Tantiriya A Gidan Yari Part 3 Complete Hausa Novel
Reading file: Tantiriya_A_Gidan_Yari_Part_3_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 10 of 20
PAGE NAKI NE
Amatullah Kamshi
*ZINARIYAR MACE⚡*
*Wai shin 'yar'uwa menene matsalarki? zubewar nono, ko kuma rashin kwankwason juyawa a falo maigida ya shiririce ya manta da tibi da matan tictok, menene matsalarki ne? rashin ni'ima ko kuma mugun sanyin da ya yi miki katutu, shin rashin taushin fata ne ko kuma kuraje da tabbani, ko bala'in ramar da ta addabeki kuma babu rashin ci ba rashin sha a gidan auranki, gwaigwayewar gashi ce matsalarki ko kuma kaushi da faso na tafin kafa da bushewar fata, kina bukatar fatarki ta yi glowing kalarki ta fita kuraje su mutu, ko kuma kina bukatar azababbun turaruka da humra tare da turarukan wuta. Na san dai kuna da yawa matan da tumbi ya yi musu karan tsaye ina nufin ya katse muku hanzarin yi wa maigida gwalli da muskuce-muskuce a falo😃 Nesa fa ta zo kusa AL-KUTUBIYYA ISLAMIC MEDICINE sun tanadar muku da nau'in magungunan da suke magance kowace irin matsala da izinin Allah. Babban burinmu shine sha'ani na aure ya inganta a samu daidaito. Muna da.*
Na gyaran nono.
Na sanyi.
Dilka tare da hadin sabulu.
Duk Wani nau'in maganin mata.
Humra turarukan wuta perfumes, original miski tahra 3in1, ciccibi budurwar kaza. Had'addun supplement irin wad'anda ba su da matsala. Maganin Sliming wato narka tumbi. Abubuwan da muke sayarwa suna da yawa, kuma babu asarar dukiya. Muna garin kano kuma muna tura kayanmu kowane gari fad'in Najeria da Nijar har ma da kasashemn ketare. Kai tsaye a tuntu'bemu ta lambobin wayarmu domin karin bayani.
*08089965176*
*07084653262*
Yar Inna tace karka fada Dan Allah bawan Allah ya mutu da dadewa,Wa yace yayi sai na fada....Umma ce ta rufewa Abba baki da tafin hannu,yace ko ba yau ba sai watarana na fada,tana sakar Masa Baki yace Jauro da babansa suka nemi budurwa daya suka dinga fada a junansu,Jauro yace da Habiba idan babansa yazo ta fasa Masa Kai da dutse,shi Kuma Baban Jauro ya sa yaran unguwa suka dinga fesawa Jauro Mari....
Shewar su Naila yaji suna hira tayi dadi,Abba yace bazai wuce hirar mazajen su suke yi ba.
Naila ce Spark ya kira ta yace yau ba Kwalbewa,Naila tace Kuma sai Nan da 3days zan dawo,yace ban yafe ba kwana daya na bayar gobe da wuri zanzo na dauke ki da kaina,Naila tace in kayi hakuri da kaina zan dawo,ban yarda ba Baby,kin San Allah ba wai maganar Kwalbewa ba kawai gidan babu dadi ba kowa da ma kin haihu ne sai ki bar min dana ko 'yata muna tare amma ba kowa ni kadai,Naila tana kashe Murya tace Baby,Spark yace Kai Ina Shan Baby Ina morewa wallahi,ga Baby Dan jakar uba Kato,dariya suka dinga yi su Chika sabo da suna Jin wayar me ake yi,tace dama dai kaga ka dade baka siya min komai ba,yace takalmi sabo ya fito kenan,Naila tace ba shi bane fa kamar zata yi kuka,Pleaseeeee....yace uhm Ina jinki,wani turare ne Babynka Kuma yaji kamshin yace Yana so,Spark yace a Ina yaji? Yana ciki ace yaji kamshi Yana so,komai aka tashi ace Baby ne,rannan kika ce yace a baki kudi,ni Gani ubansa idan so yake ya min magana da kansa,ki fada Masa ya sameni ni ubansa muyi magana,Ikhram suna ta dariya a boye an kure Naila,tace ai baza kaji muryarsa ba akwai wani Abu daga uwa sai da suke magana tun Yana ciki babu me Jin maganar sai uwarsa,Spark yace naji wannan karo wata,turare ne na daki Dana jiki,Dana ajiyar kaya,da na toilet etc,duk idan zan siya da dan yawa za a kashe 70k,baya fita kamshin,Spark Yana ji yace shi Dan ya bari a siya Masa ragon suna tukun,yace a yanka Masa ko bashi ne wannan yafi muhimmanci,Ina ATM din Dana baki? Naila tace na siyawa Baby kadara fili na siya Masa,Spark yace Dan Allah da gaske kike ko karya kike? Naila tace da gaske na cinye kudin Nan Amma ba kadara na siya ba,wai nawa ne kwata kwata a ciki,ni bana shanawa a gidan mijina,mene amfanin me kudin,Allah ya hore Maka dole naji dadi wannan kudi baza su dawo ba sisi bazan bayar ba na cinye,murmushi Spark yayi yace idan kin cinye ma ai kanki kika yiwa one Kobo bazan baki ba wlh,gwara na taimaki marasa karfi ke kina ci kina koshi,turare shine matsalarki,kin San ana ta kwana da yunwa wasu yanzu suna Nan suna cewa gari zai waye Ina ma a wuce gobe a tsallake ta a fada jibi sabo da wahala.
