Complete Hausa Novels

Zuma A Baki Part 2 Complete Hausa Novel

Reading file: Zuma_A_Baki_Part_2_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 3 of 33

*ACIGABA DA BI WANNAN SALON NASA DABAN YAKE*

*ZUMA A BAKI...!*🌹
    {  Painful love Story  }
           

         NA
*AUTAR MANYA*

_HOME OF QAULITIES WRT ASS..._

                        *003*

Daka tawa yayi da tura gate ɗin dayake ƙoƙarin yi tare da aje aslam a ƙasa sannan ya janyo islam ya turon ita gabana.
Ya kalleni yana sakin murmushin sa na rainin hankali kamar koda yaushe idan nai masa maganar yarana.
Kafin ya mayar da kallonshi gurin islam.
"My love je mama tana son ganinki"
yafaÉ—awa yarinyar haka dayake ire iren sunayen dayake gayawa yaran nasa kenan.
Wani irin daÉ—ine ya kamani jikina har rawa yake a lokacin danaji furucin nasa gareta.
Amman kafin na ɗago idanuna na dire akanta naji sautin kukan ta! tare dana gudunta tai wurin mahaifinta ta riƙeshi katamau tana kuka!.
Cikin gwarancin su na yara naji tana cewa.
"Daddy! ban canci ba daddy kaini wurin inno".
Ta ƙare faɗin haka tana wani irin kuka wanda nima ya bawa nawa kukan damar fitowa fili.
Cikin rawar jiki na karasa gabanshi ƙwarjinin shi da kamshin turaren shi suka kuma kara gudun zuciyata hannuna na ɗora a bayanta ina kuka ina magana.
"Haba islam nifa na haifeki dan Allah kijuyo na kalleki islam É—ina"
Nafaɗa ina kokarin ƙwaceta daga hannunshi still ita kuma tana kuma ƙamƙame uban nata tana shigewa jikinshi.
Cikin sauri naga ya bude gate É—in gidan inna ya tura su ciki kana ya rufo sannan ya juyo yana kallona fuskarshi babu sukuni.
"Yanzu maye amfanin sakamin yarinyata kuka da kikai ke hakan kina ganin kin kyauta min kenan?"
YafaÉ—a a zuciye har wani mayar da numfashi yake.
Ganin kamar ze doken ne yasa naja baya daga wurin shi.
"Amman dai kaima kasan ina da hakki akan yarana ko? tunda kai baka da imanin da zaka kawon su nito inada ƙafar dazan biyoka koda zaka zaneni naga wata ƙatuwa ma ka bawa su take riƙonsu amman ni uwarsu bazaka bani ba".
Nima nakai maganar a tsananin zuciye.
Murmushi ya saki kamar koda yaushe domin mawuya cin abune kaga Ɓacin ransa a fili yana da danne ɓacin rai sedai tsananin soyawa mutum aya a hannu idan ka shiga gonarshi.
Ɗago ƙwayar idanunshi yayi tare da zubamin dukkan idanun shi yana kallona dasu lokaci ɗaya naga alamun ɓacin rai tattare dashi.
Takowa yake sannu a hankali har zuwa gabana yay min tsaye akaina kamar dogari.
Ya fini tsayi nesa ba kusa ba hakan yasa naÉ—an ja baya kaÉ—an ina haÉ—e jikina wuri É—aya domin tsananin kusancina dashi yasa nakejin tsohon tsumin daya kwana biyu da lafamin na neman tasowa.
"Dan Allah ki kuma mai maita me kika faÉ—i? ke yanzu har kina da bakin faÉ—in abin da kika ce? ko kin manta abin da kikai a baya?"
Murmushi ya kuma yi.
"Gwara da kika gani da idanun ki wallahi Aisha! kona baki yaran nan bazasu barki kiyi bacci ba domin basu sanki ba, kina mahaifiyar tasu amman kika kasa basu hakki irin na uwa! ko kin manta yadda uwa keda hakki akan É—a haka shima É—an keda hakki akan uwa?"
Hanky ya fiddo daga aljihun jeans É—insa ya goge zufa sannan ya cigaba da cewa.
"Allah sarki babarsu in kinada ƙarfi kizo ki amshe su, kuma matar da kike cewa na bata su, ai ta fimin ke sau dubu ɗari tunda ita matata ce ta sunnah keko fa kokin manta kalamin ki gareni?"
