Complete Hausa Novels

Abnur Complete Hausa Novel

Reading file: Abnur_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 17 of 24

*Page 18*

A hankali cikin taku ɗai ɗaya, Yasira ta ƙaraso gaban Taufeeƙ, sai da ta sunjuyo dai dai fuskarsa, kafin tasa hannunta ta shafa fuskarsa.

"Yaya ya jikin?, Me kake faÉ—a ma masoyina?", ta faÉ—a tana kallon cikin idonsa.

Juyar da kansa yayi daga kallonta, yana jin ƙunar zuciya.

Sai da tayi ƙwafa, tana wani murmushi kafin tace

"Wato kana kan bakanka ko?, To bari kaji, Na rantse da Allah baka isa ba, yanzu zan ƙarasaka saboda bazaka ɓata min shiri ba".

Daga haka ta saka hannu ta cire oxygen ɗin, pillow ta ɗauko ta ɗaura akan fuskarsa, ta danna da iya ƙarfin ta.

Wani numfashi ya shiga fitarwa, yana miƙewa da kakkarwa a kan gadon, amma ko ajikin Yasira, sai ma sake dannawa da take da ƙarfi.

Jin numfashinsa na ƙoƙarin barin jikinsa, yasa ya ɗaga hannunsa yana bugawa a jikin gadon, cikin Sa'a kuwa hannunsa ya tabo madannin da mara lafiya yake dannawa idan yana buƙatar wani abu.

Ai kuwa É—akin ya É—au kuwwa, da sauri ta cire pillow É—in tana mayar masa da oxygen É—in cikin ruÉ—ewa.

Nurses ne suka shigo,su kusan uku, da sauri suka ƙara so suna kallon Yasira, da ke gyara masa kwanciya.

"Madam wa ya baki daman shigowa nan?"

Daya daga cikin nurses É—in ta tambaya tana kallon Yasira cikin tuhuma.

Cikin in ina tace

"dama yaya na ne, shine nazo na gansa, kuma...uhm"

Sai ta kasa ƙarasawa.

"Ok ke relative É—insa ce?"

Da sauri tace

"eh nice kaɗai Ƙanwarsa."

"Ok to but ba lokacin ganin mara lafiya bane yanzu!, saboda haka ki dawo right time."

"Eh dama abinci na kawo masa, dan Allah ku barni in bashi."

ÆŠaya daga cikin nurses É—in tace bakiji

"me akace bane, ki dawo lokacin da ake ganinsa Please"

Babu yadda ta iya haka juya ta fita, a ranta tana faÉ—in

"babu damuwa akwai wani lokacin, amma ina mai tabbatar maka bazan taɓa bari ka haramta min muradin zuciyata ba."

Daga haka ta fice tana murmushi.

Tunda Zannur ya shigo gidan, bai bi takan duk masu gaishesa ba, ya nufi sama, da sassarfa, Allah Allah,yake ya gansa a gaban Noor.

Murɗa ƙofan ɗakin yayi ya shiga, tsayawa yayi daga bakin ƙofan yana kallon kayan da ta zubo dasu daga cikin sif ɗin, ba tare da tunanin komai ba ya ƙaraso cikin ɗakin, ganin bata ciki yasa shi ƙarasawa ƙofar bandaƙin, dan ya tabbata tana ciki, jiki a sanyaye ya soma magana

"Noor, bansan me zance miki ba, wallahi ina matuƙar kunyar ki, Taufeeƙ ya tabbatar min zargina ba daidai bane." sai kuma yayi tsaki

"Mtseewww me ma nakeyi?" Ya faÉ—a yana dafe kansa, sai kuma ya cigaba

"Noor please ki fito ki saurareni, bakin ce kina so kiji abinda nake so na faɗa miki ba rannan?, to yau zan faɗa miki na miki alƙawari."

Jin bata fito ba ya sashi, É—aura hannunsa akan handle É—in

Yana shirin magana yaga ƙofar ta buɗe, alamar ba'a rufe da kyau ba, a hankali ya ƙarasa tura Kofar,
Wayam yaga banÉ—akin babu kowa.

Zuciyarsa ce tayi wani irin wawan bugun da ya sashi dafewa da sauri,

kafafuwansa da sukayi nauyi, ya ja da sauri ya juya ya nufi É—akinsa, laptop É—insa ya nufa.

Kai tsaye kitchen ya duba, bata ciki, ya duba duk wani guri a gidan amma babu ita, cikin sauri ya shiga tariyewa baya 3days ago tun sanda ya bar gidan.

Wani irin miƙewa yayi yana faɗin

"shit"

Landline ya É—auka yana kiran securities É—in gidan

Yana É—agawa yace

"where is Noor?
Why do you let her out? akan me ya sa kuka barta ta fita a gidannan ba tare da izinina ba." ya faÉ—a a tsawace.

"Sorry Sir"

"Shut up, na baku 30 minutes ku nemo min matata, idan ba haka ba..." sai kuma yayi ƙwafa yana katse wayan.

Dafe kansa yayi, yana riƙe ƙugunsa
Sai kuma ya durƙusa a wajen yana jin idanunsa na masa matuƙar raɗaɗi

"Why Noor, meyasa baki jirani na gano gaskiya ba?, Noor you are my life, Please ki dawo gareni, I promise to trust you completely, wallahi bazan sake kuskuran fahimtar ki wifey."

