Maradams Book 3 Complete Hausa Novel
Reading file: MAR ADAMS BOOK 3 COMPLETE BY AYSHA BAGUDU.txt
Chapter 28 of 29
Cigaba da kallonsa tayi yana taku yana gyara zaman hullarsa har sai data daina hangosa sannan ta lumshe idanunta .mr ata yana gama fitowa idanunshi da m.b suka soma cin karo tsaye kamar had’in baki shima farin yadi ne sanye ajikinsa “ya sakar masa murmushin yana cewa “yi hakuri abokina sarkin zuciya ai kasan bazanki rakaka gurin gimbiya kuma sarauniyar mata ba ,muje ko !”ya fad’a yana mika masa hannu bayan sun gaisa mb yace” muje masaalaci muyi sallah tukun sai muje dan lokaci sallah ya kusa tsaki mr ata yaja yace “ai kai wallahi baka da mutunci sai ka gama batawa mutun rai ka dawo kana bashi hakuri “naji dai ai gara ni tunda zan iya bada hakuri muje amamn fa abokina kayi kyau sosai wannan sai kasa maryama ta furta kalmar só batere data sani ba .”
wani irin kallon iskan yayi masa “allah baqaramin kyau kayi ba wallahi duk inda muka bi dole sai an kalleka saboda uban wanka turaren da kayi ko mace sai haka nifa ina ganin kamar har da hoda ka shafa ko ?shi dai mr ata bai tanka masa ba har suka isa massalaci yana koda kyawun da adamcyn mami yayi wanda shi bai ce masa komai ba qarshe dai yayi shiru yana cigaba da sauraronsa .”
Mmn sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
45
Daga masallaci basu tsaya koina ba sai akan titin unguwar su maryama, bayan sun samu guri sunyi parking suka fito ahankali inda m.b ya tsaya shiru yana karewa yanayin tsarin unguwar kallo ,”titin unguwar tasu babu laifi sai dai cike take da jama’a ‘yan cirani da ‘yan sikiraf “mr ata tsab ya fahimci inda hankalin m.b ya dosa dan haka tun kafin yace masa wani abu ya tsosa keyarsa yace “kaga malam ban son gulma da iskanci muje!”.wallahi wannan yarinyar bancin a mafarki ka fara ganinta da nace asiri ta maka, dan irin wannan unguwar sai dai aikin asiri ne kawai zai kawo mutun .”
a natse mr ata ya wucesa ya d’auki hanyar dogon lungun da zai shigar da mutun zuwa kofar gidansu maryama.ganin haka yasa m.b ya biyosa da d’an sauri suka jera suna tafiya acikin lungun mamakin m.b ya sake qaruwa dan duk yadda ata ya fad’a masa yanayin unguwarsu geto area ne bai d’auka haka yake ba dan har gara kan titi akan wannan lungun da suka shigo. m.b dai ya kasa hakuri yace “lallai wani abu sai aikin syya idan ba soyayya ba mai zai kawo mutun irin wanan ungu war ?”ko da yake wannan shine abinda yafi dacewa ga attajirai irinku masu jin kai soyayyarku ta qare akan yaran talakawa wanda ba kome bane.”madadin mr ata yaji zafin maganarsa sai ma yace“ashe dai kana da raunin imani kasani nasani babu wani abu da zai gagari Allah kawai zai fi kyau kace qaddarar aurena tana cikin wannan unguwar kuma ban isa na gujewa qaddarata ba ko tazo ta sameni a inda nake ko kuma ni na biyota inda take kamar dai yadda ya faru sai dai in sha Allahu da zarar na d’auke maryama daga unguwar nan daga ni har ita mun bar shigowa cikinsa”mr ata yana gama fad’ar haka ya ciro wayarsa ya soma neman layin maryama domin ya sanar mata isowarsa da kuma katse duk wata magan da zata fito daga bakin m.b sai dai akayi rashin sa’a layin nata a kashe yake .”
Har suka qaraso kofar gidan kiran bai shiga kira biyar yayi mata anace masa layin switch off yayi shiru yana tunani yayinda nan take moon dinsa ya sauya zuwa damuwa.”mb ya kallesa yace “ya’akayi ne mutumina naji kayi shiru ko akwai matsala ne?layinta ne wai akashe “okay sake kira may be matsalar network ne kasan yanayin network din yanzu bai fiyye kyau ba bare a irin wad’an nan unguwannin,sake kira idan bai shiga ba sai mu samu yaro mu tura cikin gidansu take yabi shawarar m.b ya sake kira layin cikin sa’a layin ya soma ringing sai dai bata d’aga ba sai da yayi kira biyu a karo na uku ne ta d’aga tare da yin shiru taki cewa komai illa numfashin data dinga sauke masa acikin kunnensa wanda ya haddasa masa shiga cikin wani yanayi mai tsarkakkiya da wuyar musaltuwa wani iri naunayen ajiyar zuciya mr ata ya sauke da qarfi shima .”
kamar yadda maryama tayi shiru haka shima yayi shiru har kusan mintuna sha takwas babu wanda ya cewa d’anuwansa uffan.” maryama ta sauke wayar daga kunnenta ta duba ko ya sauka akan layin ne sai dai gani tayi har lokacin yana kan layi magana ne dai bazai ba ta kalli inda umma ke zaune a kusa daita wacce ta kasa kunne domin sauraron abinda zata ce .”
da kyar maryama ta sanyawa jikinta jarumta tace “ina wuni sir….” “fito gani a kofar gidanku!” ya fad’a atakaice “what ?!ta furta a d’an firgice tana sake kallon umma kafin ahankali ta daidaita natsuwarta “ko ba zaki fito bane ? kwantar da murya tayi sosai tace “sannu da zuwa gani nan fitowa “.ta fad’a tana sauke numfashi tare da zubawa umma ido ,gabadaya duk sai yanayinta ya canza daga d’an farinciki data fara samu zuwa bakinciki ,dan a yanzu bata qaunar duk wani abinda zai zame mata damuwa arayuwar ta .“kallon tsanake umma tayi mata kafin ahankali ta motsa bakinta tace “bako kikayi ne ?cike da damuwa ta gyd’a mata Kai tare da cewa “mr ata ne yazo” mr ata sai yanzu zai nemeki ?” umma ta furta hakan
dan batayi tsamanin zai d’auki lokaci har haka batare daya kawo kansa ba dan har ta fara cire ranta akan son maryama yake .maryama tayi mamakin jin furucin umma “to yanzu mai km ya kawosa ?nima bansani ba amman may be ayyukan daya bani ne yazo kar’ba ganin kwana biyu banje aiki ba haka nan ta tsinci kanta da shara rawa umma karya “inda umma tace “ai shikenan sai kije ki samesa kiji abinda ya kawosa bata mike tsaye alokacin ba sai data d’auki kusan minti biyar zaune har sai da umma tace” ki tashi ki shirya kije mana kin bar mutun tsaye sannan ta mike da kyar ta shiga d,akinta .”
A can kofar gidan kuwa tun daga nesa baba gali ya hango tsayuwar mutane biyu a kofar gidansu cikin shiga ta alfarma tun bai qaraso ba yaji gabansa yana wani irin bugun tara tara ahankali ahankali ya dinga taku har ya kusan qarasowa inda suke tsaye , nan idanunshi ya tabbatar masa da ko waye tsaye, a fili ya sauke ajiyar zuciya had’e da kare masu kallon tsab cike da mamakin ganinsa yace “duk lalata da kayi a wajen aiki bai maka ba har sai ka biyota gida ai kuwa bazata sa’bu ba bindiga acikin ruwa nan take baba gali ya soma tunanin irin qalar wulaqancin da masu sai dai yana qarasowa gabansu yanayin yadda yaga fuskar gogan naku babu wasa bare alamun d’aukar nonsense yasa baba gali ya had’e abinda ke cikin ransa, ya ‘bige da yar gyaran murya kana yace “ashe kaina tsaye ?”m.b ya kalli baba gali sannan ya kalli mr ata sannan ya gaishesa .”baba gali ya amsa yana washe masa baki yace “sannuku da zuwa .”
”yauwa !”inji cewar mb shi kam mr ata sai da ya d’auki lokaci kafin yace masa “ina yini!” kuma daga nan bai qara ba sai ma sake had’e fuskarsa da yayi yana kallon wani banngare dabam “ku shigo daga ciki mana “ba wajenka muka zo ba ata ya fad’a yana fesar da iska mai zaki daga bakinsa jiki baba gali a sanyaye ya nufi cikin gida yana wai wayensu sauran ka d’an ya tuntsura da hannu mb ya nuna baba yana cewa ”halan waye wannan mutumin?”ban san shi ba “mr ata ya fad’a atakaice shiru m.b yayi kafin ahankali ya cigaba da magana “baka san shi ba amman kuma shi da alamun yasanka “kai ma kasan sanina ba abu ne mai wahala ba acikin kasar nan mb yaja bakinsa yayi shiru .”
Maryama ta d’aura after dress akan kayan jikinta tayi rolling mayafin after dress din ta dauki turarenta mai sanyin qamshi ta feshe ilahirin jikinta sosai tayi kyau ta fito zuwa parlour qamshin turarenta yasa umma ta waigo inda take tsaye tana qoqarin saka takalmi umma tai shiru kawai tana kallonta ,sai kace mai zuwa zance ko wani biki amman dai tayi kyau sosai Allah yasa mr ata ya furta mana yana sonta dan hakan nan take ji mutumin son maryamarta yake ,maryama ta qaraso ahankali ta tsaya kusa da umma tana cewa “sai na dawo umma” adawo lafiya amman kinyi kyau sosai maryama ta d’an murmusa tana cewa” na gode umma nah sannan tasa kai ta fice .”
ahankali take taku kamar bata son taka qasa yayinda zuciyarta ke wani irin tsinkewa tana tunanin abinda ya kawosa gidansu, har ta fito zuwa kofar gidansu ta tsaya inda idanunta suka sauka akan mr ata nata da kuma wani da bata san ko waye ba .”wani abu taji yana shigarta wanda take yawon jinsa ailahirin jikinta a duk sanda zata d’aura kwayar idanunta akanshi sai dai ta rasa gane komenene wannan abun dake shiga jikinta yana yawo acikin jini da tsokar.”
sosai taga yayi mata kyau acikin shigar da yayi looking extra ordinary mr ata ba dai kyau ba his nose is so pointed har baki ga gashin fuskarshi baki sitik kamar an ratsa golden brown aciki sai shining yake yi kamar ya zuba oil gashin yana cikin abinda yake mugun qara masa kyau ,”masha Allah ta furta ahankali.”
Numfashi da ajiyar zuciya ta sauke atare sannan a natse ta cigaba d’aga qafafunta.” tun daga nesa mr ata ya d’auki kallonta har ta qaraso ta tsaya a gabansu tana masu sannu da zuwa “sannuku da zuwa”! mb ne kawai ya amsa mata cike da kulawa shi kuwa mr ata yayi gum da bakinsa ya cigaba da kallonta wanda yasa tayi kasa da kanta ta kamo yatsun hannunta ta tsarke cikin juna tana wasa dasu.gabad’aya sai ta jita a takure sakamakon tsumammun danunshi dake yawo a sansar jikinta “bayan kamar minti biyar ta d’ago nan take kwayar idanusu ya tsarke cikin juna ,wani irin yanayi mai bugar da zuciya ya farmakesu atare ,da sauri maryama ta janye idanunta daga cikin nashi tana gaishesa “ina yini !?”har sai da dimple dinta ya lotsa kmr an saka nail da hammer anyi nailing cheeks dinsu norma normal ko bata tayi magana ba ana ganin alamun lotsawarsu still mr ata bai amsa mata ba ya cigaba da kallonta yana hukuntata da kwayar idanunshi masu firgitarwa tare da qara d’aure fuska tmkr wani zaki .”
mb yayi kusa dashi sosai tare da yin kasa da muryarshi yace “kayi mata magana mana ko za’a bamu izinin shiga ciki “still shiru yayi yaki cewa komai har sai da maryama ta sake d’ago idanunta, sosai ta tsorata da ganin yanayin yadda ya d’aure fuska yake kallonta,muryata na rawa tace” mu shiga daga ciki”still shiru yayi yaki motsawa har sai da ta sake yin magana “kayi hakuri ka shigo baza kuji dadin tsayuwa anan ba.” tana gama fad’ar haka ta juya .
Wani irin naunauyen ajiyar zuciya ya sauke da qarfi “kaga malam ka saki fuska mu da muka zo zance da ban hakuri zaka wani had’e wannan fuska tare da takure yarinyar mutane wannan fuskar zakin taka ai sai ka firgitata .” iska ya fesar mai zafi daga bakinsa sannan ya soma taku ya biyo bayanta shima mb ya biyosu sosai mr ata yake kare mata kallo yana furta masha Allah yarinyar ba dai diri ba she has the best figure kyawunta sirri ne ya godewa Allah da zai mallaketa ,kusan atare suka shiga gidan a haraban gidan suka tsaya mr ata yaki yin magana haka zalika maryama da mb babu wanda yace komai gabdaya marayam ta rasa meke mata dadi “wanna shirun nasa yasa zuciyarta Ke tsananin bugawa da qarfi ”
Cike da tsinkewar zuciya tace “please sir kayi hakuri nasan nayi maka ba daidai ba na ajiye aiki da nayi batare da sanar maka ba, dan rashin maganarka a yanzu ya fara d’aga min hankli matuka fiyye da tashin hankali dana shiga.”ta fad’a tare da yin shiru stil qirjinta na dokawa .”
baba gali dake tsaye aharaban bangarensa ya janyo hannun aunty salma suka la’be duk zufa ta rufesa “salma matso kiga ikon Allah “aiko karaf idanunta ya sauka akan mryma da ata tsaye “me zan gani kamar wancan mutumin da ya rungumeta a hoto ko ?”shine kuma shine dai wannan mutmin daya zo neman aurenta a boye na hanashi“anya salma malam bai fara girba miki karya ba?“Anya ma kuwa kinsa a farraka tsakaninsu domin muddin mukayi sakacin da maryama ta auresa mun tafka babban kuskuren da bamu ta’ba yi ba a rayuwarmu “ka yarda dani ba zan ta’ba barin muyi wannan kuskuren ba,ina ganin an samu kuskuren aiki ne amman tabbas malamina ya tabbatar min bazai aureta ba sai dai su qare rayuwarsu a neman juna.”
Maryama tayi kasa da kanta sosai tace “kayi hakuri dan Allah nasan nayi maka laifi gashi na sakaka wahalar zuwa unguwarmu ”ta qarasa maganar muryarta na rawa “mryama you should know me by now mai yasa rashin magana ta zata d’aga miki hankali ?shiru tayi tana kallonsa up & down.”
shi kuwa gogan hannu ya kai yana shafa qirjinsa yana jin wani irin sanyin dadi a ilahirin jikinsa “well yanzu ma ba saboda ke nazo ba nazo ne naga ummanki ki shiga ki sanar daita zuwana .”shiru tayi tana kallonsa cike da tsannain mamakinsa “ki shiga mana kin wani tsareni da wad’an nan idanuwan naki kmr na mage “.jiki a sanyaye ta juya tana taku ahankali tamkar kazar da kwai ya fashe acikinta .”
iskar bakinsa ya furzar yana bin every step of her “Adamcy kana mugun son yarinyar nan over wallahi mb so ba kad’an ba yanzu haka ganin da nayi mata wani irin yanayi mai tsarkakkiya da wuyar misaltuwa ke shigana da ana bud’e sansar jikin mutu nasan ana bud’e nawa tsananin soyayyar maryama da qaunarta kawai zaa gani yana yawo aciki ji nake na zarta duk mazan duniya shan wahalar soyayya amaman na godewa allah da zai mallakamin ita.”
