Maradams Book 3 Complete Hausa Novel
Reading file: MAR ADAMS BOOK 3 COMPLETE BY AYSHA BAGUDU.txt
Chapter 13 of 29
Page 19
Zuciyar maryama cunkushe da haushi had’e da takaicin mr ata ta zari pencil din zane ta soma aikin daya sakata wanda tai masa laqabi da aikin mugunta tana zane bakincikinsa na sake ninkuwa a kasan ranta, yayinda zuciyarta ke wani irin zafi da suya .
ina ma zata iya murje idanunta tare da cire d’an burbushin tsoronsa dake ranta ai wallahi data zage kunjinta ta zabga masa rashin mutunci fiyye da wanda ya iya .amman ina bazata iya ba ,bazata iya karawa da mr ata ba ,dan ko a yanzu ya gano wani abu daga cikin rauninta domin kuwa ya fahimci aikinta yana da matukar mahimanci arayuwarta.
cikin kankanin lokaci ta zana namiji sanye da kaya wondo da riga tare da jacket sannan ta zana mace tana rungume da namiji sanye da dogon riga kanta lullu’be da mayafi,ta gama amman tsabar ‘bacin ran sigarin da yaketa faman bankawa cikinsa yana busa mata hayaki ya hanata d’agowa ta kallesa bare ta sheida masa ta gama.”shi kuwa mr ata zuba mata ido yayi ganin yadda ta gama amman tana jin wani abu aranta yasa ya sake ware qafafuwansa ya kunna wani sigari a ransa yayi murmushi ,shi ko kwana zasuyi a hk daidai ne.”
“ ganin muddin bata yi managa ba zasu kwana a haka ba damuwarsa bane dan ta tabbrwa kanta miskilancisa da jin kansa bazai barshi yayi magana ba , dan haka cike da tsinkewar zuciya da kyarma jiki ta d’ago fuskarta inda yake karaf idanunsu ya tsarke cikin juna ,ganin haka yasa maryama sake had’e ranta tamau dan bata son ya kawo mata wani sabon rainin hankali ko rainin wayo tare da d’aga masa farar takardar hannunta tana nuna masa alamun ta gama .” kina son ki zamo matsalata?” yayi mata tambayar yana tsareta da tsumammun idanunshi ahankali ta girgiza masa kai tana cewa “bazan ta’ba son na zamo matsalar kowa ba ,abinda kasani kenan sir , kuma wannan shine iya abinda zan iya yi . shiru yayi kawai yana ajiye qarshen bakin sigari acikin wani dan qaramin kwanon tangaran .”sannan ya cigaba da dubanta tare da cewa “tsarin yanayi rungumar bai min ba kasancewar babu remotic .“
ta kalleshi da tarin mamaki akan fuskarta lip’s dinta take matsawa alamun magana take son tayi masa sai dai ta kasa furta komai dan zuwa yanzu gaba d’aya a firgice take dashi .”
Yanayin zamansa ,yanayin kallonsa ,yanayin maganarsa duk sun canza dan hatta kwayar idanunshi sun canza kala yayinda shirunta ya
bashi damar kallonta son ranshi dan ko son kifta
ido ba yayi ,ga wani kalar murmushi da yake wanda shi karon kanshi bai san yana yi ba sosai itama ta shagala da kallonsa amman ita kallo ne dake tattare da tashin hankali da tsoro ,ahankali ya matso kusa daita ya hura mata iskar bakinsa da sauri tayi kasa da kanta tana jin wata irin fargaba yayinda gabad’aya ilahirin jikinta rawa yake .zuciyarta ta cika fal da matsanancin tsoronsa ,jigun sukayi daga shi har ita barin maryama wacce komai ya tsaya mata cak ,yadda bai sake yin mgn ba itama bata ko motsa ba daga inda take zaune sai dai kowannen su da abinda zuciyarsa ke saqawa acikin zuciyarsa .”
zurfa goshinta ta share tana kallon mr ata tace “sir ko zan iya wucewa “?numfashi ya sauke da kyar yana soka yatsan hannunsa a gefen bakinsa.”
“ kamar yace mata “a’a sai kuma yayi mata alama da hannunsa dan ya tabbatar muddin yace zai yi taurin kai zata maimata masa abinda tasaba ,dan yana ji kuma yana gani zata wuce abunta ta barshi zaune ” ahankali ta mike ta biyo ta raba gefensa zata wuce har jikinta na zozon jikinsa saurin d’auke numfashi yayi yana jin kamar ta jona masa wutar lantarki ne
ta juya a natse ta soma daga qafafuwanta da kyar gyara zama yayi tare da ware qafafuwansa yana bin every step of her tafiyarta kad’ai aka bar mutun dashi wani abu ne mai tsayawa arai bare akai ga samunta gabad’aya .”ahankali ya dinga bin kugunta da wani mayataccen kallo cikin salon magana yace “wannnan kugun zai sha wuya a hannuna domin kuwa bazan ta’ba saurara masa ba haka zalika wannna bakin rashin kunyar zai sha kissing har sai yayi kukan neman sausauci.”sai bayan la’asar maryama ta soma shirin tafiya gida taso kwarai ta sake yi masa magana akan sabon aikinsu amman sai taga gara kawai ta rabu dashi idan ranar ta kusa zata sake nemansa da maganar wata killa zuwa lokacin ya amince suyi .” wucewa tayi abunta tana tunani hali irin na mr ata “tsarin yanayi rungumar bai min ba kasancewar babu remotic girgiza kai tayi tana murmushi.”
