Maradams Book 3 Complete Hausa Novel
Reading file: MAR ADAMS BOOK 3 COMPLETE BY AYSHA BAGUDU.txt
Chapter 10 of 29
Page 15
Cikin yanayi na tsananin tashin hankali mr ata ya cigaba da cewa “duk wannan abun ya faru ne saboda ita ba’a ta’ba tozartani ba amman yau an tozartani akanki. “kin kasa fahimtar mahimancin aikina, nayi kuskure nayi kuskure yarda da aikinki nayi kuskuren d’aukarki aiki da yakin neman soyayyarki nayi na aureki na hutawa rayuwata yaja wani dogon tsaki a lokacin daya tuno abinda yasa yayi loosing opportunities dinsa .wai akan wani matacce wanda baya exit za’a ‘bata masa aiki ” Eh mana baya exit da yana exit daya dawo gida garesu .”yana tafiya yana wannan tunani ita kuwa maryama tana can durkushe tamkar matacciya tana kallon tafiyar mr ata ,tamkar mutun mutumi haka ta koma saboda tsananin tashin hankali ta qame waje d’aya ta kasa kwakkwaran motsi . “wani irin ajiyar zuciya take ta saukewa tana jin gabad’aya duniyar tai mata zafi kuma har lokacin ta kasa yarda cewar yaya sadam dinta ya mutu .wani irin tausayi mai tattare da soyayyarsa ce ta dinga shigarta .”
“ahankali mr ata ya cigaba da tafiya har ya kawo inda direbansa yake idanunta na kashi shi din ma tausayinsa ne ya dinga shigarta yana bin kowacce jijiya dake aiki ajikinta ,yayinda zuciyarta ke wani irin tsinkewa akanshi tare da tsananin jin tsorona jikinta baqaramin sanyi yayi ba jin irin maganganun da sukai ta fitowa daga bakinsa tabbas bata kyauta masa ba amman shima abinda yayi mata ba kamata ba kamata yayi ya mata adalci .”Mr ata bai tsaya direbansa ya bud’e masa murfin mota ba ya bud’e da karfi ya shiga ya zauna zuciyarsa na tsananin dokawa kamar zata fashi .”direba ya shiga gaban mota da sauri yaja suka wuce.” duk wayar da’ake doka masa bai d’aga ko d’aya ba dan koya daga bazai iya magana ba saboda bala’i n dake cinsa dan jikinsa banda kyarma da fitar da zufa babu abinda yake .”kai tsaye gida yace a wuce dashi tafiya mintuna talatin suka qaraso abdullahi estate direba bai gama daidaita tsayuwar parking din motar ba ya bud’e murfin mota a zuciye ya fito da sauri ya shiga part din mahaifiyarsa .”
A fusace ya shiga parlour’n inda kai tsaye ya wuce maryam tare da mami zaune hira ya haye samansa batare da ya cewa mami qala ba mami na ganin haka tasan ba lafiya ya shigo ba ,dan haka ta mike. yana shiga d’akinsa ya hau cire kayansa yana fillinging dasu sannan ya fad’a bathroom ya shiga bathtube ya cika da ruwa ya shiga ya kwanta aciki. ruwan na shiga jikinsa ya kai hannunsa daidai saitin qirjinsa ya dinga shafawa ahankali yana furzar da iska yana tunanin sambatun maryama “Shikenan na rasaka sadam da gaske ka matu baka raye abida ya dinga ji yana fita daga bakinta kenan lokacin daya yi kusa daita ya lumshe tsumammun idanunshi yana girgiza kanshi nan take maganarta ta shiga masa kuwa acikin kunnuwansa da brain dinsa “Jiya ina tsaka da aiki sai bacci ya d’aukeni acikn baccina nayi mafarkin yaya sadam adaidai farm center “.
“very stupid girl kawai bakiyi tunanina ba sai wani banza da baya exit a duniya nonsense girl kawai.” ya fad’a yana sake lumshe tsumammun idanunshi wani zazzafan kishi na taso masa ya dade kwance acikin ruwan dan ya d’auki sama da mintuna talatin sannan ya fito kugunsa d’aure da farin towl yayinda dayan hannunsa Ke rike da wani qaramin towel yana goge sansar jikinsa .”byn ya gama goge koina ajikinsa ya d’auki daddad’an turare body’s spare ya feshe ilahirin jikinsa ya shirya kansa cikin kaya wondo da riga marasa nauyi ya zauna a gefen gadonsa ya mike qafafuwansa tunanin maryama ne har lokacin Ke dawainiya dashi yana zaune mami ta shigo hannunta rike da black cup wanda shigowarta na uku kenan dan ta shigo sau biyu yana wanka “Lafiya tunanin me kakeyi haka ?tayi masa tmbyr tana tattara hankalinta kacokan akanshi sai daya sauke numfashi da ajiyar zuciya atare sannan ya girgiza mata kai alamun babu komai ta mika masa black cup dinsa dake rike a hannunta wanda Ke d’auke da coffee” idan kana da damuwa adamcy karka boye ma mahaifiyarka.”
ya gyad’a mata kai kawai batare daya ce mata komai ba” shikenan idan ka gama sha ka sauko kaci abinci still kai ya gyada mata ta fita ta barshi yana kur’ban coffe yana tunani ,gbdy so yake ya fahimtar daita cewar yaga mafarkinsa da irin matsalar da yake fuskanta akanta amman yana jin tsoron abinda zai fito daga bakinta ,wata killa ma bazata amince da maganar ba kodan sbd matsalarsa da maryam .
