Complete Hausa Novels

Tantiriya A Gidan Yari Part 3 Complete Hausa Novel

Reading file: Tantiriya_A_Gidan_Yari_Part_3_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 5 of 20

Page naki ne
Iya2

Hey lovelies

Ke matar aure ce kuma kina neman business din dazakiyi daga gida da kuma baya bukatan jari?

Kai dan makaranta ne kuma kana neman inda zaka ringa samun kudin kashewa?

Ko a'a ke kinada business dinki Amma kina neman wani side hustle haka da zai Kara Miki extra source of income?

Ko kinada business idea da kikeson kifara Amma Babu jarin farawa?

Toh duk ku tarkato wannan training din, dan ga solution nan nasamo muku, kawai ki danna wannan link din Dan Samun damar shiga group din

https://wa.link/49vn47

Spark yaji Naila a jikinsa,narkewa yayi Yana shagwaba kamar yaro Dan yaye,duk ya makalkaleta Yana cewa Mummy ta tana can,Naila tana lallaba shi tace kayi hakuri zamu je ko gobe ka ganta normal,zata saba inshaallah,Yau zata yi Kwanan wahala ya furta,Naila ta gaji da korafin Spark yaki yayi shuru,ta hau romancing dinsa tace a ranta bari na gwada maganar su Misam,na tafi ace baka damu da miji ba, daga Dan fara kiss sai ga Spark ya zake,Booby daya aka sa Masa a baki tuni ya manta da wata Mummy a prison kamar Wanda aka Masa Allura ya watsake,Naila tace eyya bama ka Jin karfi a bari later kwanta ka huta kaji,muryarsa taji yace da karfi na zan iya komai ma,dariya tayi tace au da karfinka? Yace sosai .

Mero tana Isa gida sai Ganinta aka yi tsidik a cikin gidansu na bulon siminti ne amma kamar kango haka yake,wani tsohon rubabben gini ne tun ya zaman,dakuna uku ne a gidan sai kitchen din langa langa na karfe sai toilet,Inna ta iske a kitchen tana aikin soya awararta ta yamma,Mero tayi Sallama ta shiga,Jummai ta leko tace ya naji kamar Khadija,Baki ta bude duk taji kunyar yarta ta kasa zuwa su ganta a gidan yari,tace wani satin muke cewa zamu zo Khadija Ashe kina tafe,Munnir da ya fito daga daki yace wlh da kudi Yaya Khadija cewa tayi baza su ba tsada tayi yawa.

Mero tace ai gani na dawo,Jummai ta fito daga kitchen tace ya akayi na ganki Kuma? gudowa kika yi? Mero tabarma ta dakko ta shimfida ta zauna tace a bani abinci naci tukun naci na huta sai naji dadin labari,Ina Abbu? ya fita kasuwa,Jummai kitchen ta koma ta zubawa Mero shinkafa da wake da Mai da yaji ta kawo mata ta kawo mata awara a plate tace Kai Munnir ebo mata ruwa,Khadija ta zauna ta fara cin abinci sai da ta cinye komai tas ta Sha ruwa sannan bakinta ya bude,Abbu ne yayi Sallama ya shugo suka amsa,Baki ya bude ganin Khadija a gida,yace ya aka yi haka ta faru? Farin ciki ya kama shi ya washe baki yace Khadija kece?

Mero tace nice mana da baku zo ba gashi na fito,wai ku haifi 'ya a cikinku amma bakwa sonta haka ake rayuwa,kudi yafi da,Kun San bakwa son yara baza ku iya kula da su ba kuka haifo mu,Allah ya dube ku ya Baku yara biyu kacal amma baza ku iya rike su ba,sabo da son kudi,Abbu Murya a sanyaye yace wallahi tallahi Khadija ba laifi na bane laifin Jummai....Jummai itace mijin ko Kaine Abbu,ka zauna tana gara ka kamar tayar mota" ka karo kishiya mana kayi aure,yo magana ta Allah fa,Jummai baki ta bude tace Khadija ni kike cewa a karo min kishiya? Abbu yace kwantar da hankalinki Jummai bazan ma iya yi miki kishiya ba,Mero tana jinsa takaici ya kamata sosai na halin mahaifin su,Jummai tace tunda halinki zaki dawo da shi na fito na fito da ni akan ke sai kin koya min zaman rayuwa to wallahi ki koma aikatau,ya zama dole aikatau zan kaiki tunda samarin ma ke ba kula su kike ba bare ace za a miki aure to dole ki koma aikin wanke wanke da shara domin ki samo mana kudi,idan ba haka ba wallahi da katifa za a kaiki gidan miji,Khadija tace a kaini da abinda Allah ya hore,Abbu Yana ji Yana gani yayi shuru baya ko magana.

Jummai tace to gidan aiki zansa a sake samo miki,Mero tace na samo ma wlh a Kano Inshaallah gidan me kudi ne har gida za a zo a dauke ni,Inna sabo da sakaki ko a jikinta babu ruwanta da waye za a je gidansa burinta a samo mata kudi,Baki ta washe tace Allah ya kaimu Khadija Allah ya miki Albarka,ki bari ki huta ki murmure tukun,Kai Munnir zo kaje ka siyo mata kifi taci taji Dan dadi dadi,Sani uban Khadija Yana kallo Yana Jin haushi amma bazai iya magana ba,da kyar yace Jummai da dai an barta a gida ai Ina ga zai fi ko? Shawara na bayar ba umarni ba a dai duba,na yarje mata ta tafi baza ta zauna a gida ba mene amfanin Hakan,to shike nan Khadija Allah ya tsare ki kula kinji,ki tsare mutuncinki a duk Inda kike tunda kinji dai Hajiya Jummai ta gama magana.