YafaÉ—a yana kallona.
"Umar na tsaneka bana ƙaunar ka ka sakeni nagaji da zama dakai ka kwashe gayyar tsiyarka ka tafi dasu bana bukata"
Ya mai maita maganar yana jefamin fitinannan kallo.
"Laifi ne danna kwashe ƴaƴana! yaran da basu cika wata uku ba kika yaye su yaran da madara ce tai musu madadi da nonon uwa mai ƙara lafiya ajiki, basu da kowa seni kamar yadda nima bani da kowa sesu nine uwar su nine ubansu ninaci kashi da fitsarin su keki faɗi ɗaya daga cikin abinda kikai musu na jin ƙai a matsayinki na uwa.......haihuwa kaɗai kika sani shima cikin da kikai barazanar zubarwa bada ban Allah ya duba wahalar danai wajan samar dashi ba da tabbas yajima da faɗuwa a rariya sabida wata banzar son zuciyarki shasha kawai mai baƙar zuciyata data fuska har abada hakkina dana yarana baze barki ki kwanta lafiya ba".
Ya ƙarasa maganar cikin ɓacin rai.
"Wallahi Aisha bada ban karamcin mahaifanki ba da har abada bazaki kuma ganin yaran nan ba wallahi! da sena nesan taki dasu nisa na har abada, sedai kash niɗin cikakken ɗan halak ne wanda baya mayar da alkairi zuwa sharri tabbas mahaifan ki sunmin halaccin daya zama dole nima na kamanta, amman fa ki sani Aisha na tsaneki tsana mafi muni har abada bazan taɓa sonki ba kuma kada ki saka ran zan kuma sauraranki kamar iwar haka sabida ayyukan dake gabana sun fimin ke mahimman ci acikin rayuwata"
Yafaɗa yana mai fir fitomin da manyan idanun shi waje kana yaja ƙafafunshi da ƙarfi yabar ni a wurin ban kumajin duriyar shiba se karar turo gate ɗinshi kurum.
"Innalillahi wa'innah ilaihirraju'
Kalmar danake ta faman mai maitawa kena da ƙarfi kuma a bayyane.
Ƙarfin ambaton kalmar ne ya bani damar jan ƙafafuna da sukai min nauyi nabar kofar gidan kamar mahaukaciya haka na faɗa cikin gidanmu da kallo Anty ta bini tana min magana amman ban kulata ba har seda na dangana da ɗakinmu na kife kaina a gefen gado ina risgar kuka kamar wadda aka cemin yau baba ko anty wani ya rasu.
Cikin haka naji alamun shigowarta zama tai a gefena tana mai kallona.
"Wato ke humairah haka rayuwarki zata ƙare a kuka? kullum na fuskanci in Umar yazo sekin shiga wannan hali, toki bude kunnen ki da kyau kijini inma banzan tunani kike akan umar to kidaina sabida ayanzu ya miki nisa yakamata ki kauda hankalin ki gareshi ki fuskanci abinda yake gabanki"
Anty mahaifiyata ta faÉ—i hakan fuskarta babu sukuni.
Wani ƙululun abu ne yazo ya tokaran kirjina hannuna na saka na dafe wurin ina mai kallonta.
"Anty ni a yanzu nafi bukatar ya bani Æ´aÆ´ana ba wai soyayyar shiba tayaya anty kina kallo gani amman yaje yay aure ya bata su"
NafaÉ—a ina sakin marayan kuka!
Sakin baki anty tai tana kallona gaba É—aya tagama cika da mamaki.
"A,a to shi dutse ne daze zauna haka? tunda keda kika haifa kin nuna bakya so se Allah ya kawo mai sonsu, maganar gaskiya inma kishin umar kedamun ki kima daina sabida ayanzu yay miki nisan da bazaki taɓa samun shiba"
Kuka na saka a wannan karon mai karfi wanda yasa anty tai saurin fita tabarmin É—akin.
"Na shiga uku! ni humaira mai ke shirin faruwa dani? kodai na faÉ—a soyayyar tsohon mijina ne wanda nasan yaymin nisan da har abada bazan kamo shiba"
Koma wa nai saman gadon daɓar na kwanta ina risgar kuka!
Tsananin tunanin abinda ya shuÉ—e a baya ya fara dawomin daki-daki kamar haka.