Bugu da qari zaa iya samun matsala a bangaren ita maryama din karta zo taki amincewa dashi bayan ya sheida mata , dan a yadda yake kallonta wancan matacce mutumin ya tafi da zuciyarta da rayuwarta gabad’aya soyayyarta ta mutu akanshi ba lallai ta fahimcesa ba bare ta fahimci irin tarin qaunar da yake mata .”
gbdy idanunsa sun sauya kala fuskar maryama kawai yake gani ko a wani hali take ciki a inda ya barota numfasawa yayi yana dafe goshinsa yace “anya kuwa banyi kasadar barinta a wajen nan ba ?“anya kuwa bazan tura a ruwa ya koma ya dauketa ya kaita gida ba ?”wannan tunani yasa shi ya mike yayi taku zuwa inda wayoyinsa suke akan mirrow ya dauki d’aya daga ciki ya soma kiran layin aruwa bayan ya d’aga ya bashi umarni abinda yake son yayi sannan ya katse kiran ya koma ya zauna yana fidda numfashi sama sama.” bai sauko ya cin komai ba ya kwanta yana runtse tsumammun idanunshi tare da rungume hannuwansa duka aqirjnsa yana jin yadda soyayyarta ke fixgarsa .”
Bangaren maryama kuwa da kyar ta yunkura ta mike ta nufi gidan cikin tashin hankali wuni daya amman idan kaganta ta fita haiyacinta ta rame da kyar take daga qafafunta tana shiga gidansu bangaren umma ta nufa a falo ta sameta ita kad’ai umma tana ganin yanayin maryama ta mike da sauri ta tarbota ai kuwa ta zube ajiknta tana kuka “Lafiya maryama meke faruwa dake naganki kamar baa haiyacinki kike ba?umma …”sai kuma ta fashe da kuka ta kasa qarasa mgn nan fa hankalin umma ya sake tashi ta mike taje ta kawo mata ruwa a glass cup ta kai bakinta “sha ruwa kiji sanyi .”ta kurbi kad’an tana sauke naunayen ajiyar zuciya .”
umma ta sake tmbyarta bata boyewa umma komai ba ,ta zayyane mata duk abinda ya faru “wannan laifinki ne maryama shiru tayi tana duban umman bazaki fahimci yadda mutun yake shiga idan yayi alkawarin cika aiki ba “umma nima ban so haka ba nayi kokarin nayi masa aikinsa koma dai menene wannan laifinki né d’an ya kamata ki qarasa masa aikinsa ki kai masa albashi daga baya sai ki nemi excuse ki tafi duk inda zaki “shiru maryama ta sake yi tana tunanin maganganunsa “babu wani mutun da ya isa ya fadawa adam tariq abdullah magana akan aiki amman yau anyi ,and it happened because of you “gsky umma nayi kuskure amman idan kikaga yadda mr ATA ya zageni gabadaya ya hanani cewa komai “.ai duk ya faru ne saboda kuskurenki ko haka kawai zai fada miki magana “?
“Kinsan irin asarar da kikasani wai Ke dame kike takama ya tsaidaita ?”Kinsan yadda kasuwancina yake da matukar mahimanci agurina gabaday na daura raina akan designs dinki nasaka raina nayiwa wanda zaizo yagani alkwari amman sai kika ki zuwa kuma idan na kiraki sai Kiyi rijecting din kirana me ma kike yi anan ki bani amsa .”?maganarsa ta shiga yawo acikin brain dinta” idan kinje office gobe ki tabbatar kin bashi hakuri ki nuna masa kinyi Kuskure gyad’awa umma kai kawai tayi .”alamu taji .
