Abnur Complete Hausa Novel
Reading file: Abnur_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 15 of 24
*Page 16*
Itama durƙushe wa tayi a wajen tana kuka,
ta ma rasa tunanin me zatayi, wani irin tsana ne da har zai sa mutum yayi ƙoƙarin kashe mutum ɗan uwansa, wannan wani irin ƙaddara ce da ta faɗa musu.
A hankali ta ɗago idanunta, tana kallonsa, yadda ya samu guri can gefe ya zauna, yayi shiru, kai tsaye bazaka taɓa gane me ya ke tunani ba, sam sai taji batason ganinsa a haka, zuciyarta bazata iya ɗauka ba.
A hankali ta nufe sa, har tazo dab dashi bai ɗago ba, kansa a sunkuye yake, gashin kansa ya sauƙo ya rufe fuskarsa, saboda sunkuyar da kan da yayi.
Tsugunnawa tayi dai-dai ƙafafunsa, ta lalubo hannuwansa ta riƙe gam.
Sai lokacin ya ɗago kansa, yana sauƙe idanuwansa a kanta, yadda idanuwansa suka kaɗa sukayi jajir, har sai da gabanta ya faɗi, amma sai ta dake.
Cikin ido take kallonsa, kafin a hankali ta soma magana, cikin muryarta mai matuƙar sanyi.
"Dan Allah kayi haƙuri, ka zama musulmin na ƙwarai, mai yarda da ƙaddara, yau koda ace Taufeeƙ ya mutu ne, babu yadda muka iya, saboda Allah ya riga ya rubuta kwanansa ya ƙare, bare yana raye, kuma insha Allahu zai farfaɗo, kamar yau zai tashi akan ƙafafuwan sa, nasan yana da muhimmanci a wajenka, but dan Allah ka masa addu'a, kar ka kasance cikin waɗanda basa komawa ga Allah idan masifa ta samesu, kuma na yarda da kai, ɗari bisa ɗari, zaka nemo duk wanda ya aikata masa hakan kuma ka hukunta shi, hukuncin da ya dace dashi."
A hankali hawayen da ta ke ta ƙoƙarin dannewa, ya sauƙo a kan fuskarta, dan ita kanta ba juriyar ce da ita ba, but ganin haalin da yake ciki yasa dole ta danne nata raunin.
Kallonta kawai yakeyi, ya kasa cewa komai, a hankali ya sa hannunsa yana share mata hawayen da ya zubo a samman kyakkyawar fuskarta, sai kuma ya ɗagota gabaki ɗaya daga tsugunnen da tayi a gabansa, kusa da shi ya zaunar da ita, yana sauƙe numfashi, ɗago idanunta tayi, suka haɗa ido dashi har lokacin hannuwansu na cikin na juna, a hankali kuma ya kwantar da kansa a kan kafaɗar ta, yana ajiyar zuciya,
Zare hannunta tayi daga nasa, ta maida a kansa tana shafa gashin, gyara masa sumar tayi, tana cigaba da shafa kansa, tana jin zuciyarta na ƙara tsananta bugu.
Har kusan magrib, suna zaune a haka, sai lokacin ya ɗago kansa, gani yayi ta jingina bayanta da kujeran, ta lumshe ido, alamar bacci ya ɗauke ta, tashi yayi ƙoƙarin yi, amma sai yaji ta sake damƙe dayan hanunsa da ke cikin nata, bai san sanda yayi murmushi ba, yana sake kallonta, irin kallon da bai taɓa nutsuwa yayi mata ba, kallo yake mata ma ƙurilla.
Juyar da kanta tayi tana ɓata fuska dan sam baccin kawai ya ɗauke ta ne, amma ba dan tana jin ɗaɗinsa ba, lips ɗin ta ta motsa a hankali, kamar zatayi magana, sai kuma ta maida su tana tsotsan na ƙasan, ƙuri yayi ma lips ɗin nata da ido, yana kallonsu, sai kuma yayi saurin juyar da kansa, yana shafa sumarsa, wacce ta ke ɗabi'arsa.