Sai lokacin, hawaye mai zafi ya sauƙa masa, bazai yafewa ko waye yayi sanadiyyar rabasa da Noor ɗinsa ba.

Bai san tsayin lokacin da ya kwashe a wajen ba trying to calm himself, kafin ya miƙe da sauri ya nufi downstairs cikin sassarfa.

(Finally we are back, and the story continues.....)

Numfashi ta sauƙe a hankali tana share hawayen idanunta, bayan ta gama basu labarin abubuwan da ta sani.

A hankali umma ta taso ta zo kusa da ita tana shafa kanta.

Kamal kam kallonta kawai yakeyi sai kuma ya sunkuyar da kansa, yana murza hannunsa, dan ya gagara cewa komai.

Baba ne yayi gyaran murya kafin ya fara magana

"Noor, munji labarinki, kuma a gaskiya kin yi haƙuri, kuma Allah ya jiƙan Nenne, yanzu abinda nake so dake kije ki kwanta insha Allahu zamuyi magana gobe, muga ya zamu samo mafita, Allah ya miki albarka."

"Ameen" umma ta amsa dashi, tana shafa kan Noor dake cigaba da kuka.

Jin kiran sallan Asuba, yasa Baba faÉ—in

"subhanallahi, ashe ma garin har ya waye, mun kwana a zaune fah kenan, to Allah ya kyauta, kamal tashi muyi haramar tafiya masallici, A'isha sai kuyi sallah kafin ta kwanta koh?."

"Insha Allah Malam"

Umma ta faɗa tana miƙar da Noor suka fice a ɗakin.

Sai lokacin khamal ya miƙe shima, suka fice da Baba, Dan tafiya masallaci kafin a shiga sallah.

************

Ƙarfe 1:30 daidai, jirgin *Emirate Airlines* daya taso daga *Dubai* ne ya sauƙa a babban filin jirgi na Kaduna wato *Kaduna international Airport.*

A hankali mutanen ciki ke sauƙowa, ɗaya bayan ɗaya a gajiye.

Farhaana ce ta fara sauƙowa, sai sudais da namra a bayanta, duk fuskarsu a jagule, daga bayansu kuma Ammi ce, sai papi a bayanta.

Haka suka jero suna sauƙowa abin sha'awa,

sai dai fuskokinsu babu wanda yake walwala, idan ka cire sudais kasancewar bai ma san me akeyi ba shi.

Sai da suka gama yin all the formalities, kafin suka zarce gidan da papi ya saya a garin Kaduna wanda ke unguwar GRA, har suka isa babu mai cewa komai.

Suna shiga, Farhaana taja su Namra suka wuce shashinsu, Ammi ma nata ta wuce suka bar papi a tsaye, shafa sumar kansa yayi, a zuciyarsa yana faÉ—in

"Na gaji da zama da haƙƙinki, a wannan lokacin babu wanda zai hanani nemanki, dan tabbatar miki da alƙawarina a gareki, ina fatan zaki yafe min, sannan kimin kyakkyawar fahimta".

Daga haka ya wuce shashensa shima yana jin matsanancin gajiya a tattare dashi.

**********

Zannur ne a zaune kusa da Taufeeƙ da ke barci ƙura masa ido yayi yana kallonsa, bai san miye dalilin Taufeeƙ na ƙin faɗan wanda ya aikata masa haka ba, yayi iya ƙoƙarin sa, amma Taufeeƙ yaƙi cewa komai.

Miƙewa yayi ya ƙarasa jikin window yana jin zugi a ransa, meyasa ƙaddara ta zo masa a haka?, da wanne zaiji?, da ɓatan Noor ko kuwa da rashin lafiyar Taufeeƙ?.

TaufeeÆ™ É—an amanarsa ne, da bazai iya barinsa ba kuma sai ya hukunta ko waye ya aikata masa hakan,
Gashi ya kasa sanar da Maami abunda ke faruwa.

A hankali ya juya ya bar É—akin yana jinsa kamar bashi ba.

Taufeeƙ daya buɗe idanunsa yana kallonsa, dan dama ba bacci yakeyi ba, hawayen da ya ciko idanunsa suka bi gefen fuskarsa, suna sauƙa akan gefen kunnensa.

A hankali ya buÉ—e bakinsa da yake a bushe, ya furta

"bazan taɓa bari a cutar da kaiba Sir, koda kuwa hakan na nufin ƙarewar rayuwata, hakan yasa na yanke shawaran ƙin faɗa maka, kayi haƙuri zan faɗa maka, amma sai a lokacin da ya dace, sannan nayi alƙawarin zaka zauna da Noor har karshen rayuwarka, sai dai idan kai kace baka sonta Sir, bazan taɓa manta halaccin ka a gareni ba, duk da Ni ba kowa bane, amma ka nuna min zallar soyayyah da kulawa."

Sai kuma ya juyar da kansa yana jin É—aci a ransa.

Maimoon#

*💖*ABNUR💖**

*By Maimoon*

*Elegant online writers* 📚📖

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.