*****
Daren ranar daga maryama har mr ATA babu wanda ya runtsa kwana sukayi cikin tunanin juna da maganganun juna ta mike zaune akan gado ta jingina bayanta tare da daga idanunta sama “wai a haka kike son ki zama profetional a ma’aikatan mu?Kinawa mutane iskanci da kika ga dama saboda kina daukar wai dan kin iya designed yasa kike samun aiki cikin sauki ? gabadaya zagin da yayi mata babu wanda ta manta yadda take zaune haka shima bai tsaya iya daki ba har kasa falon mami ya sauko ya dinga tafiya tamkar wanda bai da laka ajikinsa ya wuce ya karya kwana zuwa parlour’nta na biyu tun saukowarsa maryam taji ajikinta dan daman baccin nata rabi da rabi né .sad’af sad’af ta fito ta gansa zaune akan kujera yayi shiru cikin tsananin tunani shiru tayi tana qare masa kallon taso ta qarasa garesa ta tambayesa damuwarsa amman tasan halinsa komai zatayi bazai ma saurareta ba ta jima tsaye kafin daga baya ta juya tana masa fatan sausauci duk da batasan abinda ke damunsa ba .”
Ya dinga jin kamar ya kirata yaji muryarta ko hankalinsa ya dan kwanta tunda a ruwa ya tabbatar masa da yaje bai sameta a wajen ba .”
Washegari daga maryam har mr ATA babu wanda
yayi kokarin zuwa aiki kwamciyata tayi dan tasan tana zuwa zai korata idan taci saa ma bai hada mata da zagi da tozarci ba, sam ransa bai iya baci ba idan ransa ya baci baya control din kansa “numfashi ta sauke tana cewa “wallahi matarka tana dan katoton matsala ta fada gabanta fadawa bangarensa shima zama yayi adaki bayan yayi wanka ya sauya kaya yana zaune mami tashigo kamar daren jiya tmbyrsa ta soma yi stil yace babu komai “idan zaka boyewa kowa damuwarka adamcy banda mahaifiya yadda bazaka yadani ba nima haka né bani da kamarka damuwarka damuwatace “sweetheart maryama ce !”ya furta yana jin bugun zuciyarsa na qaruwa .”wacece ma haka ?ta tambayesa tana tattara gabad’aya natsuwarta garesa .”
Ya d’auki minti goma sannan ya motsa labbansa yace “wannan sabuwar maaikaciyar dana d’auka ce “
ya fad’a yana sauke numfashi “ me tayi maka wanda har ya hana rayuwarka sukuni?”yayi shiru ya kasa magana “ fadawa sweetheart dinka abinda tayi maka still shiru yayi yana tunanin ta ina zai fara mata bayani ta tsura masa idanunta sosai tana karantarsa tare da nazarinsa daman kuma maryam ta fad’a mata daren jiya bai yi bacci ba gashi yayi sanadiyar daya zauna gida bashi da niyyar fita office
“Adamcy!
Ya d’ago tsumammun idanunshi ya zuba mata dan mgn wahala take masa a tsakanin jiya da yau “ko dai sabuwar ma’aikaciyar nan ta sace maka zuciya né ?da sauri ya furta “kai sweetheart, kai sweetheart ko gsky shiru yayi kawai qirjinsa na dukan uku uku “tambayarka nayi ka bani amsa kana sonta ne dan wannan damuwar tayi yawa tunda ka fara aiki daita kake cikin damuwa “haka nan ya tsinci kanshi da girgiza mata kai alamun a’a “sweetheart babu wani so “ ya fad’a mata haka ne saboda maryama bai kafa kansa a wajenta ba taya zai fad’a mata shi da yake da qatotuwar matsala a gabansa gara yasan matsayinsa tukun koda zai shigo mata da maganar soyayyarsa “adamcy idan bashi bane me zai sa ka dinga zama always busy thinking kuma nasan akanta ne ?” ta kamo hannunsa cikin nata” ina sauraronka fad’a min damuwarka bai boye mahaifiyarsa ba ya koro mata duk abinda ya faru da dalilin dayasa taki zuwa ta kawo masa aikinsa sai dai har lokacin yaki fadawa mahaifiyarsa cewar itace yarinyar mafarkinsa ce .”
“lallai wannan yarinya tayiwa shalelena Kuskuren da baa masa ya dauka ,ina kyautata zaton da wata ce da yanzu kasa an sallameta “yanzu ma tunanina kenan sweetheart gara na sallameta na huta da matsalolinta “a’a karkayi haka ita rayuwa tattare take da qalubali sannan yarinyar abar tausayi ce wata killa ma ita ce Ke dauke da dawainiyar gidansu sakamakon yadda rayuwar nan tayi tsanani sannan kai ma kace ga dalilinta na kin zuwa “ tunda mami ta soma magana bai ce uhm ba bare uhm uhm “adamcy karka koreta na rokar mata wannan alfarma ka bata wata damar kuma ina da tabbacin bazata sake aikata Kuskurenta ba.”ta cigaba da magana “ adamcy ya kamata ka daina sauran daukar zafi akan komai ka koyi hakuri da juriya sannan ita wannan yarinyar Kmr yadda ka fada zuciyarta na tattare da damuwa mai tsanani ,da ciwo a zuciya ba kowa bane zai iya dauriyar abinda ya faru daita .”dan ka dinga mata hakuri kana tausaya mata mutuwar miji fa bakaramin ciwo bane .”