******
Da daddadre da misalin karfe takwai yana zaune atsakiyar gadonsa hannusa rike da remut ya canza channel zuwa breaking news yana kallo sai dai hankalinsa baya wajen kallon labarai yana gurin tunanin yadda zai mallaki maryama ne cikin sauki har sanda mami ta shigo hannunta rike da cup din coffee'nsa bai sani ba ta tsaya shiru tana kallonsa tana nazarinsa kafin ahankali ta kira sunansa "adamcy "! yayi firgigib ya dawo haiyacinsa yana kallonta "kar’bi !" ta mika masa cup tana cewa "wai meye matsalarka madadin naga lapto agabanka kana Kan aiki amamn kayi busy kallo kana tunani ".
"na gaji ne sweetheart !"ba maganar ka gaji bane what's wrong with you?" ta tmbyesa tana kallonsa " me kake tunani yanzu koda yaushe cikin tunani kake , meye matslarka"? babu !"ya fad'a atakaice yana kai cup bakinsa "akwai gskyar ko damuwar da zaka iya boye min duk yadda mami tayi dashi yaki fad'a mata damuwarsa abinda bai saba mata ba Kenan ya ajiye cup din hannunsa ya koma Kan kujera ya zauna ya dafe goshinsa."
ta dawo kusa dashi ta zauna" abinda kake min wani lokaci yana damuna "ya d’ago ya kalleta kawai kuma zai iya kashe ne tun kwanakina basu kai ba .”ta fad'a tana dubansa shi fa duk saboda wannna yarinyar maryam ne yasa baya jin zai iya fad'a mata damuwarsa domin dai ya fad'a yaga mafarkinsa a yanzu zai iya janyo masa damuwa bugu da qari shi karon kansa bai san takamaiman makomarsa ba ta yaya zai fito da damuwarsa yana cikin zance zuci ya cigaba da jin maganarta "idan ka kamu da soyayyar yarinyar nan dake aiki a qarqashinka fine let me know?" ya sake d'agowa ya kalleta atsanake amman still bai ce mata komai ba dan ba maganar kamuwa bane magana ce tsananin qauna kuma jin zai iya hakura daita duk runtsi duk wuya sai ya mallaketa kuma acikin wannan lokaci zai organizing wasu mutane dabam su nema masa aurenta ."
“Adamcy boye abu acikin zuciya yana saurin cutar da dan Adam,sannnan boye abu shi da kyau a zuciya yana da kyau mu samu wadan da zamu dinga sharing secret dinmu dasu. wannna shine karo na farko da ka boye min damuwarka .dan haka zaka iya tsintata cikin damuwar datafi taka .sam baya ma jin maganr da mami take masa dan hankalinsa gabaday baya ga mami yana ga yadda zai mallaki maryama ne, tunanin hanyar da zai bi ya bayyana mata matsayinta da kuma su wa ya kamata ya saka zuwa neman aurenta da yake bukata arayuwarsa yake .
Mami ta kallesa taga hankalinsa da natsuwarsa baya gurinta shima wannan ne karo na farko da take masa magana hankalinsa baya gareta ba dan haka ta mike ta fito daga d’akinsa sai dai zuciyarta ta tsayu ne akan danta ya kamu da son wannan bazawarar yarinyar ita ko zata so tagansu tare domin kasancewarsu waje d’aya zai tabbatar mata da zarginta “bazawara!”zuciyarta ta furta hakan a fili .”
Yau ma kamar jiya maryama bata qaraso gida ba sai daf da sallar isha’i a gajiye ta shiga bangaren ummah tayi mata sannu da gida “sannu maryama ya aiki ?”naunauyen ajiyar zuciya ta sauke tana cewa “ummah aiki da mr ata sam babu dadi amamn a haka zamuyita lalla’bawa ,ta fad’a tare da shigewa d’akinta murmushi umma tayi tace “ke dai da wannan mutun allah ya d’auraki akanshi idan ba haka ba bazaki ji dadin aiki dashi ba “maryama tana shiga daki ta fad’a bayi tayi wanka tare da dauro alwala ta fito daure da towel orange tana goge sansar jikinta byn ta gama ta d’auki terry dream’s ta feshe ilahirin jikinta sannna ta zura doguwar riga baka ta gabatar da magrib da isha’i dan zuwa lokacin an kira sallah byn tayi sallama ta ‘daga hannuwanta zuwa sama ta soma addua ta kira allah da sunan daake kiransa yake amsawa, kuma idan an rokesa dashi yake amsawa “allahumma as alukal bi anna lakal hamda laila ailla anta ,wahdaka lasharika laka ,al mannan ya badi’us-samawati wal ardi ya zal jalalu wal ikram ya hayyu ya qayum inni as alukal janna wa auzubika Minan nar har da mr ata tasanya cikin adduarta allah ya shiga tsakaninta dashi .”
Bayan ta kammala ta mike tare da daddumar sallah tana nadewa ta fito zuwa parlour inda umma take zaune ta d’auki jakar aikinta tana cewa “umma zan shiga wajen aunty idan goma tayi baki ganni ba ki rufe gida “to shikenan abinci fa bazaki ci ba ?ko zaki turo habib ya kar’ba miki ?”ko da yake ba abincin da kike so nayi yau ba .maryama tayi murmushi tana tambayarta “umma me kika dafa ?”tuwon samoviter ne da miyar kuka nan take maryama ta kwa’be fuska dan gaskiya bata qaunar tuwo da duk wani abu daya zamo loma bata só sai dai tsananin yunwa tasa taci dole “umma bari naje Allah yasa aunty ba tuwon tayi ba itama ”to shikenan yasa ki samu abincin da yayi miki idan itama tuwon tayi ki aiko habib ko ki kirani sai na dafa miki ko indomi ce “shikenan umma nah na gode .”tasa kai ta fito ta wuce part din mahaifiyarta inda ta samu abinda take so .”
