Sanadin Caca Book 1 Complete Hausa Novels By Sadi Sakhna
Reading file: SANADIN CACA.txt
Chapter 6 of 40
Wata ajiyar zuciya suka sake a tare,kaman wanda aka basu horon É—auke numfashi idan ya tafi su sake.
"Kai Iliyah wanann É—in waye shi,shima a anguwar nan yake"
Idi yafaÉ—a yana zare ido,har sannan hankalinsa bai koma daidai ba da ganin gojen.
Dariyah wani saurayi yayi a gefe kafin yace.
"Goje kenan kake ji,watansa guda baya cikin garin,jiya dai muka ganshi ya dawo,bakada labarin sunyi caca ne shida baban su ubaidu,ya cinye shi yace yabashi kudinsa shikuma bashida ko sisi. Dayaga yana shirin yankashi ya fanshi kansa da Æ´arsa,yanzu haka muna nan mun zuba ido wai wani satin za'a É—aura aure"
"Kai mtsww yarinyar nan kuwa ga kyau ga hankali,wai a rasa dawa za'a haɗata sai goje,ai an cuceta wlh. Kai mutuminnan fah naji ƙishin ƙishin ma wai asiri ma idan akayi masa baya kamashi,gashi da wani ɗan banzan ƙarfi,sarkin garinnan ma shayin horashi yake,shiyasa idan yaci kayanka yanda kasan yaci kayan uwarsa haka yakeyi"
"To kai bakada labarin abinda yayi yai batan zana bashi ba alamunsa,naji fah wai haddashi a waÉ—anda suka 'balle masana'antar shinkafa ta garinnan,Æ´an sanda sunzo kama su suka kashe guda biyu. Amma suma sun kama barayin guda uku. An kamashi aka kulleshi,bamu san mai yayiwa shigaban fursunan ba da kansa yasako shi......hmmm wannan mutumin ai ya wuce yanda kuke tsammani"
"Kai ku bar wannan zancen haka,tunda munanan dashi ai zaiga komai mah,ya batun ni honarable neh,kuna ga zaici siyasar nan kuwa,naji ance yaraba mashina a hamsin a garinnan"
"Rabu damu da wannan barawon,ko tsafi yake da tsohuwar zaba bazan dangwala masa ƙuri'ah ta ba,haka suke barayin banza,suna zaune a office suna satar kuɗin mutane da biro,shuru bakajin ɗuriyarsu sai siyasa tazo tukunna........
Barina bar teburin mai shayinnan nayi gaba......
___**___
Gidan matsakaicine kuma na daidai ƙarfi,ginin ƙasane anyi masa ya'be da sumunti,amma wani wajen duk ya bubbule saboda daɗewa,kuma ba wani kula ake dashi sosai ba.
Kofah biyune a gidan,inda iyayen goje suke,saidai babansa ya rasu sai inna mairo kawai ita kaɗaice a ƙofar. Sai kuma ƙofar malam Audu ƙanin babansa da matarsa gaji da ƴaƴansu,yana aikine a gidan wani alhaji,daga bashi ɗaki a gidan gaji ta tattara da ƴaƴan ta suka bishi,suna can yau kusan wata shida. Ƙofarsu shuru,anan goje ya ɗaure saniyarsa.
Saikuma ƙofar goje,shima ɗaki ɗayane na kasa da banɗaki a gefe,kullum ƙofar ɗakin a garkame take da ƙwado,kaman wani abin arziƙine a ciki ba kayan dauɗa ba.
Sanda gaji tana nan kullum sai sunyi rigima idan ya daki ƴaƴanta in suka shiga ƙofar,inta fara masifah sai yace zai doketa tukunna tayi shuru,shiyasa tafiyin masifar idan baya nan,dan a gabansa kam ko mijinnata ma albarka.
Kullum cikin ƙorafi take wai inna mairo tazo itada ɗanta sun takura musu. Shiyasa da malam audu yasamu aiki itama tabishi,dan itama inna mairon da a birni suke itada mijinta,yana aikin masinja a kotu,yin ritayarsa ne yasaka su dawowa mahaifarsu,shekararsu biyar kenan da dawowa.
Amma goje ya fitini garin kaman dama anan ya tashi.
A zaune take tasaka kayan yin igiyarta tanan tukawa,gidan tsitt kaman bakowa,tun abin yana damunta har ta saba yanzu.
Bayyi sallama ba dan dama bayi yake ba saidai ta É—aga ido idan taji motsinsa.
Jijjiga kai tayi tareda yimasa magana,ganin ya yaÉ—au buta yana jijjiga wa,da alama ba ruwa a ciki.
"Yau kuma daga ina"
"Daga jeji a can na kwana"
"Ohhh gari ya hargitse da abinda ka jawo na auren ƴar gidan uwaisu,sunzo nan jiya akan batun,Nayimusu kwatancen gidan da kawunka yake,amma sunce abin baya wani buƙatar manya. Nayi ta zuba idon shigowarka amma banganka ba sai yanzu,wai dan Allah yaushe zaka daina........"