“ karka cika baki ka fara sheida mata matsayinka tukun kafin wani yazo yayi maka shigar sauri dan irin wad’an nan matan Allah ba’a sakaci dasu itama dan tana cikin lugun ne da waje take wallahi da yanzu matar wani ce.”wani murmushin yake mr ata yayi yana shafa qirjinsa cikin kankanin lokaci ya hango tahowarta tana gama qarasowa tace “muje!” tana gaba suna biye daita har bangaren umma .”
basu iske umma parlour’n ba maryama ta kallesu tace “ga guri ku zauna yanzu zata fito.” mb ne ya soma zama akan kujera mai zaman mutun daya yayinda ata sai daya kalli maryama sannan ya zauna a natse yana gyara wuyan rigarsa bayan ya zauna ya d’an kalleta a tsanake yaga duk tayi wani iri kamar a firgice take ya d’an motsa lip’s dinsa “ya naga duk kin birkice?”ta girgiza masa kai”to ki zauna!”ya nuna mata kusa dashi tayi saurin girgiza masa kanta tana sake damke yatsun hannunta .”suna nan zaune har sanda idanun mr ata ya sauka akan hoton sadam dake manne a bangon parlour’n sosai ya tsurawa hoton ido yana kallonsa kafin ahankali yace “wannna shine sadam ?da sauri ta gyad’a masa kai tana cewa “shine sadam dina sir.” wani mugun kallo yayi mata yana sauke numafshi tare da jinjina kai yana jan tsaki adaidai lokacin da umma ta fito tana masu sannu da zuwa.”
Cike da girmamawa suka rusunar da kansu suka gaisheta ta amsa masu da kulawa tana murmushi ta kalli maryama dake tsaye “ya zaki bar bakinki haka batare da kin kawo masu komai ba?” akwia sobo da nayi d’azu da safe sannan akwia cinci a fridge maza je ki kawo masu “okay !” har ta juya taji mb yace “no a koshe muke wallahi mun gode sosai ya fad’a yana murmushi amman duk da haka sai data maryama taje ta kawo a gaban mb ta ajiye ta samu waje ta tsaya tana jin wani irin mummunar fad’uwar gaba .”mb yayi gyaran murya sannan ya fara magana a tsanake cike da kamala “amm daman abinda ya kawo mu akan abinda ya faru ne atsakanin maryama da adam “.
Umma ta jinjina kai sannan tace “ai nayi mamakin ma da sai yanzu biyo sawunta “mr ata najin haka yayi kasa da kanshi “kuyi hakuri da abinda ya faru
“Ala hakika gaskiya gabadayanmu bamuji dadin faruwar wannan alamarin ba kuskure aka samu daga gyara matsala abun ya dawo matsala domin shi yayi qoqrin yaga ya rabata da damuwar dake damunta ne ba wai da wata manufa hakan ta faru ba “.
“ba wai dan adamcy yana nawa ba wallahil azim shi din mutu min kirki ne .”umma ta kalli maryama tace “maryama maza kije ki kira aunty ayi komai a gabanta ahkli maryama ta juya ta fita yayinda mb ya cigaba da zayyanowa umma komai kamar yadda maryama ta fad’a mata yana rufe bakinsa aunty da maryama suka shigo bakin aunty d’auke da sallama cikin shiga ta kamala “yauwa ga mahaifiyarta nan” a sukwane mr ata ya juyo ya kalleta adaidai lokacin da take qoqarin zama kusa da umma, yayi shiru tare da tsura mata ido yana kallonta ta banga ren fuska ba tayi kama da maryamarsa ba dai dai ta yanayin jiki kasancewarta ba wata mai kiba bace duk da cikin hijab take amman yanayin ta ya nuna masa bata da kiba, yayi kasa da kanshi sosai inda idanunsa ya sauka akan yatsun qafafuwanta abun mamaki da d’aure kai irin yatsun sweet heart dinsa sak gareta ya d’ago kanshi kad’an zuwa yatsun hannunta nan ma irin yatsun maminsa ne gareta ya sake kallon fuskarta da kyau sai ma yaga kamar yasan fuskar ko kuma yace ya ta’ba ganin mai yanayin irin fuskar .”
Shiru yayi yana nazarin fuskar sosai amamn ganin ba abinda ya kawo shi kenan ba yayi qoqarin qawar da hakan acikin ransa ,sai dai aransa yana mamaki yadda yatsunta hannu dana qafa yayi kama dana sweetheart iska ya feasar yace “ kawai halittar yatsunsu ne ya zama iri d’aya bayan sun gaisa daita umma ta bukaci mb ya sake yin magana agaban aunty bai yi mutsu ba yabi umarnin umma yana dasa aya mr ata ya soma magana kanshi a kasa cike da nadama “ kuyi hakuri da abinda ya faru idan zaku d’aura laifin ku daura laifin akaina domin ni ne mai laifi if nayi shishigi acikin rayuwarta da duk hakan bata faru ba .”yana gama fadar haka yayi shiru yana jiran yaji abinda zasu ce.”numfashi umma ta sauke sannan ta gyara zamanta tace “duk na fahimceku sannna kai ma baka da laifi haka Allah ya qaddaro bawa kuma bai isa ya canza qaddararsa ba Allah yasa mu dace duniya da lahira “haka ne sai batu na gaba naji mryam tace ta daina aiki damu ?
“kwarai kuwa haka tace ammn bisa tsarinta ne ban sani ba ko dan mahaifiyarta tace ta fito da mijin aure nan da two month ne yasa ta yankewa kanta wannan hukunci bansani ba, amman kuma aganina hakan da tayi shine daidai agaremu gbdy domin tsare mutuncinta da kuma namu,duk da ina da yarda da kuma yakinin maryama ba mutuniyar banza bace a gabana aka haifeta in fact ma nice nayi mata tarbiya nasanta ciki da bai macece data san ciwon kanta duk dai ba’a sheidar d’an yau amamn maryama she’s the best kuma ina mata kyakkwan zato .”umma fad’a haka tana tsaresa da ido domin son gano wani abu atattare dashi ita dai tun bata ganshi azahiri ba take ma maryama shaawar aurensa bare yanzu data ganshi Allah yasa hasashenta ya zamo gaskiya mutumin son maryama yake kuma da aure .”
shiru adamcy yayi yana kallon umma da aunty wacce aka kira da mahaifiyar maryama yana tunain yadda gabad’aya take son rayuwar diyarta ta lalace idan ba haka ba mai zai sa dan mutun yayi kuskure kankani ace ya fito da mijin aure nan da wata biyu ba’a jin tsoron abinda zai biyo bayan auren ,” nasan kuna da gaskiya akan hukuncinku a matsayinku na iyayenta sai dai ina jin kmar ni ne na aikata laifin ita kuma ta dauki hukuncin mai tsanani .”ya fad’a yana furzar da numfashi sanan ya cigaba da magana cike da natsuwa da kamala “nasan ko ni ne naga diyata a wannan yanayin zan yi iyakacin bakin qoqarina na kare diyata amman bata hanyar tillasta mata ta fito da mijin aure acikin tsukukun lokaci nan ba saboda yadda rayuwar nan ta zama yanzu .”
shiru sukai gabad’aya suna sauraronsa da kunnen baseera “nasan abinda ya faru ba daidai bane amman kuma wannan hukuncin da kuka yanke mata yayi mata tsauri dayawa a matsayinta na diya mace mai qaranci shekaru nasan babu wanda yake son yaga rayuwar iyalinsa ta tagayyara tunda nake d’aukar masu aiki ban ta’ba d’aukar mai aiki irinta mai tattare da basera da kamaun kai ba, wallahi na yarda kuma na amince kunyi qoqri sosai akan tarbiyarta .”
wani sanyayen numafshi aunty ta sauke tana jin natsuwa acikin zuciyarta karon farko data gansa sai dai taji natsuwa dashi ,”tsannain yadda na damu na tsanata bincike akan abinda ya faru ina son na gano wanda ya d’aukemu hoto kuma dole zan gano kuma dole zai amshi hukuncinsa dan ba dan maryama aka yi wanan tozarcin ba saboda ni ne ,ni ake son tozartawa ba ita ba .duk suka jinjina kai ya lashi lips dinsa ya dan kalli inda maryama take tsaye tana wasa da yatsun hannunta sannan ya d’auke idanunshi ,ya tsurawa umma da aunty ido kafin ahankali maganarsa ta fito “ina rokon alfaram ku bar maryama ta cigaba da aiki tare dani nayi maku alqawarin zan kare mata mutuncinta ,zan kula maku daita zan tsaya mata km zan iya zuwa kowani irin mataki akanta nasan zaku yi tunanin ina da son kaina dawa wallahi ba haka bane ita kanta bazata cigaba da rayuwa mai dadi ba kasancewar tana son aikinta.”
“haka ne sai dai wannna hukuncinta ne ba namu ba itace bata bukatar cigaba da aiki “inji cewar umma “umma ki bar maganarta fatana ku bani dama ni zan mata magana ta yadda zata dawo aiki .”
duk suka yi shiru suka kasa cewa komai umma ta kalli maryama taga tana girgiza mata kai alamun karsu yarda karaf idanun mr ata ya sauka akanta da sauri tayi kasa da kanta tana jin wani irin mummu nar fad’a uwar gaba .”Mb ma bai yi sanya ba ya fuskanci wacce akace itace mahaifiyar maryama yace “aunty kiyi hakuri munyi miki alqawarin babu abinda zai sameta da izinin Allah duk abinda ya sameta ki d’auki duk matakin da yayi miki dadi akan mu.” numfashi aunty ta sauke ta kalli ata dake zaune shiru ,ta waiga ta kalli umma sannan tace duk naji bayaninku sai dai ni bani da abinda zance sai abinda umma tace idan ta yarda ta amince shikenan idan kuma bata amince ba sai ku hakura ,sai batun aure wannan kam bazan janye maganata ba bawai na gaji da zamanta haka bane ,amamn ta fito da miji dan aure shine darajar duk wata diya mace “ku yarda dani bazan ta’ba cutar da maryama ba “shikenan .”inji cewar umma “mun gode sosai shima mijin nan kusa zata samu da iznin Allah koma nace ta samu “wani irin kallo ata yayi masa” mb ya hararesa yana fuskantar umma inda itama umman cewa tayi “ shikenan Allah ya shige mana gaba amamn kuyi magana daita idan ta yarda babu matsala allah yasa haka ne abinda yafi zama alkhairi agaremu.”Umma na gama fadar haka ta mike auny ma ta mike tai masu sallama ta fice haka ma umma ta shige d’akinta mb ma ya yunkura ya mike tsaye yace “bari naje na jiraka a mota “.
adamcy ya gyad’a masa Kai ya fice ya barsu parlour’n ya saura daga ata sai maryama dake tsaye shiru taki zama har kusan mintuna goma tana tsaye daga gefensa on expecting maryama taji ya fixgota zuwa gefen jikinsa saurin d’auke numfashi tayi sannna ta waigo a gigice tana kallonsa cike da matsanancin tsoro.” iskar bakinsa da hucin numafshin ya dinga sauka a gefen fuskarta tayi saurin lumshe ido ahankali ya dawo daita ta gabansa still tana kwnace ajikinsa yayi mata kyakkyawan rikon da bazata iya kwacewa ba ya kai bakinsa daidai saitin kunnenta ya soma rad’a mata magana cikin sanyayyar murya shi mai tsananin kashe jiki da tsuma zuciyar wanda akayi dominsa “maryama ni zaki wa butulci ?” wani bugu qirjinta yayi yayinda jikinta ya d’auki rawa “ina kallonki kina girgizawa umma kai alamun karsu yarda ki sani bazaki ta’ba iya gujewa adam ba domin shi din mai nasara ne
Duk abinda yasa a gaba sai yaga qarashnsa kuma duk abinda yake bukata sai ya zama mallakinsa duk inda nake dole ki kasance anan bare a halin yanzu da zuciyata take cikin garari “inna lillahi! ta furta a kasan zuciyarta tsigar jikinta na mikewa “.
Ya fesa mata iskan bakinsa “bama haka ba har cikin zuciyata bana son yin nesa dake zan kulawar ummanki da auntynki ke.” yayi maganar yana sake damke jikinta dake rawa kamar mazari saboda tsananin tsoro “zuciyata na tsananin jin tausayinki bazan bar wani abu ya sameki ba ,addu’at da fatana Allah ya bani ikon cika alaqawa rin dana d’aukar masu ,sosai ya sake janyota jikinsa ta shige masa wanda hakan yayi mugun mugun d’aga hankalinta yanzu fa ya gama magana zai kula daita”kenan irin wannan kula war zai mata ?”muddin irin tace gsky bazata ta’ba kasancewa dashi ba ,ya sake Kai bakinsa daidai kunneta “ance baza’a d’aga miki qafa ba lallai sai kin fitar da miji aure “?ta lumshe masa ido tana sauke numfashi dan wani iri take ji a gabad’aya ilahirin jikinta “.ya sake sauke mata numfashin bakinsa a kunnenta “kinsan na ta’ba miki mgn akan ya dace kiyi aure? “muryarta cike da in ina tace “eh zanyi qoqarin na fitar da miji kafin lokacin da aunty ta bani “kenan kina da Wanda kike so ?”bani dashi amman zan nemo “zaki nemo ki auri wanda bakya so ?”to zanyi dole zan bi umarnin mahaifiyata ta qarasa maganar hawaye na cika mata ido yayi shiru na second biyu sannan ya cigaba da magana “tunda nemo mijin zakiyi to ki aureni ”
Mmn Sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
45
zaro idanuwa maryama tayi jin furucinsa”tunda nemo miji zaki yi to ki aureni”ta maimaitawa kanta furucinsa na qarshe mai cike da tsarkakki ya da shiga tashin hankali,kai tsaye mgnrsa ta ta’ba kwakwaluwarta sannan ta samu kyakkwan mazauni a zuciyarta ,sai dai maganar tayi mugun gigitata ahankali ta kai hannunta ta murza idanuwanta domin tabbatarwa kanta gskiya ne ko kuwa mafarki take,bata gasganta a zahiri taji ya fad’i kalmar ba sai data d’an ciza yatsanta taji wani irin rad’adi sannan ta tabbatarwa kanta da shi din ne yayi maganar“.a matukar gigice take kallonsa hannuwansa duka zagaye da kungunta ya mugun tsareta da tsumammun idanunshi tamkar bashi yayi furucin ba “.
“ban ta’ba expecting ko da wasa irin wannan mganar zata fito daga bakinka ba ,plese sir can you say what you said again Ina son na sake tabbatar da naji abinda ka fad’a da kyau kuskure ne, ko kuwa da gaske ka furta wanan kalmar agareni ”tayi maganar jikinta na sake d’aukar rawa tamkar mazari ahankali ya lumshe tsumamun idanunshi tare da motsa lip’s dinsa “nace muddin kinsan baki da wanda kike so wallahi ni a shirye nake zan aureki.”sake ware idanunwanta tayi tana mai fuskantarshi sosai tasan ba da wasa yayi maganar ba tunda gashi har ya rantse .”
”maryama !”
Ya kira sunanta wanda yasa tsigar jikinta suka mike yrrrrr “ki aureni .”ya sake share mata tantamar dake damunta, bata san lokacin da ta saki murmushin yake ba tare da girgiza masa kai.”jikinta na rawa ta fara qoqarin zare jikinta daga nashi ya sake riketa da kyau ta sake girgiza masa kai a sanyaye alamun ya sakar mata jiki “.
“ki natsu maryama ki bani amsa zaki aureni ?”
