Complete Hausa Novels

Abnur Complete Hausa Novel

Reading file: Abnur_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 7 of 24

*Page* *8*

Innalillahi wa inna ilaihi raji'un,tashin hankali wanda ba'a saka mata rana.

Sam Noor Bata fahimci cewa Nenne rai yayi halinsa ba, ganin jikinta ya saki,sannan ta daina motsi,sai ta matso kusa da ita, tana faÉ—in

"Nenne kinji sauƙi ne!?,Nenne kiyi haƙuri da sassafe zamu tafi asibiti,wannan da ya zo ya gaishe ki,yace zamu je asibiti,insha Allahu zaki samu lafiya.

Jin Nenne bata amsa ba,sannan bata motsa ba,yasa hankalinta sake tashi,kukan ta ya ƙaru,

da sauri ta kama hannuwan Nenne duka biyu ta riƙe ƙam,tana kuka kamar ranta zai bar gangar jikinta,girgizata ta shiga yi tana cigaba da kiran "Nenne na ki tashi,Nenne ki taimaka min,ki tashi,idan baki tashi ba nima mutuwa zanyi.

Wani tunani da yazo ranta, ya sa tayi sauran miƙewa ta fice a ɗakin da sauri.

Ruwa ta É—ebo ta dawo da sauri tana shafawa Nenne,a tunaninta ko dogon suma tayi,but har lokacin Nenne bata motsa ba.

Wani kukan ta sake fashe wa dashi da sauri ta miƙe,fice a gidan,har lokacin kuka take.

Gidan Malam Habu,wanda yake maƙwabtansu ta shiga bugawa, duk da dare yayi amma ko tsoro bata ji, dan kusan asuba ne ma a lokacin.

Ta ɗan jima tana bugawa, babu ƙaƙƙautawa, kafin Malam Habu,ya buɗe ƴar langa langa kofar yana faɗin "waye ne da talatainin daren nan"

Cikin kuka sosai tace "Baba Noor ce".

"Ha'a Noor lafiya da darennan me ya faru kike kuka"

"Nenne, ce bata da lafiya, kuma ta ma suma,bata ko motsi, dan Allah ka taimaka min.

Da sauri Malam Habu yace "subhanallahi muje muga abinda zamu iya yi".

komawa ciki yayi da sauri ya taso matarsa Jummai, suka fito tare.

A tsakar gida ta tsaya ta kasa ƙarasawa ɗakin,tana jin malam habu da matarsa suna ta salati,
kasa gasgata abinda zuciyar ta ke sanar da ita tayi, a hankali tayi baya ta jingina da bango, tana maimata ma kanta

"Nenne bata mutuba, batada lafiya kuma zata ji sauƙi".

Jummai ta fito a É—akin idon ta cike da hawaye,
gurin Noor ta ƙara sa ta dafa ta tana faɗin"Allah ya baki haƙurin rashi Noor, Nenne rai yayi halinsa,Allah da ya fiki sonta ya karɓi abinsa"

Ai bata ƙarasa jin abinda take sanar da ita ba ta yanke jiki ta faɗi a wajen sumammiya.

Ƙarfe 7:00 na safe ya fito cikin shirinsa, Taufeeƙ na biye da shi a baya,
bayan ya fitar musu da duk wani abu nasu trolley yake ja,yayinda shi kuma TaufeeÆ™ yake É—auke da jaka na matafiya da kuma jakan kayan cameras É—in su,

A hankali yake tafiyar amma duk zuciyarsa a cunkushe,

"do you really think this is a good idea!?, is this the right step daya kamata ka É—auka!?"

abinda zuciyarsa ke tambayan sa kenan.

Da sauri ya furta

"wannan shine right step É—in da ya kamata na É—auka, idan ba haka I will regret it for the rest of my life"

Da mamaki TaufeeÆ™ ya kalleshi yace

"Sir Are You ok"

Sai lokacin ya gane ashe a bayyane yayi maganar
"i am alright" ya faɗa a taƙaice yana cigaba da tafiya.

