Age Mates Complete Hausa Novel
Reading file: Age_Mates_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 12 of 44
Adinga sharhi ko Arage yawan page🥹☺️
wannan book d'in na kudine! idan kina buk'atar siya serious 500 normal grp vip grp 1000
Acc n 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK kituro shaidar biyanki 08100084251
dan girman Allah da dajarar iyayenki karki mun mgn idan baki shirya siyaba
Bana son kira a what's app kawai zakimun mgn
Idan kika karantamun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitar mun Allah ya isa banyafe miki ba
#Mommyn fareesa
#Dr Nura Darma
#Ahyaan
#mr Mahuta
#AA mashi
#mu'az
#Khairiyyah
#Ammah
#Ummah
#ikkhee🧍 *AGE MATE'S* 🧍♀️
*21&22*
*Littafin kud'i ne!*
.......rai b'ace Dr darma ya nufota ba tare daya furta komai ba, sai Ido kawai daya zuba mata yana kallonta "ita kuwa cike da Isa ta juya ta tsayar dame nafef tana sanar masa inda zai Ajiyeta"yayinda Ikhkhee ke tsaye tana kallonsu babu ko k'iftawa "saidai bata jin me suke fad'a....k'ok'arin shiga cikin nafef d'in Ahyaan keyi taji hucin numfashinsa gefen fuskarta "Atake Tasha mur"kafin tayi mgn ya finciki hannunta da k'arfi yana watsowa me nafef d'in mugun kallo ,murya Akausashe yace"kai mlm yi tafiyarka"ke kuma wuce muje ko ranki yab'aci yanzun nan.....saidai rayukanmu su b'aci wlh"Akan me wai zaka dinga tursasani ne?"nace bazan bika ba dole ne?"ta fad'a cikin hargowa tana k'ok'arin k'wace hannunta daya rik'e"banza yamata yaci gaba da janta da k'arfi"yayinda me nafef be furta komai ba ya wuce kawai sbd shakkar Dr darma da yaji lokaci guda"duk yadda taso ta k'wace hannunta kasawa tayi ga yatsan k'afarta na mata zugi dole ta hak'ura tabishi"ga kunyar Anata kallonsu bakin titin kuma....babban kuskuran da zakiyi shine ! idan na cikaki zan hau kan mashin d'in nan ki gudu"ya fad'a murya babu Alamar wasa yana cika hannunta ya nufi gaban mashin d'in,bayan ya hau tak'i zuwa ta hau tana dai tsaye tasha mur"ya girgiza kansa kawai ya iso gefenta beyi mgn ba"Ananma banza dashi tayi"wlh kika bari na sauka d'aukar ki zanyi na d'ora saman mashin d'in naga k'arshen zafin kan naki da gaddamar taki "ba tace komai ba sbd tasan zai iya yin Abinda ya fad'a"sai kawai ta dafasa ta hau saman mashin d'in "shi kuma yaja"saidai tana ganin sunyo wajen da Ikhkhee ke tsaye har lokacin tana kallonsu"ba tare da Ahyaan tayi mgn ba kawai ta fara yi masa chakulkuli k'asa k'asa....ke wai meye haka?"baki gani Ana...sai kuma yakama murmushi "wlh koka wuce daga inda kake son mu tsaya ko kuwa bazan fasaba saidai mu fad'i da mashin d'in"bece komai ba suka wuce ta gaban Ikhkhee "Ahyaan ta tab'e baki"ganin ya fara sharara gudu ya saka ta rik'e gefen rigarsa tana masa magiyar ya rage gudun"saiya shareta"gab da zasu Isa gida ta lura dame siyar da kayan fruit da rake gefen titi"broth ! yayi shiru"kanafa jina ko?"menene?"ba rake nakeso ba da Ayaba,kuma gasu can mun wuce ka siyamun pls"Amma ba kud'i hannuna saidai in mun koma gida"yayi shiru "dan Allah nace fa"mitsssssuww! kinada matsala