Khadija takaicin Abbun su ya kamata ayi mutum kamar ba mutum ba,a ranta tace anya kuwa Abbu mutum ne? Suna haka wata bazawara ta shugo gidan Zuhuriyya Yar babba ce haka amma ba can ba baka ce kyakyawa Yar Fulani,kawar Jummai ce kut da kut,Abbu Yana kallon Zuhuriyya ta shugo ya mike Tare da gyara sallayarsa a bakin kofa ya tada Sallar Nafila ta dole ya dinga Sallah ba ji ba gani,har sai da Zuhuriyya ta gama abinda take ta tafi sannan ya sallame,Khadija tace Abbu meke nan Hakan? yace hanyar lafiya a bita da shekara Khadija kar ma mace tace ni Sani na kalle ta,ba ruwan Sani da mata,Mero shuru tayi tace ita Aunty Zuhuriyya din ai Abbu ta kirki ce,kana gani kullum shawara take bawa Inna tana nuna mata hanya Ina ruwanta da Kai,Kai da ake so ka zama mijin mace hudu,Abbu yace mace hudu Khadija? Jummai Kuma inyi ya da ita? Itama tana cikin matanka Abbu,a'a Khadija barni da ita din kawai,uhm uhm Abbu yanzu yayin mata biyu ake shine gayu shine cinyewar,yace a'a ba ruwana ,Innar su Khadija tana kitchen bata San me suke ba.

Mero tunda ta dawo mutanen garin suke cewa Yar mace ta dawo, taki aure ta gandame a gida bata da me aurenta,ko ta kansu bata bi" haka tayi sati guda duk kauyen ya isheta tace ga Inda zan ta kallon Yan gayu da wanka ko ta Ina,ko ban samu samu miji hadadde ba ai yafi min akan zaman kauye.
Waya ta samu ta Nemo karama ta siyeta dubu hudu ta sa layi ta kira Haneef,tana shiga amma ba a dagawa, yini tayi tana kira ba a dagawa,da dare ma da ta kwanta haka ta dinga gwadawa amma ba a daga ba.

Bangaren Haneef kuwa tunda gidansa suka nufa direct matarsa Ihsan ya samu a katafaren Palonsa tana zaune ta Sha gayu cikin kana Nan kaya riga da wando tight milk and brown,ta Sha hular gashi me kyau tare da Dora Yar facing cap a kanta,tana latsa wayarta me tsada,ganin mutane Bai Sa ta canja kaya ko ta saka Hijab ba haka tayi zamanta,aji take ja da kyar tace sannunku,barka da fitowa,Su Hajji suka zauna Haneef ko kulata baiyi ba ya haura sama,kin tashi tayi ta bishi sai da Hajji ya gaji yace ke wacce sakarai ce ne? Wacce shashasha ce ke ne? Mijinki guda ya fito daga prison amma ba farin ciki ba komai,Sai lokacin ta mike ta bishi sama,tana zuwa ta samu ya shiga wanka,zama tayi a gefen bed dinsa hadadden gaske tana ci gaba da chat dinta,tayi mugun Dadewa kafin ya fito daga wanka,Yana fitowa ya ganta me ya kawo ki nan? Ihsan tace Hajji yace nazo kasan in ba cewa aka yi nazo ba bazan zo ba,ka sani ba wai niyyar kaina bace abinci yana dining Kuma me dafa maka abinci ce tayi ba ni ba" tana fadar haka ta mike ta fice.

Ita Ihsan tunda auren zumunci aka musu ba wai sonta yake ba itace ta damu da shi har aka yi bikin maimakon ta kwantar da Kai tayi biyayya baza tayi ba,tunaninta kullum shi Haneef sai ya gaji ya sakko da kansa ya kawo kansa da kansa,gadara take tana da kyau da komai da namiji zai so a jikinta sabo da haka ba sai tayi biyayya ba,itace mace itace take da aji,sai dai namiji yayi fadanci a wajenta ba ita ba,sannan tana ganin tana da babban aiki,babban matsayi ne da ita a company tana samun kudi sosai ba ruwanta da kudin namiji bata ga dalilin da sai tayi biyayya ba,shi yasa take abinda taga dama,yanzu ma company ne ya dawo da ita branch din Kano shi yasa aka ganta ta dawo gidan Haneef a nan amma ita a Adamawa take can gidan Haneef na can,sanda Wuta ta Kone Khairat ba karamar murna tayi ba a haka wai duk bata son kishiya Kuma,bata aikin fari bare na baki sai dai aikinta in tana gida Kuma chat ta fesa wanka ta zauna tayi Kallo,Bata fiye fada ba Kuma ita sabo da ajinta zai wahala kayi hayaniya da ita,tana da aji ita dole me aji ce,sai dai ta guma Maka takaici ta wuce.
Tunda Haneef ya aure ta sun Kai Shekara kenan amma sau uku zuwa hudu ta taba kwana da shi,har wani Abu ya shiga tsakaninsu,tunda taga in Bata je ba bazai neme ta ba,sai idan taje wannan zai nemeta normal sai ta daina zuwa tace sai ya kawo kansa da kansa sabo da ta isa itace me aji ba shi ba.
Shi Kuma Haneef Yana ganin abinda take yi haushinta ma yake Kara ji sabo da duk wani Abu na macen aure bata yinsa shi yasa baya kulata,ya Kai kararta sau biyu duk dangi ita Ihsan suke goyawa baya ai shi zai lallabata sabo da suna ganin auren zumunci ne ko ya Kai karar ba a daukan mataki shi yasa ya gaji ya watsar da zancen ya watsar da ita kowa yake Uzurinsa.

