Best / Popular Hausa Novels

Maradams Book 3 Complete Hausa Novel

Reading file: MAR ADAMS BOOK 3 COMPLETE BY AYSHA BAGUDU.txt

Chapter 6 of 29

Page 7

Fita ata yayi daga gidan gabad’aya zuwa gidan mb sai dai har yaje gidan abinda baba qaramin yayi masa nata damunsa acikin rai , mb bai fahimci yana cikin ‘bacin rai ba dan yasan halinsa kullum cikin had’e rai da kamewa yake shiyasa ma ya fara da yi masa maganar maryam “adamcy baka ga ya kamata ka waiwayi yarinyar nan maryam da cikin jikinta ba ?shiru ata yayi tare da sake had’e fuska sosai , mb ya dawo kusa dashi tare da tsura masa ido yana dubansa “mai yasa kana girma amman har yanzu baka da wayo ?” yanzu d’an ko ‘yar da zaka fara samu a duniya zaka wulakanta?kallonsa kawai ata yake ko kifta ido ba yayi sai ma wani kalar kallon banza da yake masa .ahankali mb ya sauke numfashi “ka zauna ka natsu adamcy duk ‘yanuwanka sun kawo ido sun zuba maka saboda gudun fushinka “me zanyi mb ?”yayi maganar a zafafe yana jan tsaki “nifa yarinyar nan gabad’aya na manta daita arayuwata idan har ba maganrta akayi ba sam sam bana tunata“.

“ba ace ka dinga tunawa daita ba tunda ansan baka sonta ,abinda take d’auke dashi ake son ka waiwaya kasani ko iya rabonka kenan a duniya ?take ata yaji wani sabon damuwa ya masa mummunar kamu . sosai yaji zuciyarsa na bugawa da sauri sauri
“Ka natsu sosai ka duba maganata “.cike da jin haushi ya fesar da iskar bakinsa mai zafi yace “ka daina min mugun baki mana “ba mugun baki bane adamcy misali nayi maka domin kasan kuskure kake yi “to bana son wannan musalin please.”ya fad’a cikin tsnanin fushi “kayi hakuri adamcy ba baki bane bamusan menene a rubuce a cikin kundin littafinmu ba dan haka kayi wani abu ko sau d’aya ne kaje ka ganta “I can’t !”ya fad’a a zafafe .”zaro ido mb yayi “what do you mean adamcy ?kana da hankali kuwa? “ I don’t know ko ina dashi ko bani dashi but I don’t fell to go. “ what’s wrong with you?are you trying to say that you are not going to see her and your baby ?”exactly !”

“Please adamcy don’t do that kaje saboda babynka ba saboda ita ba “I don’t fell like zanje “okay ka kirata ko ta waya ne kaji lafiyarta data baby “dan girman allah mb banason damuwa bana jin zanje koina ,ko nace tayiwa kanta ciki ne ?ko lokacin daakayi cikin nasani bare yanzu kazo ka dameni da banza banzar magana ?ya hau mb da fad’a yana huci yana gama fad’ar haka ya d’aura kansa akan hannun kujerar da yake zaune sake matsowa kusa dashi mb yayi zai masa magan yace “enough !ya fad’a a tsawace tare da d’aga masa hannu alamun ya kyalesa “mb banason sake jin komai akan yarinyar nan .yarinyar data cuceni ta cuci rayuwata bazan ta’ba yafe mata ba tayi adduar ta rigani mutuwa domin idan nine na rigata mutuwa na barta da nauyi domin bazan yafe abinda tayi min ba .”

“zaro ido mb ya sake yi yana cewa”haba haba !!adamcy mai yayi zafi haka ?meye acikin abinda tayi bayan hakinta ne “shine akace tayi min fyade ?”dan allah ka daina fad’ar haka “na gaji mb abar maganar nan hk dan danasan dashi zaka tareni wallahi da bazan zo ba haka mutun yazo da damuwa ka sake qara masa wata damuwa ya fad’a tare da point dinsa da hannunsa “kyalesa mb yayi ba dan yaso ba sai dan sanin halinsa da yayi mutun da idan ya kafe akan abu to zai yi wuya a tankwarasa.” a natse ya mike tsaye yana jan tsaki ya fito zuwa haraban gidan inda motocinsa da masu tsaronsa ke zaman jiran fitowarsa ahankali mb ke take masa baya har suka qaraso inda motar da zai shiga yake aka bud’e masa “adamcy karkace na dameka amamn dan Allah kasamu lokaci ka duba maganata ,ka mika lamarinka zuwa ga allah ka tsarkake zuciyarka dominsa tun kafin haki ya kamaka ka tausayawa yarinyar nan wallahi ina tausayawa yanayin da take ciki ga tarin damuwa ga soyayyarka ga cikin jikinta.”

ata bai ce masa uffan ba sai ma d’aga tsumammun idanunshi yayi ya sauke aka wrist watch din dake d’aure a hannunsa ganin lokaci ya tafi yasashi jan tsaki sannan ya shiga bayan mota ya zauna aka jashi inda zuciyarsa ke wani irin bugawa da qarfin gaske kamar kar mb yayi masa maganarta haka nan kuma sai yaji abun na damunsa har ya dawo gida yana jin maganr na yawo cikin kwakwaluwarsa mai yasa ma naje wajensa?yayiwa kanshi tamabyar yana jan tsaki .” yana hawa sama bedroom dinshi ya nufa ya tsaya a bakin window dakinsa yayi shiru yana tunanin maganar mb gabadaya sai yaji duniya ta tsaya masa waje daya cak bai taba sani dan anyi masa maganar cikin jikinta abun zai tsaya masa arai har ya damesa ba ,wani irin tashin hankalin ya shiga qirjinsa na wani irin bugu “bai sonta amman abinda tayi masa yafi rashin son da baya mata ciwo "ya dauka zafi da ciwon rashin so da baya mata zai tsaya ne iya kanta kawai ashe ba iya kanta kadai zai tsaya ba har da dan cikinta “nonsense girl kawai yadda kikayi cikinki haka zaki raini abunki ki haifa I don’t care .”