yayi shiru yana sauraran mami yana tunainn lokacin da yake mata balain tana bashi hakuri akan ya tsaya ya saurareta” yau ta wuce na zuwa aiki amman gobe idan kaje office ka nemeta ka bata hakurin tozarcin da kayi mata” tana gama fadar haka ta bar dakin dan ya d’an ya samu ya huta tana fita ya mike tsaye yana tafiya yana tunanin maryama yana tunani maganr mami shi gabadaya yanzu ba rasa aikin bane damuwarsa yadda zuciyarta ta mace akan matacce shine babban tashin hankali sa washegari da sanyi jiki ya tashi ya shiga bathroom ya jima a bathtub cikin ruwa kafin ya fito ya goge jikinsa ya feshe ilahirin jikinsa da turarensa REED Kmr koda yaushe ya shirya cikin suit black and milk colour bai daura yar saman suit dinsa ba ya qarasa gaban mirrow ya dauki curm yana taje sumar kansa ya ajiye curm ya dauki agogon ya daura atsintsiyar hannunsa duk jikinsa ya sanyaye yake komai ya manne medical glas dinsa duk abinda yake tana makale aransa ya rasa wani irin zazzafan so yake mata .”
“ina maseefar sonki maryama” ya furta a fili bayan ya gama shirinsa ya tsaya cak yana kallon kansa ta cikin mirrow maryama ya gani tsaye ta cikin mirrow sanye da doguwar riga ja tayi rolling kanta da bakin mayafi fuskarta babu alamun annuri haka zalika babu alamun murmushin nan nata , yayi shiru yana kallonta tayi masa kyau sosai bai san lokacin daya kai hannunsa yana shafa fuskarta ta cikin mirrow zuwa lip’s dinta ba .”nan take ta sakar masa laulausan murmushinta .kokuwa ya shiga yi da numfashinsa ya juya da sauri zuciyarsa na rawa byn Kmr second ya juyo yaga wayam yaga babu ita babu alamunta ya lumshe tsumammun idanunshi “it was imagenation .”ya furta yana sakin numfashi da qarfi “zatazo aiki yau dan jiya an tabbatar masa bata je ba amman yau kam yana ji ajikinsa zataje “? Idan kuma taki fa ? ya tmbyi kanshi “to karita mana kace mata taje aiki kai ma kasan irin haukan daakayi mata zataji tsoron zuwa .”should I called her or not ?ya sake tmbyr zuciyarsa “a’a bazan kirata ba ya furta yana lumshe idanunshi yayi shiru yana zagaye dakin.”
bangaren maryama itama shirin zuwa aiki take saboda umma tun daren jiya ta matsamata lallai taje aiki tunda itace tayi masa laifi bugu da qari ba korarta yayi ba .ta shirya tsab cikin daguwar riga kamar koda yaushe exactly yadda ya ganta a tunaninsa haka shirin nata ya kasance cikin doguwar Riga ja mayafi baki haka baby shoes din da take sanye dashi baki ne agogon hannunta baki ne ta qarasa ta dauki takardan zanenta ta rufe ta saka cikin jakar aikinta ta rataya sai dai ta tsaya shiru tana jin tsoron fuskartasa “ko ya zamu qare yau da mr ATA ? Kinsan irin asarar da kikasani wai Ke dame kike takama ya tsaidaita Kinsan yadda kasuwancina yake da matukar mahimanci agurina gabaday na daura raina akan designs dinki na saka raina nayiwa wanda zaizo yagani alkwari amman sai kika ki zuwa kuma idan na kiraki sai Kiyi rijecting din kirana me ma kike yi anan ki bani amsa .” ?maganarsa ta shiga dawo mata kamar alokacin abun ya faru ta dan ciza harshenta tana jin wani iri ajikinta kamar karta tafi “wannan mutumin yana ban tsoro ta furta a fili .”
“Hakika baka kyauta ba abinda kayi ka kirata ka bata hakuri tun kafin kaje office,no!!akan me kenan zaka bata hakuri bayan itace tayi maka laifi ,aa adam kai ma ka fada mata abubuwa dayawa tô na bata hakuri nace ma me ?kawai sai nace maryama kiyi hakuri akan …”no impossible I can’t gbdy ya rasa yadda zai fuskanceta da wannan kalmar dan tunda yake bai ta’ba bawa wani mutun hakuri ba sai mahaifinsa da mahaifiyarsa saboda me ita zai bata capital NO no !dan haka yayi cilli da wayar akan gado yana duban wayar ai itace tayi min laifi to dan me zan kirata?Kyakkyawar zuciyarsa tace sai me ai ba wani abu bane karka tsaya girman kai akanta ka dai san irin wahalar daka sha tsawon shekaru kana nemanta alhalin tana raye kuma a kusa da kai ma dan ina gra apapa ina agege is not far kai ya kamata ace ka fahimci kayi kuskure dan haka ka kirata nan take wata zuciyar tace “saboda me zaka kirata ai tama fika laifi ita data hada maka Zafi biyu ,ita yakamata ta nemi yafiyarka .”