Dai dai layinsu yaja ya tsaya, yana kallon cincirindon mutanen dake tundaga farkon layin,
zuciyar sa ce ta buga da tsananin ƙarfi,da har sai da ya dafe ta, ya juya ya kalli Taufeeƙ ya ce
"what's going on there?"

Da sauri TaufeeÆ™ ya amsa da,
"I have no idea Sir,but ko na bincika maka...?"

kafin ma ya ƙara sa maganan, yaga ya sake trolley ɗin,ya nufi layin cikin sassarfa.

TaufeeÆ™ ya bishi da kallo, shidai daga jiya zuwa yau,he is confused, ya rasa me ke faruwa da Sir Zannur.

A dai-dai ƙofar gidan ya tsaya, yana kallon kowa, sai kuma ya ƙarasa wajen wani matashi da ke tsaye can gefe, hannu ya miƙa masa, suka gaisa, sannan ya tambaye sa abinda ke faruwa.

cikin alhini saurayin ya fara faÉ—a masa
"wallahi bawan Allah, matar gidan ne Allah ya mata rasuwa jiya cikin dare, abinda zai baka tausayin ma bazai wuce Æ´ar da ta bari ba.
Dama can batada uba, gashi tana da ƙarancin shekaru, ga maman ma ta tafi ta barta,wallahi tun jiyan an kasa gane kan yarinyar, abin tausayi wallahi", ya ƙara sa faɗa yana matso hawaye.

Baya yayi yana kallon matashin,kansa na wani irin juyawa,maganar da suka yi da ita jiya kawai yake tunawa,kenan wasiyya ta bashi ko me!?

Ya juya ya nufi cikin gidan, bai damu da mutanen da ke kallonsa ba,

mata ne birjik a cikin gidan,ya ma rasa ta ina zai fara nemanta,wata tsohuwa dake
Zaune akan tabarma tace"yaro lafiya daga ina haka" da sauri ya russuna yayi musu gaisuwa,suka amsa.

Kawai sai ya miƙe,dan ya rasa ma me zai ce,fitowa yayi waje ya koma can gefe ya tsaya.

Taufeeƙ da ya mayar da kayan su ya dawo,dan yaga alama babu tafiyar,ya ƙaraso wajensa yana tambayansa abinda ke faruwa.

"Taufeeƙ ta rasu,ta tafi ta barni da alƙawarin da bansan ta yaya zan fara cikasa ba,I thought zafin ciwo ne ashe wasiyya take bani,ya zanyi,tell me what exactly I should do!?

Ya tambaya yana kallon TaufeeÆ™,wanda ya sake shiga cikin duhu,dan bai fahimci komai ba a cikin maganganun Sir Zannur É—in,
amma ganin yadda hankalinsa yake a tashe,ya sashi dafasa ya ce

"first of all,You have to calm down Sir,kasa a ranka komai muƙaddari ne daga Allah, sannan ko wani step zaka ɗauka, ka tabbatar kayi tunani mai zurfi akansa,
though bansan abinda yake faruwa ba,but ina maka fatan ka É—auki right steps,kuma Allah yana tare da kai, so Please ka kwantar da hankalinka".

Shiru yayi,yana sauƙe ajiyar zuciya kawai,bai sake cewa komai ba, but yaji nauyin ya ragu a zuciyar sa, a hankali ya furta

"Thank you"

"No please Sir,it's always my pleasure,ban cancanci kamin godiya ba Sir,dan komai nayi maka ban biyaka ba"

Murmushin ƙarfin hali yayi masa sannan ya juya ya bar wajen.

Tare dasu aka kai Nenne gidan ta na gaskiya,
har aka watse yana tsaye a kan kabarinta, Taufeeƙ ya ƙaraso wajen sa yace "Sir...."