*ASALIN LABARIN PAGE 4 INSHA ALLAH*
*ZUMA A BAKI...!*🌹
{ Painful love Story }

NA
*AUTAR MANYA*

_HOME OF QAULITIES WRT ASS..._

*004*

Asalin labarin.

Sunana Aisha amman a gidanmu ana cemin (Humairah) nice Æ´ata biyu a wurin mahaifina malam yusuf wanda muke kira da (baba) da kuma mahaifiyata khadija da muke kira (anty).
Yaya imran shine babban É—a a wurin mahaifinmu da mahaifiyar mu kuma muna da tazarar shekaru sosai a tsakaninmu domin ya bani kusan shekaru goma sha biyar kafin Allah ya bawa anty wani cikin ta haifeni dagani se nafisa se kuma auta anisa.
Muna zaune a unguwar ɗorayi amman a salin su baba ƴan ƙauyen tofa ne mahaifan su, su biyu suka haifa daga babana yusuf se ƙanin shi sulaiman wanda muke ce masa baffa karami mahaifiyata anty itama ƴar nan dawakin tofar ce domin auren zumunci ma akai mata ita da babana wanda ita ta kasance ɗiyar ƙanin babansu uwa ɗaya uba ɗaya.
Anan tofa baba ya fara zama da anty cikin gidansu na gado wanda mahaifin su malam nuhu ya gina yakuma zauna cikinshi shida matarsa Aisha indo har Allah yayi musu rasuwa se mahaifina ya cigaba da zama agidan shida kaninshi.
Anan anty ta haifi ya imran dayake itace babba cikin gidansu yasa ƙannenta ke ce mata anty wanda jin haka ya imran ya taso da faɗa mata hakan.
Baba yana zuwa nan cikin kano sarin kayan gwari ( kayan miya ) yana kaiwa can tofa ya saidar ranar sati ya kuma dawowa ya siya anan Allah ya saka mai nasibi har baya kaiwa satin, yakan zo ma a kwanaki biyu ya siya yaje ya saidar.
Shikuma kaninshi baffa yana aikin sana'ar gini ne ma'ana leburanci.
Yawan zirga-zirgar datai yawane yasa(ayiya) mahaifiyar anty dayake mahaifin anty shima ya rasu mahaifiyarta ce kaÉ—ai ta rage se kannenta guda huÉ—u da suke aure suma anan tofar, ta kira baba ta nemi shawarar shi akan yakamata ko haya ce ya kama anan cikin garin kanon ya tafi da iyalinshi sabida ya ragema kansa zaryar baba bai musawa ayiyah ba anan yazo cikin gari ya sami abokinshi.
Malam muhammadu sarkin gida wanda suke aminci sosai dashi sarkin gida É—an garin katstsina ne domin sana'ar gini ce shima ta kawoshi kano dalilin dayasa ake kiran shi da sarkin gida kenan sabida yana harkar ginin gidane yana kuma yin hanyar samawa mutane haya.
To sun haÉ—u baba ne lokacin da yaje siyan kayan miya anan Æ´an kaba shima kuma baban yaje sari daga gaisuwa kuma abun kamar wasa seya zame musu aminta.
Shwarar sarkin gida ya nema akan yana son ya sama mai hayar É—aki mai sauki domin ya dawo da iyalinshi kusa shima kuma yana son ya sami É—an wajen daze na sayar da kayan miyan shi anan base ya dinga tafiya kauye ba.
Cikin raha sarkin gida yace masa.
Aikuwa agidan dani ke haya muna da sauran É—aki É—aya in kana so dubu goma sha biyar ne seka kama anan É—orayi unguwar bello.
Baba baiyi musu ba ya amince wa sarkin gida haka suka rankaya zuwa É—orayi, cikin mutunci sarkin gida ya shigar da baba gidan dayake hayar ya nunawa baba É—akin.
Batare da ɓata lokaci ba baba ya amince har ya bada kuɗin ɗakin sedai ya nemi sarkin gida akan dan Allah yana son ya kuma samawa ƙaninshi shagon daze na kwana.