A hankali ta buɗe idanunta, sai kuma ta ɓata fuska tana gyara zamanta akan kujeran, motsinta da yaji, yasa ya juyo yana kallonta, sai kuma ya mata murmushi yana faɗin,
"Zaki tafi gida yanzu!"
Cikin innocent and calm voice É—inta tace " tare zamu tafi?"
Ta faÉ—a da sigar tambaya, kwaikwayon yanda tayi maganan yayi yana faÉ—in
"ke kaÉ—ai zaki tafi"
Sai da ya ɗan nisa kafin ya sake damƙe hannunta yana faɗin
"bazan iya tafiya na barshi ba, Taufeeƙ yana cikin mutane masu muhimmanci a rayuwata, zan iya cewa he is my only friend, saboda bani da aboki, but ya fiye min kowani irin aboki, for the past 16 years, da nake tare dashi, bai taɓa bani ƙofar da zanyi complain ba, he was with me tun Ƙanwarsa Yasira tana da shekara biyar, shine ƙadai gatan ta, duk da kasancewar ba ciki ɗaya suka fito ba, but sukaɗai suka taso, cikin maraici, da rashin gata,
a lokacin babansu was a drunkard, mashayin giya ne, wanda bai damu da iyalinsa ba, hakan yasa iyayensu mata suka bar gidan.
TaufeeÆ™ Yana son Yasira sosai hakan yasa da ya yanke shawarar barin gida, ya taho da ita, dan yana ganin she can't handle all that alone.
tunda na haɗu dashi nake matuƙar jinsa a jikina, saboda mutum ne shi mai amana, Maami kanta tasha faɗa min Taufeeƙ mutum ne in riƙesa, haka zalika Abbu, sai kuma yayi shiru, kallonta ya kuma yi sai kuma kawai ya jawota ya rungumeta sosai a jikinsa, kamar wani zai raba sa da ita, ita ma bata hanashi ba sai ma kwanciya da tayi shiru a jikinsa tana jin yadda zuciyarsa ke bugawa da ƙarfi.
Cikin É—acin rai ya cigaba da magana
" bazan taɓa yafewa duk wanda yayi masa haka ba, koda kuwa waye ne shi a wajena, sannan zan gano ko waye ne, kuma zan hukuntasa da mafi raɗaɗin hukunci,"
sai kuma ya sake yin shiru yana sauƙe ajiyar zuciya.
Itama shiru tayi ba tare da tace masa komai ba, tana fatan Allah ya sassauta masa zuciyarsa, ya bashi daman yanke hukunci, cikin nazari, dan idan rai ya ɓaci, hankali gushewa yakeyi.
ÆŠagowa tayi daga jikinsa, tana sake kallonsa tace
" ba zaka tambaye Ni me nakeyi a kusa da TaufeeÆ™ ba "
Da sauri ya juyo yana kallonta, sai kuma ya shiga girgiza mata kansa, ba tare da yace komai ba.
Kuka ta shiga yi a hankali, kafin ta buɗe bakinta tana ƙoƙarin faɗa masa abinda ya kaita Garden ɗin, har ta riski Taufeeƙ a haka
Da sauri ya saka yatsansa a bakinta yana kallon tsakiyar idonta
"Shhhhhh not another word, ko ki faɗa min, ko karki faɗa min, nasan a haka kika samesa, bazaki taɓa koda tunanin kisa ba, bare har ki aikata, i trusted you after so many trials, so baki da buƙatar yi min bayanin komai"
Kallonsa kawai takeyi, itama ta kasa cewa komai.
"Yanzu ki tashi, za'a kaiki gida, nima zan dawo idan na tattauna da Doctor É—in kinji?"
Hawayenta ta share, kafin ta miƙe a hankali tana kallonsa, shima miƙewa yayi, har ta kai ƙofa, sai kuma ta dawo da sauri ta rungume sa, tana sakin sabon kuka
Shafa kanta yayi, yana raÉ—a mata a daidai kunnenta
"everything will be alright, ba ke kika ce in bar damuwa ba"
ÆŠago idanunta da suka kaÉ—a sukayi jaa tayi tana dubansa, sai kuma tayi murmushi tana faÉ—in
" dan Allah ka dawo, zan jiraka, kazo ka faÉ—a min abinda kace zaka faÉ—a min dazu"
Murmushi yayi shima, wanda kana gani kasan a iya fuska ya tsaya,
"kina son in fada miki ne!?"