Jollof din rice and beans aunty tayi wanda yaji busashen kifi da vegetable taci sosai kasancewar tana matukar so duk wani abu da zaa sarrafashi da wake bayan ta gama cin suka shiga hira da aunty da habib tana aiki habib ya dameta sosai da tambaya “daman kusan hayaniyarsa ke hanata zama a bangresu idan tana da aiki dan baya barinta tayi “heartbeat dan Allah ki bar aikin nan muyi hirarmu ta tsaida abinda take ta zuba masa ido “ance wannan mai kamfanin AGC din yana matukar takura miki dayawa ?Injiwa yace maka yana takura min ?yayi murmushi yana shafa fuskarsa “abakin lancin kanin yusura naji maryama tayi murmushi dan tasan tabbas a bakin yusura yaji “dan Allah ki bari naje naci miki ubansa mana ?yayi maganar cike da zolaya maryama ta zaro waje duk da tasan da wasa ya fad’a,can kuma kwashe da dariya “ai kuwa daga ranar na daina aiki dashi bayan yasa anci masa ubanmu,after dad ai wannan mutumin ya wuce da tunaninka shegen kanshi ne duk abinda mutun yake ji dashi zai sauke masa shi cikin isa da miskilanci shiyasa yanzu har cikin addua nake saka shi .”
“Ai kuwa kin kyautawa kanki gara ki dinga hadawa da addua kuma ki dinga binsa ahankali banson a cutar min dake “inji cewar aunty wacce ta mike ta nufi hanyar d’akinta ta barsu suka cigaba da hirarsu maryama lumshe idanunta ta soma tattara takardun zanen dake watsewa akan kujera ta mike tsaye tana cewa “gara na tattara na koma inda na fito dan bazaka barni nayi aiki ba ta leka dakin aunty tana cewa "aunty zan wuce part din umma "a can zaki kwana mu kulle gida ?eh ! aunty a can zan kwana halan habib ya hanaki aiki? maryama ta rausayar da kwayar idanunta kawai “to shikenan allah ya tashemu lafiya Ameen ta fad'a tana juyawa tare da kiran habib yazo ya rufe gida ta wuce part din umma,ta iske kofa a bude dan haka turawa tayi kawai ta shiga inda iske umma tana massaging kafafunta tana runtse ido da sauri ta qaraso ta ajiye jakarta ta karbin man aboniki dake rike a hannunta tana cewa”ummah sannu bari nayi miki “to maryama nã gode allah yayi miki albarka “Ameen umma maryama ta fad’a tana mai tsananin jin tausayin umma aranta kuma tana tsanani qaunarta kuma zata kasance daita muddin rai zata maye mata gurbin komai arayuwa .”
Ahankali ta dinga massaging qafafunta tana mata sannu umma tayi shiru tana jin tsananin qaunar maryama aranta amman wani lokacin sai ta dinga jin tamakar zata juya mata baya wata rana ,domin d’an wani da uwar wani sai Allah duk da dai tana mata kyakkyawan zato haihuwa na dadi amman haihuwar da tafi kowace dadi itace haihuwar diya mace tasan koda sadam dinta yana raye watan wata rana sai taji kewar rashin haihuwar diya mace sheshekan kukan umma ne yasa maryama ta bar abinda take ta dago a gigice tana cewa “umma lafiya ?” ai sai umma ta fashe mata da kuka hankalin maryama yayi matukar tashi duk ta rude ta sake bajewa daga tsugunon da take a gaban umma ta riko hannunta cikin nata itama idanunta sun cika da hawaye dan haka kawai bata ta’ba ganin umma tana zubar da hawaye ba lallai duk abinda ya sakata zubar da hawaye abu ne mai girma “dan girman allah umma kiyi hakuri ki daina kukan “ko kin tuna da yaya sadam ne ?”
Umma ta sauke wani ajiyar zuciya tana damke hannun maryama cikin nata cikin muryar kuka ta soma magana “ba akan sadam bane maryama”to akan menene haka umma kike min asarar hawayenki ?”ina jin araina kamar wata rana zaki gujeni alhalin bani da kowa daga Allah sai ke maryama zuciyata tana tsananin qaunarki maryama rashin sadam ya tabani matuka amman rashin ki shi zai fi komai damuna “numfashi da naunayen ajiyar zuciya maryama ta sauke sannan ta yunkura ta mike ta zauna kusa da umma tana goge mata hawaye tana cewa “a gsky umma baki ta’ba min abinda ya ‘bata min rai ba irin wannnan lokacin ba domin baki d’aukeni kamar yadda na d’aukeki ba nan take umma ta soma girgiza mata kai “umma nifa yar halak ce kuma nasan hallaci kuma zuciyata tana qaunarki fiyye da tunaninki bana tunanin akwai wata ranar da ni maryama zan juya miki baya ba duk runtse duk wuya umma nah tare ban ta’ba jin cewar bakece kika kawoni duniya ba zan kasance dake muddin rai mutuwa ce kawai zata rabamu dan Allah ki daina wannan tunanin ki daina tunanin zan gujeki ni amarki ce haka kema amanata ce ta qarasa maganar tana zubar da hawaye .”
Umma ta rungume maryama ajikinta umma kuka maryama kuka aka rasa wanda zai rarrashi wani acikinsu sai dai har ga allah umma ta samu natsuwar zuciya domin bata son abinda zai nisantata da maryama idan ba aure bane .kuma a kullum tana mata fatan samun miji na gari sun d’auki sama da mintuna talatin suna kuka sannna umma ta soma shafa bayanta tana cewa “kukan ya isa haka maryama kiyi min afuwa yau ummanki ta sakaki kuka sheahekan kuka kawai maryama take tana narkewa ajikin umma “dan allah umma ki daina wannan tunanin aranki “in sha allahu maryama bazan sake ba kuma na gode matuka da qaunarki allah ya barmu tare allah yayiwa rayuwarki albarka Allah ya azurtaki da samun miji na gari wanda zai kular min dake ya kuma rike minke amana addua sosai umma tayita mata tana shafa bayanta har maryama ta samu natsuwa .”