Sai da ya shirya ya canja sutura me kyau cikin jallabiya fara me tsada dai dai shi sannan ya fito ya samu su Hajji su har sun ci abinci tafiya ma zasu yi,ya raka su suka shiga mota yace a fadawa Ummi ya bata zo ba Danta ya dawo,Hajji yayi murmushi yace zata zo ne a satin nan ko na sama tace,yace shike nan zan kirata a waya,in Kun isa lafiya ku kirani,yace to driver ya kaisu airport suka wuce shi Kuma Haneef ya dawo ciki,dining ya duba gaja gaja an lalata me aikin ya kwalawa kira Salamatu" fitowa tayi da sauri yace ki gyara dining sannan zan kawo wata me tayaki aiki,bana son Yan aiki barkatai zaki dinga gyara gidan nan ita zata dinga girki,Salamatu tace to Oga Allah ya kaimu, babbar mace ce ita Salamatu,yace me gadi fa ana bashi abinci? tace kullum sai ya koshi Oga,yace Good job yana murmushi yace zuba min ta zuba Masa ya dauki plate dinsa ya koma Palo Yana kallo yace Kai sai naga plasma din ta Kara min girma ko dan a can babu ne"
ya Kalli gidansa yace Allah na gode Maka Ashe dai ba karamin hadadden gida nayi ba,sai yanzu na gano haka da naje prison,ga ac ta a can kuwa Ina wata Ac ta kirki,uhmmm ji Parlo komai me tsada ga kyau ahhh nasha wahala,shi yasa nake ganina kamar a Aljanna nake yanzu.

Yau da wuri ma zan kwanta sabo da na hau katon bed Dina naji dadi in more rayuwa ta,da ace waccen Yar iskar mutuniyar arziki ce ai da sai ta zo ta Sha madarar Nido Inji Scola,tunda tafi so a bar mata abinta haka kullum a lullube taje da abinta ta Shekara tana rufewa,Dan ta ni in taje wanka ma kar ta bude,ita kuwa Ihsan tana garden tana hutawarta Bata San me yake cewa ba.

Sai magriba yaje masallaci ya dawo Yana Sallar Isha ya kwanta abinsa,tunda ya dawo sai da ya kwashe sati guda Yana hutawa sannan ya koma aiki,Yana ganin kiran Khadija kullum amma bai San number din ba,yayi busy da yawa sai da ya cika 10days da dawowa sannan ya daga kiran Khadija,Yana dagawa yaji muryarta bai San ita ce ba,sallama tayi kana magana da Khadija ta gidan yari,Yana Jin Muryar ya gane dariya yayi yace wacce Khadija fa? Khadija me fasa gini mana dalla wacce kake ba Madara ta Yar kafa wai meye haka Dan Allah ka gane ni ka dinga wahalar da shari'a ,murmushi ya saki yace ohh Yar aikin da zan dauka?Mero tace duk Inda talaka yake sai me kudi ya nuna Masa rashin Kara kiri kiri ba komai itace ei itace Yar aikin,kin shirya ne? Mero tace tun yaushe Kuma na shirya na ma fada a gida sun yarda.

Har kin gama Shan kokon ya ishe ki da awarar taku,Mero tace na Sha mana Kuma na fika lafiya ba,yace to yaushe kika shirya? Nifa a shirye nake ko yanzu,yace to gobe da yamma ki shirya za a zo a dauke ki, Allah ya kaimu,ki bar wayarki a kunne kusa dake sabo da kwatacen gidanku,Mero tace sabo da rashin tabbas din karfen nasara bari na tura ma text ko da network yayi tsiyar kaga ai an San Inda nake,yace Alright Allah ya kaimu,badan yayi dariya ba sai Mero taji kamar bai San wace ce ba yanda yayi magana.

Washe gari sai da yamma likis mota hadaddiya tayi parking a kofar gidan su Khadija,Khadija babu suturar arziki 'Yan tsumman da suke a gida nata ta zabo kala uku masu dama dama,wacce ta dawo da ita daga prison a jikinta shi ta wanke ta goge Leshi yellow and Golden ta saka a jikinta,Mayafi ma tana so ta danyi too match amma ba dama haka ta dauki Hijabinta blue na yadi Dan Madina ta saka abinta ta fito dauke da ledar kayanta,Jummai sai murna take yi tana addua Allah yasa Khadija kije a sa'a Allah yasa wannan yasa shine silar arzikin mu,Allah ya zuba mana sugar a bakinmu Khadija karki bari ya zube bamu lashe ba,Dan Allah kiyi aiki me kyau Banda shiririta,Khadija tace to Inna baki sa min albarka ba,Inna tace Allah ya miki Albarka,Allah ya Bada sa'a,Abbun su Khadija Yana kasuwa tace ki cewa Abbu na tafi,zan fada Masa,Munnir Yana jinsu Yana tabe baki yace mutum yayi sana'arsa a gida bai fi ba amma ka dauki Yarka ka kaita wata uwa duniya baka San Inda take ba Allah ya kiyaye kar a yiwa Yaya Khadija Cikin shege,Harararsa Jummai tayi,har mota ta raka Khadija ta dawo tana ta tsalle tana murna a mota aka zo daukan 'yata,'yata tayi goshi,Munnir tashi yayi ya bar gidan gaba daya.

Khadija kuwa tana mota a baya daga ita sai driver ba Wanda ke kula wani,duk surutun Mero shuru tayi har suka je unguwar Mero sai kallon hadaddun gidaje take yi,suka Isa katafaren gidan Haneef, ta Saba ganin gidaje masu kyau a Abuja shi yasa kalle kallen nata yazo da sauki,gidan Haneef ya hadu karshe ga motocinsa nan iri iri,Driver ne yayi mata iso har Parlo,tana bayansa Yana gaba,a Palo suka samu Ihsan taci shadda sky tana zaune tana Shan fruits,Mero gabanta ya yanke ya Fadi ganin Ihsan Masha Allah da ita son kowa kin Wanda ya rasa,a ranta tace Nima da kyau na ai ba fina tayi ba,ko haske baza ta nuna min ba sai gogewa da hutu kawai,fili Kuma tace Hajiya muna ta sallama Baki amsa ba,babu kyau wlh kaji sallama ka share a Islamiyya an koya mana,tuni Driver ya juya,Ihsan ta Kalli Mero sama da kasa a wulakance tace ke kama kanki,kece Yar aikin da Haneef yace an samo? Mero tace aka samo? Kamar kifi a teku Wanda babu me shi aka dakko dai ko Aunty, Ihsan Ido ta zaro tace Kinga bana son magana ta kwalawa Salamatu kira,Salamatu ta fito tace ga Yar aiki an kawo ki nuna mata komai ki kaita dakinta Dan Allah kuje bana son damuwa.