Gyada kai tayi alamar eh
"To ki jirani komin dare zan faÉ—a miki"
"Do you promise?"
"I do" ya faÉ—a yana sakin hannunta da ke cikin nasa.
A hankali ta juya ta nufi barin wajen duk jikinta a sanyaye.
Da ido kawai ya bita, yana kallon irin baiwar kyau da Allah yayi mata, wanda shi bai taɓa lura ya gani ba sai yau, yanda take tafiya a hankali, cikin sanyi yake kallo har ta fice kafin ya sauƙe idanunsa yana sakin ajiyar zuciya.
Tana fitowa, da sauri bodyguard É—in dake jiranta, ya fito yana zagawa ya buÉ—e mata motan yana gaisheta, shiga tayi ta zauna, tana kallon compound din asibitin, har suka fice, fuskarta ta juyar daga kallon window É—in, ta mayar tsakanin cinyoyinta, tana sake tunanin wa yake son kashe TaufeeÆ™ a cikin gidan,kuma me ya musu.
Har suka iso ta kasa gano komai, yana yin parking, bata jira ya buÉ—e mata ba, ta buÉ—e motan ta fita, tana tafiya a hankali, a falo ta samu su Asabe, duk idanunsu sunyi jajir saboda kuka, Amina har lokacin kuka takeyi wiwi, suna ganinta suka nufo ta sauri,
"Madam ya jikin Sir TaufeeÆ™"
kasa ce musu komai tayi.
Yasira da ke gefe tana jira a ce mata ya mutu, sai zare ido takeyi, ta kasa nutsuwa, da sauri ta bi Noor da ke ƙoƙarin haurawa sama
"Ma dan Allah ki faÉ—a min halin da yayana yake ciki, shikadai nake dashi, ya mutu ne?"
ta tambaya tana matsar kwalla
Dafa ta Noor tayi sannan tace
"kar ki damu bai mutu ba, kuma insha Allahu bazai mutu ba, yana nan da ransa kuma za'a gano duk wanda ya aikata masa hakan."
Dakatawa tayi da kukan da takeyi, hawayen ya ƙafe jin Taufeeƙ bai mutu ba, batasan sanda ta furta
"Bai mutu ba?" da ƙarfi tana zare ido
Da mamaki Noor take kallonta, kafin tace,
"kina so ya mutu ne?, nace miki bai mutu ba, kuma insha Allahu kwanannan zai dawo akan ƙafafunsa"
Da sauri ta sake fashewa da wani irin gigitaccen kuka, tana faÉ—in shikenan na shiga uku, yayana shi kaÉ—ai nake dashi,
Abinda bakinta ke furtawa kenan amma zuciyarta tana raya mata, idan har bai mutuba ai kuwa ta kaÉ—e, ta shiga uku,
Ganin kukan da takeyi yasa Noor faÉ—in
"Yasira ki yarda da ƙaddara yayanki ya shiga coma, but insha Allah zai tashi da yardar Allah kiyi masa addu'a"
Kasa cewa komai Yasira tayi da sauri ta juya ta bar wajen, duk suka bita da kallon tausayi.
Sai da Noor tayi wanka sosai, duk da haka daga zaran ta tuna yadda jini ke malala daga jikin TaufeeÆ™ sai ta runtse idanunta,
wasu hawaye na sake taruwa a idanunta.
har ƙarfe goma babu Zannur babu alamar sa, tun tana jiransa, har bacci ya fara ɗaukan ta, a kishigiɗe haka tayi bacci, dan bataso ta kwanta bacci ya ɗauke ta batare da ya dawo ba.
A bangaren Zannur, tun bayan fitowarsa daga asibiti, kasancewar asibitin basa barin kowa a wajen majinyaci su suke kula da shi da kansu, tun da ya fito yake tunanin abinyi, tunanin cctv daya zo masa yasa shi nufar gida kai tsaye,
ÆŠakin sa ya wuce ba tare da ya bari kowa yasan da shigowar tasa ba.