Yana tsaye yana tunani mami ta turo kofar bedroom dinsa ta shigo hannunta rike da cup din shayi da d’an qaramin tray yayinda idanunta ke kansa bai san ta shigo ba sakamakon zurfin da yayi cikin tunani “ta qarasa ta ajiye tray din hannunta akan table ta sake dawowa wajensa ta tsaya tana kiran sunansa “adamcy nah ! firgigib ya dawo haiyacinsa yana sauke wani zazzafan numfashi ya tsura mata ido itama idanunta yana kanshi tana nazarinsa “lafiya tunanin me kakeyi haka ?numfashi ya sauke da karfi yana tura hannuwansa duka cikin aljihunsa sannan ya girgiza mata kai yana yamutsa fuska alamun babu komai “okay ga shayi nan na kawo maka ka dauka ka sha “ahankali yaja qafafunsa ya isa inda ta ajiye tray ya d’auki cup din ya rike yana dubanta “sweetheart ina kikaje ne tun safe banji motsinki ba kuma na kira wayoyinki duk suna shiga bakya d’auka ?”yayi maganar kwayar idanunshi na kanta “ naje hospital”da sauri ya motso kuda daita yana kallonta a d’an tsorace “lafiya ina Ke miki ciwo ?mai yasa kike je ke kad’ai baki tasheni ba ?yayi mata tmbyr ajere cike da shiga tashin hankali “lafiya ta lau adamcy naje wajen auta ne ta sauka lafiya ta samu d’a namiji “wani naunayen ajiyar zuciya ya sauke “na tsaya ne sai da’ aka gyara bby da mamansa sannna na dawo .”

Numfashi ya sauke fuskarsa yana bayyanar da wani sihirtaccen farinciki take maryam tazo ransa da sauri ya kawar daita yana cewa “masha allah auta ta zama uwa “sosai kuwa sauran kai ma ka zama uba dan nan kusa maryam zata haihu gefen bakinsa ya kamo yana cizawa ahankali ahankali batare da yace mata komai ba “Allah ya rabata da cikin lafiya !”shiru yayi yaki cewa komai ta riko hannunsa ta zaunar dashi akan gado itama ta zauna a gefensa tana dubansa kamar zatai kuka “adamcy na rokeka ka yafewa maryam wallahi rayuwarta na bani tausayi duban mami yayi yana kankance ido “wato shi ba abun tausayi bane data cucesa sai itace abar tausayi ? yayi maganar acikin ransa “ni mahaifiyarka ce ina neman alfarma ko sau d’aya ne ka yiwa maryam addaur sauka lafiya wallahi tana cikin wani hali likitoci ma sunce da kyar zata iya haihuwa da kanka runtse idanunshi yayi kawai batare da yace komai ba kusan mintuna shabiyar tana jiran yayi magana amman yaki cewa uffan “shikenan tunda baza kace komai ba ni zan koma hospital “.ta mike ta nufi kofar fita “bari nazo muje tare bata juyo ba haka zalika bata kulasa ba sakamakon nauyin da zuciyarta tayi .”

Washegari

Ahankali maryama ta tashi tana mika da salati tare da rufe bakinta sakamakon hammar data kamata kai tsare bayi ta fad’a tayi wanka ta fito tasa kaya zuwa wani had’ad’den doguwar riga blue da ratsin yellow tayi rolling kanta da qaramin mayafi yellow ta shafa powder kawai da white lips duk da ba wani kwaliya tayi ba amman she look attractive tayi kyau sosai ta feshe ilahirin jikinta da turare ta qarasa inda takalmanta suke ta sanya flat haif shoe ta fito inda ta iske umma a falo tana ajiye kular abincin akan qaramin table da alamun duk ita tayi aikin gidan dan ga koina nan fess ta qarasa inda take ta durkusa har kasa cike da girmamawa ta gaisheta”ina kwana ummah ?kin tashi lafiya maryama ?alhamd umma “har kin shirya zuwa aiki ?eh umma na shirya sannu da aikin “yauwa maryama .mai yasa baki tasheni nayi ba ? ta fad’a tana tsura mata ido “numfashi umma ta sauke tana dubanta itama “ lafiya umma ko shigata batayi bane naje na canza ?Aa shigarki tayi kinyi min kyau né sosai fiyye da lokutan baya “murmushi maryama tayi tace “na gode sosai umma zauna kici abinci atare suka zauna umma ta zuba mata abinci ta fara ci a natse tana duba lokacj bayan ta gama ci tayi mata sallama ta fita gurin aunty ta shiga ta gaisheta tace “aunty zan fita aiki aunty tace daita “tô pricess sai kin dawo allah ya tsare.” ta fito tana ma aunty bye bye itama aunty daga mata hannu tayi cike da farinciki.”

Ahankali take d’aga qafafuwanta hannunta rike da file ta nufi office din ATA hankali take tafiya tana tuna maganganunsa na jiya “idan zakizo aiki karki zo min da wannan package din Kiyi shiri kamar kowani ma’aikaci ta furzar da numfashi tana rausayar da kwayar idanunta saboda sanin cewar ba irin shiri su tayi ba ta dai sauya daga nata shirin dan gsky bazata iya shigar suit da wondo ba da wannan tunanin ta qarasa jikin glass door tayi knowking tare da neman izinin shiga daga can bangaren aka bata umarnin shiga .”cike da sanyin jiki ta tura kofar ta shiga yana zaune akan kujera ta tsaya a gabansa tana kallon kasa ya bar abinda yake ya d’ago tsumammun idanunshi ya tsura mata yana kallonta cike da tsantsar qauna ,shigar tayi masa kyau sosai dan daman shi yana mugun son yaga doguwar mace cikin shigar dogayen kaya but yanayin aikinsu kowa shigar suit yake kusan minti shabiyar yana kallonta kafin a hankali ya d’auke kwayar idanushi .”

