Auren Shehu Part 2 Complete Hausa Novel
Reading file: Auren_Shehu_Part_2_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 45 of 46
"Malam me ya kawo ka gidan nan tsakar dare haka? Yaushe ka fara haura katanga? Me ya kawo ka daki na?"
Daf da ita ya zauna hakan ya sa ta dada muskutawa domin ba da tazara a tsakanin su. Hakan ya kara sa Usman dada matsawa kusa da ita, ita ma din ta kara matsawa, haka su ka ta yi har ya kure ta jikin bango.
"Wai menene! Zan ma ka ihu wallahi!"
"Toh in kin min ihu an zo an gan ni dakin mata ta sai menene?!"
"Wacece matar ta ka? Idan ma kana shirin dawowa da ni wallahi gwara ma ka fidda rai! Ka riga ka sake ni, I don't care daya ne ko uku, babu ni babu kai"
"Saki kuma? Ni Usmanu na sake ki? Toh abin na ki kuma ya koma sharri ne Abu?"
Takaici ne ya sa ta kasa magana. Ganin ba ta da niyar tanka masa ya sake furta
"Yanzu dai menene shedar sakin da na mi ki fisabilillahi?"
Tashi ta yi a fusace har nono na fita daga bakin Shehu, ya dan saka kuka amma ko ta kan sa ba ta bi ba sai da ta dauko takardar da ya bata, ta aje masa, ya fi takardar da idanu. Cike da tsiwa ta kara da
"idan ka gama dubawa za ka iya fitar min daga daki!"
Takarda ya dauka ya buda, ganin abun da ke ciki ya sa shi dariya, tabbas zatan shi ya tabbata. Ganin yanda ya ke dariya ya sanya ran Zainab kara baci. Musammam da ta ji ya furta
"Shin ko sau daya kin bude takardar nan kuwa Abu, ko kuwa dai tsabagen ba a iya karanta ajami ba ne?"
Ba ta so ya san ba ta taba budewa ba saboda kar ya gane tsabagen tsoran yawan sakin da ya mata ya sa. Dan haka ta ba shi amsa da
"Na karanta mana da ban karanta ba ta ina zan san sakin da ka min?"
Ta karasa maganar tana mai dora Shehu bisa kafadar ta, domin ta samu yayi gyatsa. Idanun shi na mata dariya ya bude ta takardar ya ce
"Toh kuwa Abu sai dai wata takarda ki ka karanta ba wannan ba, dubi wannan da kyau ki gani, ban sani ba ko kin san yanayin rubutun Malam, Allah ya jikan sa da rahama, wannan rubutun shi ne duk da dai jinya ta sa be fita sosai ba"
Hannu na rawa Zainab ta karbi ta kardar, ko shakka babu rubutun ya fi kama da na dan koyo, kalma biyu ne kacal jiki, sai da ta nutsu da kyau ta gane menene ciki
"Zainab...... Amana...."
Fuskar ta cike da hawaye ta dago ta na duban sa. Usman be gushe ba ya furta
"Wannan shi ne nasiha ta karshe da Malam ya bar min, Malam be manta lamarin ki ba duk da ya na gabar mutuwa, Ni kuma na masa alkawarin ni da ke mutu ka raba Zainab, ba zan taba sakin ki ba duk runtsi duk wuya. Na san ban rukewa Malam amana yanda ya kamata ba, Amma wallahilazim duk nema na, da kokarin ganin ni ma na zama wayeyye dan zamani ina yi ne ba dan kowa ba sai dan ke, a tunanina ba ki kauna ta, shi ne dalilin ki na hada baki da makiya na dan a kashe ni, kuma na san babban dalilin da ya sa ba ki kauna na ta saboda ni bakauye ne bagidaje....."
