Best / Popular Hausa Novels

Hamdah Littafi Na 2 Complete Hausa Novel

Reading file: HAMDAH part 2 complete.txt

Chapter 30 of 35

muna isa garin Abuja wani kayataccen masauki aka wuce da mu, nan Mahmoud ke faÉ—a wa Bappa,
an tabadar da masaukin domin mu ne, É—akina ni da su Nasmah da ban, É—akin Bappa da ban sai na Mahmoud É—in,sai kuma na jagororin da muka taho da su,
sojojin kam suna cin abinci suka juya suka É—au hanyar Adamawa,dan da ma suma rakiyar sukayi mana yanzu kuma kulawar mu yafita a hannunsu yadawo hannun wasu hukumar da muka tarar da su a nan.
a gayiye na zauna bakin gado Naseem da Nasmah suna zaune tsakiyar gadon sunata wasan su.
bin lafiyayy É—akin nayi da kallo, numfashi na sauke ashe dai zan sake gani na cikin É—aki irin wannan, dan ni na fidda sammanin hakan arayuwa ta mai cike da tarin kaddara da jarabta.
kasan cewar mun isa ana kirana sallar magriba, dan da muka iso sai da muka tsaya a wani guri naga jagororin da aka haɗo mu da su, suka tsaya yin magana da wasu, mun ɓata lokaci a gurin kafin muka taho nan.

kayan jikina na tuɓe na ɗaura zanin a kirji nashige bathroom naje nayi wanka,sannan na fito na tuɓe su Naseem suma naje na musu, ina fita na shinfiɗa sallaya da nagani cikin ɗakin kasan cewar nayi al'wala nagabatar da sallar magrima.
tuni su Nasmah sunyi bacci sabo da gajiyar mota,
sai na gyara musu kwanciyar su a kan lafiyayyen gadon,
bayan na idar da sallar Isha ina zaune a kan sallaya akayi knocking É—in kofar,
a sannu na mike na isa bakin kofar na buÉ—e, wani mutum nagani sanye da uniform irin na masu ai kin hotel, da tray É—in abinci a hannunsa,
yayi min sannu na amsa,baya mayi na É—an ja murfin kofar ya shigo ya dire tray'n kan table É—in da ke tsakiyar É—akin mai lodin kayan abin ci da drinks kala-kala kana yafita, na mai da kofar na rufe, na koma bakin gado na zauna.
da ma yunwa na ke ji nan na janyo tray'n na soma cin abincin,
inaci ina kallon su Naseem dan na san suma yunwar suke ji sai dai gajiya ya sasu bacci,
ina gama ci naje na wanko bakina na dawo, na kwanta bakin gadon tare da yi musu addu'a nima nayi nagyara kwanciya ta.
washegari bayan nayi wanka nayiwa su Nasmah na shirya su muna zaune,a ka shigo mana da breakfast bayan mun karya.
Bappa yashigo da sallama kan kujerar É—akin ya zauna,
nan nashiga gaida shi ya amsa kana yake tanbaya ta ya gajiyar hanya?,
nace
"gajiya yabi jiki". Naseem kuwa tuni ya wuce jikin sa yana ta tsalle Nasmah ma tabi bayan sa sunata yi masa gwalaɓe,suna ta shekewa da dariya Bappa shima sai biye musu yake yana ta taya su sai zuba masa surutu suke wan da ma maganar tasu bagane ta ake ba.
zama Bappa yagyara tare da duba na kana yace
"ÆŠazun Mahmoud ya zo ya same ni da jagororin da aka haÉ—a mu da su sun bani tabbacin bazamu sami ganin shugaban kasa a yauba,
zamu É—an É—au lokaci sai dai kawai muÉ—an jira,
idan kuma zamu koma to,amma gaskiya
ni ina tunanin komawar mu domin iyanzu maganar Lu'ulu'u'n nan ya karaÉ—e cikin rugar mu har da wajen sa, ina tunanin mukoma yanzu mutane basa da gaskiya É—ai-É—ai ku ne masu gaskiya a zamanin yanzu, yan da yashiga kunnen mutanen gari kuwa na tabbata zai fita har wajen gari,
har miyagon mutane suje suji sukawo mana farmaki,
gaskiya bazamu koma ba zamu jira har lokacin da zamu sami ganawa da shi shugaban kasar".
kai na jinjina alamun gamsuwa tabbas,
kuÉ—i a gida akwai haÉ—ari musamman irin wannan da na ga gwamna yahaÉ—o mu da jami'an tsaro, nace
"To Bappa duk abun da ka yanke dai-dai ne".
yace
"Gaskiya zamu zauna ko nan da kwana uku ko huÉ—u ne in dai har zamu gana da shi É—in yafi mana komawar mu da dukiya kan hanya domin ko a hanyar komawar mu ma kaÉ—ai hatsari ne bane kuma ace mun koma cikin ruga in da babu jami'an tsaro".
nace
"Hakane Bappa muzaunan kawai".
kai ya jinjina kana ya mike yana rike da hannun Naseem, Nasmah da take ta kokarin binsu yace ta zauna ta tayani hira,
zai tafi da Naseem shima ya tayashi hira....