Fushi Naila tayi tace kudin ba yawa fa kasan bazan kashe su a banza ba wlh,kaima kasan da dalili,to me kika yi da su fada min,Yan uwana na kauye na taimakawa aka siya musu kayan abinci na raba musu,yace wai kuwa Ina Malam Ya'u Dan caca Wanda ya cinye ki a caca? Naila tace so nake in muka je tare ya ganka,okay idan nazo daukanki gobe sai muje can mu kwana Daya,Naila tace ai su Goggo suna Nan mu bari sai sun koma,yace to ba damuwa,yanzu dai kudin turare zan bayar? Tace ae akwai wani takalmi Shima...bazan siya ba Shima turaren Dan Yana da muhimmanci ne,Naila tace dan Allah in na dawo zan baka bado sau ba adadi,Spark yace ko Baki bani ba ai zan kwata ta karfi, kawai bana so turaren ya wuce ni ban siya ba,Beauty ce ta samo mana me siyarwa,Yace to an gode mata za a siya,Beauty ta siya ma bare ni ko million ne sai na siya miki,Naila taji dadi tana murna tace ai na sani,nifa nayi dacen miji.
Sun dade kafin su gama waya .
Washe gari da safe a masallaci kafin ma Mohsin yazo Abba yasa an radawa yaro suna Hasheem,Naila tace ai dai baza a Fadi ubanmu ba sai a samo suna a Dan makala Masa na saka Masa Ashraf ai akwai ma'ana me kyau,Chika tace ba gwara Misam ba,Beauty tace duk kunci ubanku sunansa Annoor shi nake so,ba Annoor mijin Iman ba kawai sunan ne ya min tun da dadewa Ina son Sunan shi yasa,Iman tana zuwa taji ana cewa jariri Annoor tace Annoor Dina? Beauty tace ba shi ba a wanne dalili so kawai nake na saka Masa abina,Allah ya Masa Albarka,Iman tace a kasar Nan naga alama kowa a cikin fushi yake amma sai a dinga nuna a farin ciki ake kowa pretending yake Yana yake,Ina shugowa wata mata ta dinga masifa zan take ta wai,Naila tace Goggo ce fa suna dariya,Mohsin ko zuwa gidan baiyi ba ya barwa Abba komai a hannunsa an radawa yaro suna an yanka raguna uku manya.
Sai da Beauty ta tsala wanka yazo gidan Abba yace sai yanzu kaga damar zuwa wai Kai me gida ka haihu ko,sai an jira ka nufinka?Mohsin yace to Abba gani nayi ka Isa komai a wajen shi yasa ban zo ba sai yanzu,Allah ya shiryeka Mohsin ga raguna Nan an yanka anyi komai,Kai Mohsin yanzu duk wannan ragunan na Beauty ne? Ina na sirikin Beauty? Zan fara hassada gaskiya,Mohsin dariya ya shiga yi yace ta Sanwa Siriki ko a plate ne,Allah ya kiyaye ai wlh da bazan karba ba,Allah sarki Yar Inna da kyar ta samu aka yi yanka a haihuwar Hidaya data Naila,lokacin muna tsananin babu sai babanta ne ya bamu rago,a haihuwar Hidaya,Naila kuwa Tinkiya aka yanka,Kai lokacin kana da gata an bar min gado rago biyu na yanka Maka,Mohsin yace shi yasa nake da Albarka,Abba yace ba wani nan,wlh idan Jauro Bai zo min Suna ba babu ni ba shi ko gidansa bazan sake zuwa ba naga har yanzu bai zo ba,
Annoor kuwa da shi aka rada suna a masallacin mutumin da ban sa rai ba yafi surukin nawa ma Nabeel,sai na ganshi yazo shi da Haidar,sun kyauta ai cewar Mohsin,ciki ya shiga ya gaida Umma,Naila tana zaune tana kwalliya a tsakar gida da mudubi a hannu,gaisawa suka yi ya shiga dakin me jego kasancewar Safiya ce babu mutane sai yamma.
Jauro da wuri yazo ya dauki Abba suka bar gidan suka tafi gidan Amaryar Jauro,Abba Yana zuwa yace shi yasa nake son Habiba wlh tana can ta tafi gidan Sunan jikanta amma ke kina nan gida, Jauro yace ban gane kana son Habiba ba wlh ko na rigaka mutuwa ka auri matata ban yafe Maka ba,Abba Dolo yayi dariya yace Allah sarki Habiba ba ajina bace duk matanka ba ajina a ciki,haba Jauro ai sai dai in na mutu kazo neman auren 'yar Inna Kuma wlh fatalwa zan Maka baza ka taba Jin dadi ba sai na dinga fito Maka a horror,duk Wanda na mutu ya auri Yar Inna ya gama Jin dadin duniya,bazan taba mutuwa gaba daya ba sai na dinga yin fatalwa,Jauro yace ka gaji ma ka mutu gaba daya din,yace in banda ma abinka Habiba ai Bata waye ba ko ka mutu ba abinda zanyi da Habiba sai dai na dinga kawo mata tallafin kayan abinci.
Maman Annoor abinci ta kawo musu Jauro yace munci a gidan suna Yar Inna ta zubo mana girki,ga waina ga sinasir,ga tuwo ga shinkafa dafaduka ga Soyayyar shinkafa ta Sha koron wake da yelluwar Masara,girkin da su Habiba da Maman Annoor har a koma ga rabbana baza a iya ba cewar Abba,Maman Annoor
Jauro Yana Jin Abba yace hmm wlh da zan iya daina Aboki da Kai da tafiya ta zanyi na daina kulaka kaddararren Aboki ka dame ni ka dami iyalina,Abba Yana Jin Jauro Yana surutu yace Jauro ka tuna Baffanka lokacin yana jinsa da jini a jika yace Habiba yake so,Jauro yayi dariya yace muka dinga takara muna fafatawa da Baffa akan Habiba,Abba yace an Dade ana abin kunya a duniya,Jauro yace na dinga gaba da shi nace da Habiba idan yazo zance kawai kar tayi tunanin Uba nane ta fasa Masa Kai,Ashe ya fini target ni Ina zuwa zancen yasa yaran unguwar suka Kwada min Mari yafi biyar,ranar da za'a daura aure naje na sace Habiba muka gudu,sai gashi ana rokona na dawo a daura Dani,lokacin ana tsoro kar na lalata ta,Habiba Kuma ita ga virgin me tsoron Allah,Komai aka yi Jauro ba kyau Allah ya hana,Miko min takalmi Allah ya Hana Jauro ni ba matarka bace babu kyau ka sa wata mata tayi Maka hidima,Maman Annoor tana dariya tana saurarensu.
