Trending Hausa Novels

Sanadin Caca Book 1 Complete Hausa Novels By Sadi Sakhna

Reading file: SANADIN CACA.txt

Chapter 9 of 40

Littafi na É—aya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na É—aya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.

3131951977
Auwal Sadiya
First bank

Ko katin mtn ta nan
09035784150

VTU ta nan
2347068390570

Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------

Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please

*SANADIN CACA*

Mallakar SADI-SAKHNA

PROFICIENT WRITER ASSOCIATION

*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[06]

[Goje a mahangar gani]

Kwanannan ban san mai yake damuna ba,amma baƙinciki nakeji a cikin raina,duk yanda zanyi shaye shaye bana jin zafin zuciyata yana sauƙata,raina jini yake so na dunga ɗauka a koda yaushe. Hakan yake raɗamin a kowanne lokaci.
Yanzuma wannan mayaudariin daba maganinsa nayi ba yau bazanyi bacci ba,mutane gani suke kaman shune na dayayi shine yasaka na yanke masa hanji ,basu san shiÉ—in muna fikin Æ´an fashin makwantanmu ne ba.
Zanyi fashi zan É—au jini a garinnan,amma bazan bar wani daban yazo ya kafa tasa kujerar ba,saboda wannan garin nikaÉ—ai ne,idan ba goje ba to kuwa ba kowa.
Duba inda nake tara dattin tabar hannun nayi,abin ya ban mamaki danaga na tara har kusan kwarkwaro bakwai,da duk yanayin danakeji daga na shata nakeji ya sauƙa,amma yanzu baya sauƙa sai nasha dayawa tukunna..
Magana naji Ragarus yanayi,banji abinda yace da farko ba,iya ƙarshen kawai na kama.
".......itace fah wacce ogah zai aura wani satin"
Inda idonsu yake kallo nima nakai nawa idon,da wata farar yarinya na haÉ—a ido. Abin yabani mamaki yanda ta tsaida idonnata cikin nawa,dukkuwa da yanda nau'ikan tsoro suka bayyana akan ruhinta. Ban É—auke nawa idon ba,dama abune da bana tunanin na tabayi wa wani a rayuwata,wato É—auke ido,bansan wata abu wai ita kunya ko tsoro ba,wannan abubuwa banida su a halittata..
ÆŠauke idonnata tayi tana diriri,kaman an kama munafuki,haka kawai sainaji dabani dariyah,kana ganinta kasan tsoro ya cikata da haÉ—a idon da mukayi.
"Ogah barina je na siyo maka abinci a wajenta,kaga saikaji ma ko yana da daÉ—in da inta dafa zaka iya ci,ko ya kace"
"Zancen banza kenan kaidai kawai kace bari kaje kasamu damar yi mata magana kuma ta zubamaka na bati,kafi kowa kuma sanin banason raini. Dan haka idan kaje karma ka ambaci sunana a wajen"
Juyawa nayi na cigaba da tunanin dayake cikin kaina.
Inaji yana mayar masu yanda sukayi da ita,wai daya tambaya daƙyar ta faɗamasa sunanta saboda tsoro.
"Sumaimah"
Na maimaita a raina danaji ya faÉ—a,hmmm ina tausaya mata inta shiga shirgina,indai zata kama kanta to babu ruwana da itah.

Ƙarar jiniya naji na ƴan sanda,ina jin su Tunga suka tashi tsaye,so suke nace musu mu tafi kaman koyaushe,saidai yanda na jingina da jikin katangar banason na tashi.
Muryar DSP ce ta ziyarci dodon kunnena,hakanne yasaka ni dagowa na kalleshi.
"Goje abubuwan da kake a garinnan kare bazai ciba,dan haka ka biyomu ofishimmu yanzunnan kaida yaranka,dolene ka fuskanci hukunci,sannann kuma ka biya tarar mutumin daka buɗewa ciki. Babu wanda yafi ƙarfin doka duk shu'umancin sa"
"Hannu ɗayane kawai ya soka masa wuƙa,kuma wannan hannun na gojene,dan haka a dokance iya gojene zai biku kawai koh,don haka muje.
Kai Tunga ko zata mutu ko kuma tayi rai to a ƙaddamar,in kunji lafiya ku sama ta gora kawai"