Da sauri ya katse sa " I will meet you outside"

Juyawa kawai TaufeeÆ™ yayi ya bar wajen yana jinjina girman abinda Nenne ta faÉ—a ma Sir,da ya É—aga masa hankali har haka.

Zama Zannur yayi a hankali,dai dai kabarin, a hankali yace,

"Meyasa kika zaɓeni, acikin duk mutane, bayan baki sanni ba,kuma kika tafi kika barni da responsibility mafi girma a rayuwata,

Shiru yayi kamar mai jiran ta bashi amsa, sai kuma ya miƙe da sauri.

Bai sake waiwaya wa ba, ya fice daga maƙabartar,yana jin wani nauyi a zuciyarsa.

Gidan su Noor ya wuce kai tsaye, ga mamakinsa sai yaga babu kowa kamar ba gidan mutuwa ba,ƙarasowa yayi,yana kallon yadda har tabarmar an naɗe,

bai gama mamaki ba sai da ya shiga cikin gidan, tsayawa yayi yana kallon tsakar gidan, nan ma babu kowa, mamakin sa yakasa ɓoyuwa.

Tsohuwar ɗazu ce ta fito daga ɗakin Nenne tana faɗin "to Allah ya ƙara bamu haƙuri".

Ganin fita zatayi yasa yayi saurin faÉ—in "Granny"
juyowa tayi badan ta gane me yace ba,sai dan ganin su kaÉ—ai ne a tsakar gidan,
"yaro me ka dawo yi kuma"ta tambayesa tana kallonsa.

Cike da mamaki yace"ina kuke tafiya kuma Granny?,naga babu kowa, masu karɓan gaisuwa"

Tsohuwar ta kunce zaninta ta É—auko jan goronta ta gutsura sannan ta kallesa tana faÉ—in
"yaro zaman me kuma za'a yi?, a wannan ƙauye ai ba'a zama, ana kai mutum, shikenan kuma kowa zai kama gabansa,wanda ya mutu ai ya riga ya mutu koh?

Ta faÉ—a tana kallonsa,
Baisan sanda ya furta
"to ita kuma yarinyar ya zakuyi da ita!?"

Tsohuwar ta ƙara kallonsa tana faɗin "ya kuwa zamuyi da ita,wanda ya ga zai iya sai ya aiko mata da abinci, kafin dai ta warware,
ai akwai inda Uwar yarinyar take aiki,gidan mai garin garinnan, Ni bance ma Æ´ar ta sani ba, ita ma sai taje ta dinga yi tana samun abinda zata ci,ah toh kowa ma fama yake da kansa"

Ta faɗa tana juyawa tana ƙoƙarin barin gidan.

"naga alama kai baƙo ne shiyasa har kake tambaya wai ya zamuyi da ita,to Ni kuwa me zan mata, ai kawai Allah ya bata haƙurin rashin uwa da tayi,
ƴar makarantar da take zuwa ma ai yanzu kam ta ƙare".
kallonta kawai yakeyi har ta fice tana cigaba da mita.

Sai yanzu ya gano dalilin Nenne,shiru yayi yana tunanin wasu irin mutane ne su, sai kuma ya nufi É—akin da tsohuwar ta fito, yana tafiya a hankali.

A bakin ƙofar ya tsaya, yana kallon ɗakin,sai kuma ya ɗaga labulen a hankali ya ƙara sa ciki.

A can dungu ya same ta a raɓe, idanun ta sun kumbura sunyi suntum, har lokacin basu daina tsiyayar da hawaye ba,gaba ɗaya ta fita hayyacinta, kallonta yayi na kamar 5seconds, sai kuma ya ɗauke kansa duk da tausayinta da yaji har cikin ransa,

A hankali ya tako har gabanta ya tsuguna yana sake kallonta, sai kuma ya yayi gyaran murya, a hankali yace

"Noor"

Kin É—agowa tayi, ya sake kiran sunan ta, nan ma bata É—ago ba bare yasa ran zata amsa,

Sai da ya sake kira a karo na uku,tukun ta É—ago jajayen idanunta ta zuba masa, wanda sai da yaji har zuciyarsa tayi rawa,
saboda yana iya hango tsananin É—imuwa a idanunta.