Sai yamma likis Annoor ya biyo daga wajen aiki ya kira Iman ta fito su tafi gida,sallama ta musu,Beauty ta bata kayan suna wani cake da tarkace a cikin wata jaka me kyau,ta shiga kwalawa Naila kira..Nailan Spark.....Nailan Spark nake nema ta leka wani daki...dai dai lokacin Spark ya shugo gidan tare da Mohsin,yaji ana kwalawa Naila kira Nailan Spark,yace ko wace wannan ta iya kiran Sunan, ya furta da kansa Nailan Spark sweet name,Iman ta sake kiran sunan Nailan Spark zan tafi,Spark yace ga dai Spark din Naila,murmushi tayi suka gaisa,yace kin iya saka suna,Naila ce ta fito tace Iman wai har tafiya? Yazo fa yana waje,Naila tace to ki gaida gida muna godiya In na dawo zanzo,Allah ya kawoki Beautyn Mohsin ta shiga wanka kice na ware na gode ta juya ta fita,tana zuwa Annoor yace Ina Hidaya? tace yau ana suna gidansu ai baza mu tafi tare ba,ban gane ba Dan Allah je kice ta fito mu tafi sauke ta zanyi a gida.
Iman ta koma ta kira Hidaya tace ki taso mu tafi inji Sweet,Hidaya zata yi musu Naila tace in kin zauna uban me zaki wa wani ke ba aiki kike ba sai kwanciya, tashi ki tafi,Hidaya zata yi magana Naila ita a dole babba tace ki tashi ki tafi wlh wai wanne irin Abu ne wannan,tashi tayi kawai ta gaida Spark tace Umma na tafi,tun yanzu? to ya turo a daukeni ya zanyi Abba ya riga da ya bada ni,to ki gaida gida, ta fita suka tafi Iman tana gaban mota Hidaya tana baya suna ta hirarsu har Annoor.
Amare kuwa Nabeela da Rahma shirye shiye suke yi Abu Yana ta tahowa kusa.
Naila Shirin tafiya ta wuce tana yi,su Chika ma haka,Beauty tace Ina ma Nima a can nake tare da ku,Spark Yana wajen Umma bayan sun gaisa ya fita Yana jiran su,sallama suka yi suka tafi Zarah da ta rako Naila tace Aunty ki tafi dani,ki bari ayi hutu da kaina zanzo na dauke ki cewar Spark,Chika,Ikhram,Naila da Spark airport suka wuce,Spark ya gansu a hanya zasu jera da shi yace bazai yuwu ba kuyi gaba ku biyu ko baya ni da Baby muna tare,sai kace me mata uku sai kallona ake yi,Ikhram da Chika suka yi gaba Naila da Spark suna baya a haka suka shiga jirgi zuwa Abuja.
Mummy ce zaune tare da Yar uwarta a gidan yari tace har yanzu Spark bai zo ya duba uwarsa ba tun Ina Jin wahalar rayuwa a gidan Nan har na fara Sabawa ma,Maman Wahida tace wannan yaro baida hali,Ina gidan nan yake zuwa wajen wata banza bazai neme ni ba,danki ba Dan mutunci bane,Mummy tayi murmushi ta furta haba Yaya duk yaran Mima akwai kamar Dana?gaskiya nasan da dalili amma zaizo ne,tunda Yana min aike ai da sauki,tabe baki Maman Wahida tayi,su biyu a gidan yari basa safgar kowa sun hade kansu suyi fada su shirya ba sa kula kowa su masu kudi ne,Mummy ma tafi saukin Kai sabo da ta canja hali sosai kafin a kawo ta gidan yari,Maman Wahida kuwa har yanzu da akidarta ta kudi ita me kudi ce.
Naila suna komawa gida tace ya kamata Muje wajen Mummy har yanzu baka je ba fa,Spark Yana kwance yace Ina sane da ita bana so naje na ganta cikin damuwa ko naje na ganta a wani hali zan iya kuka,dariya Naila tayi tace Kai kuka baya Maka wahala a yanda Maza suke da karfin zuciya,kin taba ganin kuka na in banda akan Mummy? to yanzu a kaina baza kayi kuka ba kenan sai iya Mummy? Kishi kike da uwata dama ko,a'a ni na isa na hada kaina da ita ni a wa dorin dofino kunu bayan ludayi,rufa min asiri na mutu dakin uwata, akan me zan hada kaina da Iyayenka ai ko da Yan uwanka bazan hada kaina ba,ni da nake macen aure ko yaushe za a iya sakina,su kuwa fa Yan uwanka ne har abada Kuna tare,ni kuwa a gobe kace na tafi gidan ubana ya zama dole na tafi, ni dama bance na kaita ba,mu da aka auro mu a sama,ana ganin kamar taimaka mana aka yi mu gamu talakawa kullum kallon mu akeyi a taimaka mana aka yi ai,iyayen mu basu da shi,Spark tsayawa yayi Yana kallon Naila da mamaki,dakatarta yayi yace wait wait...yanzu Nan har kinyi fushi wai? daga Yar magana shike nan kin Fadi tafi Hamsim,komawa tayi jikin mudubi ta haye kan Inda ake jera kayan kwalliya tasan ba a zama a kan irinsa ba Dan kamar glass yake ai kuwa nan take ya fashe rukukus,ta tashi hankalinta sai neman masifa take, kayan ne babu Quality,ance za a min kayan daki akace ai an zuba komai gashi yanzu ko Shekara banyi ba sun fara fashewa,Spark ya kalleta kawai yace Allah ya shiryeki,tana jin haushi kamar an mata wani Abu,ficewa tayi taje kitchen ta dauki tire ta shirya abubuwan ci ta zauna a Palo tana ci,Spark ne ya ya fito ya Kalli tire din duk tarkace ne a ciki rakwacam,Bread take ci da kifi,ga Kuma Ayaba guda uku,lemon bawo Daya,ga ruwa ga lemo Mineral roba har biyu,ga Madara peak ta ruwa.