Murmushi nayi lokacin dana shiga motsar ƴan sandan,idon DSP yayi zuru zuru,da alama ya ankare da saƙon dana aikawa su Tunga.
KishingiÉ—a nayi a cikin mota kafin a isa,har bacci ya fara É—aukata.Duk daren duniyata yanda naga ranar haka nake ganin daren,musamman ma idan na taimaki wani,kokuma wani yayimin abu ban ramaba,narasa mai yasa nake haka,shin kowa haka yake ko kuma ni kaÉ—aine tawa halittar daban.
Amma yau kam tunda nayi abinda rannawa yakeso to da alamar zan iya samun bacci.
Saida naji motar ta tsaya kafin na tashi zaune,dama bacci nake so nayi inda wadancan yaran bazasu takuramin ba,haka ma inna a gida,tunda zan kwana a wajen sai nayi ta bacci babu wani shedule a kaina.
Suna buÉ—e bayan motar na nufi É—akin danake zama idan na biyosu,babu wanda yafi doka injisu da faÉ—a,to gashi na kawo kaina amin hukunci.
Maganar DSP naji yana yiwa wani ɗan sanda da muke tafiya tareda shi,hmmm su gama abinsu ma,daga ƙungiyar BC(black cobra) sun dawo gobe da yarjenjyata ta shiga ƙungiyarsu,to bazasu sake gani na ba ma,nasan zuwa lokacin nafi ƙarfin wannan kurkunnasu,duk da yanzu ma zancen manyan garine yasaka nake biyosu,amma wannan shine na ƙarshe,shiyasa nazo nayiwa wajen bankwana.
"Kai copur wannan abinda ake yi masa ya ƙare daga yau,ku kaishi cell ɗin da ake saka mai laifi irinnasa,sannann gobe a miƙashi ga kotu,dan ƴan uwan wanda ya sokawa wuƙa sune suka kawo ƙara,kuma sunce kotu zasu kai ƙarar"
Da nayi niyyar na ƙyalleshi na wuce,saidai kuma zuciyata bazata iya ba,in ba gargaɗi nayi masa to bazanyi baccin danake mararin yi ɗin bama
Dawowa nayi da baya har zuwa inda yake tsaye,da wani tulelen cikinsa a cikin rigarsa,an bubbunka haram ciki ya nuna alama.
"DSP sambo in kana cin ƙasa kasani ka kiyayi ta shuri,babu ruwana da wata ƙara dazasu kai,abune ya haɗani dashi shiyasa nayi masa hukunci,da kunsan abinda yake muku a garinnaku ma da godiya zaku min.
Sannan da kake wani tada ƙayar baya nasan biyanka kuɗi sukayi koh? In mutum yasamu kuɗi kuma iyalansa yake tunkara dashi. To in kanaso suci wannan kuɗin cikin lumana,ƙaramin yaronnan ya dunga zuwa makaranta da ƙafafunsa,sannan wannan ta gidan kar ta haihu lokacin ta bayyi ba.
Shi dana sokeshi ya rayu bari muga in muka mata tiyatar cikinta zata rayu?....."
Cikin sigar jan kunne na ƙarisa maganar ina jaddada masa gargaɗinnawa da idanuna,aikuwa hakan yayi aiki,dan lokaci ɗaya gumin tashin hankali ya lullube jikinsa sharkaff..
Bansake bi takansa ba na nufi ɗakin dana ke sauƙa innazo,har copur ɗin ya buɗemin ƙofah.
Ai wannan mutumin dan basu san sharrinsa bane da kuma makircin daya haÉ—amin harma da garin gabaÉ—aya,dana kasheshi ma da sai hakan yafimin daÉ—i.wawaye duk a zatonsu harda ni a lalatacciyar satar da aka yi musu,sun raina aikina ma da alama.
Mutum yayi sata a garinnan ko ya kwashi tsiya,inda ma kajine ko akuyah idan za'ayi gashi da sauƙi,amma kuɗi kan basuda wannan arziƙin..
Ina nan kwance akan katifar É—akin har bacci ya É—aukeni.

