da ta fada Masa tayi bari,Spark ma haka har da kiran Mima yace Naila ce tayi bari, subhannallah Kuna asibiti yanzu? ai Abin yazo da sauki kalau take muna gida,to bari muzo cewar Mima.
Kafin wani lokaci gidan Spark ya cika da Yan Uwa su Chika,Ikhram duk sunzo,Naila ita barin ma sai murna take kamar wacce ta haihu,sai dare daga Chika sai Ikhram a gidan,Naila tana tsakiyar bed suna ta hira Spark ya shugo bedroom din,zama yayi a gefen Naila ya kalleta dariya ta bashi yanda take faman murna tayi bari,Chika tace wai korar mu zaka yi ne ai ka jira mu tafi kana babban Yaya Sam baka yin yayan Kai,Spark yace wai Yaya manya da wa zanyi wani Yaya wannan Dan iskan mijin naki da ya fini duniyanci,Arham ne ya shugo yace Chika ance ku fito na kaiku gida,Aunty ya Jikin? Naila tace Alhmdllh da sauki,Spark ya kalla yace Yaya Allah kawo wani da wuri,Spark yace a'a ba yanzu ba ai yanzu sabon Ango zan dawo,Naila ta zaro ido,Chika tana jinsu tace Kai Arham dan Allah muje"tafiya suka yi,Naila tace bari nayi wanka Yau bacci har da makara,Murmushi Spark yayi tare da furta zaki murmure ne dole na kwalbe,Naila yau dai bani da amfani ba mamora a jikina sai ayi hakuri Kuma,Spark yayi murmushi kawai.

Annoor kuwa Iman tunda ya samu ta dawo sai da ya lallabata da asuba ya sake Kwalbewa,Iman duk tayi zuru zuru da ita,abinci ma sai daga gida ake kawo musu ai kuwa ta Sha Allurai shine samun saukinta ma.
Iman yini tayi a kwance Bata iya tafiyar kirki sai zuwa yamma da ta Dan ji sauki,mayen Yana gefenta kamar zai cinyeta tace zan danyi tafiya dan Allah ko naji sauki,Annoor ya mike Yana murmushi abinsa shi duniya sabuwa,hannayenta ya rike a hankali ya mikar da ita tsaye harda cewa sama da ikon Allah,dariya ta fara tana dukan damtsensa Shima dariya yake cike shaukin so,ya riketa Yana koya mata tafiya a hankali,Hannu ta yarfe tana cije lips yace daure,ture shi tayi tana murmushi ya fada Saman bed,fadowa tayi kansa tare da sakin Kara,yace sorry tashi aci gaba ya sake riketa suna tafiya a hankali Yana ta faman tsokanarta,yace wai Ina Sunan da kika Sa min na love kin daina fada yanzu,Iman tace ai yanzu ranka ya dade kake wa zai ja da Kai,me gida ran gida baki aka fiku ba aiki ba,kune gaba da mu,yace wash Annoor ka kashe ni,murmushi tayi tace ka daina please,gwara ma ki bar fadi bazan daina ba.
Bangaren Nabeel kuwa shi jinyar Yar matarsa yake sosai kuda baya so ya taba ta,sai bakinta da ya bude sosai tun a ranar surutunta ya baci bata shuru Hidaya,ita first night din kamar an bude mata baki.

Naila ce ta kira Umma ta sanar mata tayi bari,Kubra tace Allah ya sawake ya kiyaye gaba,tace Ina Abba? Zaraf Abba yace gani Ina jinki bari kika yi Ashe to Alhmdllh yafi babu akan ace ko bari bata taba yi ba gwara ace ta taba bari ai Kinga ana sa rai,Naila tace hakane Abba kamar Dan kadangare,Abba yace ke Zubaina sati hudu ai jini ne Ina ya zama kamar kadangare din,Naila tayi dariya tace ai a haka na gane,Abba yace a'a ba da bane gaskiya gudan jini kika gani idonki ya rufe,Kubra tana jinsu Abba yace tunda lafiya kike ai anyi arziki duk wata karya ki ajiye abarki gefe Naila Allah ya baki wani ni kaina na matsu naga kin min jika wlh ki dage tun kafin Dara taci gida na fara miki gori da kaina don kuwa na gaji da Kara da kawaici na kusa fara gori,Naila tayi dariya tace Abba da kanka,to ni dai Kinga na haihu bare ace tunda nayi gori hakki ya kamani bazan haihu ba Nima da yarana,na kusa gajiya zan fara yi muku gori ke da mijinki,Naila tana dariya tace Abba Yana jinka.

