Best / Popular Hausa Novels

Hamdah Littafi Na 2 Complete Hausa Novel

Reading file: HAMDAH part 2 complete.txt

Chapter 26 of 35

Ina zaune nayi jugum zuwa lokacin kam alhamdllh zafi da zugin da hannuna yake min sai raguwa yake,
ido na zubawa su Naseem da ke jikin Inna wuro sunyi shiru sunata rarraba ido,
Bappa kuwa tun da yagama shafa mana maginin yamike yafiya sai yanzu yashigo rike da kwarya a hannunsa,
ya karaso in da muke ya mikawa Inna wuro kwaryar yana faÉ—in
"Basu susha dan su daÉ—a jin karfin jikin su".
Inna wuro ta amsa
tare da faÉ—in
"Dama yanzu nake shirin aiken Mero taje ta tatso musu madarar".
ta aje kwaryar ta mike da sauri ta shiga bokkar dake gefe da mu tafito da kwarya da ludayi guda biyu,
ta raba madarar biyu ta mika min rabi kana ta zauna tana É—ibawa da ludayi tana baiwa su Naseem,
ai ko suka karɓa suna ta sha,
A hankali na É—ibo nadarar cikin lodayi nakai bakina,
lumshe idanuna nayi jin É—umi da garÉ—in madarar ya ratsa ni,ai ko na gyara zamata sai gashi na shanye madarar tass har ina tanÉ—e baki...
Bappa ya fito da shirin tafiya masallaci ya dube ni yana faÉ—in
"To ni zan tafi masallaci yanzu ina zakuje tun da naga kun gama shan madarar?".
kaina a kasa nace
"Yola zanje".
suka haÉ—a baki da Inna wuro wajen faÉ—ar. "Yola??".
Bappa yace
"To ke da zakije Yola me ya kawo ki rugan nan Yola da yake tacan gefe Yola da yake tacan mezai sa kibiyo ta nan?".
ko mai ban ce ba sai kasa da kai na da nayi.
da sauri ya juya yanufi kofa yana faÉ—in
"Bari na tafi kar na rasa sallah".
a hankali na mike nace
"Ni ma zan yi sallar".
Mero ta mike da sauri ta zubo min ruwa a buta ta mika min tare da nuna min banÉ—aki.
na je nayi sarki kana nafito nayi al'wala,
koda na fito na samu Inna wuro ta shinfiÉ—a min sallaya Mero kuma na rike da Nasmah sai wasa da gashin kanta daya cukuikuye take,
bayan na idar da sallar ina zaune kan taburma tuni su Naseem sun yi bacci,sai na gyara musu kwanciya kan taburman na rufe su da abun goyon su.
Mero da Inna wuro ma duk lokacin sun shiga yin sallah..
ina zaune jigum...

Bappa ya shigo da sallama,
na amsa kallon in da su Naseem suke kwance yayi kana yace
"A'a ya zaki kwantar da yara a wannan gurin sanyin ke bakyajin sanyi?".
murya ya É—agaga yashiga kiran Mero,
da sauri Mero ta fito yace
"Kira Sumaye tazo ta É—aga yaran nan anan ya za'a barsu cikin sanyi".
da sauri Inna wuro tafito tana faÉ—in
"Ai kwanciya sukayi ne".
ta dube ni tana cigaba da faÉ—in
"Ke ma in kin gama ki taso a sanyin nan".
ta É—auke su ta kaisu É—aki.
numfashi na sauke wai yau mu ake ce wa mutashi a cikin sanyi kar sanyi ya kamamu Allah sarki rayuwa bayan acikin ta mukayi rayuwar wata biyu da É—ori..
A sannu na mike nabi bayan su muka shiga cikin bukka.
abakin gado gado irin na Fulanuka in da aka kwantar da su Nasmah na zauna.
tace idan ina jin bacci na gyara na kwanta a gefen su,a hankali kuwa na gyara dan kuwa baccin nake ji...