Parlour’n ya d’auki shiru har na tsawon minti goma sannna umma tace “tashi muje ki kwanta gobe zaki office ta fad’a tana mikewa tare daita ajikinta ta d’aukar mata jakar aikinta da d’ayan hannunta suka nufi d’akin maryama umma na sake kwantar wa maryama da hankali ,ta ajiye mata jakar akan table sannna ta kwantar daita akan katifa ta zauna a gefenta tana tofe mata jiki da addaua tana cigaba da shafa bayanta tamakar wata yarinya qarama maryama tace, umma kije ki kwanta ki huta kema “to maryama sai da safe, Allah ya tashemu lafiya ta mike ta fito ta shiga dakinta ta hau Kan gadonta ta kwanta “.bayn fitar umma da kusan awa uku amman maryama ta kasa bacci sai faman juyi take kwance ta mike zaune ta duba wayarta taga lokaci ya wuce sosai dan d’aya ta kusa jin idanuwanta basa jin bacci ta janyo jakar aikinta ta cigaba da aikinta ahankali ahankali ta dinga jin kamar motsin shigowar mutun tayi tsam da ranta tare da dakatar da aikin da take na wani lokaci ta kasa cigaba aikinta ta kasa kunneta sosai ko zata ji takun tafiyar mutun sai dai bataji komai ba har tsawon wasu mintuna dan haka ta maida hankalinta kan takardar gabanta ta cigaba da aikinta .sai dai haka nan ta dinga jin zuciyarta na tsinkewa tare da jin mummunar faduwar gaba .”
domin ta samarwar zuciyarta natsuwa ta ajiye takardar dake Kan pillow ta yunkura ta tashi ta sauko daga Kan gado ta soma tafiya a hankali cikin sand'a har ta fito zuwa babban falon gidan ta tsaya shiru tana kallon koina ta cikin hasken da bai gama haskaka falon ba, ta kai idanunta ga kofar shigowa taga kofar a kulle take dan haka ta sauke numfashi ta koma ta cigaba da aikinta bayan wasu lokaci ta soma jin bacci dan da kyar take iya bude idanunta tashi tayi tana hamma tare da cewa " gashi ina tsananin jin bacci gashi banga ma aikin dake gabana ba ."
ta fito zuwa falo ta nufi kitchen ta dauko dan qaramin prepand mai zurfi ta zuba ruwa kadan dan tea take bukata ta daura akan gas ta kunna ta tsaya har sai da ruwan yayi zafi ta hada tea ta zuba a cup ta fito tana sha a ahankali ..qarar faduwar abu taji ta daidai bangaren d’akin yaya sadam ta tsaya cak tason ta qara ji amman shiru .”
sai dai batayi tunanin komawa dakinta ba ta fara tafiya a hankali zata dakin inda taji motsin qarar faduwar abu har tayi taku biyu sai kafarta tayi tuntube da takalmin aunty hassna ta sauke numfashi sannan ta tsuguna ta dauka tana cewa "bansa sai yaushe aunty hasana zata daina shigowa da takalmi har parlour' ba, idan ya zama dole ai akwai takalmin yawo a parlour ba irin wannan ba da zai cire maka farce , takalmi Kmr katako gashi abun haushin ma sai tazo da takalmi amman idan ta tashi wucewa ta sai ta barshi ta kama gabanta haka .ta qarasa inda suke ajiye takalma ta ajiye nan ya kamata da irin wadan takalmar wannan abu ya dauki hankalinta yasa bata shiga dakin ba ta koma dakinta ta zauna ta tankwashe kafafaunta ta dauki takarda wayarta taji ta dauki qara ta lalubo wayar ta manna a kunnenta"okay yusura nima ina Kan aiki bazan kwanata ba sai na kammala byn ta kammala ta ajiye wayar wani kiran ya shigo taja tsaki waye kuma adaidai wannnan lokacin ? ta lalubo ta dauka tana duba number bata san number ba kamar bazata dauka amman sai tayi tunanin ko emergency call ne ta dauka tana cewa "hello !
Daga can bangaren taji ance "maryama hussein ce maaikaciyar AGC company “yes sir okay gobe muna bukatar ganinki a kamfanin da misalin karfe bakwai daidai ana gama fadar haka akayi discounting din kiran tayi shiru tana tunanin wanda ya kirata wannan dai ba muryar mr ATA bane ta lumshe idanunta tana cewa babu mamaki ko cikin yan'uwansa ne wani Ke bukatar yin aiki daita dan haka bata sake yunkurin tashi ba gara ta qarasa kafin wani aiki ya shigo mata gobe tana hamma tana aiki har ta qarasa ta kwanta da zumar tayi bacci amman ta kasa runtsawa har aka kira sallah ko byn daaka idar ma bata iya komawa ba dan haka ta yi wanka tayi shirin zuwa aiki ."Karfe bakwai daidai a AGC company tayi mata koda ta shigo ma'aikatan babu wasu mutane sai tsirarrun mutane dake kai kawo da securities da masu share maaikata ta kama hanya zuwa sama nan ma dai bbu kowa koina shiru kai tsaye office dinsu ta shiga tana sauke numfashi ta cire jakar kafadarta ta ajiye akan table ta ciro takardun zanenta tana dubawa ta sake duba agogon hannuta .”
