Majnoon Littafi Na Daya Complete Hausa Novels
Reading file: Majnoon Part 1.txt
Chapter 19 of 36
Daddy yayi saurin cewa "subhanallah" sai kuma yayi shiru
Abba yayi ajiyar zuciya sannan yaci gaba dacewa "to shine muka kawota asibiti, bayan mun kawota asibiti, likita yake sanar damu cewa tana daf da kuma da cutar hawan jini matukar bamu nema mata abinda take soba domin tunani da damuwa sun mata yawa, shine bayan ta farka aka tambayeta meye matsalarta anan take sanar damu cewa ita mahaukacin nan takeso, naso nadauki maganar tata a shirme amma Likita yace bai dace nakasa ceton rayuwar 'yataba akan wani banza kudiri nawa, Likitan ne yabada tabbacin cewa zai iya warkar da mahaukaci matukar ba asiri akayi masa ba, nikuwa shine nabi shawararsa mukaje aka daukosa, a garin daukosa kuma mota takara kadesa, yanzu haka likita yasanar dani cewa bayan cutar hauka dake jikinsa, kwakwalwarsa tayi losing wasu abubuwa wadanda koda yasamo lafiya bazai iya tunawaba, abba yadan shiru yana share hawayen dake zubo masa, jikin daddy duk yayi sanyi tausayin majnoon yaji sosai aransa, bayan abba yashare hawayensa yaci gaba dacewa "alhj kayi hakuri, kuma kabawa yaronka hakuri akan maganar aurensa da rumaisa, domin bazan zamo mai sonkaiba akan abinda 'yata kesoba, ni a yanzu farin cikinta kawai nake nema"
Daddy yayi yasauke nunfashi edonsa sunyi ja sosai, shima shirin yin hawayen yake, sai dai yadanne aransa, domin tunba yauba yaso faisal yadaina zancen auren rumaisa amma yaki, to yanzu dai komai yazo karshe, daddy yace "alhj bazan taba kamaka da laifi ko cin amanaba domin wannan hukuncin daka yanke ko nine hakan zanyi, fiyema da hakan zan iyayi domin kawai in nemawa yarona farin ciki, amma wannan shawarar daka yanke itace mafita mai kyau, mukanmu munsan dacewa rumaisa batason faisal, saidai munyi amfani da ikon mune na zama iyayenta zamu aura mata shi a dole, gaskiya bazanga laifin kaba, kuma najidadi sosai daka taimakawa yaron nan Allah yasaka maka da khairan"
Murya a sanyaye abba yace "ameen"
Sai kuma sukanyi shiru, kamar kurame saicen daddy yace "saidai wani hanzari ba guduba, abba yayi saurin dago kansa yana kallonsa "menene "
Daddy yace "sai dai akwai matsala daya, matsalar kuwa itace manta komai dayayi, domin zai iya tunawa da komai aduk lokacin dayaga abinda yataba faruwa dashi abaya, to idan yatuna ya kake ganin kenan zakayi idan yakasa amincewa da auren rumaisa, kokuwa yagudu yabarku"
Abba yadanyi shiru kamar bazaiyi magana, sai cen kuma yace "idan ma hakan zata faru tosaidai a bayan auren su, domin ana sallamarmu a asitibin nan zan fara shirye 2 aurensu, kaga kenan idan daga baya yatuna zuwa lokacin zai iya kasancewa sun samu haihuwa ita dashi, kaga kuwa bazai iya guduwaba yabar iyalansaba"
Daddy ya girgiza kai yace " kumafa hakane, Allah dai yasa shiyafi zama alkhairi"
Abba ya amsa da ameen , sannna yace "mukoma ciki koh"
Daddy yace "eh muje, yanzu ma zamu wuce gida, domin inaso naje wani gun, zuwa gobe insha Allah zamu dawo mukara dubata,
Abba yace "to shikenan Allah yakaimu goben"
Nan dai suka dan daidai kansu kafin sukoma cikin asibitin amma dakaga yananin daddy zaka gane cewa baya cikin farin ciki, domin edon nan nasa sunyi jajir....