Ta zaci Abba kunya zai ji sai yace bashi wayar ma,ta mikawa Spark Dake gefe Yana dariya Yana Jin Abba,ya karba suka gaisa, Abba yace wai Kai aiki ne yayi Maka yawa ne? ya kamata ka dauki hutu ka samu nutsuwa ance rashin hutu ma Yana hana haihuwa,na gaji da halinku ka zauna ka binciki Naila Anya ba wani Abu ta Sha ba Bata San tana da ciki ba ta gantalar da shi,Spark yace to ya mike zai bar wajen Naila ta rike shi Kam tace wlh ban yarda ba a gabana zaka gama wayar Nan ka karo volume,Spark yaki karo Volume tunda ya rage volume sai da ya gama wayarsa sannan ya kwanta abinsa a gefenta Yana tambaya yau tun safe me da me kika ci?Naila tace abincin da Kaci,wato Abba ne yace ka tambaye ni ai na gane ka.

Washe gari Abba ya bude shagonsa na kayan masarufi harda tiles yace saura katifa,takanas ya siyo katifa Yar Siririya ta Yan makaranta ya saka a can gefe kullum Yana Kai ko a zaune ko a kwance kowa in zai wuce Yana kallonsa ai ta sheka dariya shi kuwa ko a jikinsa yace kanku ake ji bazai yuwu Basir ya kashe ni ba akan Ina so gidanku a tuka tuwo sai dai idan kar a siyi Masara ta.

Rafeeq yau Mima yaje gaisarwa ya samu Arham gososo yayi matashi da cinyar Mima,Rafeeq yace Kai mene haka? Arham yace Kai kaje ka hau ta matarka mana ai kana da ita ni ka barni na hau ta Uwata ni wlh Mima da zata ci gaba da shayar Dani tsaf zan koma baya,Mima ya kalla yace Dan Allah ki Sha ruwan kaikayi su kawo,Rafeeq yayi dariya yace to ke Mima kinji danki shi yasa ya Raina ki Kinga irinta,Mima tace Kai dalla rufe min baki sanda muna talaucin mu kazo ne gudun mu kuka dinga yi sai yanzu zaka dame mu,Arham yace ai yayi mata yanzu ya daina lagawu da baki wlh da a baya ne da yanzu ya mana batsa,Dariya Rafeeq yayi yace yanzu kuwa nake batsa yaro kawai dai an daina yi a gaban ku baku da kunnen ji me kunnuwan ji tana gida,Arham yace muna ji mana me zai Hana ai mu muna Jin dadin wannan batu,Mima tashi tayi ta cire takalminta ta Kifa Rafeeq da gudu tana zage zage,Rafeeq ya shige bedroom tace zo ka tafi gidanka wlh,Mummy tana zaune tana faman kallon takadar sammacinta ta kotu,Arham ya kalleta suka hada Ido bakinsa ya danne da hannu Yana faman dariya,Mummy ta kalle shi tace Kai dan Uwarka da wa kake? Yace ba fa dake nake ba ni,wai Ina Alhaji Baseeru ne? Ina ma kin samu ciki abinki,Mummy tace Dan iska shege ba Yana can Dan wahala,kamar ni zanje bikonsa don a San ya za ayi ko wani auren nayi na fito ya sake aurena wai shi a baya ma kaddara ce dama na Masa tsufa Mamansa ce ni,Arham ya boye dariyarsa yace gaskiya bashi da mutunci duk garar da ya kwasa,Mummy tace ai ya manta,Dan Adam butulu cewar Arham,Mima ce ta fito tace kin biyewa Arham kina Hira Yana ta zurma ki wannan yaran akwai na dauka ciki tashi kaima ta fatattaki Arham Shima.