Salamatu ta ja Khadija bangaren masu aiki ta nuna mata daki da bed da mudubi harda sip dakin me kyau abinta ita kadai,Mero tace ko a gidan miji ka samu wannan ai soyayya sai ba za ayi ba,Salamatu tace ke dai bari Yar uwa kin ga sanda aka kawo ni gidan Nan Inda kisan Yar gudun hijira amma yanzu kalleni kamar takari a saudiyya,Mero tayi dariya tace ai Aunty sai ace ma kece uwar Ihsan din matar me gidan,Salamatu tace ke rabani da wannan ba mutunci ne da ita ba,Mero tace nima Ina da degree din nawa rashin mutuncin,nawa degree din na rashin mutunci dan Cotonou ne ma,Salamatu tace kar a Kore ki baiwar Allah yarinya kibi a sannu kina Yar aiki Ina ke Ina ja da masu gida,Khadija tace zauna ki zuba Ido Aunty Salamatu ni ba ruwana da matarsa Ihsan,shi fa zanwa aiki Kuma ma muna mutunci da shi Yana da kirki,Salamatu tayi murmushi tace ke akan ma'aikatansa bashi da wani sauki aiki kika zo aiki zaki yi Kuma zaki Gani zaki ce na fada miki.

Abinci ta kawowa Khadija tace sunanki Khadija ko? daga gobe zaki fara girkinki a kitchen ni ya Maida ni gyaran gida,Mero tace Allah ya kaimu.
Mero tana nan har dare Bata ga Haneef ya shugo ba,ta fito Palo ta samu Ihsan ta canja sabon wanka da key din mota a hannunta da alama fita zata yi,ko kallon Khadija Bata yi ba ta fice,Mero tace mu ai sai mutum ya bude baki ma yayi magana komai shariyarsa Ina nan dake sai Kinga na fara yiwa mijinki tausa tukun kina Nan,tana zaune a kasa tana maganganunta taji kamshi ya mamaye parlon dagowa tayi a hankali tsorata tayi sosai ganin mutum a gabanta,kirji ta dafe tace wlh na zaci aljani ne,kallonta Haneef yayi tace Ina yini,ya amsa da lfy Alhmdllh,kawai sai Taga ya shareta kamar Bai Santa ba ya zauna a kujera,Mero tace kai, Salamatu ta fadi gaskiya kuwa ba mutunci,wani film aka saka aka fara series ne American film suna ta kallo.

Khadija tace wannan yarinyar bata da wayo,Haneef yace tana kallo an kwace abin magic din an tafi Kalli yanda take tafiya,Mero tace rabu da banza ai jaka ce naga alama,Star dinne ya hadu da yarinyar suka tsurawa juna Ido Mero tace ka dauki remote a hannu za a fara iskanci, da kaga irin wannan kallon sai iskanci a canja tasha in an gama sai mu dawo,Haneef yace a'a ba wani iskanci da za ayi,Baki suka hade waje daya suka fara kiss Mero tace la'ilahhhhhhhhh....murmushi Haneef yayi,Dan Allah ka canja mana tasha kana kallo ya danneta ni dai ba ruwana, La'ilahhhhhhhhh...zai cire mata breziyya,wayyo tonon asiri marakisiyyarta ya cire,Haneef yaki canjawa yace in ana canja tasha ba a gane film,Mero kanta ta Maida bayan kujera ta buya tace in an gama ka fada min.
Ihsan ce ta dawo ta samu Haneef da Khadija suna kallo suna magana,yace tashi ki Gani tsafinta ya dawo,ta dago da kanta tace ya dawo kuwa wlh ana Raina mana hankali gaskiya,Ihsan ta Kalli Haneef ta Kalli Khadija abinda ta tsaya yi kenan tana kallon su ko kulata basu yi ba,yace gashi Nan Bos yazo,Mero tace to ita yarinyar Ina tsafin tayi maganinsa mana,Inama nice....kaiii kuturun Uba ta dirga kansa Kalli wohoho...ya masge ta ariiiii....
Tare suka Kalli season biyu sai gobe Kuma za aci gaba,Mero tace sai da ya dakko dadi,Haneef yace gobe kamar yanzu zasu ci gaba ai,Ihsan bakin ciki yasa ta ja tsaki ta wuce.

Papa ne ya kira Arham ga Mima a gefe Yana ta aikin lallaba Arham akan Basma,yace Dan Allah Arham ka rufa min asiri ka aure ta,mene laifinta kyakyawa da ita komai dai dai wlh ba Wanda bazai so wannan ba,kayi hakuri a hankali zaka so ta,Arham yace ai ni nace a zabo min laifi nane na yarda ai zan aure ta din,Papa yaji dadi yace ko me kake so zan Maka,Arham yace ai kayi min komai Ina karatu ka bamu jari muna sana'a yanzu dai ni a biya min Umrah in ana so aga na kula ta,Papa yace Inshaallah za a biya Maka amma ka Dan kirata kuyi zance ku fahimci juna ita tasan Kai zata aura na mata bayani,Arham yace yanzu a gidan ma sai naje zance?,Mima tace ji min yaro fa ni wlh wannan yaro ko tafiya yayi bazan kirashi ba ko awaya Dan bazan yi kewarsa ba,Arham yace ni din Mima? Ae Kai din idan Shaheed ne ko junior duk zan neme su in basa kusa amma ban da Kai dama ka isheni ni gwara ma ayi ma auren,Arham yace shike nan Mima za a gani ai kince dai ko a waya baza ki kirani ba in bana gari? Tace ae haka nace yace to shike nan.