ƙuri yayi ma na'urar yana kallo, ganin babu footage ɗin Garden kwata kwata, da mamaki yake sake kallon computer, ya maimaita dubawa ya kai sau biyar, Amma still babu wannan footage ɗin, a hankali ya shiga duba sauran gurare na gidan, yana so ya gano taka maimai abinda ya faru.
Cak ya tsaya akan inda Yasira ta fito tana kuka, ta samu Taufeeƙ a compound, baya iya jin me suke faɗa, amma da alama faɗa sukeyi, sai kuma yaga sun nufi Garden dukansu, baiga fitar Yasira ba sai kuma yaga Noor ta shiga, pulsing yayi, ya miƙe da sauri ya fita a ɗakin.
Ƙasa ya sauƙo, sannan ya ɗau landline ya Kira ɗakin su Yasira, Amina ce ta ɗau wayan, a taƙaice yace
"Yasira ta sameni a falo immediately" daga haka ya kashe wayar.
"Ni kuma?, meyasa yake nema na?" Yasira ta faɗa tana kallon Amina da ta isar mata da saƙon Zannur,
"Idan kinje sai ki tambayesa Ni kawai cemin yayi kije"
Miƙewa tayi zuciyarta na wani bugu ta fice a ɗakin,
A zaune ta samesa, ita ma ta samu waje can ƙasa ta zauna, tana shirin gaishesa ya ɗaga mata hannu, fuskarsa babu alamun wasa ya soma faɗin
"Me ya haÉ—a ki da yayanki É—azu?"
ÆŠago ido tayi ta kallesa, kafin tace
"Ni.. babu komai" ta faÉ—a tana kame kame
"Babu komai?"ya sake tambayan yana kafe ta ido
Daburcewa tayi, sai ta soma inda inda,
"eh dama, au babu Fah, Amma dai kawai cemin yayi zai kaini gurin baba, shine nace masa bazan je ba, shine yake min faɗa, sai kuma yace muje can muyi magana, muna cikin magana sai Madam ta zo, ranta a ɓace, shine sai ya ce min in tafi, shikenan kawai sai muka ji wai an kashesa."
tana kaiwa nan ta fashe da matsanancin kuka, harda shesheƙa.
Kallonta kawai yakeyi, kamar mai ƙoƙarin gano wani abu, kafin a hankali ya furta
"Yasira kina jina?"
GyaÉ—a masa kai kawai tayi, tana cigaba da kukan
"Yayanki zai samu lafiya, ki kwantar da hankalinki, kina jina?, na miki alƙawarin duk wanda yayi masa wannan abun, da kaina zan bincikosa, sannan in hukuntasa, ki cigaba da yi masa addu'a kinji?"
"To" ta faÉ—a tana fyace majina
"Tashi kije" ya faɗa a taƙaice, yana jingina kansa da kujera.
Miƙewa tayi, ta wuce, tana sake waiwayowa ta dubesa, a hankali kuma tayi murmushi, a zuciyarta tana faɗin
"Kaɗan ya rage na mallakeka Zannur, kuma nayi alƙawarin, duk wanda ya kawo min cikas wallahi sai na kawar dashi"
sai kuma tasa yatsa ta share guntun hawayen idanunta, sannan ta wuce É—akinsu.
Miƙewa yayi daga kan kujeran, yana jin gabaɗaya kansa ya kulle, ta yaya ma Yasira zata cutar da ɗan uwanta, bazai yiwuba,
har ya koma É—akin sa ya faÉ—a kan gadonsa yana cigaba da tunani,
to me ya kai Noor wajen Taufeeƙ?, kuma ranta a ɓace, me ya mata?, dole ne ta amsa masa waɗannan tambayoyin nasa, shin ko dai yayi kuskuren amincewa da ita ne?, wata zuciyar ta raya masa, da sauri kuma ya girgiza kansa, yana maimaita
"Allahummu ajirni fi musibati."
GabaÉ—aya ya manta da wani tana jiransa, har bacci ya dauke sa.
Mun kusa dawowa kan labari🤓so get ready, gumurzun yana gaba
Maimoon#
*💖ABNUR💖*
*By maimoon*
*Elegant online writers* 📚📖
*Free book*
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.