Shaheed ne ya dawo Yana shugowa tace juya kasan Inda dare yayi Maka,me nayi Kuma ni daga dawowata school fa naje,Mima tace kasan Allah wlh zan fadawa Papan ku,ka wuce part dinku kawai bana son magana,Mummy tace yawwa haba yara duk sun addabi mutane,Mima tace wlh ni da zasu samu mata ma duk a musu auren yafi min ai sun Isa,Shaheed ya fara murna Yana Shoky ahh Shoky ai bamu sani ba ni wlh a daura ma data Annabi,ko wace a bata ni sadaka 9mnths sai jikoki ta ko Ina,Junior ne kawai Bai Isa aure ba cewar Mummy,Shaheed yace ku bashi yarinya ku gani a kulle su a daki wlh sai ta haihu,Rafeeq ne ya fito yace daga zuwa gaisuwa ni ku tsaya na fice na tafi ya lallaba ta gefe ya fice,Shaheed ma ya tafi abinsa Yana murna ance za a musu aure.

Hanif Usman Dan asalin Adamawa ne,Fulani ne gaba da baya,tun Yana dan 3yrs Babansa ya rasu sai mahaifiyarsa a gabanta ya taso ya girma ta tsaya Masa yayi makaranta har masters a kalla zai Kai 33yrs,kyakyawan matashi ne na gaske,fari ne amma ba irin Kal Kal ba,Yana da dogon hanci,bakinsa dan daidai ne me kyau,hakoransa masu matukar kyau haka idanuwansa,Yana da yalwar gashi baki wuluk me kyau,shi bai cika tsayi ba Kuma dole a kira shi da dogo,komai na Hanif me kyau ne,haka gashi ko wanne sutura ya saka sai ya zuba kyau ta amshe shi,baida hayaniya sannan ba a fiye fada da shi ba kawai harkarsa yake, har Mamansa ta auri kanin babansa suka yi Yar gida,bayan Alhajin nasa Yana da mata da yaransa biyar amma duk mata ne Kuma duk an musu aure a yanzu suna da yara ma ko wacce.

Hanif tunda ya taso yake da kashin arziki Ya fara aikin gomnati Yana kasuwanci sai kasuwancin nasa yazo ya danne komai,kudin da yake samu har da na hauka ma Allah ya sa Masa Albarka,Yana da kudi matuka sosai,Business dinsa yafi karfi a Kano state a Nan ya kera gida na karshe a GRA Yana zaune shi kadai iyayensa suna Adamawa da dangi,Yana da kadarori sosai matashin me kudi ne.
A Yan uwansu Adamawa akwai wata Khairat wacce Alhaji kanin babansa ke riketa,tun tana karama Hanif yake son Khairat kamar ransa,wacce Kuma a sanadin gobara data kama gidan Umminsa wato gidan kanin babansa tayi ajalin Khairat wacce ya Sha kuka kullum a cikin damuwa yake sabo da ita.

Dalilin zuwansa prison kuwa a cikin Yan uwansa ne bangaren Umminsa mahaifiyarsa ta samu Dan gidan Yayarta wacce ta Dade da rasuwa ana ce Masa Sudeis zai Kai 25yrs ta turo shi Kano wajen Hanif akan zai koya Masa business zai Maida shi yaronsa,kaddara tasa satin Sudeis biyu aka neme shi aka rasa daga fita kasuwa ba a sake ganinsa ba,Hankalin Hanif ya tashi matuka sabo da a gidansa yaron yake zaune Kuma wajensa aka turo shi,dangin uban yaro suka ce baza su yarda ba dama Hanif Dan mafia ne kudin mafia yake da su matsafi ne,iya nema da cigiya an rasa Sudeis,Uban yaro ya Kai Kara bazai yarda Wanda aka kama Hanif aka tsare shi a prison bangaren Wanda ake tuhuma ana sauraron kararsu,Alkalin ma nasu yayi tafiya yaki dawowa shi yasa har yanzu ba a yanke hukunci ba,Yana Nan a ciki shima kamar Mero basu San zaman da suke ba.
Umminsa da Alhaji suna zuwa ko yaushe sannan Hanif abinci me tsada ake kawo Masa kullum,haka sutura da komai nasa classic ne,kana ganinsa kasan babu maganar wahala a tare da shi,shine Kuma Wanda Mero take kallo a TikTok tana sonsa.