Papa in naje zancen ma in banda wakar Dan maliyo maliyo me take yi,kana ji dai a gidan nan kullum sai tayi wakar Dan maliyo,ita kadai tafa tafa take yi,tafa tafa tafiyar nan da zamu tare aikinta kenan fa, Papa yace marainiya ce tausayinta nake ji Yar abokina ce a kauye tun muna yara, Allah yayi masa rasuwa tun tana Yar karama,uwarta tayi aure aka tafi da ita agolanci gidan wani,Arham yace au agola ce ma?,shike nan mijin agola ne ni,Papa yace Kai gidanku tashi ka tafi,Arham yace agola kuwa gaskiya ba sa'a,haba shi yasa kirjinta ba komai,Mima ta make shi,Papa yace kyale shi uwarka ma gata Nan haka aka daura mana aure da ita a gidana ta fara,Arham yayi dariya yace Dan dai Kaine papa amma da na Fadi wata magana sai dai da kunya amma da nace sai yayi maganar kamar me kunkuni yanda baza aji me yace ba ya furta Kai ka jawo shi kenan ya fito,ya mike tsam,Papa yace ai baza ku nutsu ba kunyi gado ya zanyi, Mima tace ban gane sunyi gado ba,me kake so kace kenan wajen wa suka gada? Papa yace a bar dai maganar kawai tone tone ba dadi.

Basma kyakyawa ce fara doguwa tana da sura da diri me kyau wulakancin Arham ne kawai sabo da yaga Yar kauye ce bata saka kaya a muhallinsu,Yana fitowa yaci karo da Basma ta fito da gudun tsiya Arham ya kurawa kirjinta Ido yace ba abinda yake motsi kyam haka, Kai ai ya kamata naga suna rawa in akwai amma kyaf kamar nawa tana gudu kyam da su,Allah ya kaimu anjima ai zanje zance wlh sai na taba naji bazan yarda da wannan rufa rufar ba,ko Kuma in tana wanka na Gani da idona baza a kawo min Abu a dukunkune ba,Su Haly ya samu a parlo suna ta Masa dariya haka kawai,suka ce yanzu matarka ta fita da gudu,Spark ya gani a parlon shima a zaune da Naila,Spark yace dama ita ce Basma din? Arham yace oho,Naila tayi dariya tace ai ni Banga laifinta ba wlh kyakyawa da ita haka,ni kyan fuska akace muku Ina so,kyawun kirji da baya ba ruwana da fuskar mace ni zan iya danne fuskar da pillow ma,Spark yayi dariya yace wai yaron nan aure za a Maka,Arham yace ya ranka abinda ka kasa ni zanyi zaka gani 9mnths da Baby boy, Naila tayi dariya tace wato Yan gidan nan baku da Kara wlh akan Allah bai bamu ba, Basma ce ta shugo da gudu kanta a kasa sanye da riga doguwa ta material silk,zata wuce tace sannunku tayi gaba
Arham ne ya rukota harda bata rai irin ba wasa yace ke zauna ki huta da guje gujen nan,ke kafarki bata gajiya ne? Kullum daga Waka sai gudu haka kika ga ana yi a garin nan?

Basma ta sa yatsa a Baki,Arham yace ke tun yanzu ba abinda zan miki wannan romantic sign ne bazan taba komai ba cire yatsanki,Spark kansa ya Dora a kafadar Naila Yana dariya,Basma ta turo baki tace to ai ni tunda nazo ban fita gari ba ban San me ake yi a garinku ba,ana gudu ba ayi ana Waka ba ayi ni Ina zan sani tunda a gida nake,Arham yace shagwaba zaki min ke Yar nan baki tafasa ba zaki Kone,Allah ya kiyaye na Maka shagwaba ni Ina na iya shagwaba,ni sirrina ma baza a sani ba Allah ya kiyaye kayi kadan kadan kasan sirri na,Arham yace ke Nan har sirri ne dake? rufa min asiri na San sirrinki yanzu ni Ina a'a ba haka nake ba ni sanin sirrin ya mace ai sai an shiga daga ciki,Basma bata gane ba tace to ni bazan shiga ciki da Kai ba,Arham yace nima haka Hallareta tana cikin rufin asirinta ba gardiyar da zata ganta,Basma Ashe tana Jin yaren tasan Hallare da fillanci,tsalle tayi tana dariya wlh yasan sunanta idan ba wannan Dan iska bane Allah ya Kona ni Dan iska ne,kana birni kasan Sunan abarku,yeeee Dan iska za a aura min ta tafi da gudu tayi cikin daki tana neman Mima zata fada mata,Bata ga Mima ba ta fito ta fice,Arham ya ja tsaki yace ta zaci tsoron magana nake agaban Mima Hallare Dan na fada mene ko Naila tana ganin ta Spark,Spark yace uhm uhm wlh kasan halina zan sa a kulleka a guard room wlh,kowa yasan tana gani mene sai ka fada tana ganin abarta ai an sani,Shaheed Yana zaune a gefe Yana ta dariya yace au abarta ce to a yanke a bata mu gani,Mufee basa wajen sun tashi tuni tare da Naila,basu San me Arham suke ba.

Mufee ce ta Kalli Naila tace Aunty Naila wai ni wannan da akace Dan gidan Sudan ne ya sunansa ne? Naila tace Haidar? Ae Dan Uwan Ikhram din Rafeeq fa,shine dai Haidar din,tace gaskiya ba karya mashaallah,ko dai kina ciki ne Mufee? Naila ta tambaya,Mufee tace uhm ni Ina zan so namiji Bai ce yana so na ba Allah ya kiyaye,Naila tace in yazo fa? In yazo ai Kinga mutum bazai ki mutum ba,dariya Naila tayi tace kyaji da shi.