Dariya ta bashi ya Kalli tire din yace wannan duk ke kadai zaki cinye? ya dauki kifin yana cewa duk yaushe kike soya kifin Nan ne baya karewa,Dan Allah ki rage ai sai cikinki ya lalace ya dauke madarar da lemo Mineral,kuka Naila ta fara,Dana Yana so yaci Kuma baza a bashi ba,Spark yayi dariya Don Naila yanzu ta haukace sai anyi hakuri da ita,yace cikin nan fa ciwon hauka ya sa miki Naila,Ina zaki Kai wannan tarkacen kin kula shi tayi tace Ina zaka je? fita zanyi yanzu zan dawo,ba Inda zaka je ka zauna tausa zaka min waye yace kayi min cikin wato Kai kullum sai dai kayi wanka ka fita fes ni ka barni a gida da katon ciki Kai ka gama aikinka shike nan,bazai yuwu ba ayi min ciki a dinga wulakantani an gama Dani an lalatani,Spark Yana kallonta yace ai na daina fada Dake ni tunda kika cijeni rannan,idonki ya rufe kika manta nine kika cijeni sai da kika fasa min fata a ranar na tabbatar wannan yaron na cikinki ya haukata ki,ni wannan yaron ban San irinsa ba,Almajiranta zan kaishi can,Kin fasa min mudubi Baki bani hakuri ba,tsokanarta yayi,hakurin me zan baka kana da kudi ka siyo wani mana ai dama kace zaka canja furniture,ni din nace zan canja furniture? yaushe? ni nace to,ai ka canja min kafin na haihu,zo ka zauna a nan na jingina,Spark idan baiyi ba dama yasan ba son sex take ba yanzu ya shiga uku baza ta yarda ba"
Bata Jin Tausayinsa yanzu,bayanta ya Koma ya zauna tana tsakanin cinyoyinsa ta Dora bayanta a kirjinsa ta mimmike kafa a Saman kujera,tire din Yana Saman cinyarta,tace yawwa ko kaifa amma kawai sai dai ka fita,da ka fita mana na Gani,yace ni na Isa Yana dariya, ai ni gaba ta kaini Baby ki dinga sani Ina miki haka kullum,rigarta ya dage ya shigar da hannunsa ya shafa Dan cikin kamar ta fara ajiye tumbi haka yake,yace bari na fara branch a wajen Baby, sai yayi sama da hannayensa ya koma kirjinta,Naila tace ai dama baka kaunar Dan nan ba ta tashi kake ba,Spark yace Nima ba kauna ta yake ba,tunda aka same shi yake takura min tun Ina sonsa har na gaji,dariya tayi yace yanzu yau da na biye Miki da yanzu munyi fada yafi sau goma a gidan nan,na fasa mudubi kayi hakuri ai akwai kudi ka siyo wani,yace ai kayanki ne Dan mutum ya fasa abinsa ai ba damuwa,yanzu tunanin da nake ko zan samu irinsu a canja mudubin, Naila tace to ka bincika dai barna dai danka ne yayi ba ni ba,da Yana ciki yaushe ya fito yayi barna.
Suna hira Yana Murza Naila a nutse,tun bata so bata ji sosai har ta fara shiga Mood,hannayenta ta goge da tissue tace bari na wanke hannuna,tunda yaji haka yasan yayi nasara.
Hannayenta ta wanke da bakinta ta dawo ta furta Allah yasa bana karnin kifi,yace ai kece da ba ruwanki da kifi amma yanzu kullum ne sai kinci abinki,tace to ya zanyi Ina so.....bakinta ya rufe mata da nasa ya shiga tsotsa sai kace mayu duk kayan jikinsa sun tashi daga aiki sunyi mutsu mutsu,sun Dade suna Abu daya kafin ya samu shiga hanyarsa ya dinga kwasar gara a Palo, samu nutsuwa hirarsu suka dora cike da nishadi.
Mero bayan tayi Sallar Isha a zaune a Saman bed, kwanciya tayi Haneef Ya sa ta a gaba Yana danna wayarsa sai da ya gaji tace baza ka kwanta ba? Kinga gado ne? ba gado,Mero tace oh gashi mu ba arna ba bare na matsa Maka ya kenan,dariya yayi ba tare da ya kalleta ba, har bacci ya kwashe ta Yana zaune,gajiya yayi da zama kafafunsa sunyi tsami,gashi bazai iya kwanciya a kasa ba shi,ta juya baya ya matsar da ita gefe can karshe ga gado Dan karami,Mero farkawa tayi kadan tace tace wash ciwona....sorry ya furta ya tsaya Yana kallonta,sai da ta koma bacci sannan ya kwanta a haka a bed din kowannensu kamar zai fado kasa.
Juyowa Mero tayi da kyar taji ko Ina ba waje da kyar ma ta juya a Jikin mutum,idonta ta bude a hankali ta ganshi suna facing juna,murmushi tayi ta zubawa kyakyawar fuskarsa Idanuwa tana kallonsa sai da ta kalle shi son ranta tace yau Ina morewa,Dan ubanki Ihsan dawo ki sake fasa min Kasusuwa na,yatsa ta saka ta taba hancinsa ta cire hannunta da sauri,duk abinda take ba bacci yake ba Yana jinta,Mero tace fuskar gata da Dan fadinta ya kaga an Mari Haneef, marin ta gwada kamar zata sharara Masa Mari ta fasa,tace bari Muji gashin da Laushi ko karza ne ta shafa tare da lumshe Ido tace ba banza ba Yan mata suke kwarewa,idonsa ya bude da sauri Mero ta rufe nata tayi baccin karya.
Yana sani yanda zata ji yace yawwa tayi bacci,Mero da sauri ta dunkule waje daya tare da boye kirjinta wuyanta ya taba ba shiri ta bude idonta,murmushi suka sakarwa juna a haka suna kallon juna ta juya Masa baya tare da furta sai da safe,yace good night.
