Auren Shehu Part 2 Complete Hausa Novel
Reading file: Auren_Shehu_Part_2_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 4 of 46
In da Rugar Shehu ke sauya sheka, gidan Malam kuwa auran su Halitta aka daura. Ba wani taro aka yi ba, auren kawai aka dora. Zainab ba ta halacci daurin auren ba bare ta kira amare ta mu su Allah ya sanya alkhairi. Babban bakin cikin ta shi ne tafiya Saudia da Sudais ya ke so yayi da Halitta a sakamakon aikin da ya samu a can. Zinaru kuwa a ranar aka mika ta dakin mijin ta.
Zainab sam ba ta canza zani ba, yanda ta ke rayuwa a da haka ta dora bayan ta koma makaranta, haka kuma ta sake bude saban account na Instagram bayan ta siyi dalleliyar wayar ta mai dauke da tambarin tufa ta cigaba da sharholiyar ta kamar yanda ta saba.
Satin su Usman da tawagar sa biyu suna yawo daga wannan dajin zuwa wannan dajin, su kutsa nan, su kutsa can, in da ya kamata a yada zango a yada cikin kokarin kare hakkin nomama ta hanyar kada shanun sa daga barin shiga gonaki, a haka har su ka iskewa wani daji arewa masogabashin kudu, dajin ya kasance mararraba tsakanin kudu da arewa.
Kasancewar dajin ya yalwatu da 'ya'yan itatuwa, ga ruwa da yanayi mai kyau, haka kuma aikwai wadataccan fili tuni su ka yada zangon su na zama dirshen, kwanan su uku suna gine ginan bukka, haka kuma masu ilimin surkulle su ma su ka dukafa wajan kafe dajin, suna shiga lungu da sako sai da su ka kafe dajin kaf ya zame mu su tamakar gida hatta macijan dajin sai da su ka san da kafuwar Rugar Shehu.
Cikin watanni biyu Usman ya kafa daular sa, Shehuntakar sa ta ginu sosai musammam da Allah ya hore masa ilimin da ya koya daga wajan Malam. Ganin yanda ya habaka gashi babu mata ne ya sanya magidan ta da yawa yiwa Usman tayin matar aure daga cikin yan matan Rugar Shehu, musammam yanda kowacce da ta ke ji da kan ta ke da burin kasancewar mata wajen Shehu. Amma Usman kullun cikin ba su uzurin cewa zai karba, Amma akwai wata ajiya da ya ke da shi birnin Kano, matukar ba ajiyar nan ya dauko ba toh be shirya aure ba.
Bayan wata biyu da sati daya da kafuwar daular Rugar Shehu, Usman ya shirya tsaf da shirin zuwa dauko ajiyar sa, in da ya wakilta Muhammadu Bello ya kula da Rugar su kafin ya dawo.
Komawar shi Kano ya so ba shi wuya kasancewar ba da mota su ka shiga dajin su ba, tafiyar kasa ce su ka yi mikakkiya. Da kyar da taimakon Allah ya sami motar da ta kai shi Mambila, daga nan ya sami motar Taraba, a can ne ya sami na Kano direct.
Ganin Usman da kuma yanda ya canza ya kara kwarjini kamar wanda ya sha maganin kwarjini ba karamin mamaki su Isa su ka yi ba, musammam Jauro da ya kama kan sa dan shi kan sa ya san akwai bambamci tsakanin Usman din da da na yanzu, har da yanda Ammy ta karbe shi hannu bibbiyu. Ta dawo Kano ita da Falmat bayan sun fita takaba. Bakin ta ya ke jin labarin auran Halitta wacce a yanzu haka ta na can Saudiya tare da mijin ta. Yayi murna kwarai tare da mata addua. Amma ko da Ammy ta kawo maganar Zainab, ta na mai tambayar sa dalilin da ya sa ya tafi babu sallama sai cewa yayi
"A yi hakuri abin ne ya zo min a gaggawa, shi ya sa ma na dawo na gyara, ta na nan ne?