Khadija Sani Uba Mero kenan Yar kauyen Kano ce cikin wani kauye dake Danbatta,Khadija su biyu Iyayensu suka Haifa,Khadija itace ta farko sai kaninta Muneer,Babar Khadija Bata da tausayi gata da masifa kamar me Wanda ba boka babu Malam ta mallake mijinta sai abinda tace kasancewar Sani shi wani gashi nan ne dai sanyin Hali ne da shi sai abinda aka ce da shi,duk Inda akace Yayi to Hakan zaiyi kuwa,bashi da gidan kansa,Yana kallo tana cutar da yaransa ba karatun addini bare na Boko sai talla da aikatau baya so amma bazai iya magana ba,komai tace an gama kawai.
Gashi duk Inda zata je kamar jaka sai tace sai ya rakata idan da kayan shi zai daukar mata har Inda zata je kawai umarni take bashi,Kuma shi zai fita ya Nemo,banbancinsa da su Abba Dolo shi Yana da zafin nema amma Kuma sai abinda aka ce da shi,matarsa Hajiya Jummai ta hanashi rawar gaban hantsi ga masifa,su Khadija haka suka taso suka ga tana yiwa ubansu,taci kwalarsa ta zazzage shi ba abinda zasu iya.

Yau ma gidan ya shugo ya Kai wani gero kasuwa Yana dawowa ya fito da kudin ya zube mata a gabanta yace gasu ki duba kiyi abinda ya dace ni na dauki dubu uku ciki,Baki ta bude ta ajiye tire din dake hannunta gata kyakyawa da ita sai masifa,tace ban gane ba akan wanne dalili zaka dauki dubu uku zube ka dauki dubu daya ta isheka,Muneer Yana zaune Yana cin tuwo yace haba Inna mutum da amfanin gonarsa ya siyar duk ya Baki kudin akan ya dauki dubu uku shine zaki ce bazai dauka ba,Kai rufe min baki ko nazo na taka wuyanka,Sani Wanda suke kira da Uba yace kyale a bata Muneer ba komai dubu dayan ma ta isheni" ya dauki dubu dayansa kawai ya koma dakinsa ya kwanta.
Zuwa yamma ta fito zata je gidan suna ta gama shiryawa tace Sani fito ka daukar min kayan barkar nan muje,haka ya fito ya karbi Yar ledar suka fice da yadinsa brown ishirunka maraya,ita Kuma ta Sha atamfa blue da hijab,suna tafiya suna Hira sai kace wasu matasa,abinda take so ita kenan duniya ta San ta mallake mijinta sai abinta tace,ana ta gulmar su ita kuwa tana Jin dadi,yace yaushe zamu je wajen Khadija ne? tace sai an siyar da Masarar da zata zo kwana nan,kasan kudin mota tsada rayuwa tayi tsada.
Yace ke da yarki kamar ba ke kika haife ta ba,fuska ta bata ya ja bakinsa ya tsuke Yana tsoro,nesa da ita ya matsa Yana tafiya tace dawo wannan hanyar,yace ta Nan tafi sauri mubi ta nan,to bazan bi ba ta nan nake so" haka ya dawo Inda tace suka ci gaba da tafiya.

Yau abokin Sani ya gaji ya sake dawowa har gida ya kira Sani,yace gaskiya ka canja hali abinda kake yi Sani a garin Nan bai dace ba Sam,ace mace ta Maida ka kamar Rakumi da akala wlh mu Maza bama Jin dadin Hakan Sam,ka duba yau fa wai gidan suna ka rakata,Sani fuska ya Bata yace Dan na raka matata laifi ne? Shi yasa ku mutanen kauye har kullum Jummai take fada min na fita sabgar ku baza ku waye ba,tace dama na daina kulaka nine na nace nake Maka alfarma,amma mene aibun Hakan? Ko Jummai ta fada min tace a Makkah ma haka ake yi karewar garin addini kenan haka Maza suke wa matansu,to Kai Sani Balarabe ne ko al'adarmu Daya? Koyi nake da su karku dameni Kuma duk Wanda ya zageni ko yayi gulmata da gulmar Iyalina ban yafe ba,Abokin Sani ana ce Masa Malam yace yanzu yau fa har hannu ka rike mata a titi haba yara suna kallo ba tsari,matar tawa Dan na rike mata hannu koyi nake da Larabawa ko a gaban yarana na cikina zan rike mata hannu,baya ga haka ma ba yin kaina bane itace tace na rike mata shike nan bazan yi ba sai na watsa mata kasa a Ido.