wlh"nidai komi zakace kace ,Amma ka siya mun sbd inaso"kin san Allah daga yau kika koma cemun kina son wani Abu kuma kud'inki zaki bada na siyo miki sai kin sani"idan har hakane meyasa bazaki tura wani ba dole sai ni?"wato kinfi k'arfin kice na siya miki kome?nidai in ba zaka tsayaba shikenan"ta fad'a kamar zatayi kuka "ya tab'e baki ya gangara gefen hanya ya juyo suka nufi wajen masu siyarwa d'in...bance ki kalli gefen da suke ba ki juya ki kalli gefen haggunki"bata kawo komai Aranta ba ta juya d'in kamar yadda yace tayi"shi kuma ya tsaya ya musu sallama yana nuna Abinda yake buk'ata"bayan sun zuba ya zaro kud'insu ya basu suka mik'a masa ledar "ungo ki rik'e nan"yafad'a yana mik'o mata ledar"haba broth! nafa rik'e gefen rigarka sbd karna fad'o taya kuma zan rik'e leda?"na rasa meyasa kake son cin zalin nawa da nuna mun rashin tausayi?"bece komai ba yamaida ledar gabansa yaja mashin d'in suka wuce"da gangan yake gudu Amma saita rintse Ido ta rirrik'esa"saida taji Alamar sun iso gida sannan ta bud'e idanunta"taga yana k'ok'arin yin parking"cika gefen rigarsa data rik'e tayi ta sauka daga saman mashin d'in tana d'an gyasa k'afar "shi kuma ya sakko ya kafe mashin d'in ya biyota da ledojin A hannunsa"itace daga gaba shi yana biye da ita"ko sallamarsu mamy bata Amsa ba tace"yaya jikin kun dawo ne??"fad'awa jikin mamyn tayi ta saki k'aramin kuka "da mamaki Dr darma ke kallonta saiya daure fuska"mamy ta bishi da wani irin kallo irin na tuhuma fuska Ad'aure tace"meye kamata da kuka fita?"ni kuwa meye zan mata mamy bayaga kyauta tawa?" shine zata kama kuka tamun sharri na mata wani abun ko?"ke kuma kin kyauta"ya fad'a yana Ajiye ledojin yasa kai ya fita kota kan Abincin da yake nufin yaje yaci be biba"mamy kuwa rarrashinta ta dingayi ta zuba mata Ayabar cikin plate da raken"sannan ta kamata ruwa tasha magungunan...har Ahyaan ta gama ciye ciyenta tayi sallar magrib da isha'i uban gayyar be koma shigowa gidan ba "ranta ya bata yaji haushin Abinda ta masa jiya"wata zuciyar kuma na sanar mata k'ilan wajen wannan yarinyar ya tafi.....
misalin k'arfe 9:48 pm ummah ce zaune Abed room d'inta tayi tagumi Abin duniya ya isheta"sbd kimanin kwana 6 kenan tana ganin Abba na nuna k'yank'yaminta ko girkinta baya ci,baya kusantarta ranar kwananta"sannan sai yace taje d'akinta ta kwana baya jin dad'in jikinsa"hankalinta ya tashi matuk'a "sbd itadai tasan tayima mama Asiri irin hakan yafaru da ita"Amma gashi taga yana neman dawowa Akanta?"saidai bata tabbatar da zaton nata ba"tana dai zaman jiran shigowar Abban sbd yau ta Amshi girki...Abba kuwa sai goma saura ya shigo cikin gidan"k'arar motarsa ta saka ummah luba fahimtar ya dawo gidan"hakan yasa ta mik'e tsaye ta fesa turare tana k'ara gyara doguwar rigar dake jikinta ta bacci ta fito tsakar gidan"tana fitowa ta samu mamah na tsaye daga bakin k'ofar parlourn ta tana masa sannu da zuwa "ya Amsa yana mik'a mata leda guda ,ta karb'a da hannu biyu tana masa godiya"tsaki ummah taja ,gaba d'aya suka juyo suka kalleta