Wannan karon da sauri ta girgiza masa tana waigen bayanta.” Sosai tayi kasa da muryarta
“ dan Allah sir ka sakar min jiki kar ummah ta fito ta ganmu haka “kinsan Allah ki bud’e baki ki amsa min zaki aureni ko a’a if not anan zan kwana.” “what !”ta furta a rud’e hankalinta na sake tashi ya d’age girarsa d’aya alamun”eh!”tayi Imani zai iya aikata abinda ya fad’a din dan haka cike da karkarwa tace “Ka kwana anan akan me zaka kwana anan ?”dan Allah sir Ina rokanka tare da girmamawa ka tashi ka tafi gidanka gun matar ka,dan wallahi idan ka qara wasu mintuna anan zan iya had’iyar zuciya .”tayi maganar tana sake waiga bayanta .”
gyara zama yayi sosai kamar yana parlour’sa ko na mami tare da sake mata riko mai kyau wanda ko maza biyu sun qaru akanta bazata iya kwace wa a hannunsa ba “dan girman Allah sir ka tashi ka tafi gidanka ka rufa min asiri Ina ni ina aurenka zan dai samu takala daidaini na aura …”maryama ta fad’a cikin marai raicewar murya tamkar zata fashe masa da kuka .”ganin idan batayi wani abu ba umma zata iya fitowa ta gansu haka idan kuwa hakan ta faru ta shiga ukunta dan bata san da wani ido zata cigaba da kallon umma ba ,idan tace abinda ya faru a hoto kuskure ne wannan dake faruwa yanzu fa “?.
a wani matsaya za’a kirasa dashi ?”dan haka cike da tashin hankali ta fara masa alamun kuka domin tasan shine kawai mafutar da zata kubutar daita daga hannunsa .”
ahankali ta cigaba da rokonsa tare da mutsumutsun kwacewa daga jikinsa tana furta masa kalmar” ka rufa min asiri idan umma ta fito ban san da wani kalma zan kare kaina ba .”
ganin haka yasa ya zare hannunwansa ajikinta ta mike da sauri tana sauke numfashi tmkr wacce tayi gudun tsere .”ya gyara zamansa sosai tare da jingina jikinsa da kujerar da yake zaune yayinda tsamammun idanunshi wad’an da suka fara canza kala ne tsaye a kanta, ya mugun tsura mata ido sai dai fuskar nan tashi a had’e take kwata kwata babu wani alamun annuri “kina rikon na rufa miki asiri kmr wanda zai yi wani abu dake byn taimakonki zanyi .“cewa nayi kawai ki aureni ba cewa nayi zan kwanta a mararki ba .”yayi maganar tsumammun idanunshi kyar acikin kwayoyin idanuwanta ba kunya ba alkunya ko alamun yaji nauyin fitowar kalmar daga bakinsa bai yi ba .”
nan da nan maryama ta qara shiga tashin hankali sai dai ta had’e fuskarta dan kar ma ya sake samun damar sake furta mata wata maganar iskanci dan ta fahimci ba kunya garesa ba duk abinda yaga dama shi yake yi ,haka duk mgnr datai masa dadi yake fad’awa mutun “.ni zan wuce ki fara shirin zuwa aiki monday “da sauri tace “nifa na fad’a maka babu wani aiki da zan cigaba da zuwa na hakura da aiki nan zan cigaba da zama a gida har zuwa lokacin da Allah zai fito min da miji “ki bar wannan maganr dan bazaki samu wani miji kina kunshe a gida ba , ni kuma da nace zan taimaka miki kince baki sona dan haka ki shirye ki fara zuwa aiki dan zai fiye miki samun kwanciyar hankali …..”
“nifa babu wani aiki da ..”wani mugun kallo ya d’auketa dashi wanda yasa da sauri ta datse harshenta zuciyarta na wani irin bugawa da sauri sauri .”anatse ya yunkura ya mike tsaye bisa qafafunsa yayi taku biyu ya tsaya a gabanta yana tura hannunwansa duka cikin aljihunsa .”amatukar firgice take kallonsa yayinda qamshin turarensa ya dinga Kai wa hancinta ziyara yana kashe masa sansar jiki lumshe idanunta tayi kamar mai jin bacci dan gabadaya yau din sai take ganin ya sake sauya mata daga mr ata din datasani zuwa wani mutun dabam “yaushe muka fara haka dake ?”tayi shir tare da sunkuyar da kanta tana Jin wata irin fad’uwar gaba mai qarfi from no where na shigarta wanda bata ta’ba jin irinsa ba a tun tsawon rayuwarta.”
“wato dan taji zai taimaka mata ya aureta shine har ta fara rainashi kenan ?”sosai tayi kasa da kanta dan bazata iya kallon fuskarsa ba ,sai dai jikinta wani irin kyarma yake tmkr mazari sakamakon idanunshi dake yawo a sansar jikinta .” lumshe idanunshi yayi na second biyu sannan ya bud’e su fes akanta ,sosai yaji zafin abinda tayi masa bai san dalili ba yaji ya d’aura maganartata acikin zuciyarsa daram sai dai bazai yarda tayi tasiri ba “muryarsa a kasalance ta fito
“ ki san Allah muddin banganki AGC ranar monday ba kullum sai kin gani a gidan nan kuma abinda kike gudun faruwarsa ne zai dinga faruwa dan bazan d’aga miki kafa ba .”ya qarasa mgnr batare da yasan ya fad’a haka ba kawai dai ya tsinci bakinsa ne da maganar “.
lumshe idanunta tayi tana mai sake shiga tashin hankali mai tsanani ,muryata can kasan makoshi tace “ai sai ka zo ka sani dole sai naje .”ya sake matsota yana shafa gefen fuskarta tayi saurin matsawa baya da sauri ya cafko tsintsi yar hannunta cikin nashi yana murzawa,kwayoyin idanunshi cikin nata yace “mryama speek loud !“.Ina son naji abinda kika fad’a yanzu “yayi mgnr yana sake murza tsintsiyar hannunta sai dai wannan karon da zafi yayi mata ,da sauri ta shiga girgiza masa kai tana waigen waige gab d’aya a rude take “okay zabi ya rage naki kizo ko karki zo abinda na sani ne bana magana biyu, kuma bazan fara akanki ba ,zabi ya rage naki kizo ko karki zo .”yana gama fad’ar haka ya sakar mata hannu ya juya ya fara tafiya ”
Ahankali tabi bayanshi da kallo yana taku a natse har ya fice daga parlour’n, da sauri ta dawo jikin widow parlour’n ta d’aga labule kad’an tana lekensa yana taku a natse cike da izza tamkar baya son taka kasa “ya salam !”ta fad’a tana dafe qirjinta da taji yayi mugun rike mata “.
maryama ta kasa matsawa daga jikin window tana tariyo abinda ya faru a tsakaninsu yanzu,.”duk maganganunsa babu wanda ta manta domin kuwa sun zauna mata daram kamar hadda acikin kwakwaluwarta sannan sunyi mugun tasiri a kwakwaluwarta har suna son suyi tasiri a gangar jikinta da zuciyarta .”ya rab meke shirin faruwa dani ne?mai yasa mr ata zai ce na auresa ?”me yasa nake Jin kamar ana zarar raina a duk sanda yake tare dani ?”shiru tayi tana sake nazarin maganarsa dan ta kasa bawa kanta amsa “anya mr ata ba sonta yake ba kuwa ?” wannan shine tambayar farko da zuciyar maryama ta fara yiwa kwakwaluwarta “kuma tambayar ta daki brain dinta sannan ta wuce har cikin zuciyarta “yes yes !! kamar fa alamunsa ya nuna haka!” zuciyarta ta bata amsa da hakan ta sake dafe qirjinta sosai .”
Ahankali taji tamkar ta kunno wa kanta wani emotion ne da take qoqarin dannewa acikin zuciyarta nan take taji hawaye ya fara zubo mata kan kuncinta ahankali ta fara rera kuka kasa kasa “idan har ya tabbata mr ata sonta yake kuma har ya kasa fitowa ya furta mata kuma yake son ta auresa matuqar ta auresa ba qaramin azaba da matsin rayuwa zata shiga a hannunsa ba koma tace tabani ta lalace dan tun ba’aje koina ba ya fara da taimaka mata zai yi Ina ga ta auresa ?” uwa uba yanayin da take ji akanshi ya bam bamta da sauran mazan “no no !!.” I can’t marry him ya Allah ka ji tausayina ka bani miji daidai dani dan wannan mutumin yafi qrfina kuma koda zuciyata ta kamu da sonshi wallahi sai nasa wuka na raba tsakanimu .”
Ahankali taji an dafa kafad’anta ta baya ,ta jiyo da sauri ganin umma yasa ta sake dafe qirjinta gam tana goge hawayen dake shirin sake gangarowa bisa kuncinta “har mr ata din ya wuce ne ?”ta gyda mata kai da sauri tana cewa”eh ya wuce “ya naga kmr kuka kika yi?numfashi kawai ta sauke dan bazata iya mutsa mata ba tunda tasan kukan take ,umma ta sake tambayarta amman taki bata gamsashiyar amsa “.to akan zuwanki aiki ne kike kuka ko wata magana ya fad’a miki “? still dai girgiza mata kai tayi “to me yasa zaki tsaya kina kuka ?” umma babu komai !”ta fad’a tana shesheka.”numfashi umma ta sauke tare da cewa “ikon allah haka kawai mutun ya zauna yana kuka to Allah ya Kyauta to amman idan kinji har cikin zuciyarki baki son zuwa aikin nan ki hakura babu lallai babu dole dan babu wanda zai takura miki shi yasa ma kikaji nace ya tuntubeki .”tana gama fad’ar haka ta juya ta barta ta shige kitchen tana tunanin me ya sakata kuka ?”Umma ta jima tsaye a kitchen tana qoqarin had’a masu abincin dare koda ta fito bata ganta ba dan haka ta wuce d’akinta .”
Acikin mota mr ata ya iske mb ya shiga ya zauna suka kama hanyar komawa gida mb ya d’an kallesa yace aboki hankalinka ya kwanta zuciya taga abincin ruhinta ”ya qarasa mgnr yana kallon gabansa yana murmurshi “babu laifi hankalina ya d’an kwanta tunda har na d’aura kwayar idanuna akanta “ata kana son maryama..” sosai mb ina sonta ina mata son da idan babu it acikin rayuwata rayuwata zata kare ne cikin garari da tashin hankali amman na rasa dalilin da yasa na kasa fad’a mata kai tsaye kuma wallahi ina son na fito na fad’a mata amman sai naji zuciyata ta kasa “girman kai da rashin son arainaka ne ya hanaka fad’a mata amman dai ya kamata ka d’aure at least tasan irin mutu war son da kake mata tunda ga dama ta samu ance aure za’a mata”friend do something before everything could have mess up to you .”
in sha Allahu i wil try dan ko yanzu nayi mata mgnr ta aureni !”yayi maganar yana fesar da iska mai zafi daga bakinsa “kai Kai masha Allah mutumina ai an gama magana ,an gama wasan kawai game over sai mu fara shirin shan biki “tsaki ata yaja yana cewa “bata amince ba fa “yayi mgnr muryarsa a sanyaye kamar mai koyon magana” kamar ya bata amince ?” .
“am telling you!” yarinyar nan so take sai taga qarshena hankalinta zai kwanta mb ya saki dry mai qarfi yana cigaba da murza stearing “kar dai tayi wuji wuji da adamcy mami ?”ya qarasa maganar yana sake kwashewa da dariya numfashi kawai mr ata ya sauke tare da kamo lip’s dinsa na kasa yana cizawa a hankali “ka bita a hankali da sannu zata amince kasan ganin abun zatayi wani iri kmr shirin drama ne ace mutun kamarka zaka aureta batare da kuna soyayya ba ”yanzu dai mu ajiye wannna maganar in sha allahu komai zai zo da sauki maryama rabonmu ce da izinin Allah.”Allah yasa”ya amsa masa jiki a sanyaye .”
“ya kukayi daita batun cigaba da zuwanta aiki “ta amince ko kuwa “uhm ai yarinyar nan akwai d’agawa mutun hankali shiyasa wallahi nake jin bazan iya tunkararta da batu na soyayya ba gara kawai na aureta a aikace zata gane son da nake mata”Kai dan Allah kana ganin yarinya kmr mummuna inji cewar m.b “ya fad’a yana masa dariyar mugunta “Ai kana ganinta wallahi muguwar yar rigima ce ta bugawa a jarida.”
“ ai na lura da yadda take girgi zawa iyayenta kai alamun karsu amince” aikuwa zata janyowa kanta sabon tashin hankali domin kuwa bazan barta ba na dinga zuwa kenan Ina d’aga mata hankali har su fahimceni a qarshe su aura min ita kaga shikenan na huta .”mb yasa dariya yana sake dukan stearing motar “wallahi tunda nake ban ta’ba maganin mutun da girman kai da miskilanci mai cutar da kanshi ba kamar kai wai ka fito ka fad’a wa yarinya kana sonta ne abun kunya ko me ?ata ya girgiza masa kai “mb me yasa ka kasa fahimtata ne “ .?
“babu wani na kasa fahimtar ka,kawai kace tsoron yarinyar nan kake ji,kai yanzu a tunanin ka akwai halittar da zanji tsoro? ” gata kuwa na gani tsoron maryama kake ji “mb ba tsoro bane akwai dalilai sannan kuma wannnan yarinyar da kake kallo rikitacciyar yarinya ce shiyasa ma ta kasa fahimtata inda na dosa ko da yake har da kuruciya ke damunta ko nace irin matan nan ne da sai an fito an fad’a masu ana son su suke fahimta if not ko acikin kalamaina ya dace ta fahimceni .”
“Taya kake son ta fahimceka?”kai ma fa da naka kana da son takurawa rai dayawa tsoro ma zai sa ta kasa gane inda ka dosa da wannan tautauna war suka isa abdullahi estate mb ya sauke ata ya wuce gida.”koda ya shigo parlour’n mami babu kowa dan haka ya haye samansa ya kirata ya sheida mata dawowarsa .
bayan sallar Ishai bayan yayi wanka ya sanya Jallabiya brown colour mai gajeren hannu mami ta nufi samansa tare da d’aya daga cikin masu aikinta dake rike da trayn wanda ke d’auke da kayan marmari da hadin salad da qaramin flaks na ruwan zafi abayanta ta same mr ata zaune a parlour’n sa akan kujera hannunsa rike da remut yayi shiru yana kallon tv sai dai hankalinsa baya kan news din daake gabatarwa .har mami ta shigo bai san ta shigo ba mami ta umarci mai aikinta data ajiye trayn ta wuce cike da girmama wa mai aiki taja dan qara min table din glass din dake tsakitar parlour’n ta daura masa akai ta Kama gabanta inda mami ta qaraso inda yake ta girgiza shi sannan ya dawo haiyacinsa .”
Muryarta a sanyaye tace “adamcy me kake tunani haka ?”ya soma in ina yana cewa” babu komai ta zauna kusa dashi tana cewa “kace babu komai ?”ya d’age mata girarsa d’aya yana shafa sumar kanshi “ka fita cikin tsananin farinciki amman kalli yadda ka dawo kamar wani mara lafiya tayi mgnr tana kamo hannunsa cikin nashi inda nan take idanuwanshi suka sauka akan yatsun hannunta masu tsananin Kama dana mahaifiyar mryama “ya ka baro maryama fatan tana lafiya?”tana lafiya!”ya fad’a atakaice tayi shiru tana nazarinsa har tsawon minti biyar ta sake cewa “halan da kaje gidansu maryama wani abu tayi maka ?”ya girgiza mata Kai da sauri sannan ahankali yayi qasa da idanunshi ya zubawa yatsunta na qafa ido ya jima yana kallon yatsun kafafun mami da kuma hannunta yana son yayi mata magana amman yana tunanin yadda zata fahimcesa .”
yana kallonta ta mike ta soma zuba masa abinci tana magana cikin sanyayye yar murya “adamcy banason kana boye min matsalarka dan baka da wacce tafini kuma na jaka ajikina ne don duk lokacin da zaka shiga damuwa ka sanar min kasacewar nasan baka da wani danuwa namiji da zai maye maka gurbin danuwa da kuma mahaifi” ta qarasa mgnr tana tura masa plet din hadin salad gabansa “wai ma me ya kaika gidansu maryama ne kaje ka sanar mata kana sonta ne ko ya !”tmabayar tazo masa wani iri wai me yasa mahaifiyarsa tasan zahirinsa da badinsa?”mami tasan mamakin maganrta yake tace “nasan zakayi mamaki Jin abinda nace amman karka manta nice na kawowa duniya ,yaakayi maryama taki amincewa ko“?yayi shiru kawai yana kallonta yana jin faduwar gaba mai tsanani aranshi “.
