Trending Hausa Novels

Sanadin Caca Book 1 Complete Hausa Novels By Sadi Sakhna

Reading file: SANADIN CACA.txt

Chapter 13 of 40

[Sumaimah a mahangar gani]

Hannu naji yana bubbagani,can kuma sai naji murya ƙasa ƙasa tana min magana..
Saida baccin ya dan bar idona kafin na naji ashe inna ce take tashina.
"Ƴar nan tashi kiyi sallah anyi assalatu,ko bakyayine"
Tasake maimaitawa a sanyaye.
Juyi nayi kafin na tashi zaune,ohh ban taba tunanin kwana na nafarko a gidan zanyi bacci hadda juyi ba kamar haka.
Kallonta nayi da farin hijabi a jikinta,hannunta riƙeda carbi tana kan sallaya.
Na lura da hakanne saboda hasken É—an Club da ake haÉ—awa ya haska É—akin..haka kawai naji ta burgeni,indai bawai mantawa nayi ba,tunda nake babu wanda ya taba tashina sallahr asuba a gidan mu.
Saƙƙowa nayi daga kan gadon wanda yanxu yazama nawa.
Inda buta take ajiye na nufa na É—auka domin zuwa banÉ—aki.
Bayan na idar da sallah gaisheta nayi ta amsa cikin sakin fuska,har zuwa lokacin lazimi takeyi,nima danaga haka ban koma baccin ba saina fara nawa.
Muryar ta can sama sama naji tanamin magana,firgit na kalleta,kenan bacci na cigaba dayi a zaune.
"Sumaimah ki koma ki kwanta mana,ke ba kaman mu ba da baccin mu yanzu yayi ƙaranci,bare kuma kunsha hidimar biki,ki koma kiyi baccin ki kinji"
ÆŠaga mata kai nayi,dan dama hakan nakeso.
Muryar inna naji tana magana da wasu yara,hakanne yasa na buÉ—e idona,lokacin rana ta fito tangargar.
Fitowa nayi daga É—akin na zauna a tabarmar da take zaune..
"Kin tashi kenan,ga abin karyawa toh.."
"ÆŠumamen tuwo ne sai kuma wani É—an kwano da awara a cikin kaman guda bakwai,sai kuma kofin kokoh"
"Hmm kiyi haƙuri fah ƴar nan,amarya da aka sani da cin kaji a ranar farko kega abinda kika samu,wlh banda kuɗine,awarar ma a wajen gaji na karbo nace ta bawa baƙuwa"
Allah sarki tausayinta ne yakamani,hmm batasan a hakan kayan daÉ—i tabani ba akan abinda nake ci a gidan.
"Lahh inna karki damu,shimfiÉ—ar fuska ma da kika bani tafimin komai da kike tunani,fatana Allah bamu ikon zama cikin aminci"
"Ameen ƴar nan,gaskiya ko kusa baki dace da wancan huhun ba,kawai dai ƙaddara ce da idan tazo baza'a tsallake ba. Sannan dan Allah kiyi haƙuri da son kaina,dan lokacin da naji wannan batun nayi niyyar na hanashi,amma kuma sai nayi tunanin wataƙila sanadin shiryuwarsa ne aurennaki. Yanzu dana ganki ma na ƙara tabbatar da hakan,dan inaga sai an zage garinnan kafin a samu mace irinki,kiyi haƙuri kiyi haƙuri kinji"
"Inna kidaina bani haƙuri,nima lokacin da Naji labarin kwana nayi ina Addu'a akan Allah kar ya hadani dashi,amma dana ga an ɗaura aurena dashi jiya sai nayi tunanin inaga shine mafi alkhairin dana daɗe ina roƙon Allah yabani,dan haka ki daina wannan bada haƙurin ba laifinki bane,fatana Allah yabani ikon jure duk abinda zaije yazo."
"Ameen kiyi ta haƙuri da sannu zakiga mafita"
Zancen duk ya isheni,tunda gani nazo gidan to kuma banason tuna wai dama ban xo ba,dan haka nayi ƙokarin kawar da zancen..
"Uhm inna wanne aikin za'ayi ne a gidan?"
"Ehh toh banice yanzu da tuwo ba gaji ce take saita bani,wanke wanke kuma atika ce take,idan bata nan kuma ninayi in su farida suna nan su jijjiƙa"
"Toh bari naje na gaishe ta ma,sainaji wanne aiki zan kama mata"
"Ahah kijidai ku gaisa,amma batun aiki ko zakiyi ma ai sai kinyi kaman sati ko sati biyu,dan haka kada ki damu kanki atika ai tana nan zata zo tayi wanke wanken"
To nacewa inna tareda kallon inda uban tulin wanke wanken yake,wasu manyan tukwane na abincin siyarwa da kuma su kansu kwanikan abincin siyarwar sun cika wajen famm,ƙudaje sai bin miyar data bushe suke,kaman dai na gidanmu haka yake..