Muryarta a hankali ta fito “good morning sir ! bai amsa ba ya nuna mata wurin zama “ki zauna jiki a sanyaye taja kujerar dake fuskarsa baya kad’an ta zauna a hankali tamkar kazar da Kwai ya fashewa aciki yayinda zuciyarta ke wani irin rawa shi kuwa gabadaya hankalinsa da natsuwarsa suna kanta amman bazaka ta’ba iya ganewa ba stil kuma idanunshi na Kan file din hannunsa .itama haka nan ta tsinci kanta da kallonsa kyakkyawan gaske ne kuma fari ne tas tmkr balarabe yana da idanu masu dan girma da dogon hanci mr ATA iyakar haduwa ya gama haduwa sosai ajin farko yana da tsayi da fadin qirji yana da saje zuwa rabin fuskarsa sai gashin bakinshi daya zagaye gemunshi gashi dogo mara kiba sai dai ya dan fita tsayi da kad’an ”.
Shiru har tsawon mintuna ashirin bata ce uffan ba “ko zamu iya yin maganar aiki dan a tunani shi ya kawoki ba wai tsayawa kallona ba ? tai saurin d’auke idanunta akansa ta sunkuyar kasa saboda tsananin kunyar data mamayeta ahankali ta kamo yatsun hannunta tana wasa dashi “zamuyi aiki ne akan wani project kuma ina son kece zakiyi .”yayi mgnr yana dago kwayar idanunshi ya zuba mata adaidai lokacin da itama ta d’ago nata kwayar idanun nan take idanunsu ya tsarke cikin juna wani abu suka ji ya tsarga masu alokacin daya yana bin jijiyoyin jikinsu barin ma ata wanda taji tamkar ana fizgar ransa ne .”

A natse ta gyada masa kanta alamun ta gamsu cigaba da kallonta yayi tare da yi mata bayanin yadda yake son aikin ya kasance still kwayar idanu shi na cikin nata dole so yake ya dasa qaunarsa cikn zuciyarta domin ta hakan ne kawai zai samu saukin fahimtar daita sirrin dake ransa .”ya mike tsaye daga Kan kujerarsa ya d’auki system dinsa ya zagayo zuwa inda take zaune , ya zagayeta da hannunwansa duka yana nuna mata irin aikin da yake bukata yana nuna mata yana shakar numfashinta yayinda kamshi turarensa ya dinga sakata jin mummunar fad’uwar gaba mai karfi .” ya dauki tsawon lokaci suna haka kafin daga bisani ya ajiye system a gabanta ya zuba hannuwansa ciki aljihu “ina fatan kin fahimci abinda nake bukata ?In sha allahu zanyi aiki mai kyau zan kwantar da hankali nayi maka abinda kake bukata” da kyau ya fad’a ya dauki file yana dubawa muryarta na rawa tace “sir ko zan iya tafiya ?da hannunsa yayi mata alamar zata wucewa ta mike tsaye da kyar ta wuce tana mamakin hali irin nasa tunda take bata ganin mutun irinsa ba mai jin kai ,mulki da nuna isa ko da yake shi din mai tarin kudi ne kudi kuma babu abinda basa saka mutu .”

Jiki a sanyaye ta koma office ta soma aikin da sectary ta bata bata wani dauki lokaci ba ta kammala ta kai mata ta dawo office byn Kmr minti goma ata yasa aka kira ta shigo da sallama ta tsaya cike da girmamawa tace “sir gani ! “set !ya fada yana kokarin bude system sannan ya fara magana ina bukatar fresh design na kamfanin wanda yafi AGC kuma ana bukatarsa ne cikin kwana daya kacal d’an haka sai ki shirya aikinsa daga yanzu “amman sir ko zai zama kwana biyu saboda na samu natsuwar yinsa akan tsari ?”no ! ya fad’a tare da tashi tsaye ya fice daga office din ya barta zaune .” ta juya da sauri tana bin bayansa da kallo yana tafiya a natse hannunsa daya cikin aljihunsa ,goshinta ta dafe “wannan wani irin mutun ne sam baya tsayawa yaji raayin mutun babu yadda ta iya haka ta mike ta fito ta koma office ta fara shirin aiki.”

Tana zaune a office tayi concentrate sosai akan aikinta ya shigo ya tsaya akanta yana qare mata kallo kamshin daddan turarensa ne yasa ta d’ago kwayar idanunta ganishi tayi tsaye rungume da hannunwansa duka a qirji yana kallonta da tsumammun idanunshi shiru tai tana mamakin irin kallon da yake mata, fahimta yayi zata iya fassara kallonsa gareta yasa cike da sanyin jiki ya soma magana “har zuwa wani lokaci zaki kammala da wannna aikin? shiru tayi kawai tana dubansa na second biyu sannan tace “sir ina Kan kokarin yi”Kinsan dai na fad’a miki akwana daya ake bukata daga yanzu zuwa gobe da safe kenan “na sani sir zanyi qoqari in sha allahu na kammala yanzu haka ma nayi nisa so..” bai tsaya jin mai zatace ba ya fita ya barta bude da baki .”byn Kmr awa daya ya sake shigowa ya kai hannu ya d’auki makeken takadar zanenta yana dubawa ta dan kallesa ta dauke kanta tana rausayar da kwayar idanunta Kan zanen da take ji yayi kamar ya zube ajikinta ya rungumeta tsam ajikinsa yana mugun qaunar kallonta . can ya ajiye takardar ya maida kansa ga kallonta idanunta na Kan takadar zane har guda biyu “wannan zanen bai min ba gasky .” ya fad’a a tsawa ce.”

