Auren Shehu Part 2 Complete Hausa Novel
Reading file: Auren_Shehu_Part_2_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 27 of 46
Jin haka Raqeeba ta tashi da sauri ta fice gudun kar Zainab ta gane shara ta take.
Nan bakin gado Zainab ta zube, so ta ke ta yi kuka amma ta nemi hawayen ta rasa.
".....mun san ba kya san shi, kamar yanda mu ma ya sha fada mana ba ya kaunar ki......"
Maganganun Raqeeba da ke yawo cikin ran Zainab kenan. Ko da ta tuna
"Sadakar ki aka ba shi, tsoran hukuma da kuma yanda ya ke jin dadin kwanciya da ke ya sa be mayar da ke gida ba, Amma ya ce da zarar kin gundire ko kuwa ki ka haife cikin da ki ke dauke da shi zai......!"
Ta yi saurin shafa cikin ta, nan ta ke wani tunani ya bugi kan ta, tun da tazo Rugar Shehu ba ta taba yin al'ada ba, duk da dai nata mai wuyar sha'ani ne ba kowani wata ta ke yi ba, Wani lokacin kuma ta kan yi sau biyu a wata. Haka kuma tun da ta fara sakarwa Usman jikin ta kusan kullum sai ya kusance ta, Tuni ta fashe da kuka ta na fadin
"Allah ya isa! Allah ya isa ba zan taba yafe ma ka ba Usman duniya da lahira! Allah ya isa!"
Babban tashin hankalin ta shi ne gaba daya ta manta zuciya ba ta da kashi, kamar yanda ta ke kokarin sace zuciyar Usman, tuni na ta zuciyar ta yi rauni, ba ta iya yin cikakken minti goma ba tare da ta yi tunanin Usman ba, haka har Allah Allah ta ke dare yayi su kebe, dama ga ta Allah yayi ta mace mai yawan bukatar mijin ta.
Sai da ta yi mai isar ta, sannan ta share hawaye bayan ta gama yanke hukunci ta kwallawa Rahila Kira, wacce dama ta yi lamo ta na tsammanin kiran. Da saurin ta ta shigo, ganin yanda idanun Zainab ya kumbura su ka yi suntun ta fara tambayar ko lafiya. Murya shake Zainab ta furta
"Ki ce da mijin ki Tanko na shirya tsaf, ya gaggauta kawo mafita idan ba haka ba zan yi gaban kai na!"
Cike da munafunci Rahila ta shiga doka salati ta na tambayar Zainab shin ko menene ya faru. Zainab ta ce ita yar sako ce ta tafi ta kai sakon ta. Rahila ta amsa da toh ta fice jiki na rawa kamar wacce za ta yi tsuntsu dan sauri.
Nan cikin gonar Bello ta wuce Usman da Bello, yanda ba ta lura da su ba haka su ma ba su ga giftawar ta ba. Musammam Bello wanda maganar Usman ta sa kan shi yayi tsawa. Cikin jinjinawa ya ke maimaita
"Za ka bar min sarautar Rugar Shehu?"
Usman na mai murmushi ya gyada masa kai, in da Bello ke masa kallan zararre. Zaune su ke karkashin bishiya da ta mu su lema, dukkanin su sanye cikin fararen ruguna yar shara. Bello na kallan fuskar Usman wanda tun da ya gane yanda Zainab ta ke satar kallan sa duk sanda be daura rawani ba ya dena saka rawanin gaba daya sai dai hula, Bello ya furta
"Akan wani dalili zan gaje ka bayan kana raye?"
"Murabus na ke so na yi"
Usman ya ba shi amsa a takaice, ya kara da
"Shi ya sa na ke ta sa ka a hanya, ban dawo Rugar Shehu dan na zauna ba, na dawo ne sanadiyar kiran Iya, Iya kuma ta kwanta dama mun kuma baro kabarin ta can falgore, bakin cikin haka ya sanya ni dauko Abu daga birni, na kawo ta daji dan kuwa a nawa wautar hakan ne zai sa na rama babban asarar da ta ja min, da zalincin da ta ma ka, Amma na huce yanzu Bello, ba zan iya jure ganin Abu cikin wahala haka ba, ba ta saba da rayuwa irin ta mu ba...."