Basma ce ta shiga part din Papa a nutse tace Mima kizo,Baki nayi? A'a nice nake nemanki zo ki gani,Mima ta taso ta zaci wani muhimmin Abu ne,suka taho tiryan tiryan har parlo ta nuna Arham tace Mima ki yiwa danki fada Dan iska ne dazu Sunan abarsu ya fada da wani yaren Yana bahaushe har ya Kai ya San sunanta da wani yare,Mima tace me? Abarsu ta fitsari mana ya Fadi sunanta kiri kiri da wani yaren Fulani Kuma Bai San na sani ba Ina Jin yaren ,ai sai Dan iska ko? Spark Yana jinsu yace Mima kizo in ganki tafiya zanyi ni,Basma tace Kuma ma Yaya Spark yaji sanda ya fada duk suna dakin nan babu Wanda ya Masa fada cewar Basma,Mima tace dole ayi Masa fada gaskiya,Arham Yana zaune ko a jikinsa,Spark Mima yayiwa magana na yan mintuna a gefe ya fice ya tafi,Mima ta juya zata tafi Arham ya Kalli Basma yace Enduu,hannaye ta Dora a Kai tace ya Kuma iskanci ya kuma iskanci wlh ya Fadi Sunan nono Mima,Mima baki ta bige mata,Basma tace ba nonon saniya ya fada ba na mutum ya fada,tsaki Mima ta ja ta harari Arham ta fice tace ki bari Basma zanyi maganinsa,tace to ta juya ta shige bedroom tana cewa wlh Dan iskan Miji ne nawa ni wayyo ni Kam na boni.

Jibson ne ya shugo dauke da ledar nama biyu ya fara mikawa uwarsa mahaifiya nata sannan ya shiga da nasu ciki,Hanan wacce tayi kiba ta Kara kyau ta Masa sannu da zuwa ta mika hannu zata karbi ledar yace a'a ba sai kin karba ba zan ma bude mana muci,Hanan tace uhm sabo da nama ne,bana son Zalama kullum Naman nan sai kin ci fa daga dawowa sai kice ledar ma sai kin karba ai abin zai miki yawa ga sannu da zuwa kin yi min Kuma ace Leda ma sai kin karba kina Amarya kyale na ajiye na karasa sauran aikin kin San Ina kaunarki,Hanan tasan duk kawo nama haka yake yi amma Kuma a banza kullum sai anci,sai Hanan tayi zuciya ya bude Naman kaza gasashiya yace to taho,Hanan tace na koshi,murmushi yayi ya kalleta yace Allah? Tace bana ci,yace na gode miki Allah ya saka da Alkhairi,yaci gaba da dumurmusar namansa,Hanan ta tuna da Mohsin shi me hankali da shi ba irin Jibson ba,takaici ya kamata ta auri shashashan miji...tashi tayi ta zauna ta fara cin kazar taga ba ruwansa shi.

Abba kwance yake a Saman katifarsa a shago wani yazo siyan wake,Ya mike ya zauna yace yawwa da Allah jawo min daron waken can,me siyan kaya yace Kai sai kace mace marar lafiya,kullum sai kana zaune ko a kwance yanzu kwanon waken ma sai na jawo maka,Abba ya mike yace duk abinda za a sa mutum ya tashi sai an nemo shi,ya auna Masa ya tafi abinsa,Abinci aka Aiko Zarah ta kawo Masa,yace har an gama girkin ranar? tace ae" to kice nace Allah ya mata albarka da take gama girki da wuri,Zarah tace to ta tafi,tana zuwa tace Umma yace Allah ya miki Albarka da kike gama girki da wuri,Yar Inna tace Ameen,bude Abincin yayi yaga shinkafa da Miya harda nama ga couslow an hada a mazubi dabam,yace bari naci sai na tafi Sallah da karfi na,ya zuba a plate ya fara ci yaji yace Kai kayan miyar nan anyi dacen su,ko dai Yar Inna ce ko kayan miyar akwai sa hannun Daya a ciki wajen bada wannan dandano.

Wayarsa ya jawo ya kira Yar Inna ta daga tace wani abin za a kawo Maka? Yace a'a girkin ne yayi dadi shine nace bari naji kayan a miyar ne ko kuwa a kece ko Naman Dabbar ne taji kiwo haka? Yar Inna tayi murmushi tace a nice,tsohon hannu wasa ne,Abba yace na yarda yau ni zan tsefe miki kitson nan sabo da kin gama dani da girkinki,tace idan yara sun tafi makaranta ba,yace ae ai suna tafiya zanzo na warware miki kitson tace to,yace Kuma saloon zamu je,Kubra tayi dariya tace tunda akwai kudi ai sai muje,yace ni da nake da Naila da Mohsin ga Hidaya itama ta taka Leda kina gani dai Yar tatsitsiya Hidaya har ta rikita mijinta Dan banza kullum sai ya kirani kullum a waya wai gaisuwa ai nasan Bata Allah bace Yar Hidaya ta aka samu ana ta kwalbe ta,dariya Kubra tayi tace Kai dai komai sai ka fada baza ka barshi a ranka ba,yace wlh bazan barshi a raina ya kashe ni ba,Yar Hidaya ta ce ya samu bagas,kullum Abba Ina Kwana Abba ina yini sai kace na gari bayan Yana Nan kullum sai yaga tsirara,ni ba mutuncinsa nake gani ba tunda nasan me yake yiwa 'yata,Umma tace Yar taka ai itama kasan me take yi ne,irin su Hidaya hmmm,shi ya koya mata cewar Abba fitsararre.

Yara suna tafiya makaranta Abba ya dawo ya zauna ya hau Warwarewa Yar Inna kitso da cumb harda rufe gidan kar ayi musu zuwan titse,Yana gamawa yace mu tafi wajen Chinaza ta wanke miki,Yar Inna ta shirya ta sa mayafi Abba yace kinyi local da yawa kamar ba kece uwar Naila da Mohsin ba saka Abaya,Kubra tayi dariya ta canja Abaya baka da mayafi yace yanzu kika fito a matar manya,baza a zaci nine mijinki ba fa an ganni Dan firit sai Kuma aga nine, dole mutane suce na cuce su,na yiwa masu kudi bakin ciki gaskiya,dole masu mota su dinga Jin haushi na a layin nan,Kuma a banza aka bani ke sadaki dubu daya,gashi a iya jikinki na Mori billions ai ni naci riba,Yar Inna tace muje Dan Allah ni ga Baby dauke ta,Abba ya dauki yarsu karama suka fito,Gidan suka kulle.