da mamaki"Abba na yamutsa fuska yace"zainab jeki ciki saida safe"to Alh Allah yabamu Alkhairi"ya Amsa da Ameen yana bud'e k'ofar d'akinsa ya shiga"ummah ta biyosa fuska bbu walwala"ko zama beyiba balle ta masa sannu da zuwa tafara da cewa"Alh na gaji da irin banbancin da kake nunawa Agidan nan"Akanme ranar kwanana zaka fara zuwa ka bata Abu?"kinga dan Allah bana son fitinah lubah, Agajiye nake"leda ce daiko ?to ga taki kema"daga yanzun idan kwanan nakine zan bayar Abata in har na shigo da Abu irin haka"idan kwananta ne zan dinga baki sbd nasan ba komai zainab ke k'orafi Akan saba"uhmm ! ba shakka, Ai gara ka ya beta gabana Ai "banza da ita yayi yak'i mgn "dama inaso muyi wata mgn dakai"Ina jinki"meyasa kusan sau biyu kwanana na zaga yowa kana k'in cin Abinci nah,sannan kace naje d'akina na kwanta??bayan kuma ranar girkin zainab nan d'akin take kwana?" cikin b'acin rai yace"sbd Ina jin kina warin jab'a ne "kuma ko yanzun haka warin kikeyi"sbd haka kije ki nemi magani zaki dawo kwana kamar da"wacce ta tsare miki gaba Arayuwa"ba sbd jin dad'in ta take kwana ba"saidan sbd nace ta dinga kwana"kuma duk ranar kwananta saita tabbatar Asma'u tayi bacci take zuwa mu kwanta" Asuba kuma nayi kafin yarinyar ta tashi zata koma d'akinta "taso ta dena kwana nine nan na hana"ke kuwa dayake kwanan ne Agabanki, dana dawo zaki kwaso jiki ki taho"da Asuba saima nadawo masallaci wani zubin nake tashinki ki koma d'akinki ko nauyin Khadija tasan nan kike kwana bakiji.... Abinda zakace kenan ko?"to nagode kaje kaida Allah "Allah ya Isa ban yafe muku ba"kullum kwanan duniya nice baka k'auna wacce bata yin daidai"zainab itace keyin daidai Awajen ka"shine yau harda sharri zaka jefeni dashi wai Ina warin jab'a....ba k'aramin sukar zuciyarsa maganganun ta suka yiba musammun Allah ya isan datayi"Amma da yake dare ne saiya barta"hakan yasa ta mik'e tsaye ta fita hankalinta tashe tare da tunanin zata je gun boka...Abbah ya sauke numfashi yana tunani"tunda ya Auri luba be tab'a jin sonta ko sha'awar taba "tunda dama mahaifiyarsa ce ta tursa sashi ya Aureta "yana dai sauke nauyine sbd ya fita hakkinta yake kwanciya da ita"tsawon zamansa da zainab ba zaice bata tab'a yimasa laifi ba sbd yau da gobe sai Allah "Amma kyawawan halayenta ya saka ya jure cin zarafin da mahaifiyarta(Ammah) ke masa ya zaunah da ita" sarai yasan itace ke cusawa Ahyaan son ta Auri me kud'i"shi kuma yaci burin kowa ta kawo sai yayi bincike kansa yaga ya cancanci ya bashi ita ko kuwa??"shi yanzun fatansa tama samu Aikin.....ya jima a zaune yana tunani"in bacin wasu dalilai da tuni ya saki luba"saidai wlh lokaci yake bata"nan gaba saiya bata mamaki....washe gari da safe Ahyaan ta tashi k'afar da sauk'i harma ta k'ame"ga Aikin had'a break fast mamy ce keyi tace ita ta huta"gaba d'aya su khaleel sai nan nan sukeyi da ita sbd wai batada lafiya"ita dai saidai tayi murmushi tana jin dad'in hakan"tana lura koda Asuba mutumin nata be shigo ba"gashi har 7 am ta d'an gota be shi goba"can ta tashi ta saka hijab taje