Cikin rarrashi ya soma faÉ—in
"me yasa kike mata kuka?, kuka a gurin mamaci ba gata bane Noor!,babu abinda Nenne take buƙata a wajenki sama da addu'ar ki,ita kanta bazata so ta ganki a yanda kike ɗin nan ba.

Ai kamar ya zuga ta,ta sake fashewa da wani sabon kukan, amma ta kasa cewa komai, rasa yadda zaiyi yayi,kawai sai ya jawota jikinsa ya rungume,Yana bubbuga bayanta,dan yasan she really need a shoulder to cry on, mutuwar mahaifiya ba wasa ba, he can't even imagine rasa Maami, yasan sai ya fita shiga tashin hankali,

Sai da tayi kukan ta mai isarta, sannan ya É—aga ta tsaye, hijab É—in da ya gani ya sanya mata a saman É—ankwalin kanta,sannan ya kalleta a hankali yace

"Nenne tace in tafi dake, zaki bini" ya faÉ—a yana kallonta.

ÆŠan dakatawa tayi da kukan tana kallonsa, ya girgiza mata kai.

Sai lokacin ta iya buÉ—e bakinta a hankali tace

"Nenne ce tace ka tafi dani?" a hankali ya gyaÉ—a mata kai.

Sunkuyar da kanta tayi, batace komai ba,
Shima bai jira ta e komai ɗin ba ya kama hannunta ya riƙe yace muje, yau zamu bar garinnan.

ba musu ta bishi har suka fito waje,yana riƙe da hannunta, gida ya wuce da ita,still bai sake hannunta ba,

kowa sai binsu yake da kallo, Taufeeƙ dake ƙofar gidan yayi saurin ƙarasowa inda yake yana tambayar sa abinda ya faru

"TaufeeÆ™ pack our things we are leaving right Now" ya faÉ—a yana jan hanunta ya shiga cikin gidan,

da sauri TaufeeÆ™ ya biyo bayansa yana faÉ—in,"ai kayanmu Are already packed bari in Kira faruÆ™ ya kawo mana mota", bai ce masa komai ba ya sake hannunta ya nufi É—akinsa,

TaufeeÆ™ dai kallonta kawai yakeyi,to me hakan yake nufi?, ganin babu amsa yasa ya shiga É—akinsa, jakunkunansu ya fito da su ya fitar waje.

dandazon mutanen da ya gani a wajen gidan ya sashi tsayawa kallonsu, ƙarasowa yayi yana faɗin "lafiya!?".

Wani dattijo yace rufa mana baki, ba gurinka muka zo ba.

Taufeeƙ ya buɗe baki da niyyar sake magana, amma sai yayi shiru, ganin Sir Zannur ya fito, hannunsa riƙe da na yarinyar,shima da mamaki yake bin mutanen da kallo,

Aikuwa fitowarsa ke da wuya,wajen ya É—au hayaniya,kowa na faÉ—an albarkacin bakinsa,shidai har lokacin bai gane me yake faruwa ba,

da sauri Taufeeƙ ya ƙarasa wajensa yana faɗin

"Sir bansan me ya kawosu ba, na tambayesu sunce wajenka suka zo"

Juyawa yayi ya kalli mutanen yana sake haÉ—e ransa yace "ina sauraranku".

wani dattijo ne ya fara magana yana faÉ—in"asirin ka ne ya tonu, daga mutuwar uwar Æ´ar nan har ka É—akkota ka kawo ta gidan ka,ko kayi zaton bama saka ido akan Æ´aÆ´anmu ne".