“gsky yau nazo da wuri sosai ko da yake na huta da complain din madam some kullum sai tayi complain akaina to gashi itama bata zo ba tukun.” ta fad'a tana sauke numfashi tare da tuna yadda take mata idan tazo late "Mis maryama hussein why are you always late ?ta fada da irin muryarta ?tana lumshe idanunta tare da saka hannunta cikin aljihun doguwar rigar dake jikinta yayinda hannunta daya ke tokare da table din gabanta exactly yadda mr ata shi kuma yake yi har da qara taku biyu ta tsaya Kmr yadda yake yi .murmushi ya bayyana akan fuskarta sakamakon tuno mr ata datayi tana jin wani iri ajiknta shi kuma matsalarsa always complain “baki daukar aikinki da mahimanci a tunaninki ke din professional ce bana bukatar mutane da basa daukar aikinsu da daraja kullum bakya son zuwa aiki da wuri , kullum da excuse din da kike kawao wata rana zan dakatar dake aiki ta fada a fili .kamar ance ta juya bayanta tana juyo kawai taga mutun tsaye ya jingina jikinsa da kofar shigowa idanunsa kyam akanta sanye cikin kanana kaya irin shigar jiya sak yayi sai dai kalar kayan dabam yana rike da farin glass dinsa,yayinda hannunsa daya na soke cikin aljihun wondonsa kmr koda yaushe yayi shiru yana jifan da wani irin mayataccen kallo mai tsantsar kashe sansar jiki .”
Mmn sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 20
A matukar rikice ta juya tana mai had'e hannu wanta waje d'aya tana jin wani irin mummunar fad'uwar gaba mai tsanani "gabad'aya yanayinsa yayi matuqar tsoratata. a bangaren mr ata kuwa wani sanyi dadi ne ya mamaye sansar jikinsa sakamakon d'aura kwayar idanunshi da yayi akan sanyi idaniyansa da sanyi safiyar nan , wani tunani maryama tayi wanda yasa ta juyo da sauri tayi taku biyu ta tsaya kusa dashi muryarta na rawa tace "good morning sir"! bai amsa mata ba ya qarasa shigowa cikin office din sosai yayi kmr yadda yake
yi a duk sanda ya shigo hannunsa d'aya cikin aljihun wondonsa yayinda d'ayan hannun kuma ya d'aura akan table . shiru tayi tana ciza harshenta kamar tayi dariya dan wannan salon nasa yana matukar burgeta kuma yana sakata jin nishad'i acikin ranta sai dai ganin yadda yayi mugun had'e rai fiyye da kullum dan fuskar nan tashi sam babu annuri kirki yasa tayi maza ta sanyawa jikinta natsuwa tare da lumshe idanunta na second biyar sannan ta bud'esu fess akan kyakkyawar fuskarsa ta sake gaishesa a karo na biyu ". “good morning sir ?!
“still shiru ne ya sake biyowa baya batare daya kalli inda take tsaye ba "maganar me kike yi ?taji saukar muryarsa ta doke dodon kunnenta,a natse ta kallesa qirjinta na dokawa da qarfin gaske tace"ba maganar komai nake yi ba "!tsumammun idanunshi ya waigo ya kalli inda take tsaye har lokacin tana wasa da yatsun hannunta ,kana kallonta kasan tayi kama da mai laifi domin ko a iya haka ma rashin gaskiyarta ta nuna ,ya motsa lip's dinsa ahankali yace "ya zakice ba maganar komai kikeyi ba byn da na shigo naji kina cewa wani abu me kikeyi cewa ?"nan take hantar cikinta ya kad'a ilahirin jikinta ya kama rawa.
sosai ta firgita "kar dai yaji abinda ta fad’a?"inna lillahi!" ta furta acikin ranta ,zuciyarta cike da matsanancin tsoro take kallonsa."ya gyara tsayuwarsa sannan ya fuskanceta tare da zura hannuwansa duka cikin aljihun wondonsa ya tsura mata tsumammun idanunshi masu firgitarwa “maryama kince wani abu, abinda kikace nake son na sani ".
muryarta cike da in ina tace "ina..ina.. dai magana da zuciyata ne yayi shiru still kwayar idanunshi na yawo a sansar jikinta wanda ke qara saka zuciyarta shiga rud’ani bayan kamar second goma ya sake motsa lip’s dinsa " amman kamar kina raact kmr ni ?da sauri ta fito da shanyayyun idanunta waje tana cewa "no no sir me yasa zanyi haka?" ni sam ban yi haka ba kawai dai ..."sauran design's din dana baki aikinsu last week sunyi ready "?ya katseta ta hanyar fad'ar haka yana cigaba da kallonta kamar zai cinyeta, shiru tayi ta kasa cewa komai dan tuni ta ajiyesu a gefe tana kan new desing's din da zasu gabatar ne ,wani kyakkwan shu'umin kallo ya d'auketa dashi wanda yasa take tsigar jikinta d'aya bayan d'aya suka fara mikewa tayi saurin cewa "no basu yi ready ba sir "ko zan iya sani dalili ?."tayi shiru qirjinta na lugud'en bugu da qarfi .”
"wai mai yasa kika rainani har haka ?"sake fito da idanuwanta tayi sosai tana kallonsa zuciyarta na sake shiga tashin hankali "na shiga uku ta fad'a acikin ranta “wallahi ta d'auka bazai nemesu da wuri ba yasa ta tattara ta ajiyesu "yaushe zaki fara bin umarnina?" yayi mata tmbyr yana qara taku d'aya zuwa gareta "yaushe ne idan na baki aiki zakiyi min shi cikin dad'in rai batare da 'bata lokaci ko jayayya ba "?ya qarasa maganar yana sake yin taku d'aya ya matso daf da inda take sosai yana mata wani wahalallen kallo." tayi saurin ja da baya tana furta kalmar "inna lillahi !”yau na bani me ya kai ni shiga wani aikin bayan ban qarasa masa nashi ba "?lallai maryama kin tarp match dan kin fara wuce limit dinki ,amman duk abinda nake ai ina yi ne domin shi ,ina yi dan na wanke masa zuciyarsa akan kuskuren da nayi masa, ya sake matsota sosai "ina jinki ki bani amsar tmbyoyina "saboda kin rainani yasa kike aikata min haka ko?