Facebook page:- Abdul-mr, smiles novel's
Website:_www.abduljega.blogspot.com
[10/20, 10:46 PM] ‪+234 905 395 7618‬: _Title:-_ *MAJNOON*😴
_The mad man_
_Author_:- *MR, SMILES*😃
81 and 82
Via *OHW*
_A love story_ðŸ’Â
Dakin jinyar rumaisa suka karasa, momy tana zaune akan kujerar roba, suka shigo, daddy yadanyi murmushi karfin hali ya dube umma sannan yace "toh mu zamu wuce, Allah yakara bata lafiya" sai kuma ya juya ya dube momy yace "tashi muje koh" momy ta mike itama tana kallon yanayin fuskarsa kamar marar gaskiya, saidai ta basar ta juya gurin su umma da hajja luba "Allah yakara bata lafiya yasa kaffarace" su umma suka amsa da ameen,
Sannan daddy yasanar dasu cewa gobe zasu dawo, yana gama sanar dasu, sukafice daga dakin,
Suna fita abba yasamu guri yazaune, anan yafara bayyana musu komai da yafaru tundaga zuwa dauko majnoon dakuma mantawa da abubuwan da yayi dama komaima saida yasanar dasu,
daga karshe dai yace musu yanzu an cire haukar dake kansa,
Bakaramin dadi rumaisa tajiba, umma ma haka, hajja luba kuwa tsoro lamarin yabata itamadai tana tsoron kar yaje yatuna daga baya ya gujesu,
Tayiwa abba magana akan wannan dalilin kawai saiya nuna mata cewa bakomai. Shidai kawai 'yarsa tasamu lafiya, edonsa ya rufe baya ganin komai sai lafiya 'yarsa ,,,
******** ******** ******
Tunda suka shiga mota daddy bai furta uffaba haka zalika momy, har suka karasa gida, itadai ta lura da yanayinsa yana cikin damuwa,
Suna karasa gida a falo suka dire, daddy ya zaune akan kujera ya furzar da iska,
Momy tadan dubesa kadan, bayan tazauna ta kasa hakura tanason tasan matsalar mijinta "abban faisal wai meke damum kane naga tunda muka baro asibitin nan baka cikin hankalinka, yana yinka gaba daya ya chanza, wai meke faruwane"
Daddy ya dago edonsa ya kalleta, yajima yana kallonta kafin yace "zan iya bawa faisal kowane gata da d'a ke samu agurin mahaifinsa, amma bazan iya saka soyayyarsa a Cikin zuciyar dabata sonsa ba, ni mahaifinsane zan kara umartarsa akaro na biyu daya fita harkar rumaisa, idan kuwa yaki magana to wlh zamu samu sabani dashi, domin ni bazanyi sonkai irin nasaba na kashe 'yar aminina"
Tunda yafara maganar momy ta tsorata sosai domin tana fargatar ayya kuwa faisal zai iya rabuwa da rumaisa, cike da mamaki da fargaba take tambayar daddy" meya farune ko wata matsala takoma taso wane"
Nan daddy ya fede mata biri har wutsiyarsa kamar yadda abba yamasa bayani, itama ta gamsu sosai kuma ta tausayawa rumaisa bakaramar girgiza tayiba dataji labari saida tayi hawaye,
Jikinta duk yayi sanyi, murya kasa2 tace "nima na goyi bayan maganarka domin nina bazanso araba wannan soyayyarba ta rumaisa da majnoon ta hanyar faisal ba, kawai fatana Allah yasa shiyafi zama alkhairi" daddy ya amsa da ameen, sannna yace tatashi taje tahada masa ruwanka zai fita yanzu"
Momy ta mike taje tahada masa ruwan wanka, sannna tazo tasanar da shi yatashi yaje yayi wanka ya shirya sannna yafita,
****** ******* ****
Daga dawowar abban zarah daga dubai yasa akayi mata transfer aka maida wani company,
Daya daga cikin nasa, ta samu natsuwa sosai, kuma ta daidai kanta ta rage tunanin faisal a kai kai, daman ganinsa ne kesa tana yawan tunaninsa, to yanzu kuwa tadaina ganinsa,
Tafito daga wanka tana shirin fita aiki feena tashigo dakin, zarah ta dube "yan mata lafiya kuwa"
Feena tayi saurin haurawa kan gadon ta kwanta tana dariya "lafiya lau anty zarah kawai fira nazo muyi, yau surutu nakeji"
Zarah tadanyi dariya sannna tace "nikuwa gashi yanzu fita zanyi, sai dai idan zakimun tatsuniya toh zan saurareki"
Dariya feena tayi kafin tace "toh shikenan anty zarah zan miki, badai kinason ta gizo da koki ba"
Zarah tace "eh inaso fara muji" zarah tahaura kan gadon tana kallon feena cike da farin ciki,
Feena tace "wata rana gizo...." sai kuma ta tsaya tana kallon zarah
Zarah ta daga mata gira "yane yan mata naji kinyi shiru"
Feena tace "anty zarah, sonake na tambayeki"
"Uhim ina jinki" zarah tafada tana kallon Feena
Feena tace "anty zarah wai naga yanzu kindaina kuka ko kindaina zuwa gurin faisal ne"
Zarah ta tsuke fuska tadakawa feena tsawa "tashi kifita daga dakin nan" ta nunawa feena kofa
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.