Yiwa Kai Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Yiwa_Kai_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 9 of 34
Tsayawa Anas ya yi sakato kamar wani shashasha yana kallon ƙofar ɗakin kamar tana gurin, mamaki da al'ajabin Hafsah sun hana shi magana, ya rasa ma abin da zai ce mata. Ba ya jin tana cikin hayyacinta gaskiya, don waɗannan abubuwan ba halinta ba ne. Girgiza kai ya yi tare da kama haɓa ya ce. "Anya ba zan kira a yi mata roƙiyya ba kuwa? A gani ko aljanu ne suka shafar mini ita, don wannan lamuran nata sun wuce hankali." Bin bayanta ya yi don ƙara tabbatarwa da kansa koma mene ne yake damun matar tasa.
Maman Nasmah tana shiga mota ta fashe da dariyar da take ta cin ta cikin rashin damuwa da kallon da drivernta yake mata, ba ƙaramin dauriya ta yi ba da ba ta ƙyaƙyace a gaban Hafsah ba. Ta daɗe da gano ita talaka ce, saboda in dai za a yi maganar wani abu na gayu ko masu kuɗi ba ta saka baki, kuma ta gwada ta da abubuwa da yawa da suka ƙara tabbatar mata da zargin ta. Amma duk da haka ba ta yi tunanin talaucin nata ya kai haka ba, don a lokacin da suka yi parking a ƙofar gidan ta kalli gidan da unguwar ta yarda gidan masu aiki ne, saboda ita a tarihin rayuwarta ma ba ta taɓa shigowa irin unguwannin nan ba, idan ta yi sa'a direbanta ya san unguwar sosai. Ta inda ta gane gidan Hafsah ne tun kafin ta shiga, su Sultan ta gani sun dawo daga makaranta, ta tambaye su sunansu suka faɗa mata, ta ce mamansu tana cikin gidan suka ce eh, kuma farkon sanin ta da Hafsah hoton Sufyan ne akan dp ɗinta, hakan ya sa tana ganin su ta gane su.
Tana sane ta ƙi nuna wa Hafsah ta gane ta ko ba ta gane ta ba, ta bar ta a cikin duhu don ta ji idan sun yi chatting anjima me za ta ce mata. Dariya ta ƙara kwashewa da ita saboda tuno yadda Hafsah ta yi tsumu-tsumu kamar an tsoma kaza a ruwan zafi, tana lura da yadda take ta share zufa a goshinta, da dibibicewar da ta yi. Kasancewar Hafsah talaka ba zai saka ta rabu da ita ba, don haka kawai Allah ya haɗa jininsu, ta ji tana son ta. Amma a yau da ta gan ta a gidanta sai ta gane dalilin da ya sa ƙaddara ta haɗa su tun farko. Numfashi ta sauke tare da lumshe idonta tana tuno Anas da murmushin da ya yi wa Hafsah lokacin da ya shigo, irin namijin da ta rayu da burin samu mai cikar zati da kamala. Tun daga sallamar da ya yi kafin ta gan shi gabanta ya faɗi, da ta gan shi kuma sai komai ya kwance mata, ta kasa ɗauke idonta daga kansa. Babban abin da ya ƙara fizgar ta a kansa soyayyar da ta ga ya nuna wa Hafsah. Kashe idon da ya yi wa Hafsah da kallon da yake bin ta shi kuwa sai da ya saka tsigar jikinta ta tashi. To a hakan ma jikinsa duk da fenti ina ga ya kintsa ya yi fes? Ta san sai ta kusa zaucewa. Lafewa ta yi a jikin kujera tana hasaso ita yake yi wa wannan kallon, tabbas ta san sai ta kusa sumewa. A rayuwarta tana bala'in son namjin da ya iya soyayya da kulawa, amma ita nata mijin da shi da katako ba su da maraba, don tana iya yin watanni ma ba ta saka shi a idonta ko ta ji muryarsa ba. Amma in dai dukiya ce yana da ita har da ta hauka, a iya kuɗin da ya mallaka mata in za ta yi kyautar 10 million ko motsi ba za su yi ba, balle kuma shi uban gayyar. Ban da kadarori da ya mallaka mata. Ta gane Hafsah ba ta so ta ga mijinta ba, ita kuma ganin shi kawai da ta yi ba ƙaramin tsintar dami a kala ba ne a gurinta. Wata irin zazzafar soyayyar shi ce ta ji tana mamaye zuciyarta. Ta yi haƙurin zama da mijinta na shekara takwas, amma a wannan karon dole za ta rabu da shi, domin ba irin mu'amalar da take da sauran maza ta ji tana son yi da Anas ba, son shi take, so take su yi rayuwa a matsayin miji da mata, ko ta samu farinciki da cikar burinta a rayuwa ita ma. Kuma sannan ta bar mummunar hanyar da take kai, ta bin wasu mazan da aurenta bisa sahalewar mijinta, kasancewar shi ɗan luwaɗi da bokansa ya haramta masa mu'amla da mace sai dai namiji ɗan'uwansa. Kuɗaɗen da ta mallaka sun ishe su yin duk irin rayuwar da take so ita da Anas.