“ka fad’a min idan bata amince bane sai na baka shawar yadda zakayi ka shawo kanta cikin sauki ko kuma mu dini zuga muyi gidansu qawwnya tayi maganar cikin tsigar zolaya “bai san sanda murmushin dole ya bayyana Akan fuskashi ba yana cewa “kai sweetheart wallahi kin bari nayi dariyar da ban shirya ba” gyaran murya yayi yace “ba wannan bane wani abu ne ya tsaya min arai har yasa kika ga yanayina haka tace ”meye shi !”?ta tambayesa adaidai lokacin daya fara ci salad tun kafin lokaci ya kure masa sai dai idanunshi na kanta yace “sweetheart yau naga mai irin yatsun qafafunki a gidansu maryama koma nace miki mahaifiyar maryama wallahi yatsunta na hannu dana qafa exactly irin naki ..”
mami tayi shiru tana dubansa cike da mamaki sannan tana duban yatsun hannunta yayinda mr ata ya cigaba da cin hadin salad dinsa dake gabansa “kuma kinsan wani abun sweet Herat “?ta girgiza masa Kai “sai kinganta wallahi sai kinyi mamaki yadda yanayinta yake Kama da aunty nu..”tun kafin ya qarasa kiran sunan ringin din wayarsa ya katse masa maganarsa ya d’auki wayar yana duba wanda ya kirasa ,ganin abokin halkal kasuwancinsa ne yasa ya nemi izini daga wajen mami kanta ta gyad’a masa alamun ya d’aga .”
Ahankali ya soma magana yana cigaba da cin salad ganin wayar tashi mai tsawo ce yasa mami ta yunkura ta mike ta bar parlour’n .”Mr ata ya jima yana tautaunawa da mutumin har kusan sha d’aya da wani Abu sannan sukai sallama ya tashi da kyar ya shiga bedroom dinsa kai tsaye bothroom ya shiga yayi pest yayi alwala ya fito ya zare Jallabiyar jikinsa ya saura daga shi sai gajeren wondo iya cinya ya qara qarfin ac d’akin yayi addua ya kwanta akan katifa yana lullube rabin jikinsa tare da kallon saman d’akin idanunshi ya saisaita kana ya lumshesu ya fara tunanin ko maryama zata bi umarninsa ko kuwa zata masa taurin kan kin zuwa .”
a daddafe yayi weekend dinsa Allah Allah yake Monday tayi .”Ranar monday da wuri ya shirya ya bar gidan dan ko breakfast bai tsaya yayi ba cikin shigar manya kaya yadi ne blue black mai shegen tsaida ,wanda akayiwa dinkin zamani sai dai gaban aljihunsa anyi masa desing da logon din ATA company ,goma daidai a AGC tayi masa sakamakon abu biyu ,abu na farko maryamarsa abu na biyu kuma hira da yan jarida suke so suyi dashi.”
ahankali manya ma’akatansa suka dinga shige da fice a office dinsa wasu magana ce mai mahimmanci wasu kuma saka hannunsa suke bukata har zuwa lokacin da 12:00 dot ta buga yan jarida suka qaraso suka yi abinda ya kawosu suka wuce amman babu alamun maryama tazo aiki ya Kira some bayan ta shigo yace “maryama fa !”?
”maryama kuma sir?ya kalleta a d’age yana karta saman table din gabansa “irin kallon da taga yana mata ne yasa da sauri tace “ai ta kwana biyu rabonta da zuwa aiki kamar yadda kasani .”
shiru yayi kawai yana sauke numfashi tare da hura hanci cike da ‘bacin rai ya kai hannunsa saman goshinsa yana murzawa ahankali ahankali yana tunanin abinda ya kamata yayi mata a qarshe dai wayarsa ya d’auka ya soma qoqarin neman layinta inda madam some ta juya ta koma bakin aikinta kira biyu yayi mata sannan ta d’aga tare da yin sallama “bai tsaya amsa sallamar datai masa ba yace “maryama kina wasa dani ko ?”tai saurin girgiza masa kai alamun a’a tamkar tana gabansa “Ina ganin baki san waye adam ba shi yasa har kike taka masa doka “shiru tayi tana sauke masa hucin numfashin Wanda dole tasa ya d’an lumshe idanunshi yana cewa “na fuskanci maryam kina son ganin iyakar taurin kaina ko“?”kayi hakuri amman ai na fad’a maka bazan ci..”oh my god wai me na fad’a miki ?”banace lallai kizo yau ba “kayi hakuri sir ni aikin ne gbdy ya fice min arai kar na dawo ayita samun matsala dani “da sauri ya mike tsaye tare da dunkule hannunsa ya naushi iska sannan ya dinga Kai kawo a filin office din inda idanun madam some da hankalinta yake kanshi sosai taga ya shiga damuwa maryama kuwa tana can rike da waya tana zance zuci “dokar daya kamata yayi akan matarsa ko damuwar daya kamata yayi akan matarsa ya tsaya yana yin abinda bai shafesa ba on expecting taji saukar muryarsa “karki ga na damu akanki ki d’auka wani dalili ne amman kisani zuwanki aiki gobe shine kwanciyar hankalinki wallahi muddin kuma kika yarda na tako gidanku zan miki abinda zai miki illa.”
Mmn sudais[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
45
zaro idanuwa maryama tayi jin furucinsa”tunda nemo miji zaki yi to ki aureni”ta maimaitawa kanta furucinsa na qarshe mai cike da tsarkakki ya da shiga tashin hankali,kai tsaye mgnrsa ta ta’ba kwakwaluwarta sannan ta samu kyakkwan mazauni a zuciyarta ,sai dai maganar tayi mugun gigitata ahankali ta kai hannunta ta murza idanuwanta domin tabbatarwa kanta gskiya ne ko kuwa mafarki take,bata gasganta a zahiri taji ya fad’i kalmar ba sai data d’an ciza yatsanta taji wani irin rad’adi sannan ta tabbatarwa kanta da shi din ne yayi maganar“.a matukar gigice take kallonsa hannuwansa duka zagaye da kungunta ya mugun tsareta da tsumammun idanunshi tamkar bashi yayi furucin ba “.
“ban ta’ba expecting ko da wasa irin wannan mganar zata fito daga bakinka ba ,plese sir can you say what you said again Ina son na sake tabbatar da naji abinda ka fad’a da kyau kuskure ne, ko kuwa da gaske ka furta wanan kalmar agareni ”tayi maganar jikinta na sake d’aukar rawa tamkar mazari ahankali ya lumshe tsumamun idanunshi tare da motsa lip’s dinsa “nace muddin kinsan baki da wanda kike so wallahi ni a shirye nake zan aureki.”sake ware idanunwanta tayi tana mai fuskantarshi sosai tasan ba da wasa yayi maganar ba tunda gashi har ya rantse .”
”maryama !”
Ya kira sunanta wanda yasa tsigar jikinta suka mike yrrrrr “ki aureni .”ya sake share mata tantamar dake damunta, bata san lokacin da ta saki murmushin yake ba tare da girgiza masa kai.”jikinta na rawa ta fara qoqarin zare jikinta daga nashi ya sake riketa da kyau ta sake girgiza masa kai a sanyaye alamun ya sakar mata jiki “.
“ki natsu maryama ki bani amsa zaki aureni ?”
Wannan karon da sauri ta girgiza masa tana waigen bayanta.” Sosai tayi kasa da muryarta
“ dan Allah sir ka sakar min jiki kar ummah ta fito ta ganmu haka “kinsan Allah ki bud’e baki ki amsa min zaki aureni ko a’a if not anan zan kwana.” “what !”ta furta a rud’e hankalinta na sake tashi ya d’age girarsa d’aya alamun”eh!”tayi Imani zai iya aikata abinda ya fad’a din dan haka cike da karkarwa tace “Ka kwana anan akan me zaka kwana anan ?”dan Allah sir Ina rokanka tare da girmamawa ka tashi ka tafi gidanka gun matar ka,dan wallahi idan ka qara wasu mintuna anan zan iya had’iyar zuciya .”tayi maganar tana sake waiga bayanta .”
gyara zama yayi sosai kamar yana parlour’sa ko na mami tare da sake mata riko mai kyau wanda ko maza biyu sun qaru akanta bazata iya kwace wa a hannunsa ba “dan girman Allah sir ka tashi ka tafi gidanka ka rufa min asiri Ina ni ina aurenka zan dai samu takala daidaini na aura …”maryama ta fad’a cikin marai raicewar murya tamkar zata fashe masa da kuka .”ganin idan batayi wani abu ba umma zata iya fitowa ta gansu haka idan kuwa hakan ta faru ta shiga ukunta dan bata san da wani ido zata cigaba da kallon umma ba ,idan tace abinda ya faru a hoto kuskure ne wannan dake faruwa yanzu fa “?.
a wani matsaya za’a kirasa dashi ?”dan haka cike da tashin hankali ta fara masa alamun kuka domin tasan shine kawai mafutar da zata kubutar daita daga hannunsa .”
ahankali ta cigaba da rokonsa tare da mutsumutsun kwacewa daga jikinsa tana furta masa kalmar” ka rufa min asiri idan umma ta fito ban san da wani kalma zan kare kaina ba .”
ganin haka yasa ya zare hannunwansa ajikinta ta mike da sauri tana sauke numfashi tmkr wacce tayi gudun tsere .”ya gyara zamansa sosai tare da jingina jikinsa da kujerar da yake zaune yayinda tsamammun idanunshi wad’an da suka fara canza kala ne tsaye a kanta, ya mugun tsura mata ido sai dai fuskar nan tashi a had’e take kwata kwata babu wani alamun annuri “kina rikon na rufa miki asiri kmr wanda zai yi wani abu dake byn taimakonki zanyi .“cewa nayi kawai ki aureni ba cewa nayi zan kwanta a mararki ba .”yayi maganar tsumammun idanunshi kyar acikin kwayoyin idanuwanta ba kunya ba alkunya ko alamun yaji nauyin fitowar kalmar daga bakinsa bai yi ba .”
nan da nan maryama ta qara shiga tashin hankali sai dai ta had’e fuskarta dan kar ma ya sake samun damar sake furta mata wata maganar iskanci dan ta fahimci ba kunya garesa ba duk abinda yaga dama shi yake yi ,haka duk mgnr datai masa dadi yake fad’awa mutun “.ni zan wuce ki fara shirin zuwa aiki monday “da sauri tace “nifa na fad’a maka babu wani aiki da zan cigaba da zuwa na hakura da aiki nan zan cigaba da zama a gida har zuwa lokacin da Allah zai fito min da miji “ki bar wannan maganr dan bazaki samu wani miji kina kunshe a gida ba , ni kuma da nace zan taimaka miki kince baki sona dan haka ki shirye ki fara zuwa aiki dan zai fiye miki samun kwanciyar hankali …..”
“nifa babu wani aiki da ..”wani mugun kallo ya d’auketa dashi wanda yasa da sauri ta datse harshenta zuciyarta na wani irin bugawa da sauri sauri .”anatse ya yunkura ya mike tsaye bisa qafafunsa yayi taku biyu ya tsaya a gabanta yana tura hannunwansa duka cikin aljihunsa .”amatukar firgice take kallonsa yayinda qamshin turarensa ya dinga Kai wa hancinta ziyara yana kashe masa sansar jiki lumshe idanunta tayi kamar mai jin bacci dan gabadaya yau din sai take ganin ya sake sauya mata daga mr ata din datasani zuwa wani mutun dabam “yaushe muka fara haka dake ?”tayi shir tare da sunkuyar da kanta tana Jin wata irin fad’uwar gaba mai qarfi from no where na shigarta wanda bata ta’ba jin irinsa ba a tun tsawon rayuwarta.”
“wato dan taji zai taimaka mata ya aureta shine har ta fara rainashi kenan ?”sosai tayi kasa da kanta dan bazata iya kallon fuskarsa ba ,sai dai jikinta wani irin kyarma yake tmkr mazari sakamakon idanunshi dake yawo a sansar jikinta .” lumshe idanunshi yayi na second biyu sannan ya bud’e su fes akanta ,sosai yaji zafin abinda tayi masa bai san dalili ba yaji ya d’aura maganartata acikin zuciyarsa daram sai dai bazai yarda tayi tasiri ba “muryarsa a kasalance ta fito
“ ki san Allah muddin banganki AGC ranar monday ba kullum sai kin gani a gidan nan kuma abinda kike gudun faruwarsa ne zai dinga faruwa dan bazan d’aga miki kafa ba .”ya qarasa mgnr batare da yasan ya fad’a haka ba kawai dai ya tsinci bakinsa ne da maganar “.
lumshe idanunta tayi tana mai sake shiga tashin hankali mai tsanani ,muryata can kasan makoshi tace “ai sai ka zo ka sani dole sai naje .”ya sake matsota yana shafa gefen fuskarta tayi saurin matsawa baya da sauri ya cafko tsintsi yar hannunta cikin nashi yana murzawa,kwayoyin idanunshi cikin nata yace “mryama speek loud !“.Ina son naji abinda kika fad’a yanzu “yayi mgnr yana sake murza tsintsiyar hannunta sai dai wannan karon da zafi yayi mata ,da sauri ta shiga girgiza masa kai tana waigen waige gab d’aya a rude take “okay zabi ya rage naki kizo ko karki zo abinda na sani ne bana magana biyu, kuma bazan fara akanki ba ,zabi ya rage naki kizo ko karki zo .”yana gama fad’ar haka ya sakar mata hannu ya juya ya fara tafiya ”
Ahankali tabi bayanshi da kallo yana taku a natse har ya fice daga parlour’n, da sauri ta dawo jikin widow parlour’n ta d’aga labule kad’an tana lekensa yana taku a natse cike da izza tamkar baya son taka kasa “ya salam !”ta fad’a tana dafe qirjinta da taji yayi mugun rike mata “.
maryama ta kasa matsawa daga jikin window tana tariyo abinda ya faru a tsakaninsu yanzu,.”duk maganganunsa babu wanda ta manta domin kuwa sun zauna mata daram kamar hadda acikin kwakwaluwarta sannan sunyi mugun tasiri a kwakwaluwarta har suna son suyi tasiri a gangar jikinta da zuciyarta .”ya rab meke shirin faruwa dani ne?mai yasa mr ata zai ce na auresa ?”me yasa nake Jin kamar ana zarar raina a duk sanda yake tare dani ?”shiru tayi tana sake nazarin maganarsa dan ta kasa bawa kanta amsa “anya mr ata ba sonta yake ba kuwa ?” wannan shine tambayar farko da zuciyar maryama ta fara yiwa kwakwaluwarta “kuma tambayar ta daki brain dinta sannan ta wuce har cikin zuciyarta “yes yes !! kamar fa alamunsa ya nuna haka!” zuciyarta ta bata amsa da hakan ta sake dafe qirjinta sosai .”
Ahankali taji tamkar ta kunno wa kanta wani emotion ne da take qoqarin dannewa acikin zuciyarta nan take taji hawaye ya fara zubo mata kan kuncinta ahankali ta fara rera kuka kasa kasa “idan har ya tabbata mr ata sonta yake kuma har ya kasa fitowa ya furta mata kuma yake son ta auresa matuqar ta auresa ba qaramin azaba da matsin rayuwa zata shiga a hannunsa ba koma tace tabani ta lalace dan tun ba’aje koina ba ya fara da taimaka mata zai yi Ina ga ta auresa ?” uwa uba yanayin da take ji akanshi ya bam bamta da sauran mazan “no no !!.” I can’t marry him ya Allah ka ji tausayina ka bani miji daidai dani dan wannan mutumin yafi qrfina kuma koda zuciyata ta kamu da sonshi wallahi sai nasa wuka na raba tsakanimu .”