ta dago daga abinda take tare da mikewa tsaye tana kallon farar takardar dake Kan table “a haka ne kike cika baki kin iya har da zaa yi alfahari dake this is totally nonsense “ ya fad’a yana jan tsaki .”sir a naka ganin zaka iya ganin kamar bai yi ba, amman mai zai hana ka bari na kammala tukun sai kasan matsayin da zaka bashi “nace abu bai min ba kina agurment dani ?yayi mgnr adaidai lokacin da sectary dinsa ta qaraso ta tsaya a bakin kofa cikin tsananin tashin hankali.”sir wannan ai ba argument bane bayani nayi maka sai magana ta gaba ai sai daka tabbatar da kwarewata kafin kasa a nemo ni kuma ina tabbatar maka babu kamfanin da zaa kai zanena su kushe suce bai yi ba ,duk wanda kaga ya kushe zanena to hassada ce .” ta fad’a tana kallon cikin kwayar idanunshi kallo daya zaka mata ka fahimci ranta a ‘bace yake “ taya na kwantar da hankalina domin nayi maka abinda ya dace amman tun ban kammala ba ka fara zariya kana kushe min aiki amman idan kana ganin akwai wanda zai maka fiyye da nawa a kamfanin nan kana iya bashi yayi maka
ko da yake babu wanda zai iya shiyasa ka..”hussein maryama! taji an kira sunanta bata juya ba dan tasan ko wacece “how dare you argument with sir ?

“No ma ba argument bane ina dai fad’a masa abinda ya zamo gaskiya ne kawai taya tun ban qare aiki ba yazo ya tsaya min yace bai yi masa kyau ba this is totally nonsense .” ta fad’a tana hura masa hanci qirjinsa ne yayi wani irin bugawa da karfin gaske ya dinga jin kamar ana tsira masa allura a duk wata jijiya dake sansar jikinsa “tunda ya kafa mata tsumammun idanunshi bai dauke ba har sanda ta dasa aya gabadaya tsoro tattare da matsanancin firgici ya kama sectary dan bata ta’ba ganin wanda yayiwa sir haka ba yana magana ana maida masa cikin fad’a wannan shine karo na farko “kallo biyu ma baka isa kayi masa ba bare jayayya ta magana dashi .office din ya dauki shiru baka jin motsin komai sai na bugun zuciyar mutun uku mr ata , some da maryama “shikenan ki cigaba zanga karshenki ya fad’a yana kokarin juyawa tace “sir ina ganin ma zan wuce gida yanzu dan akwai abinda zanyi .”da sauri ya juyo yana dubanta a tsanake Kmr zai cinyeta,in sha allahu zan kammala zuwa gobe, sannan ka rike min takardata ko zan iya kar’ba? shiru ne ya biyo baya, ganin hk yasa maryama ta kwace takadarta daya rike yake kokarin fita dashi ta saka cikin jaka ta ra’ba ta gefensa ta kama gabanta ta barshi tsaye da mamakinta har ta kai bakin kofar fita ta tsaya batare data juyo ba “karka damu sir I wil make sure a submit the design tomorrow by 7 dot .”ta wuce ta barshi tsaye yabi bayanta da kallo yana jin wani irin quna lallai akwai aiki agabansa ya fad’a acikin zuciyarsa sectary ta matso kusa dashi “sir kayi hakuri I will talk to her zata canja lumshe idanu kawai yayi ya koma zuwa office dinsa wani zufa na karyo masa a gbdy ilahirin jikinsa “.

Mmn sudais
[8/31, 11:24 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

             Page 8

Mutuwar tsaye mr ata yayi a wajen yana cigaba da kallon  hanyar da maryama tabi ,duk yadda yaso ya kai ga son motsa sansar jikinsa ko ya  bar office  din zuwa nasa ko ya tsaidaita amman ya kasa  saboda  tsananin firgicin abinda tayi masa . "hakika ya yarda ya kuma amince wa zuciyrasa ya sadaukar wani mummunar abu na shirin faruwa dashi ,ko kuma yace alqadarinsa yazo qarshe akan maryama ." soyayyarta da yake tason boye mata take son lallai sai ya fito daita sarari kowa acikin ma'aikatar ya san da zamanta wanda shi sam babu tsarin haka a ra'ayinsa yafi son sai ya shigar da soyayyarsa cikin zuciyarta ta yadda  itama zata kamu da tsananin soyayyarsa sannan ma duk abinda zai faru ya faru ."

ji yake kamar yayi kukan abinda tayi masa a yanzu a gaban some. sosai zuciyrasa ke masa zafi da qunci gashi baya son tozartata sannan baya son ta janyo masa raini a wajen sauran ma'aikatansa ."kusa dashi some ta matso kad'an tace "sir kayi hakuri dan Allah "wani zazzafan numfashi ya sauke tare da naunayen ajiyar zuciya sannan muryarsa a tsarke ta fito tamkar mai koyon magana yace "karki bari maryama ta wuce gida kiyi maza ki  tsaidaita   lallai ki dawo tare daita ". some tayi matukar jin mamakin abinda ya fito daga bakinsa dan a tunaninta kalmar dakatarwa ce zata fito daga bakinsa amman sai  taji sa'banin haka ,dan haka bata  tsaya cigaba da jin mamakinsa ba cike da hanzari ta furta "okay sir sannan  ta fice da sauri tamkar zata hantsila yayinda maryama tuni ta sauka qasan ma'aikata tana  d'aga qafafunta a natse sai dai kallo d'aya zaka mata ka fahimci ranta a matukar 'bace yake dan wani irin tafasa zuciyarta ke yi."
    