"Ina zuwa inna barina rage marata tukunna,nasha shayi yanzu a wajen Iliyah"
"Yau É—in ma,kabiyashi kuÉ—insa ne,do Allah ka tausayawa mutuminnan da shan shayinsa karka karya masa jari"
"Kai daɗina dake inna kowa yazo yamiki ƙorafi akaina saiki yarda wai,Allah zan fara karya ƙafar duk mai shigo gidannan yana kawo zancena,yanzu dai barina zaga bayan gida,banyi sallannan da ake da safe bama fah"
"Ehhh bakayi sallahr asuba ba,har goma tayi,goje yanzu goje kanaso kuwa........"
"Kai kai kai inna wai abin magana baya miki yawane,yanzu da kika rikeni da yanzu nayi alwala,kinga kenan laifinki ne idan banyi da wuri ba koh"
Sakin baki tayi tareda tsayawa da murɗa igiyar tana kallonsa har ya shige cikin banɗakin,rabonta da ganinsa tun jiya da safe data saka masa koko yasha ya fice,wai yanzu kuma yazo yana cemata laifinta ne da bayyi sallah da wuri ba,hmmm babu mamaki ma sauran sallolin babu wacce yayi a ciki,dan hakan ba ƙaramin aikinsa bane.
"Allah ya kyauta"
TafaÉ—a tana cigaba da tukarta.
Bayan ya fito daga banÉ—akin bai tashi zuge zee É—in wandon a ko ina ba saida yazo gaban inna mairon.
"To wata sabuwa,shi wandonne duk ka baro banÉ—akin baka jugeshi ba sai a gabana?"
"Mtsww bazaki gani ganeba wandonne ya matseni daƙyar nage zugeshi"
"Sai akace kuma dole sai kasaka shi koh,zauna muyi maganar nan,dan tana nan a ƙahon zuciyata da ita na kwana. Inaso kayi aure goje ina so naga wanann rana,amma ban taba tunanin irin wanan auren zakayi ba,wanda ko a tarihi ban daba jinsa,yanzu kaida shi babban kobon kunyiwa yarinyar nan adalci kenan iyee,ace kuna wai caca ku saka rayuwarta a ciki?"
"Inna mai nayine anan wajen,ina lafina a cikin wannan lamarin,ko saboda kullum ni laifi nake kai. Gayennan bani nace yayi caca dani ba bashi da ko sisi,shikansa yasan bana ɗaukar asara,kuɗi nace yabani bashida shi yabani ƴar sa. Yanzu ni bakiga ma cuta tah yayi ba,nifah saniya tah sailuba tah na saka a cacar nan,daya cinyeta fah shikenan zuwa zayyi ya siyarta,shiƙuwa ƴar sa da mutanen wajen suka roƙeni na karba wazan kaiwa yasiye ta,dole fah saidai nasaka ta a gidannan nayita kiwon da babu riba,amfanin ɗayane zata dunga yimiki aiki kinga saiki huta dama bakida lafiyar ƙafah. To banda wannan ta ina zan ƙaru da ƴarsa faɗamin shi"
"Yanzu Æ´ar adam Æ´ar mutane kake haÉ—awa da wata can dabba,nidai dan Allah in an kawo yarinyar nan karka cutar da itah kaji?"
"Dan ta wannan ne bani zaki faÉ—awa ba,ba a kaina zata zauna ba,in ta kiyaye abinda aka ce mata to ta tsira"
"To naji daÉ—in hakan,yarinyar nan tausayi take bani sosai. Ya batun inda zaku zauna toh,ko kai a gyaramuku sashen Kawunnaka ku tare a can,tunda shi baya nan"
"Nida wa zamu tare É—in,dan Allah ki bar wannan zancen,ba ga nan É—aki a gefenki ba ta zauna mana,in zancen Waccan dattijon kike kwanannan zaki gansu sun dawo,waye zai zauna da wannan matar itada tambadaÉ—É—un Æ´aÆ´annata"
Inna mairo taji haushin abinda yace,to amma yazatayi ,tasan a kaff rayuwarsa babu wanda baya maidawa magana in ka É—auketa,ciki kuwa harda sarkin garin.
"Kabar wannan zancen dama nasan shi kakeson yi,É—akinnaka dai zaka gyara ku zauna a can,wanne irin aurene kai kana can ita tana nan,taya zaku fahimci juna a haka."
"Fahimtar juna hhhhhhh wai to kawai tazo gidan ta zauna mana toh,dole sai anyi mata aure dani tukunna ......afff banyi sallar ba ashe,barina je na gurguzata kafin ta anjiman tazo"
Tashi yayi da sauri ya nufi ƙofar tasa,inna mairo ta share masa harabar wajen kuwa. Makulli yasaka ya buɗe ɗakin,bayan ya shiga ya maida ƙofar kaman munafuki.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.