Ahankali taji an dafa kafad’anta ta baya ,ta jiyo da sauri ganin umma yasa ta sake dafe qirjinta gam tana goge hawayen dake shirin sake gangarowa bisa kuncinta “har mr ata din ya wuce ne ?”ta gyda mata kai da sauri tana cewa”eh ya wuce “ya naga kmr kuka kika yi?numfashi kawai ta sauke dan bazata iya mutsa mata ba tunda tasan kukan take ,umma ta sake tambayarta amman taki bata gamsashiyar amsa “.to akan zuwanki aiki ne kike kuka ko wata magana ya fad’a miki “? still dai girgiza mata kai tayi “to me yasa zaki tsaya kina kuka ?” umma babu komai !”ta fad’a tana shesheka.”numfashi umma ta sauke tare da cewa “ikon allah haka kawai mutun ya zauna yana kuka to Allah ya Kyauta to amman idan kinji har cikin zuciyarki baki son zuwa aikin nan ki hakura babu lallai babu dole dan babu wanda zai takura miki shi yasa ma kikaji nace ya tuntubeki .”tana gama fad’ar haka ta juya ta barta ta shige kitchen tana tunanin me ya sakata kuka ?”Umma ta jima tsaye a kitchen tana qoqarin had’a masu abincin dare koda ta fito bata ganta ba dan haka ta wuce d’akinta .”
Acikin mota mr ata ya iske mb ya shiga ya zauna suka kama hanyar komawa gida mb ya d’an kallesa yace aboki hankalinka ya kwanta zuciya taga abincin ruhinta ”ya qarasa mgnr yana kallon gabansa yana murmurshi “babu laifi hankalina ya d’an kwanta tunda har na d’aura kwayar idanuna akanta “ata kana son maryama..” sosai mb ina sonta ina mata son da idan babu it acikin rayuwata rayuwata zata kare ne cikin garari da tashin hankali amman na rasa dalilin da yasa na kasa fad’a mata kai tsaye kuma wallahi ina son na fito na fad’a mata amman sai naji zuciyata ta kasa “girman kai da rashin son arainaka ne ya hanaka fad’a mata amman dai ya kamata ka d’aure at least tasan irin mutu war son da kake mata tunda ga dama ta samu ance aure za’a mata”friend do something before everything could have mess up to you .”
in sha Allahu i wil try dan ko yanzu nayi mata mgnr ta aureni !”yayi maganar yana fesar da iska mai zafi daga bakinsa “kai Kai masha Allah mutumina ai an gama magana ,an gama wasan kawai game over sai mu fara shirin shan biki “tsaki ata yaja yana cewa “bata amince ba fa “yayi mgnr muryarsa a sanyaye kamar mai koyon magana” kamar ya bata amince ?” .
“am telling you!” yarinyar nan so take sai taga qarshena hankalinta zai kwanta mb ya saki dry mai qarfi yana cigaba da murza stearing “kar dai tayi wuji wuji da adamcy mami ?”ya qarasa maganar yana sake kwashewa da dariya numfashi kawai mr ata ya sauke tare da kamo lip’s dinsa na kasa yana cizawa a hankali “ka bita a hankali da sannu zata amince kasan ganin abun zatayi wani iri kmr shirin drama ne ace mutun kamarka zaka aureta batare da kuna soyayya ba ”yanzu dai mu ajiye wannna maganar in sha allahu komai zai zo da sauki maryama rabonmu ce da izinin Allah.”Allah yasa”ya amsa masa jiki a sanyaye .”
“ya kukayi daita batun cigaba da zuwanta aiki “ta amince ko kuwa “uhm ai yarinyar nan akwai d’agawa mutun hankali shiyasa wallahi nake jin bazan iya tunkararta da batu na soyayya ba gara kawai na aureta a aikace zata gane son da nake mata”Kai dan Allah kana ganin yarinya kmr mummuna inji cewar m.b “ya fad’a yana masa dariyar mugunta “Ai kana ganinta wallahi muguwar yar rigima ce ta bugawa a jarida.”
“ ai na lura da yadda take girgi zawa iyayenta kai alamun karsu amince” aikuwa zata janyowa kanta sabon tashin hankali domin kuwa bazan barta ba na dinga zuwa kenan Ina d’aga mata hankali har su fahimceni a qarshe su aura min ita kaga shikenan na huta .”mb yasa dariya yana sake dukan stearing motar “wallahi tunda nake ban ta’ba maganin mutun da girman kai da miskilanci mai cutar da kanshi ba kamar kai wai ka fito ka fad’a wa yarinya kana sonta ne abun kunya ko me ?ata ya girgiza masa kai “mb me yasa ka kasa fahimtata ne “ .?
“babu wani na kasa fahimtar ka,kawai kace tsoron yarinyar nan kake ji,kai yanzu a tunanin ka akwai halittar da zanji tsoro? ” gata kuwa na gani tsoron maryama kake ji “mb ba tsoro bane akwai dalilai sannan kuma wannnan yarinyar da kake kallo rikitacciyar yarinya ce shiyasa ma ta kasa fahimtata inda na dosa ko da yake har da kuruciya ke damunta ko nace irin matan nan ne da sai an fito an fad’a masu ana son su suke fahimta if not ko acikin kalamaina ya dace ta fahimceni .”
“Taya kake son ta fahimceka?”kai ma fa da naka kana da son takurawa rai dayawa tsoro ma zai sa ta kasa gane inda ka dosa da wannan tautauna war suka isa abdullahi estate mb ya sauke ata ya wuce gida.”koda ya shigo parlour’n mami babu kowa dan haka ya haye samansa ya kirata ya sheida mata dawowarsa .
bayan sallar Ishai bayan yayi wanka ya sanya Jallabiya brown colour mai gajeren hannu mami ta nufi samansa tare da d’aya daga cikin masu aikinta dake rike da trayn wanda ke d’auke da kayan marmari da hadin salad da qaramin flaks na ruwan zafi abayanta ta same mr ata zaune a parlour’n sa akan kujera hannunsa rike da remut yayi shiru yana kallon tv sai dai hankalinsa baya kan news din daake gabatarwa .har mami ta shigo bai san ta shigo ba mami ta umarci mai aikinta data ajiye trayn ta wuce cike da girmama wa mai aiki taja dan qara min table din glass din dake tsakitar parlour’n ta daura masa akai ta Kama gabanta inda mami ta qaraso inda yake ta girgiza shi sannan ya dawo haiyacinsa .”
Muryarta a sanyaye tace “adamcy me kake tunani haka ?”ya soma in ina yana cewa” babu komai ta zauna kusa dashi tana cewa “kace babu komai ?”ya d’age mata girarsa d’aya yana shafa sumar kanshi “ka fita cikin tsananin farinciki amman kalli yadda ka dawo kamar wani mara lafiya tayi mgnr tana kamo hannunsa cikin nashi inda nan take idanuwanshi suka sauka akan yatsun hannunta masu tsananin Kama dana mahaifiyar mryama “ya ka baro maryama fatan tana lafiya?”tana lafiya!”ya fad’a atakaice tayi shiru tana nazarinsa har tsawon minti biyar ta sake cewa “halan da kaje gidansu maryama wani abu tayi maka ?”ya girgiza mata Kai da sauri sannan ahankali yayi qasa da idanunshi ya zubawa yatsunta na qafa ido ya jima yana kallon yatsun kafafun mami da kuma hannunta yana son yayi mata magana amman yana tunanin yadda zata fahimcesa .”
yana kallonta ta mike ta soma zuba masa abinci tana magana cikin sanyayye yar murya “adamcy banason kana boye min matsalarka dan baka da wacce tafini kuma na jaka ajikina ne don duk lokacin da zaka shiga damuwa ka sanar min kasacewar nasan baka da wani danuwa namiji da zai maye maka gurbin danuwa da kuma mahaifi” ta qarasa mgnr tana tura masa plet din hadin salad gabansa “wai ma me ya kaika gidansu maryama ne kaje ka sanar mata kana sonta ne ko ya !”tmabayar tazo masa wani iri wai me yasa mahaifiyarsa tasan zahirinsa da badinsa?”mami tasan mamakin maganrta yake tace “nasan zakayi mamaki Jin abinda nace amman karka manta nice na kawowa duniya ,yaakayi maryama taki amincewa ko“?yayi shiru kawai yana kallonta yana jin faduwar gaba mai tsanani aranshi “.
“ka fad’a min idan bata amince bane sai na baka shawar yadda zakayi ka shawo kanta cikin sauki ko kuma mu dini zuga muyi gidansu qawwnya tayi maganar cikin tsigar zolaya “bai san sanda murmushin dole ya bayyana Akan fuskashi ba yana cewa “kai sweetheart wallahi kin bari nayi dariyar da ban shirya ba” gyaran murya yayi yace “ba wannan bane wani abu ne ya tsaya min arai har yasa kika ga yanayina haka tace ”meye shi !”?ta tambayesa adaidai lokacin daya fara ci salad tun kafin lokaci ya kure masa sai dai idanunshi na kanta yace “sweetheart yau naga mai irin yatsun qafafunki a gidansu maryama koma nace miki mahaifiyar maryama wallahi yatsunta na hannu dana qafa exactly irin naki ..”
mami tayi shiru tana dubansa cike da mamaki sannan tana duban yatsun hannunta yayinda mr ata ya cigaba da cin hadin salad dinsa dake gabansa “kuma kinsan wani abun sweet Herat “?ta girgiza masa Kai “sai kinganta wallahi sai kinyi mamaki yadda yanayinta yake Kama da aunty nu..”tun kafin ya qarasa kiran sunan ringin din wayarsa ya katse masa maganarsa ya d’auki wayar yana duba wanda ya kirasa ,ganin abokin halkal kasuwancinsa ne yasa ya nemi izini daga wajen mami kanta ta gyad’a masa alamun ya d’aga .”
Ahankali ya soma magana yana cigaba da cin salad ganin wayar tashi mai tsawo ce yasa mami ta yunkura ta mike ta bar parlour’n .”Mr ata ya jima yana tautaunawa da mutumin har kusan sha d’aya da wani Abu sannan sukai sallama ya tashi da kyar ya shiga bedroom dinsa kai tsaye bothroom ya shiga yayi pest yayi alwala ya fito ya zare Jallabiyar jikinsa ya saura daga shi sai gajeren wondo iya cinya ya qara qarfin ac d’akin yayi addua ya kwanta akan katifa yana lullube rabin jikinsa tare da kallon saman d’akin idanunshi ya saisaita kana ya lumshesu ya fara tunanin ko maryama zata bi umarninsa ko kuwa zata masa taurin kan kin zuwa .”
a daddafe yayi weekend dinsa Allah Allah yake Monday tayi .”Ranar monday da wuri ya shirya ya bar gidan dan ko breakfast bai tsaya yayi ba cikin shigar manya kaya yadi ne blue black mai shegen tsaida ,wanda akayiwa dinkin zamani sai dai gaban aljihunsa anyi masa desing da logon din ATA company ,goma daidai a AGC tayi masa sakamakon abu biyu ,abu na farko maryamarsa abu na biyu kuma hira da yan jarida suke so suyi dashi.”
ahankali manya ma’akatansa suka dinga shige da fice a office dinsa wasu magana ce mai mahimmanci wasu kuma saka hannunsa suke bukata har zuwa lokacin da 12:00 dot ta buga yan jarida suka qaraso suka yi abinda ya kawosu suka wuce amman babu alamun maryama tazo aiki ya Kira some bayan ta shigo yace “maryama fa !”?
”maryama kuma sir?ya kalleta a d’age yana karta saman table din gabansa “irin kallon da taga yana mata ne yasa da sauri tace “ai ta kwana biyu rabonta da zuwa aiki kamar yadda kasani .”
shiru yayi kawai yana sauke numfashi tare da hura hanci cike da ‘bacin rai ya kai hannunsa saman goshinsa yana murzawa ahankali ahankali yana tunanin abinda ya kamata yayi mata a qarshe dai wayarsa ya d’auka ya soma qoqarin neman layinta inda madam some ta juya ta koma bakin aikinta kira biyu yayi mata sannan ta d’aga tare da yin sallama “bai tsaya amsa sallamar datai masa ba yace “maryama kina wasa dani ko ?”tai saurin girgiza masa kai alamun a’a tamkar tana gabansa “Ina ganin baki san waye adam ba shi yasa har kike taka masa doka “shiru tayi tana sauke masa hucin numfashin Wanda dole tasa ya d’an lumshe idanunshi yana cewa “na fuskanci maryam kina son ganin iyakar taurin kaina ko“?”kayi hakuri amman ai na fad’a maka bazan ci..”oh my god wai me na fad’a miki ?”banace lallai kizo yau ba “kayi hakuri sir ni aikin ne gbdy ya fice min arai kar na dawo ayita samun matsala dani “da sauri ya mike tsaye tare da dunkule hannunsa ya naushi iska sannan ya dinga Kai kawo a filin office din inda idanun madam some da hankalinta yake kanshi sosai taga ya shiga damuwa maryama kuwa tana can rike da waya tana zance zuci “dokar daya kamata yayi akan matarsa ko damuwar daya kamata yayi akan matarsa ya tsaya yana yin abinda bai shafesa ba on expecting taji saukar muryarsa “karki ga na damu akanki ki d’auka wani dalili ne amman kisani zuwanki aiki gobe shine kwanciyar hankalinki wallahi muddin kuma kika yarda na tako gidanku zan miki abinda zai miki illa.”
Mmn sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
47
“karki ga na damu akanki ki d'auka wani dalili ne amman kisani zuwanki aiki gobe shine kwanciyar hankalinki wallahi muddin kuma kika yarda na tako gidanku zan miki abinda zai miki illa."ta maimaitawa kanta furucinsa tana jin wani irin mummunar fad’uwar gaba from know where dan zuwa yanzu tasan halin mr ata kamar yunwar cikinta bashi da kyau ta kowane fanni kuma duk abinda yace zai aikata zai aikata shi babu wanda ya isa yasashi kuma babu wanda ya isa ya hanashi ,zai iya aikata fiyye da abinda yace zai mata“.to ma akan me ye zai nemi ya dinga takurawa rayuwarta alhalin ita din ba matarsa bace ba kuma kowa nasa bace ?”.ahankali ta sauke naunauyen ajiyar zuciya batare data sake cewa komai ba.”
“maryama….”!
ya kira sunanta cikin wata irin kasalalliyar muryarsa mai tsananin kashe sansar jiki da tsuma zuciya wanda yasa taji gabad’aya komai ya tsaya mata cak, yayinda ahankali ahankali tsigar jikinta suka dinga mikewa sai dai daga sunanta daya kira bai qara cewa komai ba yayi shiru ya koma ya zagaye table dinsa ya tsaya ya d’aura hannunsa d’aya,jikinsa yayi mugu mugun sanyi dan ya fara Jin alamun bazata zo ba dan haka ya wani dawo kamar wani abun tausayi muryarta a sanyaye tace “sir ka kira sunana kuma kayi shiru ?”tsaki yaja yana fesar da iska mai zafi daga bakinsa .”“please sir kayi hakuri “zaki zo goben ko zaki tsaya yi min taurin kai?”wani irin mugun tsoronsa ne taji ya shigeta wanda yasa tai saurin cewa”shikenan naji zanzo!”yana gama jin abinda ta fad’a ya katse kiran tare da lumshe tsumammun idanunshi yana jin wani irin farinciki na shigarsa with an unreadable expression akan fuskarsa.”
maryama kam numfashi ta sauke da ajiyar zuciya atare tana sake mamakin qarfin halinsa,mutun kamar wani aljani gabad’aya yana son ya canza mata tsarin rayuwarta da tunaninta koma tace ya canzata completely dan a halin yanzu bata da wani aiki sai fama da tunaninsa ,ahankali ta runtse shayayyun idanunta tana sake tariyo komai nashi most especially yadda yake nanike mata a duk sanda zasu kasance tare wasa wasa dai mr ata so yake lallai sai yayi wa rayuwarta karfa karfa da karan tsaye sai ya dasa mata matsanancin son shi ya ruguza mata rayuwa sannan hankalinsa zai tashi , ta jima zaune tana tunanisa kafin ahankali ta zame ta kwanta a gurin still dai tunaninsa bai bar zuciyarta ya huta ba.”