Washegari da safe bayan mun karya da lafiyayyen tuwon gari miyar É—anyen kuka wan da yaji man shanu, muka kara da kunu.
Bappa ya shigo da madara acikin kwarya mai É—umi ya bawa Inna wuro yace ta bawa su Nasmah,
guri ya samu a gefe ya zauna kana ya dube ni sannan yace
"To yanzu kam gari ya waye bakuwa idan kika fita zaki sami motar tafiya Yola dan daga nan babu wani nisan kirki sosai".
Kai na akasa na amsa da to,
mikewa yayi yashiga bukkan sa ya fito da robar maganin da jiya ya shafa mana,
ya dawo ya zauna yaÉ—au ki Naseem yana shafa mishi maganin a guraren da yaji ciwo yace
"Amma kam dai haɗarin mota ne wannan sai yau na daɗa ganin raunukan ashe da yawa ko ɓarayi kuka haɗu da su a hanya suka yi muku duka haka,dan yanzu ɓarayi rashin imanin su gaba yake har yara ma basu bari ba".
ƙwalla naji ya cika min ido tuno da yadda akayi muka ji ciwon, cikin zubda ƙwalla nace
"A'a ba hatsari ko dukan ɓarayi bane faɗowa mukayi daga kan wani tudu".
da mamaki Inna wuro tace
"Ikon Allah garin yaya?".
Bappa yaÉ—an sakai ta shafa masa maganin yana faÉ—in
"Garin yaya a ina kuka sami tudu ku da kuke mota ba tafiyar kafa ba kuma kince ba haÉ—ari bane".
nace
"Eh acan cikin daji acan ta wani guri da nisa zamu zan sauka a kan tudun shine na zame shi kuma ya suɓuce a hannnuna ya gungura yafaɗi kasa ita kuma tana bayana tare da ita muka isa kasa shine na faɗo a kan hannuna".
gaba É—ayan su suka zuba min ido alamun na zartata da kuma magana ta kana Bappa yace
"Menene yakai ku cikin daji da har kuka kai ga jin rauni??".
kasa nayi da kai na ina wasa da Æ´an yatsu na yayin da gudun hawaye na suka tsananta cikin rawar murya da kuka ke son kwace min.
a hankali nafara basu labarin rayuwa ta tun daga farko har yau da nake zaune a gaban su.
Salati Inna wuro ta sake gaba ɗaya jikin ta yagama yin sanyi har sai da taɗiga ƙwalla cike da tausaya wa rayuwar mu,
Bakin zanin ta takai tashare É—an guntun kwallar da ya fito mata tana faÉ—in
"Ikon Allah lallai kinga rayuwa rayuwar ki abun a duba ne, me kika tsare wa mutanen nan da zasu jefaki cikin wannan mawuyacin hali, har ya shafi yaran da basusan kansu ba bare susan mecece duniyar, wannan wani irin zalunci ne".
Inna wuro ta karashe maganar tana jan hanci.
Bappa kuwa kai ya jinjina cike da dattako
sannan yace
"Allah mai girma da É—aukaka,
lallai Allah shi ke kare ba wansa a duk inda yake, yatsare ku yakuma kare ku da sharrin namomin daji masu cutarwa har kuka fito batare da cutar wan wani dabba ba,".
shiru Bappa yayi tare da zuba min ido na É—an wani lokaci zuwa can kuma sai ya girgiza kan sa sannan yace
"Mutane dai ko da yaushe burinsu su zalunci É—an uwan su ko ribar me zasu ci da yin hakan?."
yayi maganar yana mike wa,
da sauri Inna wuro ta É—ago tana duban sa,
in da buta yake yanufa yasun kuya yasoma al'wala yana idar wa ya mike, yashige bukkar sa.
numfashi Inna wuro ta sauke,
tare da mai da duban ta kaina
tace "Allah ya tabbatar da alkhairi".
Amin nace batare da sanin inda batun nata ya dosa ba.
bayan Bappa nabi na kallo ganin yayi al'wala kuma lokacin sallah baiyi ba...

Muna nan zaune can yafito rike da jarbi a hannunsa bakinsa na motsi alamun lazumi yake, in da yatashi É—azu yadawo ya zauna,
numfashi yaja ya sauke tare da yin gyaran murya sannan yasoma magana
"Hakika asiri akayi miki mummunar asiri ma kuwa,
wanda ya sa akayi asirin da wanda ya ai kata sihirin babu imani azuciyar su,
bakin sihiri ne mai matukar duhun gaske, rashin imanin wan da ya ai kata abun yakai yakawo,
dan kuwa asirin ba zai taɓa karyewa ba har sai shi bokon da yayi asirin ya muku,
mutuwar sa shine lakanin karyewar asirin,
tabbas wan nan yacika mugu mara imani,
babu kuma wan da yasan ranar mutuwar wani sai Allah, Allah Ya takai ta ma dan basuso abun ya tsaya iya haka ba, yana ai ki da babaken aljanu marasa imani,
sunso kiyi gaba can da nisa basuso kitsaya iya nan ba,
sai dai sun mance Allah baya bacci duk kuma wan da ya dogara da shi baya taɓewa addu'a kuma makarin mumini sam addu'a bata faɗuwa kasa,
da yar dar uban giji bazakiyi gaba ba kamar yan da suka so, zamu gwada musu karfin ayar ALHAH!".
cikin matukar mamaki da kaÉ—uwa nake kallon Bappa to wacece Ni da har wani zaiyi min asiri,
ni dai nasan anyi min kazafin da har na mutu bazan taɓa mancewa da shiba,
to wacece ni da har wani zai nimi yin asiri a kai na.
"Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un".
nafurta daga zuci har kan laɓɓana.
Inna wuro ma salati ta saka tana faÉ—in
"Ikon Allah lallai mutum abun tsoro ne Allah ka shiga saka nin nagari da mugu"...
sun jinjina lamarin sosai tare da tausaya min kwarai da gaske...★

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.