Dogon numfashi ta ja ta sauke a karo na barkatai, matsaloli biyu ne za su yi mata katanga daga samun cikar burinta nan kusa, na farko ta a yadda za a yi ta samu kan Anas ya amince da ita, na biyu kuma yadda za ta raba su da Hafsah, don a matsanancin son shi da ya yi mata kamun farat É—aya ba za ta iya sharing É—insa da wata ba, nata ita kaÉ—ai take son ya zama har Æ™arshen rayuwarta. Kuma ko mene za ta yi don ganin ta mallaki Anas, saboda ita kaÉ—ai ta san me take ji a game da shi, daga lokacin da Æ™wayar idonta ta sauka a kansa zuwa yanzu......âœï¸
*Zeey Kumurya*âœï¸
[3/8, 1:37 PM] BahaushiyaðŸ‘: *YI WA KAI*
MIKIYA WRITERS ASSOCIATION
*BRIGHT PENS*
(FREE BATCH)
8.
Ina durƙushe na kifa kaina a jikin gado ina runtumar kuka kamar wadda aka aikowa da saƙon mutuwar uwarta na ji ya shigo, ƙara volume na yi ba tare da ɗago ba balle ya saka ran zan saurare shi. Ina jin shi yana zauna a gefen gado kusa da kaina. Matsawa na yi tare da ƙoƙarin tashi na bar ɗakin na ji ya ruƙo ni, ƙoƙarin ƙwacewa na yi amma ya nuna mini shi namiji ne, ya riƙe ni gam ya mayar da ni na zauna a fusace. Cikin taushin murya ya ce. "Ki yi shiru don Allah Hafsah mu yi magana, mene ne haka? Wannan kukan na mene?" Tsaki na ja na ce. "Don Allah, don darajar iyayenka ka ƙyale ni Anas, ba na son magana a yanzu." Ya ce. "Na ji zan ƙyale ki, amma don Allah ki bar wannan kukan da kike yi mara amfani, ko dan su Sultan da suke jin ki." Na ce. "To." Kawai, tare da share hawayena, duk da na san dole wasu sai sun zuɓo. Ni kaɗai na san halin baƙinciki da takaicin da nake ciki, kamar nai ta zunduma ihu haka nake ji. Babban tashin hankalina ban san me zai biyo baya ba a gurin Maman Nasmah da yadda ta zo ta gan ni, ina tsoron ta faɗa wa wasu ƴan group ɗinmu.
Wunin yau gabaɗaya haka na yi shi sukuku, zuciyata a cunkushe da jin haushin Anas. Tun bayan da na dawo daga rakiyar Maman Nasmah na kashe wayata, har dare ban kunnata ba, duk da yadda zuciyata take ta azalzalata na kunna na ji me Maman Nasmah za ta ce mini, na ji matsayin da ta ajiye ni, na Salamatu mai aiki ko kuma Hafsah Maman Sultan. Tsabar abin duniya ya bi ya dame ni ko ruwa ban kai bakina ba. Hakan ya sa nake ji na wani iri kamar mai cuta, ƙirjina har zafi yake mini.
