Trending Hausa Novels

Sanadin Caca Book 1 Complete Hausa Novels By Sadi Sakhna

Reading file: SANADIN CACA.txt

Chapter 5 of 40

Bangama jin mummunan labarin da suke ba na sulale a wajen,saboda yanda ƙafafuna suke rawa bazan iya gama ji ba sam.
Hawayene kawai yake zirara a idona,yayinda dukkan wani abu dayake amfani a cikina ya dauƙi yajin aiki na wasu daƙiƙu.
Tun inajin hayaniyarsu da shewarsu har na daina ji da alama sun bar wajen,na daÉ—e ina zargin mutanen gidannan namu basu san Allah ba,amma yau kam na tabbatar.
Gari yafara haske asuba ta gabato,kafin na bar wajen na nufi É—akinmu,ikon Allah ne kaÉ—ai ya kaini É—akin.
Dana kwanta ma ba bacci nayi ba,zuru nayi har assalatu tayi.

Ɗankwalin danake yin sallah dashi na ɗauka na fita daga ɗakin zuwa inda nake sallah,a canne ƙofar wani baban yayanmu wanda yagina ƙofarsa amma bayyi aureba,a wajen nakeyin sallah,saboda ɗakinmu kam nasan bazzayi sallah ba.

Bayan na idar da sallahr na daɗe ina roƙon Allah kaman yanda na saba,yau kam banyi karatun Ƙur'ani dayawa ba,saboda yanda bacci ke fizgata,ban samu damar komawa ɗakiba anan bacci yayi gaba dani.

Zafin rana ne yafara cin ƙafafuna,hakanne yasa na tashi na zauna,safiya tayi ashe har rana tafito bansani ba.
Ajiyar zuciya nayi dan ma yau banice dayin wanke wanke ba,shara kawai zanyi sai ɗora abincin siyarwar ammi. Dan haka cikin nutsuwa na tashi na ninke abin sallahr tawa zan bar ƙofar.
Motsin mutum naji hakanne yasa na É—aga idona.
Da yaya Musbahu na haÉ—a ido yana tsaye yana kallona.
Rusunawa nayi na gaisheshi,yanada mutunci shikam sosai,dan ko hayaniyar gidan bata wani dameshi ba,shine babban É—an ammi,yayi diploma yana koyarwa a makarantar secondry ta garin.
"Sumaimah lafiya kikazo nan kina bacci,na dawo daga sallah naga kinyi bacci anan"
"Ahh bakomai kawai baccinne ya É—an daukeni"
"Ohh toh,kiyi haƙurifah da abinda baba yayi miki kinji,in kika jure komai zai wuce kinji,yau ma nayi masa maganar a masallaci, amma sai ya hauni da faɗa,kuma jiya da mukayi masa magana yace zai bashi kuɗin yafasa aura miki shi,amma kuma yau da asuba ya dage sai ya aura miki shi,abin yabani mamaki"
Idon ne ya cicciko lokacin danaji abinda yaya Musbahu yace,maganar dasu inna rammah sukayi jiyace ta faÉ—o min araina,wato su yayah Musbahu ne suka tausheshi akan aurar dani ga wancan dodon,har ya yarda su kuma waÉ—annan matan suka sake juyar da kansa.
Saurin share hawayen idona nayi tareda jijjiga masa kai.
"Babu komai yah Musbahu in hakan shine ƙaddarata banida zabi illah na rungumeta,dama dolene bawa yayarda da ƙaddara mai kyau ko kuma akacin haka.
Har nazo fita daga ƙofar tasa yasake yimin magana.
"Kije ammi tana ta nemanki kinji,ga wannan kuma ki boye ki dunga siyan koko,an bani albashina jiyah"
Yafaɗa yana miƙomin naira ɗari biyar.
Wani kukane ya tahomin lokacin dana saka hannu na karba,wannan karon ban tare shi ba nayita kunza kayana,tun yana rarrashi na har yabari yabar ƙofar.
Allah ne kaɗai yasan yanda nake ƙaunarsa a cikin yan uwannanwa,da kuma yanda yake birgeni,shikam ya fita zakkah a gidannan.
Harna isa ƙofar ammi ina kwarara masa ruwan Addu'a ta samun nasara a raina,Allah ya haɗashi da mace tagari ba irin matan gidannan ba,dan daga kan iyayen har surukan kaman an cuɗasu an rabasu haka suke.