Washe gari Kwanan Mero daya a asibiti kawai sai ga Ihsan ta zo asibitin da kanta ganin Haneef bai kwana a gida ba,sanda ta zo ya fita siyo magani tana zuwa ta Kalli Mero a kwance Saman bed,Mero Ido ta bude yaga Ihsan ranta a hade,Ihsan tace Shegiya tsinanniya wato a Nan ya tare ya kwana a wajenki shine me jinyarki to bari na Kara rugurguza ki sai ya zauna jinyar da hujja tazo ta kama wajen da aka gyarawa Mero ta murde da hannu,Ihu Mero ta dinga tsalawa a asibiti,Ihsan ta kama Daya kafar ma ta dinga wujijjigata kamar zata cirewa Khadija kafar,Allah sarki Khadija kamar zata suma" da gudu ma'aikatan suka shugo suna rike Ihsan tare da kokarin banbare kafar Khadija a hannun Ihsan,Haneef ya dawo yaga abinda ke faruwa,Yana zuwa ya dinga zubawa Ihsan Mari har bai San iyakar su ba,amma Ihsan tace wlh ba Inda zani sai naga bayanta,Ma'aikatan ya sallama ya damki wuyan Ihsan ta fara kakari idonta ya firfito,Khadija tana kuka ta sheke da dariya me sauti taci gaba da kukanta ta sake fashewa da dariya taga ana Chaskara Ihsan,ya hadata da bango,tana Nishi tana furta a taimako,a....a...Taimaka min...Khadija Taga wani Likita ya shugo dan lukuti tace koma idan maganine na sha ciki kamar an Kifa kwarya,Likita ya rike Haneef dake faman caskara Ihsan yace mace ce fa ka shaketa tana kakari haba Sir, ya nuna Khadija yace wlh ba haka ake kishi ba,kina kallo abokiyar zamanki zai mata illa amma kiyi kuka kiyi dariya abinda kike kenan wato murna kike? Khadija tace ae murna nake ni kasan me tayi min,miji take aure shi nake aure matsayinmu Daya.
Ihsan tana hakki taci wahala fuskarta duk ta Sha Mari ta tasa tace wlh sai ka sake ni Allah ya kiyaye nayi kishi da wannan kazamar,nafi karfin zama da ita ni dama nayi saurayina ka sake ni kawai,Haneef tsaki ya ja yace ke ai mahaukaciya ce baki San me kike ba me za ayi da mace me halinki,Ihsan tace ba Inda zanje sai ka sake ni wlh ta zaro wayarta ta kira Hajji da Maman Haneef tana kuka ta fada musu ku sa danku ya sake ni na gaji da fasikancin da yake da zinace zinace,Karuwa har gida bazan iya ba,Hankalin Mama ya tashi ta zaci da gaske ne tace kiyi hakuri Ihsan gobe zanzo Inshaallah,ni ba ruwana kawai ya sake ni ya auri wacce yake so ni dama na samu wani,Mama tace a'a ban gane kin samu wani ba,da aurenki yaushe kika samu wani? Nidai a fada Masa ya sake ni auren zumunci ne ban yi na fasa kowa ya zauna da Wanda yake so tana fadar haka ta kashe wayarta.
Fitowa tayi asibitin tana sharbar kuka da kururuwa azo a taimake ni mijina ya kawo karuwarsa asibiti,Mutane da Yan zaman jinya aka taru aka cika, Ihsan tana musu bayani Yar aiki ya kawo min gida Ashe karuwarsa ce sun dade da sanin juna,bayin Allah ashe a boye dakinta yake kwana,da rana idan na tafi wajen aiki suna tare suna sabon Allah,tun suna yi a boye ya fito da shi fili,Ina zaune Yar aiki da ita yake Hira,da Yar aiki yake kallon film komai Yar aiki karshe har tayata girki yake a kitchen yanzu Bata da lafiya ya taho Yana jinyarta,ba iyayenta ba danginta babu mace shike jinya tare suke kwana ta ya bazan damu ba?
Wata mace ta dafe kirjinta da hannaye tace wannan yayi asara,ai ni tuni na dawo daga safgar Maza,basu da hali tsaf zaiyi abinda yafi haka,wata ma tace amma wannan anyi matsiyaci,wasu kuwa suka ce sai hakuri mazan duk haka suke,Mace daya ce a ciki tace to ke duk kina me? Ya kamata a bincika maybe baya sonki ya aureki,ko Kuma kece bakya abinda ya dace har ya fada wannan safgar Allah dai ya kiyaye,mazan suna ji ba Wanda ya bawa Ihsan gaskiya a Maza sai ma cewa suka yi ke dai ba matar arziki bace ba matar rufin asiri bace,da matar arziki ce baza ki iya yiwa mijinki fallasa da tijara haka ba,mene birgewarki da cinyewa,wannan halin naki yasa yake kula wata,wani yace tab wannan bashi da mata ya Kara aure kawai,idan nine sakinta zanyi cewar wani,Ihsan motarta ta ja ta ware gida ranta fes ta fashe haushinta.
Khadija da Haneef suna Jin abinda Ihsan tace da mutane,Khadija tace karka ji komai duk Wanda yayi Maka kallon banza kayi min kiss a gabansa ko uban waye na yarje Maka,dariya Haneef yayi yace banyi niyyar dariya ba fa Ina bacin rai,oh to ci gaba ke dariya koma ta furta, karka saki Ihsan Dan Allah,Haneef ya Kalli Khadija tare da sa hannunsa cikin nata yace zaki aure ni? mamaki tayi Jin abinda ya fada ba zato,tace Ina Yar aiki kalleni fa Ina ni Ina Kai me kudi, answer me" zaki aure ni? tafin hannaye tasa tare da rufe fuskarta ta furta ae,murna yayi yace na gode,su Hajji da dangina zasu iya hanawa indai ban saki Ihsan ba zasu ce bazan Kara aure ba,zanje da wasu da abokaina a daura mana aure ko basu sani ba indai Mama ta sani shike nan,ita nasan zata amince,Mero taji tayi nasara sai murna take a ranta.