Maman Nasmah kuwa bayan ta koma gidanta ta ci gaba da saƙawa da warwarar hanyar da za ta bi ta mallaki Anas, a ƙarshe ta yanke wasu shawarwari, abu na farko da za ta fara yi shi ne ta raba shi da Hafsah, na biyu kuma za ta saka a yi mata binkice akan shi, sai ta fara da bin iyayensa da ƴan'uwansa ta yi musu alkhairi, bayan ta tabbatar ta karɓu a gurinsu sai ta bayyana masa manufarta, yadda ko da ya ƙi amincewa wani nasa zai yi masa dole ya amince, fatanta kawai ya kasance mahaifansa suna raye, don idan da su komai sai ya fi tafiyar mata daidai. Tun yamma take kiran wayar Hafsah a kashe, don ta fara aiwatar da aikinta a kanta, domin da zafi-zafi ake dukan ƙarfe, ba za ta tsaya kuma garin kallon ruwa kwaɗo ya yi mata ƙafa ba.
Ina kwance a kan dardumar da na yi sallar Magriba Anas ya dawo. Ban ko kalle shi ba, har ya yi wanka ya je masallaci sallar isha'i ya dawo. Da kansa ya zuba abinci ya ci, na dinga kallon shi ina jin kamar na je na samu fuskarsa nai ta mari, ya na cin taliya da manja da yaji amma kamar mai cin wani haɗaɗɗen abincin da ya ji nama, sai wani lumshe ido yake yana zurƙuma lauma. Ban san lokacin da na ja wani dogon tsaki ba. Bayan ya gama ya dube ni ya ce. "Wace ce ta zo ɗazu?" Kamar na share shi, amma yadda na ji ya yi magana babu alamun wasa ya sa a ƙufule na ce. "Sai yanzu za ka tambaya? Me ya sa tunda ka gan ta ba ka tambaye ta, ta ba ka amsa da kanta ba?"
"Saboda ke nake da hurumin tambaya, ke kika kawo ta gidana."
Tashi zaune na yi cikin tsiwa na ce. "Ina gidan yake? Har kake wani ƙafafa kana cewa gidanka?" Na ƙarashe maganar ina keɓe baki. Girgiza kai ya yi ya ce. "Ki ba ni amsa kawai, kar ki tunzura ni, na yi miki abin da ba ki taɓa zato ba."
'Ka yi mana' Na faɗa a cikin raina, amma a fili sai na ce. "Ƙawata ce." Ya ce. "Ya yi, amma ya aka yi ban san ta ba tunda muke da ke?" Na ce. "Allah ne bai yi ba." Daga haka na tashi na shige ɗaki.
Anas ya bi ta da kallo, har yanzu tantama yake akan anya Hafsah ita kaɗai ce kuwa? Saboda tun sanin da ya yi mata bai san ta da irin waɗannan halayen ba, ya san dai tana da fushi idan aka yi mata abu, amma bayan wannan bai san wani hali nata mara kyau ba. Kuma shi abin da yake ƙara ɗaure masa kai rashin sanin dalilin da ya sa take masa hakan, a iya sanin shi bai san ya yi mata wani laifin ba, bare ya ce ko shi ne dalili. A ɗazu bayan ya koma gurin aiki yay ta tunane-tunane, shi mutum ne da ba ya son zargi ko ƙala wa mutum abin da ba shi da tabbas a kan shi. Hakan ya sa ya ƙi alaƙanta abubuwan Hafsah da matar da ya gani ɗazu, duk da wani sashe na zuciyarsa yana ta faɗa masa wataƙila ya na da nasaba da hakan, ya dinga tambayar kansa wacce mata ce ita da har Hafsah take kunyar ta gan shi a matsayin mijinta. Numfashi ya sauke cikin rashin sanin abun yi, makamancin haka bai taɓa faruwa a tsakaninsu da Hafsah ba tunda suka yi aure, shi ya sa abin ya dame shi matuƙa, ya rasa tudun da zai dafa wanda zai taimaka masa ya gano hasken da zai fitar da shi daga duhun da yake ciki. Yana son matarsa so mai tsanani, ba ya son abin da zai shiga tsakaninsu ko yaya yake. A parlour'n ya goce ya kwanta, don so yake ya ga iya gudun ruwan Hafsah.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.