Murmushi sarkin gida yayi tare da cewa baba ai babu wani abu akwai shago a kofar gidan dama babu kowa se kanin nashi yana kwana anan É—in.
Sosai baba yayma sarkin gida godiya kana ya tafi tofa suka cigaba da shirinsu na komowa kano.
Sosai Æ´an uwa da abokan arziki sukaita jajantawa anty na rabuwar su sabida an saba sabo baÉ—an kaÉ—an ba haka su anty suka rankayo zuwa cikin garin kano anan cikin unguwar É—orayi.
Abinda ze baka mamaki shine yadda matar sarkin gida wadda zata ɗan girmewa anty da tazara mai yawa ta tarɓi anty kamar kanwarta haka tai musu girki mai rai da lafiya kana ta taya anty kintsa kayanta.
Sosai anty taji daÉ—in karamcin Inna matar malam muhammadu wanda taji ana ce masa baba shima kamar yadda ake cewa malam yusuf mijinta zaman anty da inna zamane na son barka babu wata matsala datake faruwa kamar zamane na Æ´an uwan taka.
Baba inya fita wajan kayan miyarsa da safe shima kuma baba sarkin gida haka yake fita harkar ginin shi da safe basa dawowa gida se dare sabida baba sarkin gida ma da sulaiman kanin baba suke tafiya aikin.
Lokacin yaya imran yana da shekaru tara a duniya baba sarkin gida da kansa yakai yaya imran makarantar primary yana masa wasa.
"Kaganka sa'an Umarina nima na kusa na É—auko shi na haÉ—eku waje É—aya ku xama abokai"
Murmushi baba yayi tare da cewa.
"Lah daman malam kana da yaro aini ban saniba wallahi ca nake Allah bai kawo ba danaga gidan babu kowa daga kai se inna"
Dariya baba sarkin gida yayi kana yace.
"Ai ina da yarona sunan shi umari amman cika daji nake ce masa sabida jarumine na baroshi agida can ƙauye wajan mahaifina, yana koyar farauta sabida jarumtar shi, wannan dalilin nema yasa ake ce masa cika daji domin inya shiga dawa seya ɗauko ɓauna ko dai wani abun na namun daji".
Murmushi baba yayi kana ya dubi malam muhammadu.
"Amman malam niko ina ganin meze hana ka ɗaukoshi daga ƙauyen kazo nan ka gina masa rayuwa da ingantaccen ilimin zamani dana arabi ina ganin hakan zefi kodan yadda zamanin nan namu ya lalace komai sekana da ilimi ake yi dakai".
Cewar babanmu.
"Eh! nima haka nakeso to amman fitina ta tsofi kasan mahaifana sun tsufa kuma ni kaɗai Allah ya basu se kanwata ramatu ita kuma tuni ta rasu tabar yarinyarta guda ɗaya tana nan ƴar shekaru biyu wannan dalilin yasa suka dauki son duniya suka ɗora wa umari shida nuratu, kuma mahaifina mafaraucine domin shiyake da sarautar sarkin farauta na garinmu anan katstsina to baya son ya rasu baida magaji hakan yasa ya rike Umar wajansa yake fita dashi farauta ilimin arabic bani da hofi akan umari sabida yayi sauka tuni na bokon nedai babu ni yanzu babban tashin hankalina nasan tsoho baze yarda nazo da umari kano ba tunda nima da ƙyar ya barni nazo ciranin nan sabida nida ramatu kaɗai suka haifa ramatu kuma ta rasu se ƴarta nuratu, nikuma umar kaɗai na haifa kaga bamu da yawa sosai shiyasa suka ɗauki son duniya suka ɗorawa umari da nuratu amman yaya kake ganin zan bullowa lamarin?".