Arham daga kwanciyarsa Haly ta kira Mima a waya ta fada mata, Mima tana dakin Papa tace kaga ka samu Arham da kanka kayi Masa magana wlh tun kafin a Kai yarinya ko ayi mata ma gyaran Jikin yaje ya nace mata,gaskiya in baza ka Masa magana ba a basu gidansu su tafi kawai yafi,ai ba tsari kowa yasan me ake yi,Papa yace Inshaallah wani satin za a kaita ku fara shiryata,ai kafin wani satin ya gama da ita kaje ka yi Masa magana da kanka tunda mu ya Raina mu,Papa yace muje suka fito da Mima dakin Basma Muryar Papa suka ji Yana magana Kai Arham zo Ina nemanka yanzu a part dina,Yana fadar haka ya juya suka tafi,Basma tace kaje za a Maka fada,Arham yace ni Banga amfanin wannan aure ba,na kasa gane kan wannan aure,Basma tace asiri aka yiwa su Papa da su Mima, mahassada sun mana asiri,Arham ya furta naga alama Rafeeq ne yayi min asiri naga yafi kowa bakin ciki Dani sabo da nine sakonsa kar na kamo shi,Basma tace ko Kuma Kawuna ba kana gani Sadakin nan da kyar ya bada su,Arham ya furta ba abinda bazai iya ba sabo da yaga matarsa ta tsufa nononta ya zube yayi yaushi shine yake min bakin ciki,Basma tace Kai wlh da sauranta yarinya fa ya sake aure daga baya sabo da hadama,Papa ne yayi tsawa Arham baka ji ne,Basma itama ba wasa tace gashi nan dama wayarsa ya manta Papa ta furta kamar Soja mace,Arham ya gama saka kayansa ko wandon nasa bai kulle Zip ba kamar zai fado boxers a waje ya fito,Papa kamar ya fashe da kuka sabo da rashin kunyar Arham ta gallabe shi,kallo Daya ya Masa bai sake ba,yace muje marar mutunci,dariya Arham yayi,Papa yace kace baka sonta bata da kyau ban iya zabe ba,Papa subutar baki ce na gane gaskiya,idonka Yana Gani Allah ya saka da Alkhairi Allah yasa a Kara Maka matsayi a wajen aiki,komai yayi perfect,Papa yace kar na sake ganinka a dakin Basma ko tazo dakinka Kun rufe kofa,Kai baza ka bari a kaita ba,Baka sonta fa jikinta kake so wlh in na sake ganinka kaje dakinta ko tazo Kun rufe kofa zaka yi wani Abu sai na Saba Maka,in baka son albarka ka sake zuwa ku rufe kofa ko tazo ku rufe kofa,in kana son albarka Kuma ka kiyaye taba ta,duk wata mu'amula ban hanaka ba amma banda wannan safga,indai kana so in Maka baki dan Allah ka sake azo a fada min,Arham yace har da Baki,ai Allah ne yace Dokar Allah ne wannan,to shike nan kaje ka Kuma tafi ka bani waje,Arham ya juya ya tafi Yana mamaki yace a daura ma aure ace kar kula matar ni na taba Jin haka,shike nan zanyi biyayya.
Komawa yayi wajen Basma ya bar kofar a bude,Basma tace ya barka ne? Arham yace yace yayi min Baki in na sake tabaki sannan kar na rufe kofa in muna tare sai an kaiki gidana,Basma tace har da baki? Arham yace kwarai,tace tab asiri ne,Allah ya karya shi ko waye cewar Arham,yace sabo da bakin ciki a aure ma sai an jefi mutum sai da safe ya juya ya fita,Basma ta rako shi bakin kofa tace Good Night bye ya wuce.
Yana komawa a Palo ya samu Shaheed,yace Mazaje ya aka yi ne? Arham yace uhm Papa ne yayi min baki kar na sake taba Amarya,Shaheed yace illar zama gida Daya da iyaye kenan,Basma tana ganin rayuwa zama da sirikai,Arham yace duk Maman Rafeeq ce take wannan zigar,ka kiyayi matar data kashe aurenta ta dawo,ana tausayinta ashe ita bata Tausayin kanta,Allah ya kawo mata bazawari ko irin Baseeru Kusa ne cewar Shaheed,Junior Yana jinsu yace gaskiya Papa bai kyauta ba a nan ya dace ace ya bari ka dan more,Arham yace kaima dai ka fada ni basu gane nufi na ba ma bazan yi sex da ita ba wannan in ta dinga kuka ai sai kowa ya sani Dan Tabesting a hana mutum wlh duk Wanda naji ya kirani Ango a gidan nan sai na taka Masa birki ni ba Ango bane,Arham ya zauna yana ta surutunsa kamar me.
Bangaren Basma kuwa kwanciya tayi abinta tana tunanin Arham dinta tace mutum Yana son Mijinsa a hanashi sakewa.
Washe gari Misam yazo gidan Mima Yana gidan Rafeeq yazo shima Spark ya shugo suna zaune suna hira da Maman Rafeeq"Arham ne ya fito Yana Jin Haushin kowa Yana Bata rai,Misam yace Ango Ango ka Sha Mai,Arham yace duk Wanda yasan yayi min asiri yaje ya karya abinsa tun kafin ya dawo kansa Yana magana Yana kallon Rafeeq,Papa sun min aure an hanani taba Amarya,sai kulla min tuggu ake yi a gidan Nan Kuma bakin da suke gidan nan ne suke wannan hadin,Maman Rafeeq tace ni kenan? tunda nice bakuwa a gidan nan,Arham yace Nidai ban kama suna ba Baki nace karki fadawa yayarki tazo ta tsine min,Rafeeq yace baka da hankali ka zare Arham,ni dai ba ni nayi Maka aure ba...