kwaman mu uku a Abuja acikin wannan hotel É—in, alhamdllh a kwana na ukun bukatar mu ta isa ga shugaban kasa sai dai har lokacin ba'a bamu da mar ganin sa ba, a kwana na biyar,da safe ina zaune akayi knocking naje na buÉ—e kofar Mahmoud ne yashigo da sallama,
rike da babban laida a hannunsa,
na gaishesa cikin girmamawa ya amsa tare da mika min laidar dake hannunsa tare da faÉ—in
"Gashi ku shirya kuyi sauri, yau kam in sha Allah zamu sami ganawa da shi koba shi É—in bama zamu zauna da wasu manya na kusa da shi kuyi sauri ku shiriya ya zama na dai da kuna cikin shiri".
nace "Tom".
na karɓi laidar tare da yi masa godiya yafita.
na zawo bakin gado na zauna tare da buÉ—e laidar na fara ciro kayan cikin, kayane na sawa,kaya masu kyau narika É—aga na Naseem da Nasmah masu kyau Æ´arkanti, dukan su da takalmar su masu kyau,
da ma tuni na riga da na musu wanka, na cire musu kayan jikin su nasa musu wannan kayan,
yara suka fito shar da su tamkar Æ´aÆ´an turawa, sunyi kyau sosai na tasasu gaba inata kallon su cikin ban sha'awa,
sannan nima na mike na camza nawa dogon riga ne da gyalen sa Ash mai ratsin gold
É—in duwatsu haÉ—e da takalmi Black and gold, takalmin mai É—an tudu ne kaÉ—an.
nasaka kayan a hankali na isa yaban mirror abun da na daÉ—e banyi shi ba yau nayi,
nashafa
pawda da nagani kan mirror'n haÉ—e da man lips kana,
nayi rolling É—in gyalen a kaina,tsayuwa ta na gyara gaban mirror'n
masha Allah duk da na rame na dishe amma bai hanani fitowa a HAMDAH ta ta daba kaÉ—an ba,
murmushi nayi ganin yan da nayi kyau a cikin kayan yaɗan ɓoye min rama ta.
da misalin karfe 12 Mahmoud yashigo daga bakin kofa yatsaya yace nayi sauri na zo. sai ya juya yafita ,
cikin hanzari na sakawa su Nasmah takallamar su sannan na kama hannunsu muka fito,
muna fita farfajiyar hotel É—in,
nan na tadda su, Bappa yana zaune cikin mota gefen mai zaman bamza yayin da Mahmoud ke zaune a mazaunin direba. muka karaso Bappa yana ta kallon mu yana murmushi,
nima murmushin nayi muka karaso na buÉ—e gidan baya na shiga Naseem kam fir yaki shiga sai da na mika sa wa Bappa.