“ maryama me zai hana ki auresa kawai tunda ya amince zai aureki kuma kema alamu sun nuna kin fara jin wani abu akanshi ?”ta yiwa kanta tambayar tana jin wani abu tun daga tsakiyar kanta har zuwa kasan maranta mai kama da shocking din wutan lantarki “maryama matukar kika auri mutun nan wahala zaki sha a hannunsa ki manta dashi kawai ki samu wani ko kuma ki yiwa Oga amar magana ko akwai wanda ya yarda da natsuwarsa kuma wanda bashi da mata ya had’u su aure kamar hakan zai fiye mata zaman lafiya da samun kwanciyar hankali a rayuwarta “yes yes !!gara kiyi hakan dan auren mr ata ba mafuta bane gareki wahala kawai zaki bawa kanta ga matarsa dan dole kin san yana daita ga kuma baud’adden halinsa.”Juyi tayi ta gyara kwanciyar tana tunani da zance zuci tana jin kamar kartaje aikin gobe sai dai zuciyarta na tsananin jin tsoro dan bata san abinda rashin zuwan nata zai haifar ba .”
Washegari
Da misalin karfe shabiyu saura Mr ata yana tsaye a gaban ma’aikatansa a office dinsu maryama kuma har lokacin bata qaraso ba yayi shiru yana zance zuci sai gata ta shigo a natse bakinta d’auke da sallama cikin shiga ta kamala, sai bayan data shigo office din sannan taga mr ata tsaye .”office din ya d’auki shiru tamkar babu wasu halittu dake numfashi acikinsa duk wad’an da ke zaune acikin office din babu wanda bai juyo ya maida hankalinsa kanta ba sakamakon jin sautin muryarta d’aya byn d’aya take kallonsu kmr yadda suke kallonta kowa na zaune a mazauninsa sai dai bata ga alamun yusura ba .”
mr ata kuwa tun da ya d’aura tsumammun idanunshi akanta bai d’auke ba. dan tuni ya fara cire ransa da zuwanta a yau din duba ga lokaci ya fara tafiya dan har ya shaka ya fara jin haushi jira yake biyu ta buga yayi mata diran makiya kallonta ya cigaba da yi koina na jikinta a lullu’be yake tun daga saman qafarta har zuwa kanta da hijab wani irin sanyi ya ratsa shi karon farko yaji asalin shigarta ta baya tayi matuqar burgesa babu abinda ya nuna ajikinta wani zirrr ya dinga ji asansar jikinsa har tsakiyar kanshi kamar ana jona masa shocking ahankali yaji ya fara samu wadatacciyar natsuwa .”
ta kalli inda yake tsaye ganin yadda ya zuba mata ido ko kiftawa ba yayi yasa ta bud’e bakinta da kyar tace “sorry sir good morning “.bai amsa mata ba kuma bai d’auke kwayar idanunshi akanta ba ,sai dai irin kallon da yake mata yafi komai d’aga mata hankali “oh Allah ni mryama wannan kuma wani irin kallo ne haka ?”to ko dan ta ‘bata lokaci ne yasa yake kallonta haka ?”ta fad’a a kasan ranta,dan ita wallahi bata son yadda yake kallonta dan wanan kallon nasa kallo ne mai cike da kwarjini da dagulawa mutun lissafi ne .”
Ahankali ta juya ta soma taku acikin Office din yayinda mr ata bai daina kallonta ba har ta qarasa inda empty chairs suke ta samu waje tayi wa kanta matsugunni ta had’e hannuwanta waje d’aya tana kallon wani gefe dabam .” a natse ya dawo kusa daita ya tsaya ta d’an saci kallonsa sai kuma ta d’auke shayayyun idanunta da sauri ganin ta bar kallon wanan bangaren da yake ya dawo d’ayan bangaren da ta maida fuskarta ya tsaya ya soma mgn“ guys abinda nake son nace shine nan da sati biyu masu zuwa zamu bar kamfanin nan zamu koma sabon kamfani wanda acan zamu cigaba da aiwatar da ayyukan creation dinmu” ahankali ya cigaba da yi masu bayanin irin cigaba da yake son su kawowa kamfani kuma har zuwa wannan lokacin da yake masu bayani bai fad’a masu inda zasu koma da aikin ba
kuma duk yawo su babu wanda yayi qoqarin tambayarsa inda zasu koma din yadda sukai shiru haka mryama tayi tare da tsura masa idanun tana kallon sa tana nazarinsa har sanda ya dasa aya ya qara da cewa “ ina fatan kun fahimceni “.
“yes sir !” suka had’a baki wajen fad’ar haka still babu wanda yayi tunanin tambayesa wanda maryama bata raba dayan biyu tsoro ne “.
“sir mai yasa zamu bar nan din ?kawai ta tsinci bakinta da cewa haka ,shiru yayi mata batare da yace mata uffan ba “naga nan din kamar ..” “keep queit…”ya katseta ta hanyar fad’ar haka yana hura hanci shiru tayi kamar yadda ya bukata yana hukuntata da kwayar idanunshi “maryama what’s this nonsense?”what’s every time if am talking you most disobey me “? nasan kinsan bana son haka but why ?am sorry sir! but nayi tambayar ne saboda musan..”
”maryama ki min shiru banason ki sake cewa komai” tace “okay sir “.!
ta fad’a sai dai tayi kasa da kanta muryarta can kasan makoshi tace “ko me yasa zai daddakemu daga nan ya maidamu wani waje kamar wasu tsuntsaye ?”me kike ce ?ya tambayeta da sauri ta d’ago kanta gabanta na fad’uwa ta zuba masa shayayyun idanunta tare da sanya kwayar idanunta cikin nashi “ba kallona nace Kiyi ba what did you say ?”bance komai ba sir, kawai dai kunnenuwanka ne suka ji kamar nace wani abu.”
“Maryama nasan kince wani abu” tai shiru kawai” ina jinki! “nifa babu abinda nace kawai dan dai kana jin haushina ne yasa kunnuwanka suka jiyo maka kamar nace wani abu “keep quiet bansan me yasa kika rainani over ba ,kisani na d’auki aikina da mahimmanci ban d’aukesa shirme ba sannan idan kinga zaki bimu fine idan kuma zaki cigaba da zama anan gud ya rage naki.” dumm taji gabanta ya fad’i “daman yace tazo aiki ne dan kawai ya samu damar wulakantata kome ?”tayi mugun zuba masa ido tana dubansa ya juya a natse ya fuskanci ma’akatan sa “guys ina fatan zakuyi aiki dani kuma zaku bini duk inda na bukata?”.sure sir okay back to work ”yana gama fad’ar haka ya wuce ya fita ko kallon inda take bai yi ba dan har lokacin haushinta yake ji kamar yadda ta fahimta Itama ko kallonsa batai ba sai dai abinda yayi mata ya dameta matuka idan tai bleming kanta akan saka bakinta cikin maganarsa ko zuwanta aiki sai kuma ta dawo ta bashi laifi wulakancin da yayi mata .”
Jiki a sanyaye ta bude littafi tana duba zane tana zance zuci “ya ma bari mutun yayi magana yaji me mutun zai ce amman yaki ya hau mutun da matsefa ,masefaffe kawai abinda ya kamata yace min me nake qoqarin cewa .?”Ko me yasa zai daddakemu daga nan zuwa wani guri da alamun inda zai maidasu din akwai nisa sosai may be shiyasa yayi masu kyautar mota amman ita ya hanata ko ita uwar wa ta kashe masa da zai bawa kowa ya hanata ?”tayi maganar tana jan tsaki a fili ita dai gasky zata samesa taji inda zasu koma matuqar akwai nisa daga unguwarsu bazataje ba ,gara ta hakura da aikin gabad’aya ta huta tunda daman akwai sharad’i akanta.”
ahankali ta soma qoqarin mikewa tsaye tana gyara zaman hijab dinta sai ga madam some ta shigo “yauwa maryama latest desing na royal palace zaki zana “okay ma ,zuwa yaushe ake bukata ?”eh to ko zuwa gobe da safe haka “okay ma zanyi qoqari in sha allahu .”
Madam some ta juya ta fita ta shiga wani office din ita kuma ta nufi office din mr ata bata tsaya neman izini ba ta fad’a kanshi na sunkuye yana duba wani file din zane sai dai nan take ya fahimci Itace ta shigo masa office babu neman izini,a natse ta qaraso ta tsaya a gabansa tare da goya hannuwanta duka abaya tace “sir !”ya d’ago kanshi ya had’e hannuwansa waje d’aya ya dafe ha’barsa tare da zuba mata ido .”amm daman nazo ne nasan inda zamu koma aiki idan wajen yayi min zan biku .”
“Idan kuma wajen bai miki ba fa ?”zan ajiye aikin gabad’aya”.ta bashi amsa kai tsaye batare da wani shayi ko ‘bata lokacin ba “okay lekki zamu koma”. “lekki!?ta furta a fili tana d’an ware idanunta ya gyad’a mata kai yana lumshe mata ido “ammm gaskiya Ina ganin zan ajiye aiki dan …”sai kuma tayi shiru ta kasa cigaba da magana “uhm Ina jikin dan me ?”dan na samu wanda zan aura mgnarta ta daki kunnuwansa ta wuce har cikin zuciyarsa tamkar ta soka masa mashi haka yaji maganartata a kahon zuciyarsa “yayi shiru kawai yana kallonta wanda kallon nasa yasa ta sunkuyar da kanta kasa dan bata son wannan kallon nasa mai firgitarwa .”
ahankali ya motsa lip’s dinsa yace “daga yaushe zuwa yau she ne har kika samu wanda zaki aura ?yayi mata tambayar kamar zai yi kuka ta d’ago kanta a natse har lokacin ita yake kallo fuskarsa a had’e “daga sunday wani d’an uwa zan aura”ta fad’a masa tana son tabbatar da abinda yake boye wa aransa,ya lamgwabar da kai gefe kamar abun tausayi “me yasa ni bazaki aure ne ba ?”yayi mgnr acikin ransa yana jin wani irin tuttukin bakinciki mara misaltuwa ahankali ya sauke hannunsa ya mike tsaye ya dawo inda take tsaye ya tsaya a gabanta yana lissafin abinda zai yi kamar bazai yi magana ba sai kuma ya motsa lip’s dinsa “ni me yasa bazaki aure ni ba sai wani dabam “.?
“Saboda baka sona!”.
“Saboda bana sonki ?” yes of course baka sona shi kuma yana sona kai kuma kace taimakona zakayi kaga gara na auri mai sona ba mai taimkona ba ,dan Kai daman kafi qarfin aurena bare km tun kafin aje koina ka fara da taimakona zakayi “naji but shi da yace yana sonki ke kuma kinji aranki kina son shi ko kawai zaki auresa ne dan kina son kiyi aure?” ta gyad’a masa kai tana cewa “eh to bawai ina son shi bane amman zan auresa dan naji ya d’an kwanta min arai nan take moond dinsa ya sake canzawa ya shiga kai kawo a filin office din .”Sosai tai mamaki yadda ya shiga damuwa “kar dai da gaske mr ata sonta yake kamar yadda ta fara tunani kamar yasan tunanin da take kawai taga ya dawo gabanta daf daita ya tsaya yasa hannuwansa ya rike kafad’unta yace “karki ga na shiga wani hali kiyi tunanin Ina yin shishigi ne acikin rayuwarki ,jikina ya bani baki son auren nan kuma banason ki auri wanda baki so kasancewar akwai illa saboda ni nan hakan ta faru dani kuma babu abinda auren ya haifar sai zallar damuwa ki manta da wannan ni ki aureni “
Tayi shiru tana tunani wannan Iko nashi “gaskiya ni dai gara na auresa zai fiyye min kwanciyar hankali akan na aureka shi mutun ne mai sauki hali mai kyakkwan muamula da mutane mutun ne mara girman kai da sanin kimar mutane mutun ne mai…”ai kafin ta qarasa mganrta sai Jin saukar mari tayi akan kuncinta sosai ta firgita ta dafe kuncinta ta tsura masa ido shima ita yake kallo ranshi a matukar’bace hawaye ya zubo mata akan fuska yace “kina hauka ne ko kuma kin fara shaye shaye ne ?”a gabana kike yabon wani katon banza har kike kuranta shi ?bayan ya gama maganar sai kuma yayi shiru ya juya mata baya yana fesar da iska yana duban hannunsa da ya mareta dashi “oh my god why adam ?”me yasa ka mareta?”yana cikin wannan halin yaji motsin takalmanta alamun zata bar office din juyowa yayi da sauri ya rungumeta tsam tsam ajikinsa gabansa na fad’uwa nan take jikinta ya d’auki kyarma amman ta kasa kwacewa yadda yake ji ajikinsa haka take ji ajikinta kamar an jona mata wutar lantarki cikin sanyi murya yake magana “ki fahimceni maryama banason ki aure wani ,ba wai Ina nufin karki yi aure bane a’a banason ki auri wanda bakya so ne .”
Wani haushi da bakinciki ya dinga shigarta yana mamaye ilahirin jikinta domin alokacin tayi tunanin zai ce mata shi yana sonta ne dan tafi son ya furta mata cewar yana sonta ba wai ta auresa batare da tasan matsa yinta ba kuma tayi Imani idan ta auresa a haka duk ranar data bata masa rai kai tsaye zai wulaqantata .wani haushi ya sake kamata sbd bai ce yana sonta ba ya wani rungumeta yana faman sauke ajiyar zuciya tamkar jinjirin daya kwana uku batare daya sha nono ba tana fama da radadin marin da yayi mata da rashin furta mata yana sonta bare ta samu damar aurensa ,ya wani rungumeta yana mata maganar banzar ko ina ruwan shi da zata auri wanda bata so oho ?”
ahankali ta soma mutsu mutsun kwacewa ya juyo daita suka fuskanci juna ya sake matseta yayi mata kyakkywan riko yana cewa“haba maryama me yasa kike jin cewar zaki iya auren wani ki bar ni “zan fi samun natsuwa da kwanciyar hankali ta bashi amsa da haka tana sheshekar kuka “bazaki samu ba maryama bazaki iya rayuwa da wani ba ke har yanzu baki fara Jin alamun cewar kina son adam ba ?”wannan kam gakiya ne ta fara Jin son shi har ma tana jin cewar bazata iya kwanaki dayawa batare datayi magana dashi ba domin duk yadda yake mata kallon tana son shi ashe abun da gaske ne lallai zuciyarta ta tafka mata babban kuskure domin dai son shine kuskure na farko da zatayi arayuwarta.”