ahankali tasa kai ta shiga cikin ma'aikatan dake  qoqarin fita daga cikin ma'aikatar sai ga some ta sauko tana ihun kiran sunanta "maryma! mryma !! sarai maryama ta jita amman tayi mata banza taki juyowa bare ma tayi tunanin zata tsaya ta saurareta kanta a kasa ta qarasa ficewa "securities karku bari yarinyar ce mai doguwar riga ta fita ku tsaidaita min ku tsaidaita !!sai dai ina tuni koda suka je tsaidaita tuni maryama ta tsaida mai adaidaita ta shige tana bashi umarnin su wuce ."
cikin tsanani tashin hankali some ta rike kugunta tana kallon bayan motar da maryama ta shiga yayinda hankalinta na qara tashi dan bata san yadda zata fuskanci mr ata ba ."tsabar mamakin maryama yaki barin zuciyarta bata san rashin mutuncinta har ya kai haka ba ,mr ata din zata dinga sa'insa dashi."? "Mai take taka dashi ?shiru tayi na second biyu kafin daga bisani ta girgiza kai ta fara tana zance zuci "anya ma kuwa babu wata a qasa ?sosai ta dinga tariyo irin kallon da mr ata din yake bin maryama din dashi  a d'an tsakankanin wannan lokacin  saurin kawar da tunaninta tayi domin tana jin hakan ba mai yuwa bane mr ata bazai ta'ba kamuwa da son maryama ba, wasu irin mata ne bai gani ba a rayuwarsa, bai kamu da soyayarsu ba sai wata maryama ."

bangaren mr ata kuwa cikin tsantsar 'bacin rai ya nufi office dinsa gabdaya duniya ta chakud'e masa waje d'aya jira kawai yake some ta dawo masa da maryama ya samu yayi mata ko mari d'aya ne  ya d'an huce abinda tayi masa zai d'auki komai amman ban da raini .  ahankali ya fara zariya acikin office din kwakwaluwarsa na sake tariyo masa magan ganun mryma sosai zuciyrsa ta dinga motsawa ."
da sauri some ta biyo bayansa zuwa office dinsa kamar wacce aka jefo haka ta shiga office din  cikin tsananin tashin hankali ta kame nisa kad'an dashi tana had'e hannuwanta waje d'aya yayinda zuciyarta ke cike  da matsanancin tsoro da fargaba ,magana take son yi amman ta rasa ta inda zata fara dan tasan  shi kamar yunwar cikinta kad'an daga halinsa sai ya huce akanta."

"ina ma hakan zai faru da zai fiyye mata sauki akan action din da zai iya d'auka dan tasan ita kanta ba tsira zatayi ba tunda fushinsa ba iya kan wanda yayi laifi kad'ai yake tsayawa ba ."zariya ya cigaba da yi tamkar wanda yayiwa sarki karya yana sake aunawa kwakwaluwarsa maganr mryama .daga kalmominta ya gane komai fa ya sauya agaresa yanzu ne zai gane shi din ba komai bane dan bai isa ya dakatar daita aiki ba kamar yadda ya saba yiwa sauran worker's dinsa  sai daí bazai barta haka batare daya hukuntata ba dan dole ma ya ganar daita kurenta ko dan gaba anya kuwa adam zaka iya d'aukar mataki akan maryama "?yayiwa kanshi tamabyar yana mai juyowa."

cak ya tsaya sakamakon ganin some tsaye a bayansa dan bai san da shigowarta ba aikuwa ya  kafeta da tsumammun idanunshi  tamkar itace tayi masa laifi , haka nan taji gabanta yayi wani irin mummunar fad'uwa da sauri ta soma magana  cike da in inna "sir.."!sir !!  kayi hakuri ban samu damar tsaidaita ba amman ka barta dani  hakika zan bari tayi datasani abinda tayi maka , ina ganin ma wannan shine karonta na qarshe da zata tako cikin ma'aikatan nan da sunan aiki ,dan ko zamu d'auki komai bazamu d'auki wulakancinta ba we can't take it any more cikin tashin hankali da tsoro take magana ." wani banzan kallo yayi mata mai tattare da jin tashin hankali mara misaltuwa wanda yasa take some tayi shiru cike da girmamawa tana dubansa ".

da sanyin jiki yake qarasowa inda take tsaye hannuwansa duka ya zura cikin aljihunsa wondonsa yana qare mata kallo atsanake  wanda shi a zahiri ba ita yake kallo ba fuskar maryama ce ke masa yawo acikin kwayar idanunshi ."kusan minti goma ya d'auka  yana kallonta sannan yaja wani dogon tsaki lokacin daya fahimci halin daya shiga ya  koma mazauninsa ya zauna yana sauke wani wahallalen numfashi sannan  a natse ya d'auki wani file ya rike kawai ba dan yin aiki akansa ba, gabad'aya ya rasa me zai yi ya huce  "sir kayi hakuri  zan rubuta mata takardar dakatarwa? ta fad'a tare da juyawa ta nufi kofar fita da sauri "wa ya baki damar aikata hakan ?."ta jiyo sautin muryarsa cikin tsananin fushi .cak ta tsaya tare da juyowa ta zuba masa idanunta tana mamakin jin abinda ya fito daga bakinsa ,sai dai  idanunshi na kan kallon file din dake rike a hannunsa ,sam  bazakace shine  mutumin da yayi maganar ba ".