Tayi min komai na gidan ta tuka min tuwo na ci da yarana Dan kawai tace rike min hannu Sani sai na kasa sabo da ni Dan iska ne ko me? Ko a garin Fir'auna aka haife ni,karku sake shiga harkarta da iyalina,gaisawa dai mu gaisa amma Banda shiga lamarin auratayya ta,gaisuwar ma ba dole In Kuna ganin da matsala ku kyaleni,amma ni sai me Dankwali sai abinda Jummai tace yawwa.
Malam yace Allah ya ganar da Kai,yace Ameen ya shige gidansa
Yana shiga gidan ya kwashe zancen ya fadawa Jummai,Jummai tace ai na Dade da fahimtar Malam munafuki ne rabu da su makiya mahassada.

Chika tana zaune a Palonta ta mimmike Misam Yana mata tausa sabo da tana da ciki,sai langabewa take tana Nishi,Me unguwa Maman Chika da Baban Chika mahaifi ne suka zo,Chika tayi mamaki babu Sanarwa,Misam ne ya bude musu kofa suka shugo Sanyi da kamshi ya daki hancin su,Chika tana ganin Me unguwa ta hade rai tace me ya kawoka gidana,Abban Chika yace Suhailat bana son shashanci ki nutsu,Misam gaida su yayi a mutunce Yana musu sannu da zuwa.

Chika ta zauna ta hade rai ganin Me Unguwa,Mamanta ce ta kalleta ta Harareta sannan ta gaishe su ta mike taje ta kawo musu kayan Sha da ci tace kar wannan ya sake ya Sha min lemo na,Kin San Allah zan Saba miki me yasa bakya ji ne,Misam ne ya mata rada yace calm down su Abba ne fa,Abba ne yayi magana yace dama Me unguwa ne yayi nadamar abinda yayi yazo baki hakuri akan ki yafe Masa,bazan yafe Masa ba kuwa sai dai a bar shari'ar nan ayi ta a gaban Allah.
Abba ne ya share Suhailat ya Kalli Misam yace Kai nasan kana da hankali,Suhailat da kake Ganinta bata Jin magana,ni na haife ta amma nasan halinta sarai,lokacin Ina auren babarta Ashe Me Unguwa tsohon saurayin Maman Suhailat ne" to ni ban sani ba Ashe haushina yake ji na kasa shi na aure Masa budurwa,tunda na aureta ta haifi Suhailat yarta ta fari kenan muna zaune lafiya ashe me Unguwa shi kullum budurwarsa tana ransa burinsa ya kashe mata aure ta fito ya aure ta.

To bayan Suhailat ta girma ta Kai 13yrs Bata sake haihuwa ba,da ta samu ciki sai bari,Ashe Me unguwa ne yayi mata asiri ake zubar da cikin bamu sani ba,karshe da yaga dai baza ta fito ba sai ya hada baki da wani ya bashi kudi ya shiga dakin matata da dare lokacin tana kitchen ni Kuma na shiga Ina shiga na iske Kato a kan gadona na sunna a tube zigidir,kuskure na banyi bincike ba sai na saketa saki uku,ta koma gida katsina kenan Inda Me Unguwa suke dake duk unguwar su daya,da Suhailat ta tafi,cikin ikon Allah data fito shima bai aure ta ba sai ta auri wani,daga Nan ya fara Jin haushi Yana binta da sharri,ita Kuma Suhailat haushinsa take ji Yana son uwarta tunda taji Labari.