takure jikinta tayi waje d'aya tana wata irin kyarma tace "wayyo allah tsigar jikina " gbdy ta kasa motsi duk ta rikice sakamakon kusancinsu da yayi yawa dan har suna iya jiyo bugun zukatansu da saukar numfashinsu "wannan shirun ma kanshi cikin rainin da kika min ne ko ba haka ba ?"da sauri ta girgiza masa kai "alamun a’a!”idan ba haka bane taya ina magana kina jina amman kiyi min shiru?" kayi hakuri sir sabon aikin dana nemi izininka na fara "wa ya sakaki ?"wa ya baki izini ?yayi mata tambayar ajere yana sauke mata zazzafan numfashinsa a fuskarta da wuyanta ,ta firxgo numfashi da kyar sannan ta d’ago ta kallesa zuciyarta na karkarwa “banace bana supporting ba ?"kayi hakuri kace but .."but what ?wannan karon a matukar tsorace yayi maganar wanda yasa tasa hannunwanta duka ta toshe kunnenta tana durkushewa qasa a gabansa.”
wani dogon numfashi ya sauke yana binta da kallo ganin yadda ta gigice ta rikice ta mugun bashi dariya kasa rike dariyar yayi har sai data bayyana akan fuskarsa ,inda ya kamo gefen lip’s dinsa na kasa ya fara cizawa ahankali ahankali,suna cikin wannan halin sai ga oga amar tun daga nesa ya hango bayan mr ata kuma nan take jikinsa ya bashi maryama ce durkushe a gabansa domin dai yayi imani babu wannan macen a duniya da ata zai tasata gaba irin haka ."Jin shiru yasa maryama d'ago idanunta sha'be sha'be da ruwan hawaye ta zuba masa tana “kayi hakuri nayi kuskure sir,amman zan ‘bata komai na aikin ,haka zalika zan dakatar da kowa kuma in sha allahu gobe zanzo maka da desing’s dinka .”ta qarasa maganar wasu hawaye masu zafi suna gangarowa akan kuncinta adaidai lokacin oga amar ya samu qarasowa wajen. ya tsaya yana kallonsu da bayyana nen mamaki akan fuskarsa kafin daga bisa yace "ya haka ata ?".
Mr ata ya juyo ya kallesa alokacin da oga amar ya bud’e baki zai sake cewa wani abu nan take mr ata yaja hannunsa suka fita daga office din dan yasan zai iya masa ' baran 'barama a gaban maryama shi kuma bai shiryawa hakan ba tukun, yana da plan akanta suna shiga office dinsa oga amar yace "ata ka dinga jin tsoron Allah fa “me nayi?!” dan ubanka ya kake tsoratar da yar mutane kaga yadda yarinyar nan ta fita haiyacinta tana zubar da hawaye wallahi zaka ballowa kanka ruwa ,kai yanzu soyayyar ma sai ka nuna mata seniority?"mr ata yayi bayyana nen murmushi mai d’an sauti kad'an abinda bai ta'ba yi ba kenan a tsawon rayuwarsa sannan yace "yarinyar nan wallahi bazaka ta'ba gane rashin kirkinta ba bugani take kamar ta samu kwallon kafa ga rashin bin umarnina ka shigo min da kaidodin na babu gaira babu dalili ." karya kakeyi ata " kai dai wallahi mugu ne sam maryama bata haka kawai dai kayi niyyar kasa yarinyar mutane kuka ne da sassafe "ai daman nasan haka zakace tunda kai ma sonta kake yi ."
Oga amar ya kyalkyace da wata dariya yana kaiwa kafad'ansa duka "gsky ata ka gama dani amman kasani da son maryama nake da tuni an wuce gurin da sai dai ka bud'e idanunka ka ganta a gidana a matsayin matata "da kuwa anyi burouba!"ya fad'a yana zabga masa wata qatuwsr harara "sorry friend maryama taka ce kai kad’ai daman kace babu macen da zaka bi sai ita kuma naga hk sauran ka zama bita zai zai ko da yake shima ka fara zama " anji cewar oga amar "ai soyayyar yarinyar nan tana wujijjjiga rayuwata ,ni yanzu kiran da nai maka nace mu hadu anan shawara zamuyi ina son naje nema aurenta "
“waya fada maka barno gabas take ,suka kwashe da dariya "suka samu waje suka zauna alokacin da karfe takwas ta buga wanda zuwa wannan lokacin wasu daga cikin maaikata sun fara zuwa "ina jinka abokina wannan labari yafi kowani irin labari dadi domin ina matukar son na g maryama a qarqashinka ."
Mr ata ya numfasa kana ya cigaba da magana a natse "ina son naje neman aurenta koma nace ina son tazama mallakina acikin tsukukun lokacin nan dan sai nafi samun kwanciyar hankali idan na aureta ahankali kuma sai na shigar da soyayyata sai dai kasan wani abu bana son sweetheart da kowa nawa su san da wannna auren zai tsaya ne a tsakaninmu dagani sai kai ita kanta yarinyar bana son tasani yanzu “ya qarasa maganar tare da yin shiru ya zuba ma oga amar idanu yana son yaki me zai ce "Ko me yasa ka zabi kayi haka ?bayyana maryama a halin yanzu zai iya janyo min abubuwa da yawa. abu na farko idan sweetheart da sauran yan’uwana suka san mafarkina ce zata fuskanci mummunar tsana daga garesu kasamcewar naki zama da zabinsu abinda ka rigada kasani ne bazan d'auki raini ga matar danafi so ba haka zalika bazan wulakanta yanuwana da Mahaifiyata akanta ba,shiyasa nake son na aureta a boye ,muyi rayuwarmu dagani sai ita da yaran da zata haifa min ".