ta qara taku biyu ta tsaya  gabansa cike da girmamawa tace "amman sir kana ganin ya dace abarta ta cigaba da aiki damu alhalin bata cancata ba ".?oh yanzu ne kikasan bata cancata ba ?yayi mata tambayar a wulakance tare da d'ago kanshi  ya tsura mata ido  "só .."sorry sir bansan mugun halinta ya kai haka bane shi yasa na .." "enough !ya furta a tsawace yana d'aga mata hannu "ke kinfi kowa  sanin  ko ni waye ba'a sani haka zalika ba hanani idan nayi niyyar dakatar daita ba sai kince  ba ". yana gama fad'ar haka yace "leave my office! da sauri ta juya tana cewa "okay sir. " sorry sir !ta  fice."wani dogon tsaki ya sake ja tare da ajiye file din hannunsa ya kai hannunsa   daidai habarsa ya rike yana ciza lip's dinsa da karfi ."

shiru yana zaune yana sake sake can yaja tsaki tare da sake mikewa yana zagaye office din "bai ka mata nã bar maryama haka ba dole ne na nuna mata kalata domin na lura yarinyar bata da tsoro shirunsa da qarfafan idanunshi basa firgitata ya kamata na shigar da tsorona cikin zuciyarta kai da kake bukatar ta soka idan ka shigar da tsoronka sai ya kenan ."?mr ata yayi shiru a tsaye kamar gunki  yana nazari da tunanin abinda zai yi sai ga d'aya daga cikin wayoyinsa ya d'auki sauti a natse ya juya  yasa hannu ya d'auki wayar dake ringing ya soma magana cikin had'addden turancinsa "No it  will be possible zuwa gobe zaku samu  ok ba damuwa."  yana gama fad'ar haka kashe wayar ya  ajiye wayar ya cigaba da tunanin maryama ."yanzu me zai faru idan yarinyar nan batayi aikin nan gobe ba ?"yayiwa kanshi tmbyr hannu ya kai goshinsa yana murzawa ahankali "adamcy ka natsu ka bar yarinyar nan tayi aikinta kai ma abinda kayi baka kyauta ba sam sam bai dace ba ,dole ka tunzura zuciyar maryama ya dace ka barta tayi aikinta ."numfashi ya sauke yayi taku biyu ya zube akan kujera yana kallon saman office din wani  murmushi dole ya bayyana akan fuskarsa yana cewa zuciyarsa "duk duniya ke kad'ai ce macen da zata kawowa adam rainin hankali ya barta ta kwana lafiya ."

A matukar gajiye maryama ta qarasa gida , ga tarin gajiya ga 'bacin ran mr ata  bata iske umma a parlour'n ba sai dai taji  alamu  tana kitchen dan haka kai tsaye d'akinta na bangaren  umma ta shiga ta ajiye jakar aikinta tana sauke numfashi sannan ta shiga bayi ta dauro alwala ta fito ta gabatar da sallah la'asar byn ta idar ta fito zuwa parlour inda ta iske umma zaune tana gyara efo,ta samu guri ta  zauna acikin daya daga cikin kujerun parlour'n tare da yi mata sannu da gida "umma ta amsa cike da kulawa maryama ta  yi  shiru gbdy ta kasa yin komai hatta aikin da ta kan taya umma idan tana gida  bata yi yunkurin yi ba bare wani aikin mr ata wanda take jin a yanzu bata da lokacinsa." umma ta kalleta a tsanake tana nazarinta sai dai bata ce mata komai ba yayinda  maryama  ke kukan zuci  zuciyarta na mata zafi da qunci. gashi bata da damar nunawa saboda yanzu ne umma zata fita shiga tashin hankali shiyasa tayita danne quncinta ita kad'ai."

ganin idan ta cigaba da zaman falon umma zata fahimci damuwarta dan har ta fara tambayarta da kwayar idanunta yasa ta mike ta koma d'aki ta kwanta  tana danne damuwarta batayi cikakken minti goma ba umma ta kirata ta fito jikinta a sanyaye ta tsaya tmkr wata mara lafiya  "lafiyarki kuwa tunda kika dawo na ganki wani iri meke faruwa dake ?"ahankali maryama ta nuna wa umma bata  da damuwar komai yanayin aiki ne "amman shine zaki shige d'aki ki zauna   ke kad'ai ga "? ba zama nayi ba na d'an kwanta ne ,"kwanciya adaidai wannna lokacin da magriba ta karato ?shiru maryama tayi dan yanzu kam bata da abun cewa ba umma ta tsura mata ido kafin ta cigaba da magana "ni nasan kina da damuwa yau kina dai son boye min ne ."

"Allah umma babu wata damuwa kawai dai yanayin aiki ne babu dadi ta fad'a tana zama kusa daita umma ta mike ta shige kitchen batare da tace mata komai ba dan tasan lallai akwai abinda ke damunta maryama umma ta fito rike da wata roba ta cigaba da aikinta yayinda maryama ta dan saki ranta kad'an tasa hannu suka cigaba da aikin tare da umma tun umma na saka mata ido domin son sanin damuwar maryama har ta sake domin dai ta fahimci babu komai din yanayin aikin ne kamar yadda ta furta abinda umma batasani ba shine kowace second da dare ke karatowa tashin hankali ga maryama domin kuwa damuwarta qaruwa sukeyi duk lokacin data tuna yanayin data  baro mr ata da yanayin tashin hankalin some ta biyo dashi sai taji zuciyarta ta buga da qarfi .sai hawaye ya cika idanunta da sauri take dannesu ."