Cewar baba sarkin gida yana kallon babanmu.
Nisawa malam yusufa yayi tare da kamo hannun aminin nashi.
"Ina ganin ranar sati zamu tafi tare dakai can katstsinan naiwa tsoho bayani sosai yadda ze gamsu amman kafin nan muyi addu'a"
Sosai baba sarkin gida ya gamsu da maganar babanmu hakan yasa suka ida cin abincin su na dare kana sukai Æ´ar hirarsu sannan sukai sallama suka wuce É—akunan su.
Haka zaman ya cigaba har Allah ya nuna mana ranar sati.
Ranar asabar suka tafi can katstsina anan wata ƙaramar hukuma ta bakori cikin wani ɗan karamin ƙauye mai yalwar arziki, sosai tsoho mahaifin baba sarkin gida kamar yadda ake ce mai suka tarbi ɗan nasu shida abokin nashi.
Haka nan iyatu matar tsoho mahaifiyar sarkin gida tai ta nan nan dasu nan da nan ta kawo musu damin fura nasu na fulanin ƙauyen tare da ɗumaman tuwo.
Seda sukaci suka hantse sannan sukai sallah zaman hutu sukai har zuwa faÉ—uwar rana.
Tsoho ya kuma dawowa ɗakin da aka sauke su nan suka ɗan taɓa hira da ɗan nasa.
"Tsoho nikam ina umari?"
Cewar baba sarkin gida yafaÉ—i hakan cikin son ganin É—an nashi.
Murmushi tsoho yay tare da washe bakinshi mai cike da goro.
"Ai CIKA DAJI, yana can dauji ya tafi kaso ɓauna da barewa sabida gobe muke saka ran za,a bikin auren ɗan gidan dagacin dawa shine muke son kowa ya nuna jarumtar shi anan".
Murmushi baba sarkin gida yay kana yace.
"A,a kai masha Allah ubangiji ya taimaka, daman tsoho nazone akan kaÉ—an bani aron umari ina son ze tayani wani aikine acan kano amman ze dawo".
YafaÉ—awa tsoho hakanne sabida in yace masa tafiya ce ta din din bafa ze bari ba.
HaÉ—e rai tsoho yay.
"Kodai kazo ka tafimin dashi kamar yadda kai nesa dani kabar sana'armu ta gado ka koma can bariki kake zama baka da Æ´an uwa duba nan ko ina dangin kane amman ka ware kai É—aya".
Babanmu ne ya mike ya fuskanci tsoho cike da lafazi mai taushi yake tausarshi har Allah yasa ya yarje musu akan zasu tafi da umari amman baxe jima ba.
Sosai su baba sukai murna tare dayi masa godiya.
Umari bai dawo ba se goshin almuru.
Sosai babanmu yay mamakin girman umari inka dube shi bazaka ce ɗan shekaru goma sha biyu bane sabida ya girmewa imran da shekaru biyu namijine ingarma mai ƙirar ƙarfafan maza dogone sosai mai girman jiki farin bafulatani, tass mai mugun kyau na asali.
Cikin rashin sabo yake gaisar da su baba sabida shi bai wani saba da mahaifansa ba sabida tun daga yaye iyatu ta É—aukeshi.
Haka nan baba yayta jansa da labari shiko baya wani sakin fuska daga um se um haka yake basu amsa.
Washe gari su baba suka juyo hanyar kano da umari wanda sam shi tafiyar batai mai daÉ—i ba sedai yana marmarin yaga innarshi gefe É—aya kuma yana kewar nuratu É—iyar kanwar babanshi wadda suka kusan tashi tare sun shaku sosai ba kaÉ—an ba.
Sun shigo kano lafiya a hanyar ƙauyukan kano sukai mugun gamo da babbar motar kaya ta haye saman tasu motar.
Inda suka sami mugun hatsari umar ya karye a cinyarshi shi kuma babanmu idanunshi É—aya ya tsiyaye shiko baba sarkin gida bai ko shura ba Allah ya amshi ran abinshi.