Ganin bai samu uwa ba sai ya dawo kan Suhailat tsofai tsofai wai ita yake so,tayi tayi ya daina kulata yaki,sai sharri ma da yayi mata duk abinda ya faru sai yace Suhailat tana ciki,Kullum tana wajen Yan sanda,karshen sharri wata yarinya aka tsinta a bola an mata Yankan rago,me Unguwa kiri kiri kiri yace yaga Suhailat da idonsa da mutane sun sauke yarinya a mota karama,ya kira Yan sanda ya bada rahoto kawai bata San zance ba aka kamata Kuma ya dage da hadin bakin wasu dattawan na unguwa tsofaffin banza sai da aka kaita gidan yari bada hakkinta ba,sharri ba Wanda baiyi mata ba,yaje ya bada shedar zirrrr a kotu,gashi yanzu Yana dana sani da nadama,Misam Yana gama saurara yace ahhh da gaskiyar Suhailat a bar sharia sai a lahira

Me unguwa ya dinga rokon Suhailat da kyar da lallashi Chika tace ta yafe Masa a haka ma dole aka mata,Maman Chika ta furta idan Allah Bai baka abu ba duk duniya ba Wanda ya isa ya baka,Me unguwa ka cuceni ka kashe min aure Kuma da na fito ban aure ka ba shine ka koma kan 'yata itama Allah baiyi ba sai da ka kulla mata sharri,wani mutumin babu amfanin saninsa a rayuwa wlh,Me unguwa kansa a kasa yace a yafe min sharrin shedan ne inshaallah zan gyara Halayena,Misam shi dai tunda yaji ance ai ya taba cewa Yana son Chika sai haushin Me unguwa yake ji ya matsu su tafi,Chika ya kira bedroom ya bata hijab yace ungo saka ga tsohon saurayinki nan matsiyaci Dan iska tsohon banza tsohon wofi,ai a haka zai kare rayuwarsa azzalumi wlh na tsane shi tunda yace Yana sonki ni da shi gaba har mutuwa,Chika tayi dariya tace Dan ma baka sani ba lokacin ya zaci bani da wayo naje wucewa watarana ta kusa da gidansa da dare ya taba min duwawu,ai kuwa na saka kuka naje na Kai kararsa sai da aka mana tsakani.

Misam ya rike baki yace fyade zai miki ai da haka ake yin fyade ni kiyi sauri su tafi suma su mama mene na zuwa da shi ko ta waya ai a yafe Masa,Hannunsa taja tare da dorawa a Saman cikinta tace kaji babyn mu,Murmushi yayi tare da shafa cikin yace ko mace ko namiji Allah yayi albarka, suka fito suna zuwa palon Misam yace ai Mama da Kun sani ma ta waya kuka kira sai a yafe Masa ko kuzo ku kadai ba sai da shi ba,gwara dai da muka zo yafi yana ta binmu Yana bada hakuri,Misam haka ya kaisu har wajen Mima suka gaisa suka ce tafiya zasu yi harda sauri siya musu ticket din jirgi sabo da kar ma ace dare yayi zasu kwana,da dai iya Iyayen Chika ne ba matsala,Yana kaisu airport bayan sun tafi ya dawo ya iske Haly da Mufee wai sunzo zasu kwana.

Misam yace me kuka ce kwana? Muna gari Daya ga baki ga hanci" to ba a nan ba ku koma gidan ubanku, Nan ba waje ko Ina a gidan nan lungu da sako sunna muke yi,munafukai haka kuka ce ba bikina kuke yi ba ku anko ma na Rafeeq kuka yi ku tafi gidan Malama ku kwana,Chika tace haba My Prince,yace ba ruwanki ku tashi ku kama gaban ku bana tsarki ba na hanya,Haly ta mike Mufee ma haka suka fice ,Chika tace me kayi kenan Hakan? Misam yace duk naji maganganunsu sun dawo kunnena ki kyale su kawai ko Mima baza tace komai ba,in sun gyara halinsu sai mu shirya.