motar mutanen da mukazo da su a gaba namu yana biye da shi a haka muka fita a cikin hotel É—in, duk san da na É—ago kaina sai mun haka ido da Mahmoud,na lura tun fitowar mu idanun sa a kaina, kawar da kaina nayi gefe ganin sai satar kallo na yake tacikin mirror,
munyi tafiya mai nisa kafin muka isa wani katon gida mai matukar girma da kyau da tsaruwa,
a bakin get É—in gidan motar gaban mu ya faka a bakin get É—in Mahmoud ma ya tsaya a bayan sa,
É—aya daga cikin mutanen ya fito ya isa in da sojoji ke zaune a bakin get É—in,
yayi magana da su kana ya koma cikin motar,
nam sojojin suka buÉ—e get É—in,
motar ta fara shiga kafin mu muka bi bayan sa.
sai da na shiga gidan na daÉ—a ganin tsaruwa da girman sa,
muka paka a parking lot.
kana mutanen suka fito daga cikin motar,É—aya daga cikin su yazo yace, muma mu sauko.
daga can wasu sojoji suka taho in da muke,jogororin da muka taho da su suna gaba muna biye da su muka nufi cikin gidan, yayin da sojoji
biyu ke gaban mu.
wani lafiyayyen parlour muka bayyana cikin sa,nan da nan aka cike mu da kayan ciye-ciye da na sha.
munkai kimanin awa É—aya zuwa can mukaji takun sauka daga step's a hankali na É—ago kaina wani mutum ne ya karaso cikin parlour'n cikin girmamawa gaba É—aya Æ´an cikin parlour'n suka mike tsaye,
a sannu ya karatsa ya zauna kan wani kujera lafiyayye,nan kowa ya zube yana mika gaisuwa,
nima dai É—an tutsunawa nayi na gaishe sa,
É—an shiru ne yabiyo bayan gaishe-gaishe sannan mutumin yayi gyaran mursa sannan yace
"Sannun ku da zuwa kune ba'in ko?".
waÉ—an da muka zo da su suka amsa da Eh.
waya ya É—aga ya daddanna sannan ya kara a kunnen sa,
yayi magana zuwa can ya sauke wayar,
kana ya mike yadubi su Bappa yace su biyo shi,suka mike da waÉ—an da mukazo da su É—in da sojojin da suke tsaye har lokacin a cikin parlour'n suka fita,suka bar ni ni da su Nasmah a cikin parlour'n.
tun da suka fita har akayi sallar azahar ina nan zaune har wajen karfe biyu da rabi, babban damuwa ta ma sallar da banyi ba.
can wani soja ya shigo yayi min magana cikin harshen turanci yace na biyo shi,
na mike na ruko hannun su Nasmah muka bi bayan shi.
muna fita wani mota ya nuna min na shiga,
direba na zaune cikin motar shikuma ya zauna mazaunin mai zaman banza, nan direba yaja motar muka fita a gidan.
tafiya muka yitayi har na fara tsorata da tafiyar,naÉ—an ji tsoro ganin dukkamsu ban san suba,
ganin mu nayi bakin wani ramɓasheshen get mai girman gaske,
aka buÉ—e mana get É—in muka shiga shima tafiya mai tsawo mukayi a cikin wannan get É—in kafin muka kuma isowa wata get É—in,
nan mukayi ta wuce get-get kuma ko wanne da sojoji.
wata get muka iso mai kyau da tsaruwa muka tsaya nan kira yashigo wayar sojan, ya É—aga bayan ya sauke wayan ya dube ni yace na sauko.
nafito jiki a sanyaye,
tafiyar kafa mukayi mai tsawo,
kafin nan muka iso wani kofa,
Hmm in da ranka ka sha kallo tsaruwar wannan guri bazai misaltuba,
sojoji ne a tsaye a gun duk kanin su foskokin su sanye da bakin glass,
nan suka shiga saka mana na'ura a jikin mu suna gwada mu,ni da su Naseem,kafin muka haura kan step É—in da zata sada mu da kofar, nan kofar ma,
tafara bada wani sauti tana É—aukar hotunan mu,abun mamaki da al'ajabi,