A baranda na sameta tana tsince shinkafar daza'a dafa in anjima,wajen kaca kaca da miyar tuwo da kuma kunu,ina yara suka zuzzubar lokacin da suka karya.
Gaisheta nayi kafin na leƙa ɗakin inna rammah mah. Tanata masifah da yaranta suna rashin ji.
Fuskarta dauke da murmushi da amsamin,kaman ba itace ta gama faÉ—in kalaman da mutumin dayasan zai mutu bai kamata ya furta ba.
Tuwo nah na É—auka naci nakai kwanon wajen wanke wanke.
Bishirah da asiyah ne suke wanke wanken,Æ´ar rammah da kuma ammi.
Harara ta Bishirah tayi dana ajiye kwanon cikeda tsiwa.
"Wai mutum bazai ci abinci da wuri ba dan mulki,sai an kusa gama wanke wanke ya kawo kwano"
Kunnenta na riƙe ta bangaren danake,dan abin yayimim ciwo,yarinyar da in auren shekara sha biyu zanyi saina kusa haifarta take faɗamin wannan maganar.
"Ke wato kin iya rashin kunya koh,yaushene ma kuke wanke wanken,naga saikuyi sati bakuyi ba nina ke,dan an fara baku shine har kun fara tsiya koh?"
Maganar inna rammah najiyo daga bakin É—akinta lokacin da Bishirah ta kwanÉ—a ihu kaman ina zare mata rai.
"Sake mata kunne to ƴar gadon marasa mutunci,baƙin cikin menene haka da har zaki cire mata kunne,so kike ki nakasata tayi zaman gida kaman ke?"
Sakin kunnennan ta nayi,yayinda maganganunta kemin zafi a rai,kallon baki isheni ba nayi mata kafin na ɗau tsintsiya na fita share harabar ƙofar tamu,duk abinta dai nasan bazata dakeni ba,da dai ta dakeni komai ma tayimin,amma yanzu na wuce duka,saidai tayi min muguntar boye ta asiri.
Abinda yafarune ma ya faÉ—omin a rai,hakanne yasa na nufi kewayen dabbobin kaman da niyyar cewa shara zanyi.
Akan wajen da sukayi binne binnen idona ya sauƙa,tabbas kam ba mafarki nake ba..
Jan lilon ƙafafuna nayi zuwa wajen,tsugunnawa nayi idon kyam akan abinda ƙarfi da yaji yakeson rabani da gidanmu.
Harna saka hannun zan tone wajen saikuma na tuna maganganunsu,wataƙila inna tone asirinnan ya karye baba yagane kuskuren da yayi a caca,har ya nemi kin auramin goje,to amma su inna rammah fah,zasu barni na cigaba da zama harna samu miji daidai dani nayi aure. Tabbas ba karamin aikinsu bane su aikata abinda sukayi iƙirarin faɗa.
Inkuma yanda suka fada dagskene na tarewa Æ´aÆ´ansu farin jininsu wanda nasan bokane yafadamusu dan ya ci kudinsu,toh zan tursasa ammi sake cutar dani muddin akan Æ´ar tane Asiyah.
Wanda hakan zai zama abune da bazanso ya kasance ba.
Maida kasar dana fara tonewa nayi na binne wajen cikin sanyin jiki,na zabi barin gidan kawai,koma mai zaimin yayimin Allah ne ke riƙeda rai na ai,wuya kuwa bata kisa sai kwana yaƙare.
Tashi nayi na barbaje ƙasar tareda fara share wajen,banyi niyya ba amma inna ƙiyi kar suyi tunanin naga abinda sukayi jiyan.

Wannan wace irin rayuwa ce,ace wai aisiri akayi maka amma ka ƙwammaci ka barshi ya hau kanka......ke duniyah.

Littafi na É—aya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na É—aya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.