kitchen ta sanarwa mamy zataje ta gaida su mamah"bayan ta fito har zata wuce ta lura da d'akinsa bud'e yake"ga mashin nasa shima gefe Ajiye yasha wanki"tsintar kanta tayi da nufar k'ofar d'akin"sau biyu tayi knocking! waye ne?"shiru tayi ta turo k'ofar ta shigo da sallama.....da sauri ta juya k'irjinta na wani irin bugawa" sbd ganinsa tsaye gaban mirror sanye da dogon wondo na jeans"yana warware farar vest zai saka.... yad'an kalleta ya tab'e baki sbd ganin duk illahir jikinta rawa yakeyi tanama k'ok'arin fita...dama gulma ce ta kawoki kenan ko?"ya fad'a cikin taushin muryansa yana Ida saka vest d'in"kayi hak'uri bansan shiryawa kakeyi ba"ta fad'a cikin jin fad'uwar gaba"dukda dama ta fahimci yanada k'iran mazan taka Amma ta tsorata da k'iran jikinsa"musammun curarran uban gashin data gani saman faffad'an k'irjinsa "ga jikin nasa duk gashi Amurd'e"itafa wlh tsoron ganin namiji babba takeyi irin haka....ki jira! na gama saka rigar Ai"shiru tayi bata juyo ba"shi kuwa turarukansa yamatsa ya d'auka yafeshe jikinsa dasu"kafin ya d'auki Agogo ya zauna gefen bed d'in yana fad'in idan bazaki iya juyowa ba kije mana"Amasife ta juyo ta gallah masa harara tana fad'in dan kama samu nazo na gaisheka shine zaka gayan bak'ar mgn?"kece dai kika d'auka bak'ar maganar ce"sai tayi shiru ta zauna saman sofa tana fad'in Ina kwana?"ya d'auki kusan second 5 kafin ya Amsa da lafiya qlau ya jikin ?"itama biris tayi dashi saida ta mula tasha iska harma ya mik'e tsaye yana dai binta da kallon k'asan Ido,kafin tace"daka damu da sanin ya jikin daka je tun d'azun ka duba kaji"zan wani gaida kai ka Amsa mun irin haka" sai kace irin y'an matan dake cusa kansu mararsa Aji"Amamakinta saiya saki d'an murmushi ya matso gefenta ya zauna"tad'an lumshe Ido sbd yadda k'amshin turarensa ke dukan hancinta....kin gama?"ah ah"ke matsalata dake masifa"Amma Ai kaine kamun k'orafin bana gaisheka bana girmamaka"shine nazo zaka wani d'auke mun kai"hmm! ke yanzun Abinda kika mun jiya kin kyauta?"oh ban kyautaba fa tunda ban bari kayi zance da budurwarka marar class ba ko?"baki canka daidai ba"wannan yarinyar bata daga cikin irin tsarin macen dana ke so"okay to wacece k'anwar tawa?"kaga ranar friday sai muje na rakaka zance"saidai wlh kama sanar mata ni Antyn tace ko kuwa yasin na baka kunya Agabanta ba ruwanah....Uhmmm! shafawa kanki ruwan sanyi ni banida wata budurwa"saidai ko kece keda saurayin ko?"Allah yasawak'a"ta fad'a cikin jin haushi tana mik'ewa tsaye"shiru kawai yayi sbd Al'amarin nata har tsoro yake bashi ,saidai zasu cigaba da Addu'a da bata taimakon har Allah yasa Adace"Ina zakije?"mama zanje na gaido"jirani muje"nidai gaskiya ban zuwa dakai"kaje kai d'aya daga baya nina je"kuma saina maka gami da mamy "ta fad'a tana d'an murmushin da yayi mata masifar kyau"sai kuma ta wani marairaice murya tace" broth bani turarukan naka na fesa"bazan bayarba ke Ina naki?"banza ta masa ta fice daga cikin d'akin"ya bita da kallo yana sauke numfashi "Anutse ya fito daga cikin d'akin ya rufe