Complete Hausa Novels

Auren Shehu Part 2 Complete Hausa Novel

Reading file: Auren_Shehu_Part_2_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 43 of 46

Zainab na jin haka ta shuna baki. Ta mike Tsaye ta na gunguni. Doguwar rigar atamfa ce jikin ta, dake jikin jego ta kara cikowa ta koina ta murmure. Dankwalin atamfar ta daura irin wannan daurin da ake kira ture ka ga tsiya, ta ja mayafi ta yafa a kafada. Ganin ta na kokarin daukar Shehu Ammy ta furta

"Ki bar shi mana tun da bacci ya ke"
Ta na mai aza shi kafada ta ce

"Ah ah ai na zaci barka su ka zo yi, na je ma yan barka ba jinjiri?"

Ba ta tsaya ta saurari amsar Ammy ba ta yi waje fuu kamar wacce za ta tashi sama.

Usman kuwa tunda su ka zauna ya tsurawa kofa idanu duk da Umar ne zaune daidai kofar. Umar na kokarin masa hira amma ina hankalin sa ba ya jikin sa, yayi nisa baya jin kira.

Sallamar ta da shigan ta falon lokaci daya ne, idanun ta kan Umar ya fara sauka, in da shi kuma Usman ya shiga duban ta cikin rudani. Idan aka dauke yanayin tsiwar da ta shigo da shi, da Kuma tsayin ta komai na Zainab ya canza, dama tunda Zainab dirarriyar mace ce, Amma yanzu sai ta zama irin matan nan da aka fi sani da zaratan mata, kamar wacce makerin dare ya kyara. Baban abin da ya saka shi cikin rudani shi ne yanda ya ga alamun kumburi kafar ta, da kuma yanda alamun jego ya bayyana dukkanin gabobobin jikin ta, dadin dadawa ga jinjiri kwance kafadar ta.
Ba kunya ta gama karewa Umar kallo tas, ta tabbatar ko mai kama da shi ba ta sani ba, ta na kokarin kallan Usman ta karasa ciki, fadi ta ke

"Sannu da zuwa, gashi kuma ni ban san ku ba bare na san a dangin wa ku ka zo min........"
Cak ta tsaya ta na duban shi kamar yanda shi ma idanun sa ke cikin na ta. Idanun da har ta koma ga mahaliccin ta ba za ta taba mantawa ba. Baki ta bude da niyar magana, bayan sakanni ta sake rufewa, ji ta ke tamkar mafarki ta ke, sai kuwa ta lumshe idanun ta na dab wani dan sakanni, sannan ta sake budewa. Mai kama da Usman din nan dai be bace ba, sai ma tasowa da yayi ya nufo ta. Kallan sa ta ke tun daga sama har kasa, shigar da yayi ya sa ya kara kwarjini kai ka ce wani basarake ne ko kuma wayayyen dan kasuwa wanda ya ci ya tara. Ba ta dada gasgata abin da zuciyar ta ke fada mata ba, sai da ya tsaya gaban ta, ya kalle ta, sai ya kalli jinjirin da ke kafadar ta da lokacin be samu ya ga fuskar sa ba, cikin yanayi mai wuyar fasaltuwa ya furta

"Abu......"

Zainab ta runtse idanun ta dan tun daga kwakwalwar kan ta, har zuwa yatsun kafarta ta ji kiran.

"Abu......"

Ya sake kiranta ya na kokarin ruko ta, Zainab ta ja da baya da sauri ta na mai girgiza masa kai. Murya na rawa ya furta

"Na sani Abu, na san ban kyauta mi ki ba, ban mi ki adalci ba......."

Juyawa ta yi da sauri za ta fita, sai a sannan Usman ya ga fuskar takwarar shi, wanda ganin sa sai da ya zauna dirshen kasa.

Umar ne ya taso ya tsugunna gaban sa tare da taba kafadar sa. Usman ya dago da sauri ya dube shi, gaba daya ya manta da zaman shi a falon. A hankali ya furta

"Da na ne.....na zalinci Abu Umar"

"Ba da niya ka yi ba, za ta fahimce ka, za kuma ta yafe ma ka....."