daga bisa ni kofar ta buÉ—e muka shiga,
sojan na gaba ina biye da shi a hankali,
koda muka kuma isowa wata kofar nan sojan ya tsaya wani sojan da ke tsaye nan bakin kofar shi yayi gaba, yayi min alama da na biyo shi,
koda muka kuma zuwa wani kofar ma, tsayuwa wannan sojan yayi kana sojan da ke tsaye a wannan bakin kofar yayi gaba da ni.
muna zuwa wata kofar mai shigen, kama dana farko yakuma É—aukar mu a hota,ina tsaye ina kallon ikon Allah abun dai ya fara bani tsoro,
shima still anan sojan ya tsaya sojan dake wannan bakin kofar yayi ciki.
"Innalillahi ya ilahi ya lillahi".
abun da na furta kenan,
wani mashahuriyar katon parlour ne kamar ba a duniya yake ba,
wannan parlour'n muka shiga yanuna min gurin zama na zauna.
sai na janyo Æ´aÆ´ana na rungume su dan nasan sun gama gajiya da wannan tafiyar,
munyi zaman da yakai na 30min,
kafin daga can wata kofa ta buÉ—e wani mutum yafito yayi min alama da nazo na mike nabi bayan sa,
nan muka kuma shiga wani gurin na daban wan da yafi ko ina girma da tsaruwa.
muna shiga gurin can da nisa na hango su Bappa zaune kan wasu tsararrun kujeru,
numfashi na sauke,
cikin tsananin mamaki da kaÉ—uwa nake kallon wan da yake zaune kan kuje ran dake gaban su Bappa,
da mamaki nake lallon mutumin,
shugaban kasar mu na Nigeria ke zaune gaban su Bappa na karaso in da suke na zauna a kasa har lokacin mamakin ganin sa fal zuciya ta, mutumin da nake ganin sa a TV da mujallu,sai kuma cikin ɓarin baki nashiga gai da shi.
cikin sakin fuska fuska É—auke da annuri ya amsa gaisuwar,
kai Bappa ya É—an dukar cikin ladabi da girmama wan da yariga da yafi ka cikin girmama shugaba yace
"Ranka shi daÉ—e wannan itace yarin yar".
yafaÉ—a yana nuna ni.
annurin fuskar sa ya faÉ—aÉ—a idanun sa a kai na, ya jinjina kansa.
hannu ya miko yayi wa su Naseem alama da suzo, ai ko Naseem sarkin sabo ya mike ganin ya mike sai Nasmah itama ta bi bayan sa,
hannun su ya ruko yana faÉ—in
"Masha Allah sannun ku jarumai".
yafaÉ—a yana shafa kawunan su.
baki suka washe kamar sun san abun da yafaÉ—a shima yabisu da murmushi haÉ—e da yi musu wasa...
bayan wasu maganganun da yayi da na kusa da shi,
wan da duk kanin mu babu wanda yaji abun da suke faÉ—a, kana ya mike yabita wata kofa.
É—aya daga cikin mutanen da suke zaune a gefen sa yadube mu yace wa wasu da ke gefen mu a tsaye sukai mu masauki.
nan muka mike muka bi bayan su wani masauki na musamman a ka kai mu, nan ma kowa da É—akin sa.
anan muka kwana É—aya washegari
da safe aka buga min kofa koda na buÉ—e breakfast a ka shigo da shi wan da ya kawon cikin harahen turanci yace min na hanzarta mushirya a kwai kaya acikin É—akin muyi amfani da su, nace to.
na É—aga su Nasmah na basu abinci nima na ci, sannan mukayi wanka ,muka kimsa cikin kayan da naganau cikin wardrobe É—in É—akin lafiyayyun kaya na manya da yara.
muna gama shirin akayi knocking na kofar koda na buÉ—e wasu mutane ne maza guda biyu sukace min muje,
To. nace sannan na koma cikin É—akin na kamo hannun su Nasmah mukabi bayan mutanen.
acan waje muka haÉ—u da su Bappa nan muka shige mota mukayi gaba.
ido nazubawa hanya a raina nake faÉ—in
"Yau kuma ina za'a yi da mu?"....★

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.