numfashi oga amar ya sauke "amman kace itama maryama din baka son tasani ?"a yanzu ba amman daga baya ai dole zata sani idan lokacin da ya kamata tasani yayi, zan aureta a yanzu na dinga janta ajikina ina d’an rage zafi "tunda ita shasha ce da zata yarda ka dinga ta'bata batare data san meye matsayinta ba "wannan kuma matsalarta ce tunda ni nasan matsayinta ai shikenan."kai dai wallahi mugun jarababbabe ne “sosai kuwa number one ma ni kad'ai nasan irin dauriyar da nake akanta wallahi amar ina da mugun karfin shaawa akanta idan shaawarta ta taso mun kwana nake gabana a mike duk na rasa yadda zanyi ,inga ya maka jijiya ta bata kwanciya har sai asuba tayi wata rana ma haka zan yini kaga gara nasan abunyi.” naunayen ajiyar zuciya oga amar ya sauke yana cewa "ni dai gsky kayi tunani sosai akan wannan raayi naka gara ka fahimtar daita idan yaso sai abar maganar daga kai sai ita sai kuma ni da zan zamo sheida saboda halin rayuwa ".
“kai ma kazo da magana mai kyau amman kasan wani abu ?oga amar ya girgiza masa kai "bazan iya fahimtar daita da bakina ba "akan wani dalili ?i don’t know,kai dai kace tsoronta kake ji “wani irin tsoro kuma amar yarinyar da loma d'aya zanyi daita na gama daita ni kawai damuwar sweetheart ne data yanuwana ce banaso, sun dade suna tautaunawa a qarshe suka ajiye ranar da zasuje su samu baba gali ."qarfe goma daidai oga amar yayi masa sallama ya wuce yayinda maryama ke ta faman kuka surayya wacce ta shigo ta isketa tana kuka ta fara rallashi tana tambayarta dalilin kuka sai dai bata ce mata kalallahu ba dan haka taje ta kira yusura itama dai tmbyrta dalilin kukanta tayi a qarshe tace "ko dai mr ata ne ?"maryama ta gyada mata kai alamun eh me ya had’aki dashi ?tayi shiru dan bazata iya fad'a ba ,da kyar yusura ta rarrasheta ta tsaida sheshekar kukanta tana cigaba da tmbyeta "aikin banza kawai kuna damun kanku akan wannan figaggar yarinyar kuma tunda kukaga tayi shiru har yanzu taki cewa da ku komai saboda munafunci da shegen zurfin ciki irin nata ai sai ku rabu daita haka ".sultana dake tsaye a bakin kofa ta fadi haka tana mazurai yusura kam ta yarda maryama tana da zurfin ciki sosai "ban wani d'auki lokaci mai tsawo daita ba amman na karanci maryama din nan tana kafiya da zurfin ciki maryama ta kalleta da idanunta da suka canza kala "kina kallona kamar karya na fad'a akanki “tana gama fadar haka maryama ta d'auki jakar aikinta ta rataya a kafad’anta ta fita ta bar office din da idanu suka bita da kallo ."
Har qarfe biyu da wasu mintuna maryama bata dawo office ba, yayinda mr ata ya shiga office din yafi sau babu adadi amman bai ganta ba ya yi mamakin inda ta shige har zuwa wannna lokacin dan ya lura tun shabiyu bai sanyata acikin kwayar idanunshi ba kuma shi bai ga fitarta ba dan hk ya kira layinta bai shiga ba ,hankalinsa ya dan tashi ya kira madam some zuwa office dinsa bayan ta shigo ya kalleta atsanake yace "ko maryama tana ina ne ?na ganta dazu da safe ,”yanzu nake magana "eh gsky bansan inda taje ba amman yau din dai kamar bata da lafiya dan naga yanayinta wani iri kamar ma tayi kuka amman naga su surayya suna ta rarrashinta nafi tunanin ko akwai matsala daga gidansu ne sir "numfashi da ajiyar zuciya ya sauke atare yana cewa "you can go "!ta juya a natse ta fita .”
Ya mike ahankali ya nufi d’akin da camerar cctv suke masu kula da bangaren wajen suna ganinsa suka mike cike da girmamawa domin dai duk lokacin da zasu ganshi da kansa abu ne mai mahimanci ya kawosa ,mr ata ya zauna a mazauninsa na musam man wanda an tanadi wajen ne dan shi kad’ai camera mai kula da bangaren office dinsu maryama zuwa first flow ya bukaci gani tukun, da sauri suka fara tariyo masa wanda zuwa wannnan lokacin ya hade hannunwansa duka waje d’aya ya tokare habarsa yana duban screen din tv ahankali ya fara kallon d’aukar yau inda mutane da suke shiga da fita har yazo kan shi da maryama yayi shiru yana kallon shi daita sosai yaga yanayinta cikin tsananin damuwa d’aukar tayi gaba zuwa inda su surayya da yusura ke tsaye akanta da sanda sultana tayi mgnrta ta juya ta bar office din kuma at the same time alokaci maryama ta mike tana goge hawaye ta fice daga ma’aikatar gabad’aya .
"me yarinyar nan take nufi dashi ?"yasan duk akan abinda ya faru ne da safe ta kama hanya ta wuce gida abunta ahlin lokacin tashi bai yi ba yayi kwafa yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa ."bayan ya gama ganin komai ya mike ya fito daga office din cike da jin kai ya koma office dinsa ransa a matukar bace dan ganinsa maryama tayi mugun mugun rainashi babu wani maaikaci ko maaikaciyar da zata masa haka ya d’auka itama dan matsayinta ne yake d’aga mata kafa yaja tsaki yana rike kugunsa da hannu d’aya,bangaren maryama kam kai tsaye gidansu ta wuce abunta, ta zarce zuwa bangaren aunty tayi kwanciyarta akan doguwar kujera tare da kashe wayarta nan da nan bacci ya dauketa sakamakon daman daren jiya bata runtsa ba ."