__***__

Tarin bola ce tsiri guda kaman zata dabo sama,da alama duk faÉ—in birnin garin anan suke tara tarkashen sharar.
A can cikin bolar saika kula ga hango motsin mutane ledodi sun lullubesu,suna nan kwance har yanzu basu tashi daga suma ko baccin wahala ba.
Malam audu ne yafara buÉ—e idonsa tareda ture ledar da take kansa,waya sani ma kota kashi ce.
Tashi yayi daƙyar ya zauna yana nishi,saboda tsamin da jikinsa yayi.
Gabas ya kalla kana da yamma,mai kuma suke a tsakiyar bola da ranar Allah.
Zaro ido yayi lokacin daya tuno izayar da suka sha a jiya a gidan dasuke aikin.
Gefensa ya kalla inda gaji ke kwance shame shame akan wasu tsummokara,saikace mahaukaciyah.
Ƙoƙartawa yayi yakai hannunsa ya kwaɗa mata duka a kunkuminta,aikuwa ta saki azababben ihu tana wangale baki.
"Wayyo wayyo kunkumina ku taimakeni jama'a zai cire"
"Ke dallah tashi mubar wajennan idan zamu iya tashi,waÉ—ancan dangin fir'aunan bayan gari suka kawomu cikin bola"
"Bola kuma wacce iri"
Itama ta yunƙura tana kallon tsummokaran da take kai"
Motsin Atika da sukaji a gefensu ne ya sakasu waiwayawa,kuma gaji ta fasa faÉ—in abinda yazo bakinta.
Kuka take tanan kururuwa kaman a cikin bacci,da alama abinda yafaru jiyanne yake dawo mata.
Jijjigata gaji tayi cikin baƙin ciki,dan koma mai yafaru ai ita ta jawo musu,da yanzu sun gama aikace aikacen gidan suna karyawa da lafiyayyen abinci.
"Shegiyar yarinya mai É—uwawun bin maza,ai gashinan abinda kika jawo mata,in sonsa kike tun farko da ki faÉ—amin mana asan surkullen da za'ayi,amma daga ke har ubannaki dayake garorine ku kagu jimanaye kunga kuÉ—i,sai karba kawai kuke bakwa tunanin mai ya faru. Ban tashi sanin mai yake faruwa ba sai ranar dazan sha duka tukunna.
Sai ku tashi mu tafi ai .......ahhh......."
Shuru tayi tana jujjuya kunkumi,dan dama sojan kunkuminnata yayi ta sambaɗawa kulƙensa.
Hararar malam audu tayi dayayi mata sannu,yunƙurawa tayi ta shi kana ta tashi sauran yaran wanda suke baccinsu hankali kwance.
Bayan sun tashi a wajen tafiya suka farayi zuwa tasha,kowa sai komaÉ—ewa yake yana tafi kaman horon cikin film É—in mayu.
Duk inda suka wuce kallon su ake,amma ko a jikinsu,tsamin da ƙashushuwansu suke ma ya isa.
Sa'ar da sukayi daga inda suka zubar dasu bashida nisa da tasha,saidai kuma ba a nan gizo yake saƙar ba kuɗin motar komawa garinnasu ne aiki.
Tun safe suke tashar har yamma,ganin bazasu samu mota ba yasa suka samu wani waje a tashar suka zauna.
Hayam hayam kowa sai baza hamma yake kaman zaici babu,idonsu yayi zuru.
"Yanzu kana gani zamu mutu bazaka nemo mana abinda zamuci ba,huhulahu kawai"
"Wai nikam gaji meyasa tunda kika shi a cikin bolar nan ni kike sauƙewa tujara,ya isheki fah haka,wlh zan sake mangareki ba ruwana da ciwukan da suke jikinka"
"Hehehe to ko sun duka ƙwalƙwalwarka ne take faɗa maka zaka iya dukana iyeee,kalleka fah kaima a doddoken kake ba iya ni kaɗai ba,ƴan ƙafafunka ma daƙyar kake ɗagasu sai kace lagwani. Kaff danginku haka kuke sai kace ƴaƴan kunika,zama dakai yasa duk ƴaƴana haka suke ƙafafu kaman liƙo cikin kuwa kaman randa,ni ba abinna zagesu ba kaima haka kake. Shiyasa nake mamakin ya akayi goje yakeda ƙira da ƙarfi,ubansa da uwarsa ba haka suke ba,har Addu'a nake ko ƴaƴana zasu iyoshi,na huta da aikin kashinsu da yawa,yaro in ka haifeshi bazayyi tafiya ba sai ya shekara uku tukunna wani abin ma..........."