Beauty ce tayi parking da sabuwar motarta da babanta ya canja mata,ta fito da katon cikinta,Abba yace ya kamata ki daina fita yanzu,Beauty tace na gaji da Zama Abba,Ina zaku je ne? Abba yace Saloon zan kaita,Beauty ta boye dariyarta ita Kam birgeta suke yi,tace to gashi nazo Kuma,yace to akan kinzo sai mu fasa zuwa Inda muka yi niyya ga key ki jira mu,Umma tace ba Nisa Beauty kinji yanzu zamu dawo,tace to na kaiku a mota mana Nima daga Nan sai a wanke min gashin,Abba yace a'a mu a kafa zamu tafi muna hirar mu,Kuma baza a kwaiwaye mu ba,kije wani wajen ayi miki naki kalar,Ina wajen za ayiwa Yar Inna ni zan tsaya kallon na suruka ta ne,Beauty tayi dariya kamar me tace Abba in aka mata sai ku fita ku shiga mota idan aka yi min sai mu taho gida,Abba yace to mijinki ya sani ne? Tace ba matsala zai yafe ma,Yace haka ake so kinyi kokari gwara ki dinga juya shi,motar suka shiga,Yar Inna ta shiga gaba Abba yace sai dai ki dawo baya sai a barni a bayan mota kamar birin turawa.

Kubra ta dawo baya Beauty ta ja mota suka tafi,Abba yace Allah ya bani kudi na siyawa Yar Inna mota itama ta dinga kaimu unguwa,Beauty tace Kai fa Abba,Ina ni ko Keke bazan iya tukawa ba ai sai nayi hatsari naje na daki trailer bani da wannan kokarin Yar Inna dai Jaruma ita ta tuka,suna hira suka je Abba yace Chinaza ayi mata me kyau har relaxer a sa mata, gashin nan nata a Maida min shi na turawa,Chinaza ita kanta dariya take,Yar Inna tace baza ayi min kitso ba? Yace a'a sai wani Jikon na gaji da shi,aka gyarawa Yar Inna gashi gyara na gaske kamar Amarya za a kaita gidan miji haka aka mata,Abba ya nuna donut a Jikin hoto yace shi za ayiwa Yar Inna,Chinaza tayi mata sosai gashi ya zuba kyau,suna zaune sunfi 1hr ana Abu daya sannan Beauty ta shugo Abba yace ni na gaji Ina jiranku a mota ya shiga mota,aka yiwa Beauty itama nata ana gamawa Abba ya dawo ya biya kudin duka, Beauty tace har zan biya ma,yace a'a an gode miki jeki da abinki,da a baya ne ai bazan biya miki ba ko Yar Innar tayi kadan na biya mata kudin saloon,ki tambayeta kiji taci wahala,ko man gyada bana siya,yanzu kuwa bani da matsala zan mata ko mene.
Beauty tayi murmushi suka tafi.

Suna mota Abba yace yau Yar Inna sai ta Sha Ice cream a garin nan, Kai mu a siyo mata,Beauty ta wuce wajen Ice cream da kayan makulashe,Abba ATM dinsa ya mikawa Yar Inna yace kuje ku siyo, Beauty da Yar Inna suka shiga abinsu suna Hira suka yo siyayyar kayan makulashe sosai kuwa har yara aka siyowa,Beauty ma ta siyo nata duk a cikin kudin Abba suka dawo mota,Yar Inna ta mika Masa ATM card dinsa tace gashi,ya karba kawai yace nasan an min tafka tafka da barnar kudi,Kubra tace to ba kudinmu bane kudinka ai nawa ne,yace uhm haka kuka iya da wayo.

Gida suka koma suka baje kayan makulashe har Abba kowa Yana cin abinda ya Masa,har yara suka dawo suma suka karbi nasu,Beauty har dare tana gidan,Abba yace kinyi girki dai ko? Kinzo nan kin rashe ana ta cin kudina dake ya batun Dana an Masa girki ko? Beauty tace har can naje na Kai Masa abinci Kuma nayi wani ma ya sani,a gidan ne tunani nake yi ko zan sauka lafiya ko Kuma a'a,Abba yace ki sauka daga Ina? da Ina kika hau ? Dariya Beauty tayi tace Abba ko zan haihu nace,yace au lafiya zaki haihu Inshaallah,tace Allah yasa,yace Ameen,yace Naila ta nake wa kwadayin samun cikin nan gata da dangin Miji masu surutun tsiya,bari na kirata naji Yaya,Naila ya kira ta daga suka gaisa yace ya gidan tace Abba lafiya so nake na wani satin zanzo,yace yanzu Naila kina wannan gidan me kyau har marmarin fita unguwa kike? Ai idan da nine ke wlh ba Inda zan fita Ina gida kullum Ina Jin dadina,Naila tace Abba ni na gaji da shi ma makaranta fa zai sani,Abba yace Inye Ashe dai za a gaji Yar Inna a Ilimi,to Allah ya taimaka,yanzu watanki nawa da bari ne? Naila tace wata biyu da Yan kwanaki Abba,yace Kuma ba komai? Tace ba komai Abba banji komai ba ko ciwon Kai bana yi bare na sa rai,Abba yace to na kusa Kuma fara yi miki kuka Naila abin nan yayi yawa sai tausayinki ya sani kuka Kuma,Kuma mijin naki kalau yake? Naila tace kalau yake Abba lafiya lafiya muke komai,Abba da Yar tasa Naila ba kunya,yace to Allah ya kawo Ina ta Miki addua,jiya ma tsohuwarki bacci na hanata sai da muka yi sallar dare sabo da muyi muku addua,Naila tace na gode Abba amma na karaya da haihuwar nan,Abba ko wacce in aka yi aurenta sai ta samu ciki.