Basma ce ta fito sanye cikin doguwar riga fitted tayi kyau sosai,Arham ya bita da kallo Yana cewa Allah ya Kai damo ga harawa ranar kawai ku taho daukan patient zuwa asibiti,Basma ta karaso ta gaida su suka Amsa, Arham dake tsaye ta dan kalle shi ta rike hannunsa ta saki ta wuce, Maman Rafeeq tace nidai bari na tashi daga nan bazan iya Jin wannan Abu ba,Arham yace wlh yanzu na fara batsa a gidan man kowa ya gyara kunnensa ko a bani matata ko aji zancen Hallare da bado,haka kawai ba dama na kebe da iyalina na,Arham yayi Iyali inji Spark Yana dariya,Arham ya bi Basma,Misam yace Dan iskan yaro Hallare ta motsa Kai na tsorata da yaron nan Spark ya gado,Spark yace Kai baka ga iskancinka ba sai ni zaka ce ni ya gado Rafeeq ya gado,Rafeeq yace kwarai ni haka nake lafiya ce,inyi In Kara in sake yi bana gajiya haka nake,ni da naga Ikhram ma ba zaman lafiya,Spark yace tab sai kace Mima ya Kalli kofa yace kar ta jini suna dariya,Misam yace Allah yasa ta jika wlh yanzu Mima ta musulunta fada take yiwa yaranta.
Arham Yana shiga kitchen wajen Basma ya samu Mima a ciki,Mima ya kalla ya Harare shi tace Ina Nan to,yace dan Allah Mima magana zan mata,ba ruwanka da ita na fada maka ayi mutum kamar ayu wai meke damunka ne,Arham yace gado masifa ne musamman irin na kaka Zeenatu,Basma tana jinsu tace Ina so in kulaka Sunshine to kar Baki ya bika na hakura ya jiya din?Dan kadan me Albarka cewar Arham,Mima ta dakko ludayi ta biyo shi da gudu,tana dawowa wajen Basma tace ke ana so a kwato miki yanci kafin a kaiki ya fara sonki na gaskiya kina shirme,Yana nunawa jikinki yake so ke Baki fahimta,Basma tace ai duk cikin so ne a so Jikin mace ma ai so ne yanzu idan wata ce bazai taba ta ba,ni kuwa nayi Masa na birge shi,ai kune da Kun San haka Mima sai ku bari kar a daura sai ya fara so na,kina biye Masa din Yana tabaki ba dole a daura ba,nidai tausayinsa nake ji gaskiya cewar Basama,jiya ma haka yace yace sirikai sun hanashi sakewa,kice dai sirikai sun hanaki sakewa,Dan Allah ki bamu hadin Kai Basma ya fara sonki da gaskiya,Basma tace abi ta shortcut Mima yafi,zaki ga Shortcut ki sake kulashi ki gani a gidan nan ana kwatar miki yanci bakya gani.
Basma tayi shuru a ranta tace Ina naga wani yanci tunda aka yi min aure,a fili tace da dai an barshi ya karasa ragowar yancin dama babu ai Mima,Ina yanci ga macen aure,Mima Bata sake magana ba,tana kallo ta dakko sabon flask a kwali Shima zata farke,Mima tace wannan na Maman Rafeeq ne ta siyi abinta,ai bata da miji me zata yi da shi zan siya ya min kyau,Fisgewa Mima tayi ta Maida ta boye,Basma ta fito tana kuka indai ba a wannan flask ba to yau sai dai in Arham ya kwana da yunwa wlh baza ta Kai ba,Mima tace na Kai Masa da Kai na ta zuba Masa ta ba me aiki ta Kai,Arham yace Ina Basma fa kika kawo? tace baza ta kawo Maka ba sai a sabon flask,to a Bata sabon flask din mana bazan ci ba Nima a bata sabon tunda tana so,yanzu na kwace Sunan abokin Baban Naila Jauro bawan mata Nima na cancanci Sunan sai abinda mace tace wlh, Yar aiki ta koma ta fadawa Mima" tace ajiye a kitchen yunwa ai ba kanwata bace da kansa zaizo.
Mima dai Papa ta samu tace Dan Allah tunda an gama komai a bar Arham su tafi gobe a Kai Basma haka sunfi karfina tun kafin ya fara danneta a gabana,Papa yace Allah ya kaimu ni kaina naga yau ko gaishe ni bai zo ba alamar fushi yake,kyale su a kaita haka ta gane kurenta a can, washe gari Papa ya kira Arham yace babu bikin da za ayi Arham zo ka dauki matarka ka bar min gida,an hada komai ku tafi,Arham yaji dadi kamar me yace ai yanzu Safiya ce sai yamma,Papa yace a'a ta ebo kayanta ga Lefenta suna wajen Mima ku dauka ku tafi,Arham yace da safe? Ae da safen fa ku tattara ku tafi karka Kara 30mnt a gidan nan,amma ai ba fushi kayi ba ko Papa? Ba fushi nayi ba Arham ai kasan fushina tunda ka matsu ku tafi ai ya fi,yace to mun gode ayi min nasiha,Papa yace a'a ai Kuna da hankali Kun fimu sanin ya kamata wacce nasiha,Arham yace ni ba a so na kowa an Masa nasiha ban da ni ,amma ai ita dai Basma din ayi mata nasiha ta kula dani sosai,Papa yace itama tana da hankali ai,ka karasa ladanka Papa in ka barmu haka sai muce fushi kayi, amma dai ko ayi hakuri da zaman tare ai kace.
Basma da safe taji Mima tace tayi wanka ta shirya ta zabo mata sabon kaya cikin na lefe riga da skert na Leshi fari tace ki sa wannan,ta zaci unguwa zasu je ta shirya abinta sosai,Mima ta zauna dake ita uwa ce tayiwa Basma nasiha da fada na zaman aure,Basma tace wai ina zamu je ne? gidan miji za a kaiki,Basma a ranta tace sun ga haazaa,wa ya gaya muku barno gabas take,a fili tace tun yanzu za a kaini ai da yamma ake Kai Amarya,Mima tace ku yanzu za a kaiki shi zai tafi Dake daga baya zamu zo ganin gida,Basma tace to Allah ya kawo ku.