Suna fitowa Haly tace ai da kunya mu koma gida muce an Kore mu,Yaya Rafeeq Kuma in kaje ma ya dinga wani cin magani kenan,Mufee tace cikin kwanciyar hankali mu tafi gidan Naila tunda tayi bari muje kawai muce aiki zamu dan dinga tayata,ai kuwa can suka nufa sai kace dole,Suna zuwa suka same su a Palo sun saka kana Nan kaya wasu silk silver iri daya riga da wando,na Naila na mata na Spark na Maza,ba karamin kyau suka yi ba,Naila ya aika yace je ki kawo min wayata,Naila tace na gaji wlh Baby sai juyani kake yi yanda kake so,yace to na taba cin bashin ki ban biya ba? tace a'a,yace na hanaki ci Sha da sutura? tace a'a,yace ya batun Kwalbewa? tace Nan ma zam zam,kin taba cewa na baki abu na hana? tace a'a,yace ki taba bani sisinki kyauta? Naila tace Ina naga kudin baka,yace to ta ya bazan juyaki ba,Dan ma kin rainani ne Ina kyaleki shi yasa kike fadar haka,in wata ce jiki na rawa zata yi kafin nace anyi duk da kema kina kokari,Naila tace karfa ka manta Nima Yar gata ce a wajen Kaka,Inda na girma ban San babu ba duk abinda nake so shi ake min,Kuma Allah ya bamu rufin asiri bare kace kudinka na bi ato kana min zan maka,Kai kasanni wlh ko so kake na dawo Maka Naila ta ne ta farko,dariya yayi yanda take zazzare Masa Ido,yace kwana biyu ai kina Off ban saki a corner ba shi yasa kike haka,Naila tayi fari tace na saka dai a corner badan Ina tausaya Maka ba sai na Maida Kai Baseeru na Kone ma ruwan jikinka,dariya Spark yayi sosai yace Allah ya baki lafiya wlh na daina tausaya miki,Naila da kuri tace ni dama bana so ka dinga daga min kafa, a yini a kwana digir digir zaka gani...su Haly ne suka yi sallama tare da kwankwasa kofa,Naila ta ce Spark tashi ka bude kofar nan murmushi yayi ya jawota ta fado jikinsa"kissing dinta ya shiga yi a lips sannan ya mike ya bude kofar ta tafi dakko Masa wayar.

Haly ne suka suka shugo da fara'a,Spark yace kune ashe,suka ce ae Yaya, Mufee ta mika Masa hannu wai su tafa,ya Kalli hannun yace sa'anki ne ni? tunda muke na taba handshake da ku? Kuna mata au kin manta uwar mu Daya uban mu daya dadina zaki ji Mufee? Baki suka bude da sauri Mufee tace sorry wlh gani nayi muharramina nane Kai,Spark ya kalle ta yace uhmm to ki fito da miji a muku aure sai kuyi ta handshake shine karshen kusanci Bada ni ba wannan iskancin na koma Dan kauye dankwali ya ja zakara matata ta Jani duk wannan iskancin bada ni ba,dariya suka yi Haly tace kawai dai fada kayi Yaya ba wani Dan kauye Itama ai ba Yar kauye ce ba,au na zaci ai zaku ce itama tayi clean yanzu kuci ubanku yanzu,suka ce a'a, Alright ya furta ku zauna.

Naila ce ta fito da dan gudu da wayar tana taka steps tana kawo Masa tana yiwa su Haly barka da zuwa,Da wayar da hannun ya hada ya rike tare da jawo Naila ta zauna a tsakiyar cinyoyinsa,su Haly ya saci kallo yaga sunyi sauri sunyi kasa da Kai,yace dama Mima ta haifi masu kunya? film suka koma kallo ta dole,Naila tace akwai komai fa a kitchen kuje ku zuba kuci abinda kuke so,Mufee tace a kawo mana mudai kar ace munyi shishigi,to baza ta tashi ba sai dai in baza kuci ba ku barshi" ku baki ne ko gidan bakon ku ne,Haly ta mike Mufee ma ta mike suka nufi kitchen,Bayanta ta kwantar a kirjinsa Yana shafa gashinta yana danna waya,Spark yace gobe ranar ziyara ki shirya muje wajen Mero,Naila fuska ta bata Nan take,kishi ya cika mata zuciya,Jin shurun yayi yawa ya leka fuskarta yace Allah ya shiryeki Naila,tace Ameen zanje ai Allah ya kaimu.