“Ya zareta ajikinsa ya riko hannunta cikin nashi yana murzawa ahankali yace “maryama me yasa bakya tausayawa kanki ?”tayi saurin zare hannunta daga nashi tana yarfarwa kamar wanda wuta ta kona saboda wani blood rush da taji ya taso mata daga hannunsa zuwa nata cikin second d’aya ya zagaye duk ilahirin jikinta cikin tsarke war murya tace “me ya sameni da zanji tausayin kaina?”sannan dan nace zan auri wani ne yasa ka mareni ?”ya lumshe mata idanunshi ya bud’e yana kallon yadda take yarfe hannunta tace to “nasan kana da komai da duk wata mace zata so aurenka amman ni maryama bazan aurenka kuma kome zakayi gara na auri wani akan dai na auri mutun irinka “ bai san sanda dariya ya subuce masa ba, ..ya mugun tsareta da ido sannan yace “kamar zaki iya!” ta d’an tsaya tana kallonsa Tana assessing maganarsa yana kallonta with a broad smile akan fuskashi ta d’auke kanta tana lissafi “kamar fa ya gane ta fara son shi idan kuma bai gane ba tabbas cigaba da tsuyuwarta a wajen zai iya tona asirin zuciyarta bugu da qari ga tsayuwa na neman gagararta dan haka ta juya ahankali zata bar masa offie din taji ya riko tsintsiyar hannunta tare da fixgota zuwa jikinsa ya rungumeta yana jin wata irin tsantsar soyayyarta na ratsashi “
“Ina zaki ?”gida zan wuce !”kuma in sha Allahu daga yau bazan sake ta kowa inda kake ba dan baka you’re so wicked shiru yayi yana shafata kafin ahankali ya cigaba da mgn “gobe ne fa asirin wanda ya fitar da hadad’dun hotunamu zai tono ko bakya son kisan ko waye ?”ya fad’a tare da sausauta rikon da yayi mata zuciyarta na matukar zafi ta tsura masa ido tare da alamun son ya mata qarin bayani ajiyar zuciya ya sauke nan ya kwashe yadda akayi bincike komai ya fad’a mata “waye wanda ya fitar da hotunan?”zaki sani a gobe ta sauke numfashi tace “to sakar min jikina kuma dan Allah wannan yazamo karo na qarshe da zaka kai hannuka jikina “ba jikinki ba hatta komai naki nawa ne kuma ke baki isa ki hanani ta’ba wa ba “ni kam wannan abu ya fara damuna idan kana sona ne ka fito ka fad’a min tai mgnr tana harararsa “baza’a fada ba !ya qarasa maganar ahankali yana had’e fuskarsu waje yana qoqarin kamo lip’s dinta, tayi saurin kawar da fuskarsa gefe tana cewa “bana so abinda kake min kana sa Ina cin raina dayawa
Ina jin nadamar aiki a kamfanin AGC wallahi if Ina son naga wanda ya d’auke mu hoto da har abada bazaka sake sanyani acikin idanunka ba
ga ta’ba min jiki da kake yi ga rashin so ga mari.”
sarai ya fahimci abu biyu din nan sun fi bata mata rai ba wai ta’ba mata jiki ba ,rashin bai furta mata yana sonta ba da kuma marin da yayi mata yayi kasa da muryarsa sosai “kina son na furta miki kalmar so ne kafin ki amince ki aureni ?”tayi shiru tana kallonsa ,ya sauke mata numfashinsa a fuska ya cigaba da magana “ko kuwa kina son na baki hakurin marin da na miki ne ?wad’an nan maganganun d’aya fad’a mata ba iya cikin kwakwaluwarta da zuciyarta suka tsaya ba har ilahirin jikinta take jin tafiyarsu zata so ya aikata abu biyu din nan ,furta mata yana sonta da kuma bata hakuri “naga alamun kina bukatar hakan sai dai kuma bazan yi ko d’aya aciki ba idan zaki aureni a yadda nace fine idan bazakiyi na leave my office “ ya fad’a yana sakar mata jiki ya zagayeta ya nufi wajen zamansa.”
Idan ta fahimcesa so yake ya nuna mata qarfin Iko bayn yayi nasarar tursasa zuciyarta da gangar jikinta sun fara jin wani abu akan shi ,ya fara koyar daita soyayyarsa ,to ko dai zata amincewa aurensa ne kamr yadda ya bukata ?kai Ina bazata iya wannan kasadar ba domin auren irinsa babu abinda mutun zai tsinta aciki sai zallar damuwa ta kasa motsa gangar jikinta tana shawara da zuciyarta bata jin zata sake d’aukar dogon lokaci tana aiki dashi yana zaune zai ji ta auri wani irin kallon da take masa ya fahimci kallon mugu azzalamu take masa haka nan yaji babu dadi aransa jiki a sanyaye ta juya ta fice daga office din tana jin tarin damuwa bayanta yabi da kallo yana hura hanci tare da lumshe idanunshi bayan wasu mintuna talatin da fitartata daga office dinsa ya hango fitowarta tana goge idanuta ta nufi hanyar sauka qasa aranshi yace sarkin yan kuka ranshi bai masa dadi ba yaji kamar ya tashi ya bita ya dawo daita sai kuma yaga gara kawai ya barta wuce .”
Tunda maryama ta koma gida ta rasa meke mata dadi ,ka kasa sakewa da zarar ta tuno kamaninsa sai gabanta ya yanke ya fad’i “ya ilahi kanta ta sunkuyar kan daks din daikinta tana addua acikin zuciyarta dan ta rasa me yake mata dadi ,Ina ma batasan shi ba ,Ina ma aiki bai had’ata dashi ba haka dai tayita tunani tana addua kar Allah yasa son shi yayi tasiri a zuciyarta, da adduar Allah ya cire mata tunaninsa cikin zuciyarta suku suku ta qarasa wuni umma ta lura da yanayinta amman ta share ta dan kota tambayeta tasan zatace mata babu komai qarfe takwas da wasu mintuna na dare tana kwance akan katifarta taji shigowar sako wayarta nan take ta soma qoqarin dubawa taga sakon daga mr ata ne da sauri ta shiga ta soma dubawa .”
“Slm how are you doing ?I just want to apologize for what happened today I’m sorry for today I’m not a wicked man has you think and I’m not a bad person I’m so sorry I’m not intention to hurt you please kizo gobe koda shine zai zamo zuwanki na qarshe .”
Wani irin sanyayyen ajiyar zuciya ta sauke tana sake karanta sakon tana jin wani sanyi na ratsa ilahirin jikinta sai dai tayi shiru tana tunanin amsar da zata tura masa ta d’auki sama da wasu mintuna talatin a qarshe ta tura masa “is okay “Tana gama tura masa ya kirata har missed call hudu bata d’aga ba dan bata son ya sake dasa mata abinda zai dameta wanda take ji ma akanshi zatayi iyakar qoqarin ta ta raba kanta dashi bazata ta’ba yarda sonshi tayi tasiri ba .”
*****
Washegari Wanda ya kama ranar laraba da kusan jiya maryama tazo aiki tana zaune tana aikin zane tana daddaga littafai tana dubawa sai ga yusura ta shigo ta qaraso kusa daita ta tsaya tana cewa maryama ina son muyi wata magana dake dan nayi tunanin nazo gida na sameki amman kunyar haka yasa na kasa zuwa maryama ta bar abinda take tare da mikewa tsaye tana fuskartata ina jinki yusura
“dan Allah Kiyi hakuri” hakuri kuma wani hakuri ai tunda mr ata yace kubani hakuri km kin bani hakuri komai ya wuce araina ,nasani ina sake baki hakuri ne saboda ban kyauta ba domin idan kowa yayi zarginki ni bai kamata ba kasamcewar tare muka taso ki yafe min karki tsaneni dan Allah “kai haba yusura wallahi babu komai nasan qauna ce tasa haka duk mai sonka shine zai ga kayi wani abun batancin ya nuna damuwarsa wallahi babu komai komai ya wuce ni dake qawaye ne kuma wannan matsalar bazata rabamu ba ,”haka ne maryama ta fad’a tana rungumota jikinta ta sausata rungumar datai mata tana cewa amman idan bazaki damu ba mai yasa kukayi wannan hotunan?” mukayi ko akayi mana?” to waye wanda ya iya munafurci haka ?”wallahi yusura ban sani ba kuma har yanzu nan da nake tsaye a gabanki ina wannan tunanin amman mr ata jiya ya tabbatar min an gama bincike” nifa tunanin yan gidanku dan wallahi idan gidanku suka gani akwai damuwa gara duk ma’aikatan kowa yasani akan mutanen gidanku .”
“ai tunin an wuce gurin dan sun gani shine ma dalilin rashin zuwana aiki kwana biyu sai da mr ata da wani abokinsa kukaje gida suka bada hakuri sukai masu bayani dalilin da yasa hakan ta faru yanzu dai komai ya wuce yanzu haka ban jima da fitowa daga office dinsa ba kuma yace zuwa anjima za’a kar’bi wayar kowa dake office din nan ,duk maganar da maryama take acikin kunnen sultana tayisa daga office dinsa ya hango maryama tana magana da yusura abayansu kuma sultana ce tsaye tana sauraronsu tana zance zuci “ina ai bazan bari ya duba wyata ba kafin ma ya duba na goge komai , sosai yake kallonsu ta cikin glass sai dai idanunshi kyam akan sultana yake yana nazarinta yana kallonta ta juya da sauri yayinda shi kuma ya cigaba da juyi akan kujera kai tsaye wani office dabam sultana ta shiga ta fad’a bayi jikinta na rawa ta shiga photos dinta tana cikin neman hotunan taji ya fixge wayar a hannunta yana cewa “me kikeyi anan ?
Mmn sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
48
saurin d’auke numfashi sultana tayi tana dubansa fuskarta da bayyananen tsoro tace “uhmm amm babu komai kawai ina son goge wasu tsofafin hotuna ne acikin wayata “tsuma mmun idanunshi ya zuba mata yana mata wani irin wulakantaccen kallo mai razanarwa”lallai ma yarinyar nan tana da matuqar rainin hankali kenan har yanzu bata ma san waye shi ba ?“tsofaffin hotunanki zaki goge ?”ya fad’a yana kallon wayarta dake rike a hannunsa“eh tsofafin hotuna nake son na goge dan wayar tana hanging da alamun hotuna ne suka masa yawa.“
“kin tabbatar?”tayi saurin gyad’a masa kai alamun “eh!”jikinta na wani irin shaking alamun rashin gasky tana jin kamar ta fixge wayar daga hannunsa sai dai babu dama aikata hakan dan ko giyar meye akanta bata isa ba,bama zata fara gwadawa ba “.
“maryama !”
Ya kira sunanta tare da lasar lip’s dinsa na qasa “yes sir !”ta amsa masa cike da girmamawa tana kallonsa” ungo wayar nan ki duba min hotunan dake cikin har recently deleted ”yayi taku biyu ya qaraso inda maryama take tsaye ya mika mata wayar .”maryama tasa hannunta ta amsa ta shiga daddanawa tana dubawa ,shi kuma yayi shiru tsaye yana kallon sultana wacce hankalinta yayi matukar tashi fiyye da tunanin mai karatu”.
muryar maryama na rawa tace “ga..”gasu nan sir! “ga hotunanmu nan acikin wayar sultana wanda ke nuna alamun da wannan wayar aka fara d’aukarmu “nan take gaban sultana ya bada wani irin dum jikinta ya cigaba da kyarmar da yake mr ata ya kar’bi wayar a hannun maryama yana duba wa” ai nasani nasan itace.”
maryama ta d’ago kanta da sauri ta kallesa “na dade da sanin itace nayi haka ne kawai dan na kamata da hujja “.yayi maganar yana dawo wa kusa da sultana ya tsaya ji kake tass tass!! ya d’auketa da wasu gigitattun mari har biyu ajere wanda yayi sanadiyyar da numfashin maryama ya tsayawa cak, ya daina bugawa tare da dafe kuncinta tamkar itace ta sha marin dan tasan zafin marinsa yaso qara mata wani marin sai dai ganin maryama na shirin fad’uwa ne ya rikota cikin zafin nama ya makaleta da jikinsa hankalin maryama yayi mugun tashi ta kwanta lamo ajikinsa tana kyarma numfashi ya fesar ta hancinsa sannan ya kai bakinsa daidai saitin kunnenta yana mata magana .”
halin da sultana ta shiga kafin ta dawo haiyacinta kuwa Allah ne kad’ai masani , ta wani zuba masu ido ganin yadda yanayin adamcy ya canza duk ya wani susuce akanta yana shafa kanta zuwa bayanta kamar wata jinjira yayinda bakinta yake motsawa ahankali ahankali “kayi hakuri karka sake marinta “tayi magan cikin tsananin tashin hankali ,bakinciki ne ya tokare ma sultana kahon zuciya wanda yasa hawaye ya fara zuba daga idanunta tunda take arayuwarta ba’a ta’ba tozartata irin na yau ba“mari kuma agaban maryama?mr ata ya maida kallonsa ga sultana yana hura hanci “this is your last warning sultan if I ever seen you do something like this wallahi zan kasheki da hanuna dan babu wanda zai min irin wannan tozarcin na kyalesa.”
“Kuma karki d’auka dangantakar dake tsakaninmu na duba”no ban duba wannnan halakar ba, kuma daman Kinsan bazan ta’ba duba wannan danganta kar ba, abinda na duba ke ma’aikaciya ce acikin wannan kamfanin kuma dokar ma’aikata shine idan an kama mutun da laifi za’a fara bashi warning tare da dakatarwa “.
yana gama fad’ar haka ya mika mata wayar ya tsaida idanushi akan maryama wacce ke kwance ajikinsa ya sake kai bakinsa daidai saitin kunnenta“malama ai sai ki tashi ko dan kin lafe.”
ya fad’a tare da qoqarin d’agota daga yadda ta kwanta ajikinsa da sauri ta qarasa barin jikinsa ta koma gefe guda ta tsaya tana cewa “ I’m very sorry sir bansan ya’akayi na kwanta ajikinka ba .”sultana kuwa ranta a matukar ‘bace take kallonta batasan adadin tsanar da takewa maryama ba ita dai tasan tsanace irin wacce take jin zata iya rabata da duniyar gabad’aya.”
“Ya adam you slapped me in front of this useless girl “?zaki ‘bace anan ne ko sai na qara miki nonsense kawai and kuma na dakatar dake zuwa aiki karki kuskura na d’aura kwayar idanuna akanki da sunan kinzo “ maryama muje ya tasa maryama gaba suka fice daga office din suka bar sultana tsaye cikin quna rai da ‘bacin rai .”kai tsaye office dinsa ya shige inda maryama take biye dashi abaya ya zauna a mazauninsa tare da tsura mata ido yana kallonta”.muryarta a sanyaye tace “na gode sosai sir duk da nasan kai din mutun ne da baka son ana yawon maka godiya akan abu amman dai dole zan gode maka thank you so much mr ATA ban cin kai ni nasan bazan ta’ba gano wannan gaskiyar ba a karo na biyu ka sake zama silar yaye duk wata damuwata” .”
Tunda ta soma magana ya tsurawa bakinta ido yana kallo yana Jin kamar ya Kai bakinsa ya tsosa ,sai dai har tai shiru na second goma bai iya aikata komai ba ta cigaba da magana “dan Allah sir kayi hakuri da sultana ka barta ta cigaba da zuwa aikinta dan ni na yafe mata coz I think she’ll not do it again in sha allahu .”haushi yaji har cikin zuciyarsa ”.bai sanda yayi magana a harzuke ba“Idan ke sha sha ce ni bashi bane idan ke sallamamiyar zuciya gareki ni ba itace dani ba nasan me nakeyi kuma nasan ciwon abinda aka min okay “.duk naji abinda kace amman kayi hakuri dan Allah dogon tsaki taja yana watsa mata harara yace “kin wani damu kanki ita datai laifi kinji ta bud’e baki ta bada hakuri !?“ya tambayeta yana sake jan tsaki “idan ta baka hakuri zaka hakura ?dan nasan dai dole zata ..”!
”shiiiiiii !”