Cewar Umar yana kokarin karfafa gwiwar Usman. Zainab kuwa da ta shiga ciki ta tarar da Ammy, Anty Sauda, da Hallitta zaune falo ko takan su ba ta bi ba, ta shige dakin ta yayinda hawaye ke gudana daga idanun ta. Kallan kallo su ka shiga yi, kowanne na tunanin ko lafiya? Kafin daga bisani Ammy da Halitta su ka bi bayan ta, Anty Sauda ta yi zaman ta cewar ta koma menene ita dai ta na daga nan.

Ammy da Halitta sun yi juyin duniyar nan akan Zainab ta fada mu su dalilin kukan ta, Amma ta ki, sai kai da gwiwa da ta hada ta na rera kuka mai sauti, in da Shehu da ke kwance kusa da ita ya ke taya ta da na shi kukan.

Ganin ba za su sami abin da su ke so kusa ba Halitta ba ta dau Shehu ta mikawa Ammy tare da fadin

"Ammy bari dai na bi sahun bakin da ku ka ce sun zo gun ta, babu mamaki sakon mutuwa su ka zo mata da shi"

"Eh gaskiya, maza bi bayan su, Allah ya sa dai ba su tafi ba"

Da saurin ta ta fita. Anty Sauda na tambayar ko lafiya? Ta ce mata ta na zuwa. Cikin falon Dady tadda su zaune in da Zainab ta bar su. Kallo daya ta yiwa Usman ta gane shi. Fuskar ta dauke da emotions iri daban daban ta furta

"Me ya sa Usman? Me ya sa sai yanzu ka zo? Me ya makarar da kai har haka? Kar ka fada min duk watannin nan ba ka farga da kuskuran da kuka tafka ba sai yanzu?"

Be taba tunanin wani daga cikin dangin Zainab za su iya ganin shi su kyale ba tare da sun masa wankin babban bargo ba, Amma duka tunanin na sa ya manta Malam na da diya kamar Halitta, wacce har abada ba za ta taba canzawa ba. Ya na mai duban ta cike da godiya ya ce

"Na yi kuskure mafi girma kanwa ta... Shin ko za ku iya yafe min?"

"Yafiyar mutum daya ce mafi muhummanci a gare ka, shin za ka zauna ne nan ka na dana sani, ko kuwa ka shirya gyara lamarin ka da iyalin ka?"

Cewar Halitta ta na mai duban Usman. Wanda ya tashi cikin azama ya na fadin

"A shirye na ke kanwata"

"Toh bisimillah"

Nan su ka bar Umar, Halitta na tafe Usman na biye da ita, a bakin kofar ya dakata Halitta ta shiga ta ce da Ammy ta dan shirya za ta shigo da bakon da ya zo.
Har ya shigo ya tsugunna gaban ta ba ta gane shi ba, be sa ta cikin rudani ba sai da ta ji ya bude baki ya ce

"Hajiya ban san da wani ido zan kalle ku ba, ban san da wani baki zan ba ku hakuri ba......"

"Waye wannan wai Halitta?"

Ammy ta katse shi cikin kin gasgata zuciyar ta. Ta na nuna shi da dan yatsa ta sake furta

"Kar dai wannan maci amanan maigadin nan da Malam ya dau diyar cikin sa ya basa amma karshe ya saka mana da sharri"

Jin haka Anty Sauda ta ware idonu zuciyar ta daya ta furta

"Haba ke kuwa Hajja Aleesha, duba ki gani fa da kyau! Ina ke ina hada wannan wayye kamulallen mutum mai daraja ta wannan tsinannen almajirin...."

"Haba Anty Sauda, kada ki manta wannan da ki ke magana akai shi ne mahaifin dan da Yakura ta haifa, in da kara ba kya zagi uban dan Yakura ba"

Jiki sanyaye Anty Sauda ta ke kara duban shi, wato lalle da gaske shi ne mijin Yakura? Toh dama karya ake da aka ce shi maigadin gidan Malam ne, ko dai dama bad da kama yayi tun asali dan masu hali ne ya zo mu su a almajiri. Shi dai Usman ya sunkuyar da kai, zai iya jure duk hukuncin da za su dauka matukar ba za su hana shi iyalin sa.
Anty Sauda na sosa kyeya ta ce

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.