Ya tambaya ko Zainab ta na nan ne ba dan ya na so ya ji amsar da Ammy za ta ba shi ba, abu daya da ya sani shi ne ya zo tafiya da ita, ko ta nan ko bata nan kwana daya kacal ya ba ta za ta dawo ta same shi har in da ya ke.
Ammy ce ta masa bayanin Zainab din ta na makaranta, jami'ar da ta ke yi a Yola, Amma kada ya damu ai ta ma kusa fara jarabawa, kuma da ta dawo be fi watanni biyu zuwa uku za su kara su gama makarantar gaba daya ma
'ai kuwa na ta makarantar ya kare daga gobe!'
Cewar Usman cikin ran sa, zahiri kuma cewa yayi
"babu komai ai kamar yau ne, Allah ya ba da sa'a"
BQ din nan dai da Malam ya basu nan aka sauke shi. Allah ya amsa adduar shi har lokacin akwai wasu daga cikin kayan Zainab, dan haka a daren ranar ya yanki daya daga cikin bakaken rugunan ta da ta bari a dakin, ya hada da wani ganyen turare da ya taho da shi daga Rugar Shehu. Sai da ya kulle dakin sannan ya hada garwashi ya ruru sosai yayi jajur, sannan ya dauki kyallen da ya yanka, ya hada da ganyen turare ya dora kan garwashin, yana murmushin mugunta ya ke duban yanda tufar ke konewa hayaki na ta shi, ya ce
"Kamar yanda tufar ki ke konewa haka zuciyar ki za ta na mi ki kuna matukar ba ki baro duk abin da ki ke kin zo gare ni ba Zainab, kamar yanda hayakin nan daya ke bin daya haka za ki bini duk in da na sa kafa....matata Abu"
***
Duk yanda Zainab ta so ta yi karatu daren ranar kasawa ta yi, ga shi ta na da jarabawar safiya. Washagari tun da asuba ta hado kayan ta, ba tare da ta nemi shawarar kowa ba ta na kallo kowa na shirin fita jarabawa amma ta tsallake ta dauki hanyar Kano a motar haya abin da ba ta taba shiga ba tun da ta fara karatu a Yola. Sai yamma likis ta isa Kano, wanda tun isowar ta jikin Usman ya bashi dan haka shi ma din ya fita kofar gida da shirin sa ba tare da ya bari su Jauro sun san da fitar shi ba. Be yi cakakken minti talatin da tsayuwa kofar gidan ba sai ga dan sahu ya zo ya tsaya gaban gidan Malam. Zainab ta fito sanye da bakar abaya, hannun ta rike da dan akwatin ta da ta debo kadan daga cikin kayan ta. Ta na sallamar dan sahu ta karasa gaban Usman ta tsaya, wanda tun saukowar ta ya tsura mata Ido cike da tsana. Wani farin mayafi da ya sha ado da kaloli irin na fulbe ya mika mata, Zainab ta sa hannu ta karba.
"Ki yafa shi yanzu"
Cewar Usman. Zainab ta amsa da toh sannan ta ware mayafin ta yafa.
"Sunan ki Abu...."
Cikin gasgatawa ta furta
"Sunana Abu..."
Usman ya kara da
"Ni mijin ki ne Shehu"
"Kai miji na ne, Shehu"
"Mu na hanyar komawa gida Rugar Shehu"
"Mu na hanyar komawa gida Rugar Shehu"
Zainab ta sake maimaitawa.
"Duk wanda ya mi ki magana a hanya kada ki tanka masa, matukar ba ni Shehu mijin ki ba ne ya baki umarni kin ji ko?"
Zainab ta na mai girgiza kai cike da ladabi ta furta
"Toh miji na Shehu..."
Kallan ta yayi sama da kasa ya gamsu da yanda mayafin da ta yafa ya dan ragewa rigar da ke sanye jikin ta kyau, cikin ran sa ya na mai neman yafiyar Ammy da Malam, ya ce da ita
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.