3131951977
Auwal Sadiya
First bank

Ko katin mtn ta nan
09035784150

VTU ta nan
2347068390570

Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------

Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please

*SANADIN CACA*

Mallakar SADI-SAKHNA

PROFICIENT WRITER ASSOCIATION

*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[04]

Saida ya daidaita hasken a cikin idonsa kafin ya buɗe idon dukka. A kwance yake a inda ya suma jiya,wato cikin bukkar,yunƙurawa yayi babu salati bare godiya ga Allah.
Kakkaɗe jikinsa yayi daga ƙurar dayayi kafin ya fito daga cikin bukkar yayi wata miƙa.
Ido ya haɗa da karnuka guda uku,murtuƙa murtuƙa a kwance a filin wajen,suna kallon ya fito suka nufi inda yake.
FeÉ—uwa yayi dukka suka amsa masa kaman sunji mai yace.
Hanyar dazata kaishi cikin gari ya nufah kansa tsaye yana tafe suna take masa baya,yanda yake baƙi fuskarnan duk gashi haka suma suke.
Duk hanyar dayabi yara matsawa suke harda samari.
A wajen mai shayin unguwarsu ya zauna akan benci,su kuma karnukan suka tsaya a bayansa kaman wasu fadawa.
"Kai iliyah yiyomin haÉ—in shayinnan da kake min,kaga na juyeshi a cikina nan"
Dama murya a shaqe,ta kuma haÉ—u da tashi a bacci,banda hamami babu abinda yake,amma hakan ko kaÉ—an bai dameshi ba,haka wanda yake gefensa ma ko mai zayyi bai isa yace ya dame shin ba.
Ido suka haÉ—a da Iliyah wanda yake ta aikin juyah shayi daga wannan kofin zuwa wannan.
"Amma goje na wata biyar fah ya taru akan ka ko ƙwandala baka rage ba"
"To dolene saina rage koda banni da kuÉ—i iyee,kai akan shayin zaka dunga tsayarmin,idan bazaka yimin haÉ—i ba faÉ—amin naji"
"Ahah ba haka bane,kawai dai nima kuÉ—in hannun nawa ne ya......"
"Kaga banason jin wannan muryartaka mai kamada ta ƴan hamsin,haɗomin shayin kasamu taska injini ya rage maka wani abun,in kuma kasake magana zan baje rumfar nan yanzunnan,kafi kowa sanin banason ƙorafi tamm"
"To shikenan ogah goje barina gama sheƙawa idi tukunna"
"Wanene kuma idi?"
Goje ya faÉ—a yana duban mazan dasuke zaune a wajen. Wani tsamurarre a gefe Iliyah ya nunawa goje. Suna haÉ—a ido yayi saurin kawar da kai tareda cewa.
"Ahh bakomai Iliyah haÉ—a masa zan jira ai"
YafaÉ—a muryarsa tana rawa. Ganin har bayan yayi maganar goje bai daina kallonsa ba.
"Kai É—an garinnan ne kuwa,bansan ka anan yankin ba,ka sanni?"
Goje ya tambayeshi yana ƙare masa kallo kaman yaga ɗan ƙwaro.
"Eh .......hhhh to rani nazo,wannan shine karona na farko,wata na guda kenan a garin"
"Ohh toh...in kanada dabbobi ko wani abu muhimmi karka barshi a waje har zuwa dare,in ba haka ba yazama na bayin Allah,sannan in faɗa ya kaure a lungunku kaji ƙarar wuƙa kada ka fito, ina tausayinka shiyasa na faɗa maka"
ÆŠaga kai yayi alamar yaji.
Suna cikin maganar ne Iliyah ya miƙowa goje ruwan shayin tareda yankan biredi.
Karba yayi maƙwat saida yayi rabin kofin,kafin yanki rabin biredin ya tauna.
Kafin kaceme yatashi dashi,wata gyatsa yayi kana ya miƙe daga kan bencin.
"Sai gobe kuma"
Dukka a tare suka masa a sauƙa lafiya mutanen wajen.
Cikin gida ya nufah yana haÉ—a hanya.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.