Innalillahi wa'inna ilaihirra ju'un.
Haka aka É—ebu zuwa babban asibitin murtala.
Kafin a soma basu tai makon gaggawa baba sarkin gida kuma aka kaisa matuware.
Seda sukai kwanaki uku sannan aka sami bakin babanmu ya bada lambar wayar sulaiman baffa karami aka kirashi sosai iyalan su suka shiga tashin hankali.
Musamman inna datai katari da gawar mijinta da kuma kallon karayar tillon É—anta a take anan ta faÉ—i wajan bata motsi.
Da taimakon likitoci aka samu inna ta farfaÉ—o wanda garin gwaji aka gano tana É—auke da cikin wata biyu.
Haka aka sallamo babanmu da fulasta a idanunshi akayo gida da baba sarkin gida aka sallace shi zuwa makwancin shi.
Su tsoho basuji labari ba se ranar bakwai sabida matsalar network da babu a kauyen.
Mota kusan biyar sukai da dangi suka taho kano sosai tsoho yake kuka kamar babu gobe.
Haka nan iyatu da nuratu wadda karayar umari tafi komai É—aga mata hankali.
Seda sukai sati biyu sannan tsoho yace zasu koma kauye tare da su inna tunda umari yaÉ—an soma taka kafarshi.
Anan babanmu yasa kuka! wiwi yana cewa shikam abar masa su ze rikesu sabida yana tuna wasiyar abokinshi na cewa.
"Yusufa ni rasuwa zanyi dan Allah ga umari nan ka zame mai uba, ka taimakeni kada kabar É—annan ya koma kauye kabarshi a birni ya mori rayuwarshi ko dan ya tallafi mahaifana da mahaifiyarshi".
Da ƙyar tsoho ya yarda da rokon baba haka suka tafi aka bar inna da umari a hannun Allah a kuma hannun babanmu.
Umari yana warkewa babanmu yakaishi makarantar sakandire aji É—aya bayan an masa cuku-cuku ya zana jarabawar kwaman Æ´antaras tare da imran.
Haka suka taso shida imran tamkar uwa É—aya uba É—aya komi tare baba ke musu haka nan yake fama da É—awainiyar inna da anty wadda take É—auke itama da juna biyu É—an kimanin wata guda.
Rayuwa na tafiya cikin amincin Allah baba yana samun rufin asirin Allah gefe ɗaya kuma yana kula da iyalanshi tare da taimakon ƙaninshi sulaiman baffa karami wanda Allah yay masa nasibi ta harkar ginin dayake domin bayan rasuwar baba muhammadu sarkin gida, se ragamar harkar gine ginen ta koma kan baffa karami komai ya xamana na fitowa daga hannunshi.
Cikin wannan ƙadamin baffa karami yasai filoti anan cikin unguwar ya fidda ginin waje biyu a hankali yake ginin shi lokacin yakai kuɗin auren umma.
Ƴar nan makotansu wadda take ƴar ɗakin anty domin hatta zance a ɗakin anty akeyin shi.
Ahaka su umari suka shiga aji biyu a sakandire ranar da suka shiga aji biyu inna ta haihu zokuga murna wajan umar kamar ya lashe yarinyar da inna ta haifa wadda taci suna maryam.
Ranar suna baffa karami shiyay hakika sabida a wannan lokacin yamafi baba samun kuÉ—i.
Ranar da su anty suka tashi daga wannan gidan hayar suka koma gidan da baffa ya gina wanda yay ɗakuna biyu a ɓangaren shi ɗakuna uku kuma a ɓangaren babanmu na baba ɗaya na anty ɗaya na inna ɗaya se kicin da banɗaki.
Ranar da suka koma da daddare aka haifoni nazo duniya.