yana duba wristwatch d'insa sbd karya makara"yaso ya bata keys ta gyara masa d'akin ,to yasanta da shegen Lambo zatace bata lafiya "sashen su mama ya wuce yasha Lipton be sami Ahyaan Acan ba"wato sbd nace zanje shine tak'i zuwa?"ya fad'a Aransa yana wucewa sashen su mamy"Ahyaan na kwance saman kujerah, kanta na saman cinyar mamy tanata shagwab'a"kallo d'aya Dr darma ya mata ya d'auke kansa ya shigo ya duk'a fuska bbu walwala yace mamy Ina kwana?"lafiya qlau.....Ina d'an kwalinki ko hula?batayi mgn ba sai mik'ewa tsaye da tayi ta wuce d'aki "wai mamy meyasa kike gani tana yin Abinda ba daidai ba fisabilillahi baki tsawatar mata?"dubi kayan dake jikinta ?"bayan maza na shigowa kuma....sai yayi shiru "ita dai mamy kallonsa takeyi sbd ganin yadda yake maganar cikin nuna jin zafinsa"saidai bata samu damar yin mgn ba Ahyaan ta fito sanye da hularta ta gifta shi ta wuce"ya d'an lumshe Ido sbd jin k'amshin turarukan jikinta"be koma mgn ba ya mik'e tsaye yana jin mamy na cewa Adawo lafiya yayi kamar be jiba ya fita"da dabara mamy tayi mata nasihar ta rage saka k'ananun kaya sbd mazan dake shigowa musammun dangin daddy irinsu sadeeq"dato ta Amsa tama wuce d'aki ta canza kayan....
yau daya taso daga Asibiti be biya ta chemist ba sbd yau laraba zaije wajen wa'azi"kasancewar 2 pm ne lokacin tashi sai kuma wata safiyar"saidai dayake babban likitane idan Ansami patient emergency za'a kiransa ko wane lokaci yazo"hakan yasa wajen biyu da rabi ya dawo gidan cikin wata had'ad'd'iyar zukek'iyar sabuwar mota bak'a"Mercedes Benz k'irar E350 "wacce zatayi million 8"yana isowa bakin get yayi parking ya fito yana d'an murmushi ya bud'e get d'in gaba d'aya sannan ya dawo cikin motar ya shigo cikin gidan yana danno horn"kafin yayi parking ya koma fitowa ya rufe motar"yana d'ago kansa ya lura da Mubarak na tsaye yana kallonsa shida motar"sai yaga ya juya da sauri ya wuce sashen su"ya tab'e baki sbd yasan uwarshi zaije ya kaima labari"d'an murmushi ya saki daya tuna tsiyar daya saka Aka mata....p cap d'in saman kansa yaja baya"Atake kyakykyawar choko face d'insa ta fito sosai"ya saki d'an guntun murmushi sbd tuna koya Ahyaan zataji idan yace wannan motar sace??"cikin gidan ya wuce "tun kafin ya shigo cikin parlourn yake k'wala mata kira" Ahyaan! Ahyaan!! ya furta cikin nutsatstsiyar muryansa data rage sauti sbd gajiya da rashin sabo da duba patient.....Oh yah rabbih broth! "wannan wane irin kira ne kuma?"ta fad'a tana lek'owa suka had'a Ido dashi"sosai yaji sanyin ganinta da riga da siket na Atamfa kuma ba sosai suka kama taba"wai baza kayi mgn ba?"ta fad'a cikin shagwab'a "zo muje kiga wani Abu"saida ta turo baki sannan ta kallesa saiya harareta yace"idan bazaki zoba ki koma mana"sbd kinga na damu dake ko?"to Amma broth basai...shiru tayi sbd ganin ya juya zai tafi"saita biyosa Abaya"suna isowa bakin get d'in taga motar"wow ! motar waye pls?"ta fad'a tana matsawa gefen motar ta shafeta tana sakin murmushi "shima murmushin ya saki yace"tamuce ! Ihun murna tayi harda d'an