Ta yi saurin katse shi ta hanyar dora yatsun ta bisa leban sa. Hannu ya sa ya kama yatsun na ta, ya yi kissing. Sannan ya tashi tsaye ya karbi Shehu daga hannun ta, babu mu su ta sakar ma sa shi ya kwantar da shi gefe sannan ya dada jawo ta jikin sa, ya yayinda ya zauna bakin gado ya dora ta bisa cinyar sa. Ya na mai goge hawayen da ke gangarowa daga idanun ta ya ce
"Na sani Abu, na san ki na so na, Rakeeba ta fada min ki na so na, ki na Kauna ta tun sanda na ke bagidaje na, shi ya sa ma na kasa jira na gama wayewar gaba daya, na falfalo da gudu domin neman yafiyar ki, ashe ina can an haifa min Shehu ....tsaya sunan wa ma ya ci be?"
Cike da kunya Zainab ta cusa kanta cikin wuyar sa. Usman na mai runtse idanu ya furta
"Idan ki ka cigaba da kalallame ni haka Abu zan fa baki kanin shehu a daren yau...!"
Jin haka ta yi saurin zame jikin ta daga na shi, yanda ya sa dariya ya fitar da sauti ne ta gane zolayar ta ya ke, ita ma din dariyar ta saka. Har sai da dariyar ta koma ta farin cikin yau gasu dai tare cikin so da kauna. Su ka yi mai isar su sannan Zainab ta furta
"Usman"
"Ummm"
Usman ya amsa ya na mai dada hanyo ta jikin sa.
"Ba kai ba, jinjiri na sunan shi Shehu Usman...."
Dago ta yayi ya na kallan ta, kallo mai narka zuciyar wanda ake yiwa. Idanun sa na shekin kwalla ya furta
"Duk bakin cikin da na sa ki ciki, ki na tunanin na sake ki amma ki ka sanyawa dan mu sunana Abu?"
Zainab ta gyada kai alamar eh. Ga mamakin ta sai gashi ya tada ita tsaye. Kana shi kuma ya durkusa har kasa, hakan ya sa ta yi yunkurin tada shi, Amma ya ki, cewa yayi
"Dan Allah Zainab ki yafe min, Dan Allah ba dan hali na ba ki yafe min, matukar ba ki yafe min ba toh wallahi ko dada sace ki zan yi sai dai na yi, Amma ba zan iya rayuwa babu ke ba Zainab"
Dadi kamar zai kashe ta, ta ma rasa abin cewa kawai sai rungume shi ta yi, hakan yayi daidai da shigowar Anty Sauda, Halitta, Ammy. Usman yayi saurin sakin ta cike da kunya. Ammy kuwa juyawa ta yi da sauri ta na fadin
"Kai yaran zamani! Wallahi Halitta kin cuce ni!"
Anty Sauda ma sim sim ta bi bayan ta, ya rage sai Halittt wacce bakin ta ke kunshe da dariyar mugunta, hakan ne ya sa Zainab fahimtar abin da ke faruwa, cikin tuhuma ta ce
"Halitta ke ce ko?"
"Ah ah fa, na dan ji hayaniya a dakin nan, tsoro ya kama ni dan kuwa na san ke da baby Shehu kun yi kadan ku yi making all those noises, shi ne fa na taso su su zo su ga ko lafiya.."
Ta karasa maganar ta na mai kashe mata ido daya.
"Kai yarinyar nan ba ki da mutunci wallahi!"
Cewar Zainab ta na mai jifan Halitta da filo, Halitta ta yi saurin kaucewa. Ta na duban Usman wanda tun shigowar su kunya ya sa ya kasa sukuni, ta ce
"Malam Usman bayan abin da ya faru yau zai fi kyau ka wuce da matar ka gobe, dan ko ban ji akwai wanda zai so ya kara hana ka..."
"Halitta!"
Zainab ta daka mata tsawa, in da Halitta ta yi saurin ficewa ta na mai rufo musu kofa. Ta na fita Zainab ta ce oya Usman ya zo shi ma ya kama hanya. Ta yaya ma ya shigo gidan? Ya bata amsa da
"sabon maigadin ku za ku sake kawai, duba ta biyar na bashi ya bude min kofa, abokina Umar na can ta bayan gida ya na jira na, ba zan tafi ba sai kin min alkawarin za ki bi ni mu koma Yola"
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.