Hannunta ta cire ta kwantar da kanta kan hannun kujera ta shiga duniyar tunani had'uwarta da mr ata gobe shi yafi komai gigitata matukar tsoronsa take ji bata san yaake take samun kwarin gwiawar musayar yawu dashi ba,anya kuwa zaki aiki gobe ?"tayiwa kanta tmbyr "no bazan je aiki gobe ba gara nayi zamana   "to me ke nan kikayi ?ai kin sake qarawa kanki sabon laifi kiyi qoqarin ki qarasa masa aikinsa idan Allah ya taimakeki kafin gobe zai  huce kai maryama karki je wannan mutumin bashi da kirki sai ya wulakantaki " zuciyarta ta gargadeta mikewa tayi tsam ta shiga d'akinta ta shig toilet ta kunnawa kanta ruwa tana qoqarin jan numfashi da karfafa zuciyarta karta yankewa hukunci kin zuwa aiki gobe dole itace qarama kuma dole itace zatayi hakuri da duk wani abinda zai yi domin ta samu damar cigaba da aikinta cikin salama ."

Karfe shida daidai  ya mike ya soma tattara abubuwan amfaninsa ya fito domin wucewa gida
Bayan sallar isha' i bayan yayi wanka ya  sanya gajeren wondo da farar riga ya kwashi  wayoyin kasuwancinsa guda biyu ya  fito zuwa parlour qasa qafafunsa sanye cikin wasu  hadadden silipas farare sol ga qamshin turarensa red na tashi ta koina a sansar ajikinsa kai tsaye dinnig ya nufa ya ja kujera baya kad'an ya zauna yana  daddana wayarsa  daya . yana  zaune saman dining dayar wayarsa  ta soma ringing ya d'auka ya duba yaga mai kiran  mutanen da suka bashi aiki ne dan hk  ya manna wayar a kunnensa tare da yin shiru yana sauraran mai magana "."ai nace maka it will be possible tomorrow zuwa 11 am haka I think komai yayi ready okay yana gama fad'ar haka yayi discounting din kiran ya soma neman  layin maryama kira biyu yayi mata bata d'aga ba har zai hakura dan bai saba 'bata lokacinsa akan kira ba da zarar yayi kira d'aya baa d'auka ba shikenan zai hakura sai dai a biyasa ."

Amman wannan karon sai ya tsinci kanshi da kasa hakuri ya cigaba da kiranta ai a karo  na hud'u ne ta dauka batare da sanin ko shine mai kiran ba"Slm alaikum ta furta cikin sanyayyar muryarta mai matukar sanyi da ratsa sansar jiki "shiru yayi yana jin yadda sautin muryarta ke saka bugun zuciyarsa na qaruwa fiyye da kaida yayinda kowace jijiya dake  jikinsa ta natsu tana amsar sakonni daga muryarta wani irin shauki soyayyarta ne ke fizgarshi  bai san sanda ya kai hannusansa daya daidai saitin qirjinsa ya fara shafawa ba daga can bangarenta ya sake jiyo sautin muryarta "hello wake magana  ?ta sake furta muryarta cike da rauni hannunsa daya ya cire daga qirjinsa ya kai daidai tsakankanin dogon hanshinsa zuwa goshinsa sai da ta sake maimaita hello sannna ya fixgo magana da kyar yace "hello !sai kuma yayi shiru yana jin wani irin mummunar faduwar gaba ".

"An kira mutun kuma anyi shiru dan Allah wake magana ina son na kwanta  bacci ." sauri ware idanunshi yayi sosai tamkar tana gabanshi "wato ma ba aikinsa bane agabanta bacci zatayi? ahankali ya kalli agogon wayarsa yanzu tara zata buga "idan mutun bazai yi magana ba ni gsky zan kashe wayata."  ya lumshe idanunshi yana furzar da iska mai zafi yayinda sonta ke sake huda zuciyarsa dama gangar jikinsa  tana cikin haka sai ga umma tace "ke kuma da waye ?"wallahi umma kirana akayi  tun dazu na d'auki kiran amamn tun daga hello basake cewa komai ba" muga number ko irin daya ce da wacce ake kirana ayi shiru."

maryama ta sauke wayar a kunnenta tare da katse kiran yayinda umma ta qarasa inda wayarta take ta dauko ta dawo kusa daita ta mika mata  wayar "umma ba number daya bace ."to Allah ya kyauta amman babu dadi a dinga kiran mutun ayi shiru ni yanzu ma yanke shawarar bazan sake daukar kiran layin ba koma Kiyi min blooking din layin na huta inji cewar ummah "uhm umma ki barshi kawai idan mai shi ya gaji ya daina kiranki tana rufe baki wani kiran ya sake shigowa wayar maryama  the same number daaka kirata ,da kamar bazata dauka ba sai kuma tayi tunanin ta dauka idan baa yi magana ba ta kashe wayar gabad'aya dan haka ta dauka tare da sallama sannan tace hello wai wake magana ne ?"

A zafafe yace "zakice baki gane mai magana ba ?"ni  gsky ban gane mai magana ba hassalima ban san number ba bare muryar mai magana "okay kina magana da mr ata "what !? ta fad'a tare da zaro ido waje jikinta na d'aukar rawa  daga haka bata sake cewa komai ba ta katse kiran jikinta na wani irin rawa "tabbas muryarsa ne" shikenan na rasa aikina inna lillahi wa inna ilaihi rajiun  umma ta matso kusa daita ta zauna akan hannun kujerar da take zaune  tana tambayarta "wani aikin zaki rasa ?cikin kuka ta girgiza mata kai tana saka hannu ta rufe bakinta saboda wani kukan da yake sake kufce mata.