Tana fitowa ta zauna a Palo ana ta Kai kayan Lefenta mota,Mufee suna zaune suka ce Basma kin dakko shanyarki kuwa? tace na manta na gaji ne ni an kusa kaini gidan mijina ma na huta da wahala,ga Inda zanje na huta na harde kafa daya kan daya" Nan kuwa duk an dameni ,Haly tace Allah ya taimaka Basma Allah ya baki hakuri Kuma,Papa yasa aka kira Masa Basma ya mata nasiha Shima a haka ma Mima ce ta dage sai anyi amma wlh yace bazai wa Arham ba,Ita Mima ta samu Danta tayi Masa nasiha,Arham sai da yaga an bashi matarsa sannan ya kwanta a cinyar Mima yace zanyi missing dinki yau Allah ya nuna zan koma Shan abincin yara,Shekara ashirin da Yan hayaniya da yayeni,Mima ta durma masa duka ya saki Kara,ni kake fadawa haka Dan ubanka? Kishi kike? Ke kika yayeni sai dai kiyi hakuri,Mima tace sai naji bana so ka tafi,Arham yayi dariya yace ya zama dole kuwa ai namiji Dan gidan wata ne,ya mace ake cewa Yar gidan wani ce inji Mima,yace Shima namijin haka Mima tunda ai dole ya bar gidan su,tace shike nan gobe kazo da wuri na ganka,to zanzo ai ko baki ce ba ma,za a kawo muku abinci? Arham yace Papa yace an hada komai na girki idan naga normal sai tayi in baza ta iya ba Kuma an samu matsala sai na kiraki a waya,amma na rana Dana dare kar a kawo da safe dai nasan za a iya samun matsala gobe da safe akwai matsala za a iya kawowa,tace to shike nan babban magidanci,dariya yayi yace kayana kadan na eba zan dawo na tafi da wasu gobe,tace to,yace Spark Yana cewa sai Nan da 4yrs za a Kara biki a gidan Nan to gashi matarsa ma bata haihu ba anyi wani,Kuma fa namu Albarka zaiyi ko ganga Daya ba a buga ba,ko kwano bai ce kwal ba bare a tara mata da Maza a gwamutse,Mima tace kar dai ka zauce,Dan Allah ka kula da yarinyar mutane,ka bi komai a hankali yace nine fa Mima Arham dinki guda karki ji komai.
Arham ya shirya an fesa wanka na gaske kamar yau aka daura auren,Papa ya sa Driver ya kaisu,Arham yace to gobe na sa a kawo min motata,ba Wanda aka fadawa Kai Amarya daga Ango sai Amarya suka tafi.
Amarya tana bayan mota tare da Angonta da hantsi gatsai gatsai.
Maman Haneef washe gari tazo tare da Hajji da wasu Dattijai Maza dangi su biyu sun taho sulhu,Haneef Yana asibiti ,Khadija ta dingiso daga toilet tayi wanka ta fito ta zauna da kyar tana dafe bango,wayar Haneef ce tayi ringing,ya daga,Mama cikin fushi tace yazo gida suna Nan,sun samu Ihsan tayi girki ta kula dasu ta sake fada musu karya da gaskiya sun hau sun zauna,shi yasa cikin fushi tace yazo gida,Salamatu ya kira a waya tazo ta kula da Khadija sannan yace Khadija zanje naji,tace duk tsiya karka saketa Dan Allah tace ai tayi saurayi naga ta yanda zata auri saurayin nata mu gani,duk so take yanzu a sake ta sabo da ta samu Wanda zata iya juyawa son ranta,irinsu haka suke basa aure Dan soyayyar tsakani da Allah sai in zasu juya mutum son ransu sannan suke aurensa,ai yanzu taga baza ka juyu ba,karka saketa kace ka fasa auren in sun matsa daga baya sai suji a salansa,dariya yayi yace haka za ayi sai na dawo ya fice Salamatu tazo suna ta hira da Mero.
Haidar sabo da ya samu kafar zuwa zance gidan su Mufee ya nace sai da aka daura auren Sudan da Rahma Maman Iman,ita kanta Iman sai labari taji,sannan Haidar ya dage wai biko zai Masa na Maman Rafeeq sabo da kawai ya fake da zuwa can,ana daura aure Jauro yace tunda miji a shirye yake itama in ta shirya za a iya sa rana su Habiba su rakata,tace Nan da sati zata tare,Iman sai labari taji ma,tace Allah Sanya Alkhairi.
Haidar kamar uwarsa ce ta tare harda kiran Ikhram yace wani satin muna hanya zamu kawo Amarya,tace Allah ya kaimu,yace Ina yarinyar nan kuwa me hankali ta gidan su mijinki kanwar mijinki? Ikhram tace Mufee? Ai tana nan lfy,yace yarinyar nan Inda take birgeni akwai hankali ga ladabi,tayi a rayuwa Ina son mutum me hankali da nutsuwa,ga gaisuwa tana ganinka zata gaishe ka,Ikhram tana ta dariya a ranta tace bai san iskancin da suka tsula ba duniya ce ta bi da su,Ikhram taci gaba da zuga shi tace ai duk tafi matan gidan hankali,yace gata kyakyawa,tafiyarta kawai abar kallo ce wani chafe chaf chaf....zanzo ki jawo min ita,duk da Ina da number dinta amma kwarjini take min gashi tana ta ja min rai,haka nake son mace me aji...Ikhram tace ai indai kana ciki zan Maka campaign,yace Dan Allah ki taimakawa Dan gaba da fatiha,irinku sai an tsaya mana muke samun aure,tausayi ya bawa Ikhram tace a ranta Iyaye suna cutar yara irin wannan,mutum har mutum irin Yaya Haidar,tace Inshaallah Yaya Haidar kamar ta zama taka,su basu da matsala wuyarta na fadawa Spark wlh sai an baka,ko Rafeeq sai Inda karfinsa ya kare akan wani nawa ya samu ci gaba ba abinda bazai min ba,yace na gode sister Allah ya bar zumunci Mama ta kusa zuwa gari tace nan da sati inshaallah tare zamu zo Abuja,tace Allah ya kaimu dan Uwa" ya kashe wayar tare da furta Ameen.
Masu Sharhi Wanda basa gajiya Ina matukar godiya.
AsmaBaffa
[2/28, 7:36 PM] AsmaBaffa: 🏫TANTIRIYA🏫
A GIDAN YARI
BOOK 3
~TAIMAKO~
51-55
Official
By
AsmaBaffa
SADAUKARWA NE GA
AIDA MAMAN TASNIM
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.