Sosai baba da baffa sukai rawar gani ranar suna na, domin haka danginmu na tofa suka cika gida ana shagali hatta su tsoho ba abarsu abaya sabida an riga an zama Æ´an uwan juna.
Tunda Umari ya saka idanun shi akaina ya kafa ya tsare ko anty wanka xata shiga tofa shizata barwa ni yana min wasa gaba É—aya gidanmu humaira ake cemin amman shi kaÉ—ai yake kirana da Aisha ko yace min nana baka ganin dariyar shi se akaina baka ganin kukan shi se bani da lafiya wanda har cutar shima yake kwanciya.
Suna jss three na sakandire nai shekaru biyu a duniya sosai yake min hidima da kuÉ—in shi dayake bin baffa gini yake samowa komai ni alokacin nima bani da magana seta yaya domin da sunanshi na buÉ—i bakina.
Tare muka taso da maryam kanwarshi komai namu tare, alokacin da muka shiga shekaru uku aka auro umma wadda itama ta shigo cikin su anty suka haÉ—e kansu su uku.
Kowa da sana'ar dayakeyi.
Shekaru na tafiya lokacin anty ta haifi nafisa umma ta haifi nuhu É—anta na farko nida maryam kuma mun shiga aji É—aya na primary.
Su kuma su ya umar suna jarabarwa karshe ta sakandire alokacin kuma yasai wani filoti dake gabanmu wanda ya tara kuÉ—in da kansa acikin kudinshi na aikin dayake bin baffa.
Sannu a hankali suka fidda fandishan lokacin sunyi candy shida ya imran suke zuwa wajan ginin tare da abokanshi na unguwa.
Da kansu suka soma ginin cikin amin cin Allah seda ya umar ya ginawa inna É—aki da kuma É—an tsakar gida sannan shima yay nashi É—akin ragowar filin kuma yace se nan gaba za,a cigaba da ginashi.
Ranar da inna taga ginin seda tai kuka haka suka tarkata suka koma É—an nan gaban layinmu amman kuma kusan kullum se inna tazo ko maryam koni naje.
Mun shiga aji uku a primary suka sami gurbin shiga jami'a anan makaranta B.u.k, sosai ya umar ya dage yana fita makaranta yana kuma harkar bin baffa wajan gininsu, wannan dalilin yasa wahalar rayuwa tai mashi yawa ga hidimar kanwarshi gata mahaifiyar shi, gakuma tawa wadda ya mayar da ita dolen shi.
Muma gidanmu yay albarka sabida anty ta haifi anisa umma ma tana da yaranta uku nuhu da sadiya da kuma hafiza,
Rayuwa tana tafiya lamura na sauyawa yanxu haka na shiga aji na shida xan zana jarrabawar fita a primary.
Alokacin abubuwa sun soma sauyamin domin ni sam bana son ya umar yana cemin matar shi sabida yadda kawayena kemin dariya suna cemin matar ƙato.
Na taso cikin wata irin ɗabi'a ta kafiya da taurin kai sam inna kafe a abu babu wanda ya isa ya juyani gani da ɗan karen baƙi kamar bayan tukunya saɓanin su anisa da suke farare tar kamar su baba.
Kullum ina zuwa makaranta baba yana wajan kayan miyarshi baffa yana wajan sana'ar ginin shi tare dasu ya umar.
Haka nan su sadiya suma suna xuwa makaranta rayuwa muke cikin rufin asirin Allah domin mu É—in bama su shi bane.
Lokacin dasu ya umar suka shiga lavel 2 alokacin muka shiga jss1 gaba É—aya alamun girma sun bayyana atare dani sabida daman tun usul ina da jikin girma duka duka banfi shekaru goma ba lokacin amman inka duben seka ce nakai sha biyar.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.