Abba yace to ai lamarin Allah ne ba a Masa dole shi yake bayarwa,irin su Jauro Kuma suce me? Gwara ke kinyi bari Jauro ko Jinin Haila bayayi,Naila ta kwashe da dariya,Abba yace Allah da Jauro mace ne ko Jinin Haila bazai yi ba bare ma a sa rai zai haihu.
Naila tayi dariya kamar me har suka gama waya,suna gama waya yace Beauty tashi ki tafi gida kar Dana ya dawo bakya nan,kije ki kular min da Dana,ga surukanki amma bakya kiyi da ita,Beauty tana dariya ta mike ta dauki Jakarta,tace Abba zan Kara cake din nan,Abba yace ajiye Yar Inna ce zata karya da shi da safe,Kubra tace na bar mata,Abba yace gobe ma rana ce Kubra,Beauty dai ta dauki cake tayi Sallama ta tafi,Abba yace kice Ina gaida me gidan.

Spark ne ya dawo ya samu Nailansa tayi shuru tana tunani,a gefenta ya zauna tare da Dora kansa a kirjinta ya kwanta ya furta duk tunanin cikin ne? Nasan bazai wuce tunanin haihuwa ba,wai ni da kika damu kanki Naila na taba miki complain? Ni wlh ban damu da dole sai na haihu ba,idan Allah bai bawa mutum ba kashe kansa zaiyi,wani yaron ma da masifa ne in aka baka shi,Kuma ko Shekara bamu yi ba amma kinbi Kin damu kanki,damuwarki baza ta Baki ba ko ta hanaki,in ma zaki hakura ki karbi kaddara ki hakura,addua ce kawai taki na mene na damuwa,bana son wannan abin da kike yi,da Allah kike fushi ko da wa tunda shine bai baki ba,Naila tace nifa ba tunanin haihuwa nake ba,bana son karya fada min meke damunki to ko takalma kika samo latest a siya miki a huta tunda ke rayuwarki a takalmin sawa zata kare,dariya tayi tace Allah ba wannan bane kawai yau ne naji bana Jin dadi sai na dinga Jin kunci da haushin kowa,Spark yace ko period ne? tace a'a haka kawai sai naji kamar nayi kuka, Spark yace to yi kukan mana tunda gani ba sai na lallashe ki ba,gidan Rafeeq zaka kaini na Dade banje ba naje naga me ciki Ikhram,murmushi yayi yace dazu naji yace yau bazai bude gida ba Kwalbewa zai yini Yana yi na matsa Masa a Office kwana biyu baiyi komai ba

Muje mu hanashi sakewa,dariya Naila tayi tace ku dai wlh kamar abokai,Spark yace Khalid yazo ma da matarsa suna gari yace zai je can muje kawai,tashi tayi suka shiga wanka tare, Spark duk yanda hankalinsa ya tashi a toilet ya so ya kwalbe Naila taki yarda yau,shi tunda ya aureta bai taba nema ta hanashi ba sai yau,sai ta dinga Wayancewa,kyaleta yayi Bai nuna ya damu ba tunda jiki da jini sai ya rabu da ita suka ci kwalliya suka fito zuwa gidan Rafeeq,itace ke driving dinsu suna ta hirar su ta masoya,yace an dai hanani Kwalbewa,Naila tayi murmushi tace sai mun dawo zan baka Bado karka damu,nasan halinka sai ka fara Jin Haushin mutane.

Washe gari Mero ta shirya breakfast,tana tsaye a Palo tana jiran Ihsan ta fito sai ta ganta ta fito daga bedroom a kasa,Haneef ta gani ya sakko daga sama dakinsa,Mero tace a'a lafiya? Haneef yace da aka yi me? tace naga ka fito daga sama dakinka daban,itama ta fito daga kasa dakinta daban fada kuka yi?me ya hada ku kamata yayi ace Kuna Jone ana tashin ku da kyar,ta bude Ido tace Baby kace uhm uhm koma bacci ban gama Jin dumin jikinki ba,amma sai na ganku baram baram,Kai kayi gabas da Kai ita tayi arewa da nata kan,Kai da zanji kace I love you,tace I miss you,ta lumshe ido,kayi mata kallon kauna,ya haka ne bafa mu gane ba mu,Ihsan tace amma ke ban taba ganin Yar shishigi irinki ba,Ina ruwanki to,mata da miji kika sani ko dazu na sakko na shiga wannan dakin.

Mero tace karya ne Aunty tun asuba Ina palon nan Banga motsin kowa ba,Haneef yace kowa dakinsa daban yake kwana Khadija bama hada shimfida,Mero ta bude Baki tace ka kyaleta? Wlh ka Mori sadakinka ko ka Kara aure hauka ake a garin Fir'auna ka taso wlh karka yarda,Haneef ya boye dariyarsa,Ihsan takaicin Khadija ya kamata tace ke na Kore ki daga aiki Yar iska marar mutunci marar tarbiyya Ina ruwanki da aurena,bana shiga harkar mutum amma ke wlh mun sa kafar wando Daya dake,Mero tace Oga ya dakko ni ba ke ba Kuma gyara nayi Allah ya Gani ko a Islamiyya Malam yace in kaga ana ba daidai ba in har kana da hali ka Hana to naga Ina da hali Kuma zan iya shi yasa,Allah ya bamu Ilimi mun nema Kuma mun samu dole mu Fadi gaskiya Mero ta furta kamar gidanta ne,Shi Haneef dadi yaji ta birge shi,dama Ihsan ta dame shi,dining suka zauna,Ihsan ta bude abubuwan sai ta toshe hanci tace wannan wanne irin soye soye ne,Haneef ya kalla yaga shi normal komai ya Masa ya zauna yace serve me,Mero tace ya Maka Kai? Yace yes yayi min,tace an gama ta fara zuba Masa.

AsmaBaffa
[2/20, 2:14 AM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫
A GIDAN YARI

BOOK 3
~TAIMAKO~

26-30

Official

By
AsmaBaffa

SADAUKARWA NE GA AIDA MAMAN TASNIM

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.