"Dan Allah gaji kiyi shuru haka,dan Allah ku bar faÉ—annan sai munje gida,kowa sai kallon ku yake"
Kaman tayiwa dutsi magana ko kallonta basuyi ba,wata harara malam audu ke yiwa gaji kaman idonsa ya fito,dan yaji zafin wannan wankin babban bargon da tayi masa a tasha.
"Hmmm ke yanzu har zakice ma danasanin aure na kikeyi,daɗinta ma mu gidanmu ba mayu bane bama tanɗe kuruwar mutane,kowa yayiwa wannan ubannaki shaidar ko tsuntsune ya gifta da kan gidanku sai ya tanɗe kuruwarsa. Bandama ƙaddara data haɗani take,kaff abokaina da ƴan uwana babu wanda yayi na'am da aure na dake,nima kaina bansaniba ko tanɗeni kikayi"
"Hhhhhh narasa mai zan tanÉ—a inma maitarce sai kuruwarka,ko ban tanÉ—e ta bama a tanÉ—en take,dan daga ganinka yanda kake haka ma kuruwar taka take"
Tashi atika tayi tabar wajen,kowa sai kallonsu yake amma su babu ruwansu,ina zatakai wannan abin kunyar,wai dama haka auren yakene,kowa na ganin hanjin kowa,shiyasa fah ta tsani aurenma ita a rayuwarta,tafiso kawai a hole in holewar tazo a wuce wajen.
Tana cikin tunaninne taji muryar wani É—an garinsu. Juyowa tayi suka haÉ—a ido da tasi'u,shima da yace yana sonta,kayan gwari yake kawowa daga garinnasu zuwa nan,dama sana'arsa kenan.
"Lahhh tasi'u kaine"
"Ehh nine atika mai kike anan wajen ga jikinki duk ciwo?"
Inda inda tafara na ƙaryar dazata yimasa,can kuwa wani abu ya faɗo mata a rai.
"Uhmm dama gida zamu tafi to shine jiya barayi suka shiga mana gida,bayan sun ƙwace komai kuma suka yimana duka"
"Innalillahi garin ya haka,in su malam É—in suke,dama tafiya gida zanyi ko zakuzo mu tafi kawai,saidai zamuyi dare a hanya saboda motar tawa batada gudu"
"Babu komai hakanma mun gode,barina ƙirasu toh"
Wajen iyayennata ta koma,zuwa yanzu sun daina faÉ—an kowa ya karyar da kai yana nishi na wahala da yunwa.
Lokacin data faɗamusu yanda sukayi da tasi'un ba ƙaramin murna sukayi ba.
Biredi ya siya musu da zobo irinna É—urawar nan ganin sun fita hayyacinsu.
Kaman almajirai kuwa haka suke turawa a cikinsu,kowa so yake yayi maganin yunwarsa. Banda ruwan albarka babu abinda suke masa,kaman basune sukayi masa cin mutunci ba dayace neman auren atika,a ganinsu shi ba sa'anta bane,yanzu gashinan babu kunya suke masa godiya daya taimakesu.
(Shiyasa a duniya ba'a son kaci mutuncin mutum ko ya yake kuwa,saboda Allah ne kaÉ—ai yasan ranar da zai maka rana,a lokacin da bakayi tsammani ba. Allah yasa mu dace dai.)
Daff da magriba suka kamo hanyar garinnasu,tunda suka tafi wata shida sai yau zasu koma,dama ance in daÉ—i bai kawoka gida ba wuya ai zata kawo ka.
Shuru sukayi a cikin bodin motar a tsakiyar kayan miyan da bai siyar ba,sai wulla ido suke,ga motar batada gudu ko kaÉ—an,ko yaushe zasu isa oho.
Kaman a sama sukaji muryar tasi'un yana tashinsu,abin kunya sunyi bacci duk sunyi rugu rugu da tumatir É—insa,wani abinma hadda taruhu da tattasai,gasu da É—anyen ciwo a jikinsu.
Banda mutsu mutsu da nishin azaba babu abinda suke.
Motar ba wani tudu bane da ita,amma saida sukayi dagaske kafin suka iyah fitowa,ko tsayawa yimasa kyakykyawar godiya basuyi ba suka shige gida,dan basa cikin hankalinsu.
Lokacin gari duru duru yake ana shirin ƙiran assalatu.
Inna mairo ta fito da butarta zata shiga banÉ—aki sai ganin mutane tayi sun shigo gidan,salati tafara jiki yakama karkarwa,dan tayi zaton gamo tayi,saikuma ta kula ashe su gaji ne
"Gaji kuma?"
TafaÉ—a cikeda mamaki.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.