tsalle"taji dad'in da yace tamuce"ta d'auka zaice tawa ce"gaskiya tayi kyau broth "Allah ya tsare yasa Alkhairi "cikin jin dad'in kalamanta ya Amsa da Ameen"kafin yayi mgn ta wuce da gudu sashen su mamy,shidai ya girgiza kansa tare dashan Alwashin zai mata Jan Ido ta dena guje guje "be gama wannan tunanin ba ta fito ta wuce sashen su mamah"ba tafi mintina 5 ba saiga mamah da Asma'u da Khadija da luba sun fito"Ahyaan na gefen mamah tana fad'in kunga motar nan mama"kai Masha Allah! Allah yasa Albarka ya tsare yasa rabo ce nurah"Ameen mamah"saidai yana lura da ummah luba na ganin motar ta juya ta koma ciki"dama sbd ta tabbatar da Abinda taji Ahyaan ta shigo cikin murna tana fad'i "kuma duk suna tsakar gidan"d'age kafad'a yayi sbd dama baya buk'atar Allah yasa Alkhairin ta"Allah yasa Alkhairi"cewar Khadija "yayi banza da ita"saidai Ahyaan ce ta Amsa "ya matsa ya bud'e k'ofar motar"Ahyaan tayi saurin shiga driver sit ta zauna "mama ki matso ki gani mana"ya fad'a yana d'an murmushi yana satar kallon Ahyaan " Ai na gani ma ,abu yayi kyau kam"Ina mamy?"tana ciki nace tazo ta gani kinga bata fito ba "wai naje na kiraki kece mamansa in kin gani ya wadatar"cewar Ahyaan "ah ah itama yaka mata tazo ta gani ta sanya Albarka ko? cewar mama tana nufar sashen mamy "Asma'u tayi masa Allah yasa Alkhairi itama ta wuce ciki"broth in kunna tah?"ta fad'a tana d'an lek'owa suka had'a Ido"saidai kafin yace" wani Abu sunji muryar mamy na cewa ". na gani mama Allah yasa Alkhairi yasa rabo ce"ya Amsa da Ameen su kuma ko wace ta wuce ciki"zagayowa gefen me zaman banza yayi ya zauna"Ahyaan kuwa kunnah motar tayi"kina nufin kin iya driving dama?"da meka d'aukeni?"ta fad'a tana rufe k'ofar ta zuge glass d'in tana murmushi "cike da k'warewa ta fara zagaye haraban gidan tana murmushi"shidai yana kallonta,sai kuma tayi parking daidai get"Allah broth kanada kud'i nima saika siya mun tawa motar"Allah ya hore Abinda yafi motama zan siya miki Ai"kuma wannan Ai tamuce ko?"sannan duka million biyu da rabi na biya cikin Albashina duk month zan dinga biyan su har na biya 8 million"to nidai dan Allah karka sanarwa da kowa broth "kawai dai kaci gaba da biya in sha Allah harka Ida cika musu d'in"kinsan dai bana yin k'arya ko?"Allah ko?"to rantse tunda kake baka tab'a yiba ustazah "yayi shiru shima kansa beda tsarin ya sanarwa kowa itama besan meye yasa ya sanar mata ba?"muje ciki naci Abinci ya fad'a tamkar bayaso yana duba time"gaskiya naji dad'in motar nan "dama nayi rantsuwar na gama hawa mashin naka duk rintsi "saida ya tab'e baki kafin yace"saiki shirya yin kaffara kuwa yarinya "dan hawa mashin d'ina yanzun kika fara"wacece yarinyar?"dama Anan mu nawane?"kaje kaida Allah"murmushi had'e da dariya ya saki"ta masa banza ta fito daga cikin motar rai b'ace"shima fitowa yayi ya rufe Adaidai lokacin kuma mu'az ya shigo cikin get d'in gidan"Ahyaan sarai ta gansa Amma sbd Abokin sa ya b'ata mata rai kallo be ishetaba ta wuce ciki.....✍️
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.