"Ashe  maryama  akwai damuwar da zaki kasa fad'a min ?tayi shiru tana kuka kafin ahankali taji shigowar sako wayarta nan jikinta ya sake daukar rawa ta sake tabbatarwa kanta sakon dakatarwa ce "shikenan na rasa aikina ".shine kawai abinda ta dinga  maimatawa a fili cikin kankanin sakanni idanunta suka kada suka koma jazur ta dinga fidda huci " wani bala'in tausayin maryama din ya mamaye umma , "me kikayi  har aka dakatar dake aiki ?shiru maryama ba magana sai kuka "ni daman tun da kika dawo na fahimci kina tattare da damuwa amman kikace babu komai kinfi son kiyita boye  damuwa a zuciyarki tana cutar dake kina tunanin  boye damuwar shi zai miki maganin halin da kike cikine?"

cikin  murayar kuka ta shiga fad'awa umma abinda ya faru shiru umma tayi tana sauraronta har ta dasa aya umma  tace "maryama baki kyuata ba ya dace kisan yadda zaki masa magana duk da nasan kureki yayi ."wallahi umma kureni yayi sam mr ata bai da mutunci ni bansan sanda yana fad'a ina fad'a ba "amamn tunda a qarqashin ikonsa kike dole sai kinbi dokarsa sannan zaki zauna lafiya nan dai umma tayi mata fada sosai tare da kwantar mata da hankali dan bata son tana  yawan shiga damuwa da tunani saboda ba wai ta gama dawowa normal bane  da kyar ta  samu maryama tayi shiru ta share hawayenta  tace ta bata wayar ta duba taga sakon daaka turo  mata."

"A'a umma karki bude kawai ni nasan babu abinda zai saka mr ata kirana adaidai wannan lokacin ko ganin sakon madam some sai dan dakatar dani "ni umma miko min charbinki kawai na fara ja  ko
tunani  da damuwa zasu barni  ta qarasa mgnr tana sake furta kalmar "Inna lillahi wa inna ilaihir raji un, tana hadawa da salatin Annabi da istigifar "maryama ki natsu  in sha allahu ba abinda kike tunani bane Allah yana sane dake kuma zai kawo miki dauki bani wayar na duba jiki a sanyaye ta mikawa umma wayar  ta amsa ta shiga inbox dinta  umma ta fara karanta sokon a fili  "ki tabbatar da kin zo da aikin da muka baki Gobe karfe tara daidai wani irin juyowa maryama tayi ta fuskanci umma hawaye na bin kuncinta ."

Kallon kallo suka shiga yiwa juna "kingani ba duk da abinda kikayi masa amman har yanzu suna bukatarki a ma'aikatan su lumshe seyx eyes dinta tayi tana godewa allah da ba dakatar daita sukayi ba sako na farko umma ta karanta "ki dauki kiran mr ata magana ce akan desing's din daaka baki aiki shine sakon some dayafi komai daga mata hankali naunayen ajiyar zuciya ta sauke " yanzu sai ki tashi kije ki fara abinda ake bukata daga gareki "wallahi ni yanzu duk jikina a sanyayye yake akan aikin baa wa mr ata gwaninta komai kayi baka iya ba komai bai masa ba wallahi umma bansan ta ina zan fara ba ."

" haka zaki karfafa zuciyarki ki tashi kije ki fara sosai umma ta dinga karfafa mata gwiwa har  ta samu natsuwa da jin zata iya masa fiyye da abinda yake bukata daga gareta ."ahankali ta mike ta shiga dakinta taja kujera ta zauan ta fito da kayan aikinta d'auki farar takardar data fara zanen tana duba zanen da yace bai masa ba zanen yayi kyau sosai tana cikin tunanin yadda zata kawo wani sauyi akan zanen ya sake  kiranta  jiki a sanyaye ta d'aga cike da sanyi muryar tace " barka da dare sir ?you are very stupid dake da  gaisuwarki".shiru tayi hankalinta na sake tashi "ni zaki katsewa kira ?muryata nã rawa ta soma bashi hakuri ai kuwa hakan ya bawa mr ata damar zuba  mata ruwan matseefa."

Aiko  hanakalinta yay mugun mugun   tashi gabanta ya dinga  dukan tara tara cike da jin tashin hankali tace "nifa sir bana son fad'a kabi komai ahankali tunda kace tara ka bari taran gobe tayi mana idan banyi abinda kake bukata ba sai ka dauki mataki akai ".daga can inda yake zaune ya gyara zama tare da motsa bakinsa da niyyar sake mata wani sabon rashin mutunci  tunin maryama  ta kashe wayarta gabad'aya ta zuba tagumi da hannuwanta duka  tana mai runtse idanunta wayar ya cire a kunnensa yaga dip alamun ta kashe ya sake kira yaji swichoff
Tsaki yaja yasan zata rina ga rashin kunya ga tsoro wanda shine abinda yafi bukata tagani atattare daita
Ata nã zaune  yana tunanin had'uwarsu da maryama Gobe kamar ance ya d'ago kwayar idashin kawai yaga fitowar mutun daga kitchen ."

Tsumammun idanunshi ya ware akanta maryam ce da  ritsetsen cikinta da  yayi  girma sosai tana d'aga kafafuwanta da kyar yayi mugun tsura mata ido yana    kallota  nan take  yaji qirjinsa na wani irin  bugawa da qarfi  "duk da  cikin jikinta yayi girma sosai sai dai cikin bai  sa  tayi wata kiba ba sai uban fari data qara da gajarcewa yayinda hannunta ke rike da plet wanda bai san ko meye aciki ba ,ahankali ta cigaba da tafiya da kyar irin tafiyar masu ciki ta samu waje opposite dinsa ta zauna  tana danne damuwarta dan ita kad'ai tasan irin damuwar da zuciyarta take ciki akanshi ,dan ta  dauka kiyayyar da yake mata zata tsaya ne a iya kanta a she har da cikin jikinta kiyayyar  zata shafa ta sunkuyar da kanta kasa tana danne hawayen daya cika kwarnin idanunta ta soma cin d'anwake  wanda shi har lokacin bai san ko meye acikin plet din ba  sakamakon tazarar dake tsakaninsu tsumammun idanunshi kawai ya zuba mata yana kallonta da cikin jikinta ."

Mmn sudais
[8/31, 11:24 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

BOOK 3

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.