******
Qarfe takwas na dare da mintuna ashirin mr ata ya tako cikin parlour'n Mami wanda babu motsin kowa sai na na'urori da kuma hasken qwayaye, samanshi ya nufa kai tsaye yana furzar da hucin iska daga bakinsa yana tuno gamuwarsa da maryama d'azu da safe sannan zuciyarsa na tafasa akan barin office da tai batare da neman izininsa ba gamuwarsu a gobe kawai yake jira dan lamarinta na matukar 'bata ranshi ya tabbatar da cewa ta tafi ne dan musguna masa ta nuna masa iyakar shi wanda hakan ya sake tabbatar masa da bai isa daita ba kamar yadda ya isa da duk wanda ke qarqashinsa ,shima kuma yana nan akan nashi qudurin da raayi bai ga abinda zai sanya shi daga mata qafa ba koda kuwa suma zai dingayi akanta ko mutuwa zai yi sai ya juyata ya tankwasata ya laddatar daita, qarfin soyayyarta bazai sa ya juri iskanci ba haka zai aureta ya kasa zama tsayayyen nmj acikin gidansa "never maryama dolenki ki bini sannan ki zauna lfiya."
Tsab tsab ya iske dakinsa koina neat sai kamshi turare yake wannan kuma yasan aikin sweetheart dinsa ne ita ke tsayawa akan masu gyara masa daki
A natse ya qarasa bakin gado ya soma fidda kayan jikinsa byn ya gama cirewa bandaki ya shige yana niyyar hada ruwan wanka,yaga an had'a masa tsayawa yayi cike da shakku yana tunani ta ina aka samu haka? , cikin kokwanto ya sanya hannunshi cikin ruwan, anya ba jinnu ke neman yi masa wasa da hankali ba,dan tun da yake sweetheart bata ta'ba sawa an masa haka ba ,share mamakinsa yayi yayi wankan ya fito ya saka kayan shan iska farare sol ya fito yana taka step da kyar turus yayi sakamakon ganin maryam da sweetheart tare da aunty shahida zaune suna magana ganinsa yasa duk sukai shiru ya qaraso ya gaishe da mami da aunty shahida duk suka amsa masa ".maryam tayi karfin halin gaishesa duk da tasan bazai amsa mata ba "ina yini yaya ?"shareta yayi kamar yadda ya saba “ adamcy maryam na gaisheka ".
“lafiya!” ya fad'a atakaice sannan ya zauna mr ya daura kafarsa daya akan daya ya dauki remut ya kunna tv ya Kure volum alokacin da aunty shahida da maryam suka mike "to mami mu mun wuce sai an kwana biyu kuma "Allah ya kaiku lafiya zan lekoku in sha allahu maryam ki kula da kanki ki dinga shan maganinki akan lokaci Allah ya sauke min ke lafiya bai ji abinda suke tautaunawa ba shi dai yaga sun fice ko cikakken minti goma basuyi ba sai ga baba qaramin ya shigo kamar wanda aka jehosa kai tsaye kan mr ata yayi yana nunasa da dan yatsa yana cewa "duk tsarinka ne bana wacce sabuwar maaikaciyar bace maryama akace sunanta ko me ,to kasani na samu labari komai kuma bamu yarda ba bamu amince ba ayi wani aiki a boye sai dai a bari lokacin da kowa ya hada nashi sai ayi atare" .
Baba qarami ya kalli inda mami take zaune yana sauke numfashi “ki gaya ma danki dan nasan yana da matukar taurin ka idan kuma yayi Kuskuren yin yadda nace zai hadu da mummunar bacin raina da bai ta'ba gani ba ."wai meke faruwa ne baba qarami kai da danka kullum sai a jiku "karki qara cewa dana dan ba dana bane nasan ya'yana shima yasan ubansa numfashi mami ta sauke kana tace "shikenan Allah ya kyauta karka damu baba qarami zai ji maganata in sha allahu company AGC din ma zan sa ya bar maku tunda shi allah ya rufa masa asiri yafi qarfinsa " okay haka ma zaki ce ?to me kake son nace wannan yaron danka né halak malak kace a'a ."adamcy danka ne banga amfanin idan zakayi mgn dashi ba ka dinga daukar zafi ,idan kabi shi a hankali zai yi abinda kake só ta juya inda mr ata yake zaune wanda yayi kamar tunda akayi duniya bai san da wani halitta baba qarami ba bare ma yasan me yake cewa .”
"adamcy tashi kaje dakinka zan kawo maka abincinka "zazzafan numfashi ya sauke sannan ya yunkura ya tashi ya wuce cikin zafin zuciya saka makon bai samu damar fadawa baba qarami mgn ba kuma daman mami tayi haka ne saboda gudun abinda zai biyo baya ."da kyar mami ta sauko da baba qarami akan lallai adamcy zai janye akan komai suyi duk yadda suke so jin haka ya hakura sai dai tafiya yayi yana bambame yayinda mr ata ya shiga zariya a parlour'nsa goye da hannuwansa duka abayansa tunanin wanda ya fad'a ma baba qarami shirin maryama yake." tabbas ko waye yasan bai wuce sultana ba saboda da ita aka shirya komai . tafiya ya fara yi acikin parlour'n lallai tayi haka ne dan ta janyowa maryama mummunar tsana daga garesa amman shi hakan ba damuwarsa bace dan zai iya karawa da kowa most especially akace za'a ta'bo masa zuciyarsa , abarshi shi a karon kanshi yayi mata duk abinda yaga dama amman wani yayi mata he can't take it sai inda qarfinsa ya qare,da fari bai yi suppoting din plan din maryama ba amman a yanzu zuciyarsa ta yarda kuma ta amince bazai karyar mata da gwiwa ba zai yi supporting dinta da dukkanin karfinsa da rayuwarsa.”
Mmn Sudais
[8/31, 11:25 AM] Safwan Libiya 2: 💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
BOOK 3
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.