Fitowa suka yi da plate da lemuka Naila tace Kun min ta'adi fa amma ai duk daya tunda jininsa ne ku amma plates din bana kowa bane duk kalolin nasa baku ga na musamman bane,Haly tayi murmushi tace to ayi hakuri amma miji ma komai nasa ba a tabawa? Naila tace Kai Baku sani ba? to spoon ma kala kala sunfi kala goma duk irin nasa daban ne wlh Kuma kullum da kalar da za bashi ya ci da shi,plates ma haka nasa irin iri ne Kuma kullum da kalar da za a bashi komai da kuka sani nasa ba a tabawa na daban ne,Kai Sallaya ma sai da izininsa wani zai hau Masa,Haly tace ai Kinga mun karu shi yasa kitchen din kamar ana siyar da kaya,Naila tace ba a wasa,Spark Yana jinsu Yana danna waya har wani dadi yake ji shi Kam ana girmama shi ya Dade Yana mamaki ko cokulansa gasu da yawa iri iri amma baza a bawa wani irin nasa ba,yace bala'i da masifa ya kare akan Wanda baiyi dacen mace ba.

Su Haly a gidan suka kwana abinsu sai abinda suka ga dama suke yi indai baza su taba mata kayan Spark ba to suyi komai ma,sun sake sun samu waje sai suka fasa tafiya suka yi zamansu a gidan, a gidan Naila da Spark suka barsu suka tafi Kano wajen Mero.
Naila burinta taje taga su Goje ko zasu ganeta.
Har da cewa amma zamu fara ganin Maza Wanda muka dan sani a Dan musu alheri ko ka samu Lada kaji please,Spark ya kalleta a jirgi yace kice kawai kina son ganin samarinki,Naila ta wayance tace daga nace kayi sadaka Dan Allah,banza ya mata yace kin ma rainani Ina kallo zan barki ki wani gaisa da kartan banza wlh idan kika kula wani a ciki ranki sai ya baci ya hade rai,Naila tayi shuru Yana ta faman tsaki har suka sauka.

Haidar ne ya samu Jauro a gidan Amaryarsa Jauro Yana Palo Yana hutawa,Haidar ya shiga gidan,bayan sun gaisa ya gaida Maman Annoor ma yace Kawu dama fada Maka zanyi gobe zan koma gidana na zauna a can,Jauro yace aure kayi? Aure Kuma Kawu zanyi baka sani ba,to baza ka koma ba kana gida dadin kaje kana baligi ba kowa Kai kadai a gida ka dinga kawo yaran banza to ban amince,in kana so ka koma ka Nemo matar aure dama ka isheni,dariya Haidar yayi yace Inshaallah zan kawo matar auren Allah kawo ta gari, Jauro yace Ameen ko Kai fa kaima ai ko Dan Hubby ka samu me fada Maka amma kullum Haidar Haidar ba canji ko Hashimu ai an canja Masa suna shi da yake local ma ana fada Masa Abban Mohsin,mu kuwa da ba Da ba jika kamar samari muke ai mu sai Hubby,Honey,Sugar,Haidar ya dinga dariya yace Kawu yanzu in aka kiraka da Hubby sai ka amsa? Kawu ya furta na dade da amsawa ma tuni,yaro sa wasa ana ta ci gaba Banda kai gaka kyakyawa sankacece sai bulayi kake yi a gari,Kunkumar ma taki samuwa,Haidar dai ya Dade Jauro yana ta babatu akan ya samo mata shima,sai da ya gama fadan sannan ya Kalli matarsa Amarya yace a karrama min Dana da kayan motsa baki,dariya suka yi taje ta kawowa Haidar kayan ci da Sha sosai.

Naila kuwa suna zuwa lokacin Maza ne duk,driver da ya kaisu yayi parking suka fito,Spark yace kinji me nace ai karki kula wani ko da wasa muje ya rike hannunta suka shiga,sai kallonsu ake yi kowa ya gane Spark Naila sai kallonta akeyi duk mazan Nan kallon sani suke mata sun rasa Ina suka Santa,Naila kamar tayi kuka tana kallon su Malam Jilani duk gasu Nan anzo musu amma Spark yace in ta sake tayi magana tam,su Goje suna ganin Spark da mace suka tabbatar Jamilu ce ba karya tunda shi ya aureta Kuma gata sun zo tare ma kowa ya kalleta yasan itace sai dai ta Kara kyau,ta Kara haske da kiba ta goge gata Kuma a shigar mata ta alfarma domin shadda ce a jikinta peach color.

Masu Sharhi Ina godiya matuka.

AsmaBaffa
[2/14, 8:52 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫
A GIDAN YARI

BOOK 3
~TAIMAKO~

6-10

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.