“Idan mai hankali ce kuma tana bukatar aiki dani ai ya kamata ace ta kirani since tayi apologize abinda tayi amman taki saboda tana tunanin bata aikata kuskure ba. dan haka she’s the one who wil apologize she must apologize” ya furta a fili kuma idan ma taki zan sata dole tayi apologize da wannan shawarar zuciyarsa ta samu natsuwa .”yana tsaye mami ta shigo tana kiran sunansa “Adamcy Nah !kallonta yayi tare da cewa “good morning sweetheart morning my dear fatan ka tashi lafiya lumshe tsumammun idanuwansa yayi ya zagayo ya tsaya kusa daita ta dauki yar saman suit dinsa ta saka masa tana cewa “ kayi aure da ban huta ba ,shima yanzu ban huta ba har sai yashe zaka bar mahaifiyarka ta huta ?sai randa mafarkina ta bayyana ya bata amsa da haka yana kallonta .”
Murmushin mami tayi “wannan mafarki da gskiya ne da zanji dadi kadan “idan ta tabbata gsky ce sweetheart zaki sota kamar yadda kike sona ?” ya fad’a yana cigaba da kallonta yana son yaji amsar da zata bashi “ zan sota mana amman kadan tunda kai ma baka so zabina ba ,son 50 50 zan mata mur mushi ya bayyana akan labbansa “sai abu na gaba “karka manta idan kaje office ka kira yarinyar nan ka bata hakuri ka nuna mata shima Adam mai kuskure ne ka nemi yafiyarta yace “uhm alamun yaji idan ka gama ka sauko kasa abincinka yayi ready .shiru yayi kawai yana tunanin ta ina hakan zai faru “kabi umarnin mahaifitarka zai zame maka alkhairi ki rata tun kana gida kyakkyawar zuciyarsa ta bashi kwarin gwiwa , jiki a sanyaye ya dauki wayarsa ya soma neman layinta tare da tsurawa sunanta idanunshi .”
Mmn sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 16
Fuskar wayar yake kallo tare da raya abubuwa da dama acikin zuciyarsa ,wani irin abu yake ji yana tsarga masa a gbdy sansar jikinsa, sai wayar ta kusan shiga sai ya katse ,yayi haka ya kai sau uku yana katsewa cike da fargaba ya rike wayar a hannunsa yana tafiya acikin d'akin yana tunani ." maganar mahaifiyarsa ta shiga dawo masa "zuciyarta na tattare da damuwa mai tsanani ,da ciwo a zuciya ba kowa bane zai iya dauriyar abinda ya faru daita .
“Dan hk ka dinga mata hakuri kana tausaya mata mutuwar miji fa baqaramin ciwo bane ," runtse idanuwanshi yayi sosai yana kiran sunan Allah a lokacin da ya tuna yadda hawayenta ya dinga zuba akan wani matacce .”wani dogon tsaki yaja ya sake cilla wayar akan gado yana sake jan tsaki tare da kai hannu ya dafe goshinsa ahankali ya bud'e idanunshi wad'an da suka kad'a sukayi jajur saboda tuno abinda ya faru jiya. kukanta da damuwarta akan wani namiji wanda bashi ba ."wannan abu yayi matuqar masa ciwo ,qirjinsa na wani quna ya juya wa wayar baya kamar itace tayi masa laifi ."
Ya kamo lip's dinsa na qasa gabad'aya ya dinga taunewa da karfi gashi dai zafi yake ji amman zafin kishin maryama ya zarta zafin da yake ji acikin zuciyarsa ,byn kmr second goma ya sake juyowa da sauri yana kallon wayar kmr zaiyi kuka ,"bazan ta'ba bayyana miki soyayyata a yanzu ba dan nasan ko na bayyana miki a acikin wannan halin bazaki ta'ba sona ba amman zan san abunyi ," ya furta a fili yana sauke wani naunayen ajiyar zuciya ya sake d'aukar wayar stil numberta ya shiga kira yana tunanin mgnr da zai fad'a mata da zai sa tazo aiki dan yayi imani tunda bata zo jiya ba tabbas yau din ma bazata zo ba "to idan ina kirata ta d’aga me zance mata ?” ya sake tambayar kanshi yana sake danne lip's dinsa da hakori "idan ta d'auka kace mata tazo aiki amman karta zo maka da past dinta , ta bar komai a gida baka buqata that's all ."