"Toh ka sake ta mana..."
Bello ya katse shi da iya gaskiyar sa. Murmusawa Usman yayi, kana ya ce
"Ai ko da da Allah be jarrabe ni da soyayyar Abu ba ba zan iya sakin ta ba saboda alkawari mai girma da na daukarwa mahaifin ta, bare yanzu da son ta ya bi jiki na jini da tsokana, ina san mata ta Muhamadu, ina san ta lillahi warasulihi, ba zan iya rayuwa babu Abu ba"
Shiru ne ya biyo baya, kafin daga bisani Bello ya nisa ya ce
"Shin ita maidakin ta ka ka ji ta bakin ta? Idan ita kuma ba ta da wannan ra'ayin fa? Shi fa kado ba shi da tabbas..."
"Ko ban yarda da komai ba, na sheda Abu ta na kauna ta, Abu na ta na so na, daren yau zan sheda mata soyayyar da na ke mata, Zan nemi yafiyar ta akan dauko ta da na yi daga birni duk da dai ni banyi dana sanin hakan ba, Rugar Shehu shi ne tsatson soyayyar mu"
"Yanzu Shehu akan mace za ka bar sarauta? Ka bar shanu? Ka bar yan uwa ka tai birni?"
"In ka dauke yan uwa duka sauran abubuwan da ka lissafa na dade da barin su, sai dai wannan karan zan yi amfani da dama ta na gina gidan gona cikin birni, yanda za mu bunkasa tattalin arzikin Rugar Shehu a can birni, in Sha Allah ko ban iya yin yanda Shugaban kasa ke da hashashen kawo cigaba birni ba, zan kwantata, haka kuma zan sayar da wasu daga cikin shanu wanda su ke mallaki na domin ginawa Abu gida irin na yan birni"
Ya kare maganar ya na murmushi yayinda ya ke ayyana irin gidan da zai gina mata cikin ran sa. Jikin Bello sanyaye ya ke duban sa, ya sha ji ana cewa asiri ba ya kama Usman, Amma ko shakka babu wanda Zainab ta yiwa Usman bakara min asiri ba ne. Cewar Bello cikin ran sa.
Aure shehu 2
12.
Muhammad Bello be bari sun yi sallama da Usman ba sai da ya tabbatar ya ma sa alkawarin zai kara tunani akan lamaran.
Rahila kuwa ko da ta shedawa Tanko sakon Zainab, Tanko ya dara ya na mai jinjinawa matar shi akan makircin da ta iya kulkawa, haka kuma ya na mamakin rashin dabara irin na Zainab, Dan kuwa ko shi da ba ya cikin Rugar Shehu ya sheda da irin soyayyar da Shehu ya ke yiwa Zainab. Tanko ya ce dama shi ma a shirye ya ke, abu daya sa ya ke so Zainab za ta ma sa, shi ne ta tabbatar ta ja Usman bakin ruwan da ke makota da gidan gona lokacin da ake tsaka da bikin sharo, shi kuma ya mata alkawarin matukar ta masa wannan to zai mata hanyar da za ta koma gida a ranar.
Rahila ta ba ta yi kasa a gwiwa ba ta koma Rugar Shehu in da ta bar Tanko ya na shirin yanda goben za ta kasance ta hanyar aika sako ga yaran sa wanda dama suna nan cikin Taraba suna jira.
Jin sakon Tanko Zainab ta fara shirya kayan ta a boye. Sai da ta hade kayan ta tsaf cikin akwati sannan ta haye gadon karfe yayinda kirjin ta ke bugun uku uku, gaba daya hankalin ta ya kasa kwanciya. Sai bayan Ishai'i Usman ya nufi gida, bayan ya gama hidimar sa kaf, ya tsaya kogi yayi wankan sa na musammam dan kuwa so ya ke ya raya daren ranar suna soyayya da Zainab, sannan ya sheda mata burin sa na mayar da ita birni su karasa rayuwar su a can.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.