Abrah Complete Hausa Novel
Reading file: Abrah_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 21 of 21
*page42&43*
🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚
__________📖jirgin su ya sauka ingila lafiya da man Ansan da.zuwansu sarauniya ta aiko daukar su masarautar ingala Aka nufa dasu
Sun samu tarba mai Kyau so sai Aka karrama su
Wani makeken part guda Aka basu mai dauke hudu koya ya Shiga da matar shi Sarauniya taji dadin zuwansu sosai sai murna take
Laila taga ba fuska ga Dr ta Dan haka bata tusa kantaba itama tasamu miji aure zatai sai Jan Abra take Ajiki musamman ma cikin da kegareta komai ta kawo Abra take nufa dashi ita Abra ta sake da ita
Sun zaga wajajan shaqatawa so sai daga cikiko harda fadar sugaban qasar na ingila wato kaka ga Dr Ambasadar ma'aruf kanada
Garin ingila yayi so sai ga Abubun tarahi Dana bude ido satin su biyu suka daga madina domin yin ibada da kuma Adu'o'i
Nan ma sati biyu sukayi daganan suka wuce Jordon sakayi sati guda sun zaga qasashe dadama duk sunyi siyayyar kayan bby
Suma su sirina da khairat matar Sauban duk sun qunshi nasu cikin tafiya yayi Albarka sun dawo gida lpy
Lokacin cikin Abra wata takwass da ya shiga watan haihuwa suka tattara suka dawo katsina A Cewar Dr ta haihu gaban iyayanta gidan su na katsina suka yada zango da man kaka Nana yanzu nan ta dawo da zama wajan Dan haka ita ta dawo da zama wajan Abra tana bata yan jiqejiqen magungunar na masu cikin
Cikin ikon Allah cikinta na shiga watan haihuwa ta haifo yaranta yan biyu macce da na miji duk masu kama da ubansu
Murna ga wannan family Abin ba'a magana ko da yaushe gidan tamtsan da jama'a sai Alkairi suke samu mai tarin yawa inda mai Naira shima
Yai ta sadaka ga yan UWA da Abokan Arziqi murnan samun jikoki da yayi
Haka Abban Abra shima ya taka tashi rawar gani balle mai gayya mai aiki harda kujerar makka ya rarrabama jama'a
Ta kowanne bangare dangi sunzo ranar suna Anti gagarumen biki na gani da fada yara sunci sunan kakannin su na mujin Akasama sunan Abban Abra maccen kuma sunan Gimbiya taci suncemata Gimbiya qarama
Taro ya tashi lpy Baki suntafi da gagarumar tsaraba a gidajen su Maijego da yaranta sunyi shar da su
Bayan tayi Alba'in tazaga dangi har jibya saida Abra taje wajan dangin ubanta daganan ta wuce zamfara wajan dangin uwar ta bayan ta dawo ta huta Dr yazo ya dauke suka koma Abuja
Dr Arziqi ya qara bunqasa Dan yanzu harda kasuwanci yake tabawa kuma Allah yasama Abin Albarka
Yaran su sun murmuge suna samun kulawa da gata
Abra ta qara zama babbar macce ta qara Kyau Dan inka ganta ba ka Gane ta
Yanzu ta wuce karatunta na low
Sirina ta haihu ita khairat suma duk sun wuce karatu
Sirina na karantar business khairat na karantar nursing
Laurat ta haihu Amma Dr kanwa inda taci sunan yarta ta baya wadda tarassa wato Amal Dr na matuqar qaunar Amal so sai
Kwanci tashi ba wuya Abra ta zama cikakkiyar barrister
Yaune ta fara zuwa kotu domin yin wata shari'a kuma Alhmdll ta samu nasara domin itace shari'a farko da ta fara kuma ta samu nasara
Dr ya sake Gina masu wani qaton gida sun koma Sabin gidan su Anan Abra ta sake haihu da na miji soyayyar su da Dr sai Abinda yayi gaba suna qaunar junan so sai sukeba junansu kulawa Dan yanda suke kula da junan su Abin sai ya birgeka yan biyu sun girma
So sai suna matakin secondary
Haka rayuwa taci gaba da tafiya cikin nasara
Da Annashuwa
Afannin kasuwanci Abra ta kudance tana tai makon yan uwanta da kuma mabuqata
Ko INA sai San barka Ake mata da fatan Alkairi
*Alhamdulillah Anan na kawo qarshen wannan labari nawa mai taken Abra kurakuran dake ciki Allah ka yafe man ðŸ‘ðŸ»*
Ammyn khairat
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.