sai dai wayar na daf da shiga ya sake ya katse wa yana sauke zazzafan numfashi ."maryama ta tsaya shiru acikin haraban ma'aikatan tana tunanin hawa sama ,kallo d'aya zaka mata ka fahimci tana cikin tsananin fargaba, ita ba wai tsoronsa take ji haka nan ba kamar yadda sauran ma'aikatan suke rawar jiki idan sun gashi disgi da tozarcinsa ne bata so kuma shi babu ruwansa ko gaban uban waye shuka rashin mutuncinsa yake kuma kamar bai d'auki hakan a wani abu ba ."da kyar ta tattare jarumta ta sanya ajikinta ta nufi kofar shiga lift byn ta shiga ta shiga, mutane da dama sun shiga a natse ta danna number inda zata sauka sannan ta ra'be jikinta waje d'aya tana jin mummunar fad’uwar gaba ,kofar na gama rufewa wani sabon fargaba yayi mata diran makiya gabanta ya dinga luguden bugu har sanda kofar ta bud'e , sai da kowa ya fita ya barta kamar ta koma kasa amman wata zuciyar ta dinga karfafa mata gwiwa.”
Ahankali ta fito zuciyarta na bata kwarin gwiwa "haba maryam kowa tsoronsa yake ,ya kamata ki zama zaka acikinsu ba wai ki masa taurin kai ba aa ki zama jaruma ."kai tsaye ki shiga office dinsa ko kuma ki kirasa “ta zaro wayarta ta rike tana tunanin abinda zata ce masa idan ta kirasa "sir kayi hakuri nayi realize din mistakes dina bazan sake aikata wannan kuskure ba shikenan kina yin hk zai yafe miki ."tana cikin tunanin kawai taji wayarta ta d'auki qara a matukar tsorace ta duba sunanshi ta gani yana yawo a scren din wayar nan take bugawar da zuciyarta take ta qaru yayinda sansar jikinta ya kama kyarma ,amman tayi karfin halin ta daidaita natsuwarta ta d'aga kiran cikin sanyayyar muryarta mai sanyi da bugar da zuciya duk wanda ya saurara "assalamu alaikum " !.
shiru taji bai amsa ba ,dan a can bangarensa bai san kiran ya shiga har ta d'aga ba yana can yana tunaninsa sai jin sautin muryarta yaji "assalamu alaikum .""hello ta sake maimaitawa duk da yana jinta amman yayi mata shiru yaki yin magan yana shan kamshi kamar tana gabansa . ji tayi kamar ta saki fitsari ajikinta tsabar yadda gabanta yake dukan tara tara ."jin shirun yana son yayi yawa ta sake motsa labbanta cike da girmamawa tace "good morning sir" morning !ya fad'a atakaice yana ciccin magani sannan ya juya ya cigaba da tafiya acikin d'akin batare da ya sake cewa komai ba." itama shiru tayi .”har kusan second talatin bai ce komai ba ga mutane sai faman wuceta suke suna kallonta dan Allah yayi mata baiwar kyau mai d’aukar hankali da tafiyar da ruhi ,dole ne idan ka kalleta ka sake kallonta sannan ka yaba da irin zallar kyawun da Allah tabaraka wata ala yayi mata .”
ta sauke naunayen ajiyar tana sake duba screen din wayar ta gani ko kiran ya katse ne yasa taji shiru gani tayi still yana kan layi can dai tace "sir ko akwai abinda zakace ne ?"no...sai kuma yace "yes !"what !?
“what do you want to say sir ?ta furta a dan kid'ime shiru yayi yana sauke mata numfashinsa a kunne wanda hakan ke sake haddasawa zuciyarta mummu nar kidima da shiga tashin hankali muryata a matuqar raunane ta sake tambayarsa ” me kake son kace sir ? "abinda zance kizo office akan lokaci "okay sir ..!kafin tace wani abu ya katse kiran murna da farinciki suka taru suka lullu’beta ,kafin ahankali tayi shiru tsaye tana nazarinsa " ko me yake son fad'a mata? kamar ba wannan maganar yaso fad'a mata ba" kai koma dai menene matsalarsa ce wannan tunda har ya furta tazo tana da hujja kare kanta idan zai tozartata .""wayyo allah dadi "ta furta a fili cikin tsananin farinciki bai ma san na kusan shiga office ba, allah na gode maka da kasa ya furta nazo da bakinsa .”
Cike da kuzari ta soma tafiya cike ta shiga office dinsu lokacin kowa ya hallarar "sautin muryarta suka jiyo daga sama "good morning !good morning!!ta furta gbdy suka mike sakamakon ganinta sectary tace "me yasa shekaranjiya da jiya baki zo aiki ba ?”gsky baki kyautawa mr ATA ba kin kunyata shi tunda nake aiki dashi ban ta'ba ganin abokan kasuwamcinsa sun masa haka ba yusura da surayya duk suka matsota suma dai tmbyarta dalilin rashin zuwa kwana biyu suke "nima ba haka naso ba na .."