Yayi mata alamar tayi masa shiru nan take tayi tsit ta shiga taitayinta tun kafin itama ta samu nata marin sai daya numfasa kana yace “idan kina da abunyi je kiyi dan ni bani da lokacin ‘bata wa akan wannan nonsense girl din” ya fad’a tare da mikewa tsaye ya shige d’akin dake cikin Office dinsa .”
ahankali tabi bayansa da kallo dole bata yadda ta iya ta fito anan suka ci karo da madam some ta qarasa kusa daita tana gaisheta tare da fad’a mata an gano wanda ya d’aukesu hoto sai dai bata fad’a mata ko wacece ba “kai marayama amamn gaskiya naji dadi sosai da’aka gano ko waye ,wallahi mr ata yayi min qoqari sosai banida abinda zance masa dan allah ki tayani masa godiya” ai ke din tabance a zuciyarsa sau nawa zan fad’a miki matsyainki a wajensa ?mutane nawa ne sukai aiki dashi amman ban ta’ba ganin wacce ya damu da damuwarta ba kamarki wanda hakan ke nuna alamun yana matukar sonki ne “haka dai kike fad’a amamn ni walalhi bazan ta’ba yarda ba, dan maganarki ma mamaki take bani ta yaya hakan ma zai kasance gara ma idan kince tausayina yake ji zan fi yarda da hakan amman batu na maganar so kam babu alamunsa saboda shi kulkum yayi min wani taimako cewa yake akan baya son ya samu matsala ne da aikinsa sai dai ban ta’ba jin ya burgeni ba kamar yau dan ya kwantar min da hanakali sosai .”
“da fari yasa naji zan iya cigaba da rayuwata ko babu kowa ,yasa na daina kwana ina kuka akan damuwa .” “ke dai kinyi sa’a ko babu so kinsamu matsayin kulawa a wajensa wannan ma kawai abun godiya ne bare kuma mu musan akwai so wanda kema kinsan da zaman haka mryama tayi murmushi ta juya tana cewa “a’a ni dai gaskiya bansan da zaman komai ba tana daf da shigewa office dinsu madam some ta biyota “maryama waye ya d’auke hotunan?.”maryama tai shiru na second goma sannan tace “gaskiya ban so na fad’a ko waye ba dan duk wanda ya rufa wani danuwansa asiri ,to fa asirin kansa ya rufa kawai Abar magana kamar zai fi “okay shikenan amman jikina ya bani kamar sultana ce amman Allah ya Kyauta ta fad’a tare da juyawa ta koma mazauninta .”
Mr ata na zaune yana amsa waya sultana ta shigo Office din kamar wacce aka jeho kai tsaye ta soma magana cikin wata irin murya mai karfi wanda yasa mr ata yace “excuse me just give me fiver second, disconecting din kiran yayi tare da had’e hannuwansa waje d’aya ya rike ha’barsa dashi tare da zubawa sarautar Allah ido “ban san me na kashe maka ba arayuwar nan “baka san abinda kayi a yau din nan ba sake qara min tsanar maryama kawai kayi a zuciyata .”
“amman kasani zan baka mamaki kuma lallai kasa hankalinka da kyau akanta duk abinda zai faru ,dan duk abinda ya samu maryama kasani kai ne sila ,kuma ka sawa ranka nice nan sultana na aikata ,wallahi wallahi maryama ce zata d’auki zazzafan hukuncin abinda kayi min .”
jin ta ambaci sunan maryama ce zata d’auki hukunci yaji gabansa yayi mummunar fad’uwa a sukwane ya mike tsaye yana taku yana mata wani mugun kallo mai tarwatsa zuciya kafin a natse ya motsa lip’s dinsa “look sultan bazan ce karki yi duk abinda kike so ba ,kiyi komai kike so but kisani ni ne na wulakantaki idan abinda nayi miki wulaqanci ne ba maryama ba why not ni kiyi facing dina ni da nayi miki hukunci “.
“okay saboda kinsan ni ba abokin karawarki bane shine zaki huce akan maryama we’ll go and head dan girman Allah karki fasa ki tabbatar kinyi abinda kike son kiyi karki fasa amman kasani duk abinda kike ji dashi nafiki iyashi ya fad’a a tsawace yana nuna mata kofar fita da yatsan hannunsa “leave my office.”””
da sauri ta juya ta nufi kofar fita tana wani irin haki ,kamar wata zautacciyar mahaukaciya ta sauka zuwa qasa ta nufi inda motarta take da kyar ta lalaba ta shiga motarta ta zauna ta kifa kanta akan sitiyarin mota wani irin kuka ne ya kufce mata ba dan taso ba , tayita kuka sosai dan haka ne kawai zai iya sanyaya mata zuciyarta sai datai kukan mai isarta ba mai rarrashinta tukun tayi shiru taja motarta ta wuce gida sai dai aranta ta kudurta duk runtse duk wuya sai taga bayan maryama sai tayi mata abinda har ta mutu bazata manta daita arayuwarta ba .”tana isa gida ta zayyanewa aunty abida komai daya faru a Office jin abinda tace ta fadawa ata yasa gabanta yayi wani irin mummunar fad’uwa hankalinta ya tashi sosai tace “kinga babu kyau ire item wad’an nan maganganun wani Abu yaje ya sameta ace kece maganganunki sunyi tsauri dayawa me yasa baki kirani ba ?ko me yasa bayan yaga hotunan a wayarki baki dawo gida ba ?.”
kinga irin taurin kanki tunda kika tura wa wad’an da kike bukatar suga hotunan nace ki goge kika ki ban san meye amfanin zamansa a wayar ki ba gashi kin ruguza komai dan damar data rage mana kinsa ta subuce mana tayi shiru tana jan tsaki tare da neman mafuta dan dole su samo mafuta kafin komai ya rincabe masu mikewa tayi tsaye ta shiga Kai kawo acikin parlour’n tana Neman mafuta can ya tsaya cak tace “dole ki bashi hakuri .”wa kenan zan bawa hakuri ?”adam zaki bawa hakuri “I can’t aunty duk wannan wulakacin da yayi min kuma na bashi hakuri ?”mari har biyu fa yayi a gaban wannan tsinanniyar yarinyar wallahi idan ban kashe yarinyar nan ba hankalina bazai ta’ba kwanta wa ba..”Kinga sultana dole fa yanzu ki ajiye komai ki nemi adam ki bashi hakuri dan nasan halinsa mahaukaci ne na bugawa a jarida zai iya sakawa ‘batar dake kuma babu abinda za’ayi .”
Sultana tayi shiru tana dubanta tana mamaki “kinyi shiru kina kallonta sanin halinsa ne danayi dan ga hindu nan ta isheni misali tunda aka ne metà aka rasa da kyar uwarsa tasa ya fad’i gaskyr inda take kuma duk da haka baa bada belinta ba ana kan bincike akanta dan haka ki kirasa ki bashi hakuri tun wuri ki kuma janye kalamanki kar wani abu yaje ya samu yarinyar yace kece kinga kin sakamu cikin damuwa .”
Bana tunanin aikata hakan ,bana tunanin zan iya bashi hakuri “ni dai ki tabbatar anjima idan ya dawo kije ki bashi hakuri idan ba haka duk abinda yabiyo baya babu hannuna”ban gane hausar babu hannunki ba ?ai kece kuwa mai hannu dumu dumu aciki ma kuwa dan Ina zaman zamana kika janyoni cikin matseefar da bansan ranar fitata acikinsa ba “sultana daga abun arziki ?ina arzikin yake ?tunda nazo wani kwanciyar hankali na samu ?”kullum daga wannan matsalar sai wannan I can’t take any more kuma zance naje na bashi hakuri bazanje na bashi hakuri komai ba bare na janye wata magana da nayi duk abinda zai faru ya faru am ready to die “ta fad’a da qarfi har sai da gidan ya amsa sannan ta fashe da kuka .”
Ganin ta fita haiyacinta yasa aunty abida ta rungumeta zuww jikinta tana rarrashinta “kiyi hakuri sultana Nima bansan abun zai zama haka ba, nayi tunanin zai amince da aurenki cikin sauki , amman kiyi hakuri “aunty Ina tsananin son ya adam akan na rasashi wallahi gara na mutu “subhanallah!”ki daina fad’ar haka bama zaki mutu ba muryarta da sheshekar kuka tace “to kiyi wani abu ko kiyi abinda zaki cire min son shi ko kuma kiyi abinda zai aureni “ki kwantar da hankalinki sultana muddin Ina raye zaki auresa ko ya aureki da girma da arziki ko kuma ya aureki da tsiya amman wannna auren babu fashi sultana sai kin auresa wani irin naunauyen ajiyar zuciya ta sauke tana sake rungume yaruwarta ajiki aunty abida tai shiru kwakwaluwarta na tunanin abun yi .”
Wunin ranar cikin farinciki maryama tayi sa cike da farinciki ta koma gida tana shiga bangaren umma ta shige tana cewa” umma nah na dawo ta fad’a tare da zama a kusa da umma ta ajiye jakarta “sannu da zuwa ya aiki”?” wayyo allah umma na gaji sosai kaina ciwo yake amman kuma alamun sun nuna kina cikin farinciki ?”
“sosai kuwa ammn wallahi kaina ciwo yake bari naje na kawo miki magani ki sha umma ta mike ta shige dakin bata jima ba ta fito rike da magani “ungo ki sha zaki ji daidai ta kai maganin bakinta saurin runtse idanunta tayi dan ta tsani shan magani umma ta dafa bayanata tana shafawa
da kyar ta amince ta sha “sannu kinji !”yauwa bari naje na kawo miki abinci umma me kika dafa ne mutuminki na dafa” shinkafa !? sosai kuwa shinkafa da miyar dayen kifi nayi “wow umma wallahi naji dadi sosai amman bari nayi fresh up nayi sallah ta mike ta shige d’akinta bayan ta gama komai ta fito adaidai lokacin da tuni umma ta kawo mata abincin ta d’aura akan qaramin table tana zaune tana jiran fitowarta.”
ahankali ta zauna kusa da umma ta soma cin abinci suna hira da umma “amm ummah ina son na tambayeki wani abu ?”ina jinki misali mutun ne yake da zafin rai sosai sai dai yana da kulawa da duk wani damuwarka, idan kana cikin damuwa shima yana tsintar kanshi ciki kuma bai ta’ba cewa yana sonka ba hassalima idan magana zata had’aku dashi maganr kaje kayi aure yake maka , amaman mutanen dake tare daku sai suna masa kallon yana sonka ne kuma umma kinsan wani abu, shi dai wannan mutumin ya dawo daga baya yace a auresa batare daya furta kalmar so ba .”ta qarasa maganar tana kallon fuskar mr ata acikin kwayar idanunta”umma tayi shiru tana saurarenta.”ahankali maryama ta numfasa sannan ta cigaba da magana “umma Ina son ki fahimtar da wani abu a cikin maganata .”?
“eh to ni dai abinda na fahimta hakan zai iya yuwuwa ace so ne, saboda kowani d’an adam da yanayinsa da kuma yanayin yadda yake shigar da soyayya rsa,” su waye wadan nan mutane ?” “amm wasu mutane ne a office dinmu”maryama kodai kice da mr ata?umma tayi mata tambayar kai tsaye “ware idanuwanta tayi tare da cewa “kai no no haba umma ina ni ina shi wannan mutumin da bai da sakin fuska ,ai muddin ya zamo mijina to nasan kwanaki da allah ya bani a duniya bamasu yawa bane .”ta qarasa maganar tana dariya sun jima suna hira maryama tayiwa umma sallama ta shige dakinta ta kwanta zuciyarta fess babu wani alamun damuwa sai dai hakan nan zuciyarta ta dinga tunanin mr ata wanda ya zame mata jiki tana son raba zuciyarta da wannan tunanin amman abun ya citura most especially a yau din nan ahankali ta gyara kwanciyarta tana sake rungume pillow ajikinta tana jin kamar shi ta rungume .”
Bayan kwana biyu akayi ma maryama salary sannan ranar ta kasance babu wani aiki a Office dan duk wani aikin da’aka bata ta kammala dan haka tayi tunanin da zaman da take ta tashi taje tay masu siyayya abubuwan da basu dashi a gida ta mike ta fito rataye da jakarta ta fito ta sanarwa madam some sannan ta sauko zuwa qasa .”
tunda ta sauko taji gabanta yayi wani irin mummunar fad’uwa sai dai bata kawo komai ba ta biyo dogon titin da zai fito da mutun zuwa babban titi stil dai gabanta bai daina fad’uwa ba duk ilahirin jikinta yayi mata wani iri taji kamar ana mganrta a baya , ta tsaya tare da juyowa wasu mutane tagani sanye da suit suna magana wanda ke nuna alamun bama daita suke ba dan haka ta sake juyawa ahankali ta cigaba da tafiya har ta fito bakin titi kai tsaye mota ta shiga zuwa bank mafi kusa da inda take ta ciro kudi masu yawa ta shiga wani shago siyar da Kayan sakawa na mata dana maza ta siyawa aunty da umma kala biyu biyu ,habib ma haka da takalmin itama ta siyawa kanta dogayen riguna guda uku kowanne da kalar takalminsa da jaka ta biya kudin ta fito ta shiga wani super market domin siya masu kayan kwalama ,anan ne ta hadu da wani alhaji mansoor wanda ya nuna qaunarsa agareta baro baro .”
ba wani dogon turanci maryama ta aminta dashi saboda daman irin wannan damar take nema wanda zai aureta ido rufe tunda bata da wani tsayayye maganar mr ata kam shirme ta daukesa duk da tana tsananin jinsa aranta .”nan sukai musanyar number da Alahji mansoor dan zuciyarta ta natsu dashi haka zalika bugun da zuciyarta take ta kau har tai tunanin watakilla haduwarsu dashi ne yasa taji wannan yanayin ajikinta , taiwa kanta fatan Allah yasa haduwarsu ta zame mata alkhairi arayuwarta alhji mansoor ne ya biya maku kudin shopping din da tai ya kuma kawota gida bayan ta shigar da siyayyar datai ciki ta dawo inda alhaji mansoor yace mata shi fa da gaske aurenta yake so yi kuma cikin kankanin lokaci sai dai yana da mata biyu da yara takwas kai tsaye maryama tace ta amince sai dai ta fad’a masa tana zuwa aiki .”
Yace ai wannan ba matsala bane bazai hanata zuwa aikinta ba ,wannan ne abinda ya qara sa zuciyar maryama ta sakankance dashi har ma tayi tunanin zuwa satin da zasu shiga zata gabatar dashi ga iyayenta ,tun daga wannan lokacin alhji monsoor ya fara zuwa zance gidansu maryama wanda hakan yasa gabad’aya maryama ta cire tunanin wani adam aranta ta soma saka tunanin alhji mansoor aranta duk lokacin daya so ganinta yana ganinta ranar da suka cika sati biyu da haduwa ne yazo wajen aikinta suna tsaye dashi ajikin motarsa kwatsam sai ga mr ata ya fito daga masallaci tun daga nesa ya hangota tsaye tare da alhji mansoor ,gabansa ne yayi wani irin mummunar fad’uwa ganinta tare da wani Wanda bashi ba ,nan take zufa ta shiga karyo masa .”ahankali ya cigaba da d’aga qafafuwansa ya zagayo ta bayansu ya tsaya ta yadda bazasu gansa ba sai dai qirjinsa ne ke wani irin bugu da matsanacin qarfin gaske “cike da tashin hankali ya zuba duka hannunwansa cikin aljihunsa .”
Tunani yake anya kuwa ba mafarki yake ba ?”maryamarsa ce tare da wani kato tsaye tana washe masa baki ?to ya bazaka ganta da wani ba tunda Kai ka kasa furta mata kana sonta ai dole ka ganta tare da wani “to kuma ai duk alamunta sun nuna tana sonka “okay kenan jira kake tace kana sonta ?”yayiwa kanshi tbayar yana sake shiga rudani da tashin hankali “adam kaga irin abinda zaka janyowa kanka ko?“ka bud’e baki kace mata kana sonta ne matsala to ai gashi nan wani zai maka shigar sauri ?”yayiwa kanshi magana yana datse harshensa da qarfin .”ahankali ahankali yake jiyo duk hirarsu da suke sai dai zance auren da yaji suke har da tsare tsare yadda komai zai guduna shine yafi komai daga masa hankali “aure kuma maryama “?
Mmn sudais💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.