Wani kallo yayi masa,sannan cikin takaici yace "saka ido akan yaranku?,shiyasa kuka barta ita kaɗai duk da ƙarantar shekarunta,abinda baku sani ba shine,a yanzun nan ba sai gobe ba, zan bar garinnan da ita, kuma babu wanda ya isa ya hanani tafiya da ita, saboda wannan wasiyyar mahaifiyar tace"

Da sauri TaufeeÆ™ ya kalleshi kamar yadda kowa ya zuba masa idanu yana kallonsa.

Wani tsohu yace"to a wani dalilin zaka tafi da ita,bayan babu abinda ka haÉ—a da ita,sannan ita ba muharramar ka bace, saboda haka ba inda zakaje da ita.

Wani yawu mai É—aci ya haÉ—iye kafin yace "to idan ta zama muharrama ta kuma Fah!?"ya faÉ—a yana kallonsu duka

Duk shiru sukayi babu wanda ya masa.

Ya nisa yace, yanzunnan ba sai anjima ba, ina so in cika alƙawarin da na ɗauka ma mahaifiyar ta, ina so a ɗaura min aure da Noor"

Ba iya Æ´an garin da TaufeeÆ™ ba, hatta Noor dake kuka sai da ta tsaya cak da kukan tana kallonsa,

Taufeeƙ ya ƙara so da sauri yana faɗin "Sir"

Bai bashi damar magana ba yace "that's my final decision".

Jiki a sanyaye wani tsoho yace to ai shikenan, sai mu É—unguma muje gurin mai gari,idan dai har an É—aura, kuma mun shaida, babu wanda zai hana ka tafiya da matar ka.

Hakan kuwa akayi,gabaɗaya suka nufi gidan mai gari, ba'a wani ɓata lokaci ba aka ɗaura auren _ABUBAKAR SHURAIM_ (Zannur)tare da _NA'IMA RAZAƘ ABDULKARIM_(Noor) akan sadaki Naira dubu hamsin lakadan ba ajalan ba.

Gaba É—aya wajen aka shaida,ita dai Noor bin kowa take da Kallo,
meyake faruwa da rayuwar ta ne?,jiya mahaifiyarta ta rasu, yau an É—aura mata aure, shin mafarki takeyi ko kuwa a zahiri komai yake faruwa?,

Miƙewa Zannur yayi,sannan ya miƙar da ita, yana riƙe da hannunta yace "mun barku lafiya"

Daga haka ya juya ya kalli TaufeeÆ™ wanda shima komai yazo masa a bazata, da sauri yabi bayansa,suka bar wajen,

tafiya kawai sukeyi babu mai cewa komai,yana riƙe da hannunta yana janta tana binsa Taufeeƙ kuma na biye da su da kayansu, ya goya jakan yana Jan trolley ɗin, har suka iso dai dai inda suka bar motarsu.

kasancewar TaufeeÆ™ ya riga ya kira faruÆ™ yasa basu jima a wajenba faruÆ™ ya iso da motar, bai kalli inda take ba ya juya ya shiga baya, TaufeeÆ™ kuma ya shiga gaba,tsayawa tayi tana kallonsu.

Ganin batada alamar shiga motar, yasa Taufeeƙ sauƙa a motar ya buɗe mata baya yana murmushi yace"Madam shall we?"

A hankali ta ƙara sa ta shiga Taufeeƙ ya rufe motar,ya koma gaba,faruƙ ya tada motar.
shi kansa yasan ba lafiya ba ganin yanayinsu gaba ki É—aya,amma bayida hurumin tambaya yasa yaja bakinsa yayi shiru,

har suka fita a garin ba mai cewa komai sai ma faruÆ™ da ya gaishe da Sir Zannur, ganin bai amsa ba yasa bai sake cewa komai ba

Jinginar da kansa yayi da jikin kujera, yana tunanin abubuwan da suka faru,
itakam can dungu ta rakuɓe tana cigaba da kukan ta ƙasa ƙasa.

Maimoon🤓#
https://www.facebook.com/groups/1627491150723081/?ref=share

💖*ABNUR*💖

*By* *maimoon* 🤓

*Elegant* *online* *writers* 📚📖

*Free* *book*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.