“ba haka kika só din wa ba ?”daman dayawa ya'yan talakawa basu iya samun guri ba sannan basu iya d'aukar aikinsu da mahimmanci ba "inji cewar sultana dake zaune tana watsawa maryama wani mugun kallo ajiyar zuciya maryama ta sauke sannan tace "haba sultana gsky banji dadin kalmarki ba rayuwar nan fa da mai arziki da talaka duk daya né a wurin allah babu bambamci sai wanda yafi wani jin tsoron allah ."
Maryama tana cikin wannan bayanin mr ata ya taho a hankali hannunsa daya cikin aljihun wondonsa tun kafin ya qaraso kamshin daddaren turarensa ya kawo masu ziyara, bai tsaya a koina ba sai a bayan maryama yana kallonta” tayi kmr zata juyo ya bar gurin kad'an still dai yana bayanta kuma idanunshi na kanta numfashinta kawai take janyowa da kyar tana fesarwa dan gbdy acikinsu babu wanda bai firgita da ganinsa ba kafin a hankali suka shiga gaishesa daya byn daya da girmamawa ."itama maryama ta bude baki da kyar ta gaishesa dan zuwa alokacin ya dawo gabanta ya tsaya kyam yana kallonta sai dai bai amsa gaisuwarta ba illa tsura mata tsumammun idanunshi da yayi ta cikin medical glas dinsa yana kallonta itama shi din take kallo sai dai ita a dan rikice take ."
“sosai ya tsareta da idanunshi duk tayi masa laifi mai girma amman kallonta a yanzu ya d’an rage masa kashi hamsin na cikin damuwar data haifar masa sakamakon wani zazzafan kyau datai masa domin sosai kayan dake sanye a jikinta suka mata masifar kyau gashi dai bata bayyanar da surarta afili, amman kowani kaya ta saka sai ya zauna ajikinta kuma suyi mata kyau “princess kinyi masifar kyau yau..."ya furta a can qasan ranshi yayinda ita kuwa tashiga tsananin damuwa dan a zahiri yake iya kallon yadda take hadiyar zuciya
irin kallon da yake mata yasa numfashinta ya soma qoqari d'aukewa "sir ..!tana furta hakan ya juya ya wuceta da sauri ya shige office dinsa .”aiko nan take wani sabon fargaba da tsorone sukayima maryama dirar mikiya, jitake kamar tasaki fitsari mai wasali a wando tsabar yanda gabanta yake bugawa .”
Yayinda duka wata gaba da Allah subhanahu wata'ala ya halitta ajikinta rawa takeyi,kallo daya zaka mata kagane hankalinta amatukar tashe yaje . qafafuwanta dake karkarwa ta shiga motsawa ta juya da zumar zata bi bayansa gbdy sukayo kanta har sectary "karki kuskura ki shiga office dinsa yanzu “ki barshi zuwa wani lokacin sai ki gansa "cikin tsananin tashin hankali tace "karku damu ku barni na gansa yanzu domin a yanzu ya kamata naje na nemi yafiyarsa ba sai an dauki lokaci ba , idan naki zuwa yanzu zai dauka cewar da gangan nayi , ko ya d'auka girman kai zan masa ,ku dai kuyi min addaur da fatan nasara tana gama fad’ar haka ta wuce su "uhmm ba dai ya Adam ba sai kin gwamace baki je ba sultana ta fad'a a kasan ranta tana murmushin mugunta sannan ta gyara zamanta zuwa kallon office din mr ata tana jiran taga irin korar wulakancin da zai mata."
Ahankali maryama tayi knowking tare da cewa" ko zan iya shigowa sir "abun mamaki sai ji tayi yace "comming "! zazzafan numfashi da ajiyar zuciya ta sauke tana mai tura kofar glass din ta shiga idanunta kyam akanshi tare da maida kofar ta rufe ahankali batare data juya ba, yana tsaye yana waya ahankali cikin yin kasa da murya "okay kuna bukatar qarafe kimanin adadi nawa ?okay okay !!
"shikenan zan hadaka da ahmed zan tura masa komai yanzu zai nemeka amman fa bazan qarfi wannan farashin ba zaa sauke komai akan tsare no gsky bazan bada a wannan farshin ba gbdy mun qara farashin komai namu saboda ingancin abubuwan da muke amfani dasu dan haka ka tura kudi sai tura maka kaya."
Cike da sanyi muryar maryama ta bude baki "sir ! ya dakatar daita da yatsan hannunsa yana cigaba da magana "ka tsaya ka fahimceni wannan matsalar ba daga gareni bane ,Okay idan yayi maka shin kenan sai najika idan kuma bai maka ba babu matsala ma hadu zuwa gaba".shayayyun idanunta ta tsura masa tana kallon yadda yake magana a natse cikin harshen tsadadden turancinsa bakinsa ma da kyar yake motsawa har sanda ya ajiya wayar office yana kallonta tare da qara girman idanunshi akanta tunda daga kasanta ya dauki kallonta har zuwa samanta yadda bai ce mata komai ba haka itama bata ce masa ba saboda gudun wulakancinsa.”
ta lumshe idanunta ta sake rungume littafin dake hannunta "dan kawai ki tsareni da wadan nan idanuwan naki kika shigo min office? "no sir ammm actually actually ..!!sai kuma tayi shiru ta kasa cigaba da magana "actually what ?"ya tambyeta yana sake tsareta da tsumammun idanunshi ."idan baki da abun cewa kina iya wucewa ki bar min office dina "no sir ina dashi daman nazo maka design din shejaranjiya ne na qarasa shi ajiya gashi nazo dashi ta ajiye agabansa ."tana mai sunkuyar da kanta kasa tare da jin wani sabon fad'uwar gaba mai tsanani ."
"this is totally nonsense maryama “me zanyi dashi?ya tamvayeta cikin zafin zuciya yana tsareta da kwayar idanunshi .”
ahankali ta dago kanta ta zuba masa idanunta " ki dauke min wannan shirmen daga gabana dan basu da wani amfani a wajena yanzu dan takalmin kafarki ma ya fishi daraja a wajena dan hk ki daukeshi banason ganinsa .”tana kallonsa jikinta na rawa dan azahiri ake iya ganin yadda jikinta yake rawa Matsowa tayi kusa dashi kad'an still tana kallonsa tana jin kamar ta kamo hannuwansa gabadaya cikin nata ta rike ta rarrashesa dan tabbas ta aikata masa ba daidai ba.” manzon Allah sallallahu alaihi wasalam yace “idan aka ‘bata maka ka nuna fushinka dan kai ba jaki bane ." haka zalika idan aka baka hakuri ka hakura dan kai ba sheidan bane sai dai tasan duk abinda zatayi a yanzu bazai sauko ya karbi aikin ba sakamakon mugun taurin kan dake garesa uwa uba zuciya " kin wani tsaya kina kallona ?”
ta marairaice masa fuska kamar zatai kuka .”
"maryama leave my office right now I don’t want to see your face ." ya fad'a yana nuna mata kofar fita ."
"Dan girman Allah sir ka sake bani wata dama .”
"babu wata dama da zaa baki domin ke kullum cikin matsala kike sannan rayuwarki kullum acikin second chance take ko wace dama zaa baki sai wannan mataccen yasa kinyi loose "ya fad'a yana jan tsaki tai shiru tana nazarinsa da mamakinsa ta rasa dalilinsa na daukar zafi har haka akan mijinta "bata gama tunaninta ba ta sake jiyo muryarsa "there's no second chance maryama go back to your work ."
"am so sorry sir ..."I said go back to your work ya fad'a a tsawace "go! ya sake furtawa yana nuna mata kofa da bakinsa jikinta a sanyaye ta kallesa sai dai hankalinta a tashe yake, ta juya da sauri tun kafin ya rufeta da duka dan taga alamun zai iya aikatawa yabi bayanta da kallo kafin a hankali ya zauna akan kujera ya sauke numfashi ya dauki wayarsa dake ringing "yes sweetheart daga can bangaren tace "fatan ka isa office lafiya ?lafiya sweetheart “yarinyar tazo office ne ."?
"yes sweetheart !" fatan kayi abinda nace kayi "? ya juya ya kalli kofar da maryama ta fita yanzu "ai nasan bazakayi ba ,wacece ni da zance kayi abu kayi min alokacin da nace ? tana gama fadar hk ta katse yayi shiru kawai yana tuna maganar daya gama fada mata tanzu "I said go back to your work yana cikin wannan halin ya sake jiyo muryarta tana neman izinin , itama kasa samun natsuwa da kwanciyar hankali tayi koda ta koma office dinsu bata iya aikata komai ba ,zuciyarta ce ta dinga azalzatar ta dawo garesa ko zai kasheta gara ya kasheta ta huta."
ya tsura mata ido kawai ganin irin kallon da yake mata ya sake kidima ta tana qoqarin sake juyawa ta fice idanunta suka sauka akan takardar zanen data ajiye masa da hannu ta nuna masa saman table dinsa "sir na manta file dina .”
ya nuna mata da hannunsa alamun ta d’auka tasa hannu ta d’auka "madadin ta wuce sai tayi tunanin ta sake bashi hakuri "kayiwa girman allah da girman iyayenka kayi hakuri akan laifina bazan sake aikata wannan Kuskuren ba idan nayi ka d’auki kowani irin hukunci akaina “ ta qarasa maganar cike da raunin zuciya wanda adaidai lokacin ya juyar da kanshi gefe ganin hk yasa itama ta juya cikin sanyin jiki ."
Har tayi taku biyu taji sautin muryarsa ta doki dodon kunnenta "am sorry too for yesterday ."da wani irin mugun sauri ta juyo ta tsura masa ido.”
Mmn Sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.