Sallama nayi a bakin ƙofar,babu wanda ya amsa,sai hayani ya suke,inaga ma basuji shigowa ta ba.
Ban dai yi ƙasa a gwiwa ba na ƙarisa wajen da suke zaunen.
Gaji ce suke ta musu itada wata matashiyar budurwa,wacce ta juya bayan ta can.
"Haba gaji,idan baki yarda dani ba wazai yarda da nine,nace miki ban É—au kuÉ—inki ba,yakikeso nayi ne wai?"
"Atika nafasan halinki,kwanannan na kula bakida kuÉ—i,koya nayi wasafai dana wa É—ebewa zakiyi,ya za'ayi ace har dubu biyu ta b'ata a cikin cinikin"
"To shikenan ai gani ki cazeni mana,kokuma ka jaka ta nan"
"Ohh shasha zaki mayarni ma,na caje........"
"Salamu alaikum"
Nasake sallama dan su san ina wajen..
A tare suka juyo inda na É—ora idona akan Budurwar..
"Atika??"
"Na faÉ—a cikeda mamaki"
Wani kallon juya ido tayimin tareda cewa cikin muryar duniyanci..
"To ya ranki,kinyi mamakin gani nane komai?"

Littafi na É—aya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na É—aya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.

3131951977
Auwal Sadiya
First bank

Ko katin mtn ta nan
09035784150

VTU ta nan
2347068390570

Shaida kuma ta nan
09035784150

Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------

Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please

*SANADIN CACA*

Mallakar SADI-SAKHNA

PROFICIENT WRITER ASSOCIATION

*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[10]

Atika....dama Æ´ar gidannan ce? Nayiwa kaina wannan tambayar,har sannan ban gaskata hakan ba.
Tun tana yarinya dama na santa,fitinanniya ce ga faÉ—a ga kuma kwaÉ—ayi na abin hannun maza..
Ko zuwa na na ƙarshe ma a wajen talle saida ta nemi muyi,nice na shareta kaman bata wajen,gashi idan taga wani yana ciniki ita batayi zaka ga jaraba da msganganu,dan ma ita bata kwantai,dama ƙirarinta kenan,idan tayi ma mutanenta zasu saye ta..
Tabb dole kam tayi,yanzu nagane dalili ba'a ƙasa ta ɗiba ba.
Ko hanya banason mu haÉ—u da itah,ba kunya takeji ba saita tara maka mutane,ashe zamuzo mu haÉ—a gida É—aya da ita ma,tabbb É—i jan.
Dauke kaina nayi daga kanta na kalli gajin.
"Uhm Inna gaji ina kwana,an tashi lafiya?"
Wani rausaya tayi tareda gyara ƙunzugun zaninta,nasan bazai wuce nace mata inna ba yasa ta wannan shan ƙamshin.
Amsawa tayi a fizge tareda cewa..
"Amarya bakya laifi ko kina kashe É—an masu gida,ya kwanan amarci keda angonnaki,naji su farida sunce wai a wajen mairo kika kwana,ince dai ba wani abin cutarwa yayi miki ba koh"
Ta faɗa tana ƙara matsowa kusa dani tareda rage murya. Lallai wannan matar akwai gulma,ji yanda ta lanƙwashe murya kaman rantse duniya zakace tausayina take ji,kaman ba itace suke husuma da ƴar ta akan kuɗi ba..
Ƴar dariya nayi ta wayance wa kafin nace.
"Ahhah babu komai inna gaji,ba abinda yayimin,kawai dai zan zauna a wajen inna ne na É—an wani lokaci kafinna koma sashen mijinnawa,ni barina tafi idan babu wani abin"
Miƙewa nayi xan bar ƙofar muryar Atika ta tsayar dani.
"Lahh gaji kin manta wanke wanken can fah,cikina jiya ciwo yake ban kwanta da wuri ba,shiyasa na makara da safe banyi wanke wanken ba,ga kuma talle da zan fita,gaji ko zata taimakamin dashi dan Allah"
Kaman zatayi kuka take maganar harda sakin wani munafukin nishi,shuru nayi naji abinda gajin zatace.
"Ohh ehh hakane kam bazayyi wu harki gama wanke wanke ki fitamin da awarar nan ba. Sumaimah in bazakiyi komai ba ko zakiyi wanke wanke can kai,yi haƙuri nasaka amarya aiki"
Banyi mamaki ba,dan dama nasaka a raina hakan zata faru,saurin haÉ—iye takaici na nayi tareda ajiye murmushi akan fuskata na kallesu..
"Ahh ba komai ai bari nayi wanke wanken toh"
"Yawwa to bari zan kawo miki omon yin wanke wanken."
Inna wacce tafara tuka igiyarta sai gani tayi nafara jijjiƙa kayan wanke wanke,mamaki abin yabata tasaki baki..
"Ahh keda nace ki barshi akwai meyi"
"Ahah vakomai inna,wai atikan ce cikinta yana ciwo batayi bacci da wuri ba saita makara,gakuma zata fita talle"
"Atikance ta faÉ—a miki haka,zancen banza kenan,yarinyar da har nayi bacci na tashi fitsari na ganta ta shigo gidan,itace za'ace batada lafiyah,kawai dai suda sun iya rainawa mutane hankali kai.. Kin ajiye kwanukannan barinaje na samu gajin,wannan ai rashin daidai ne,daga kawo ki gida jiya har an baki aiki yau"
"Waye ke nema na gani nan nakawo mata soso da omo,harda za'ace wani ban kyautaba na bata wanke wanke,menene rashin kyautawar tawa a ciki iyee,dan kawai maiyin aikin batada lafiya nace tayi na rana É—aya shine abin magana,bata wanke wanken a gidansu ne? Naga kowa a garinnan yasani itakeyin aikin gidnasu kaff,ba wani gata ne da itaba ballantana a ce bata tab'a yi ba.
Ni nace me a gidannan,kullum sai nayi tuwo na ciyarda wata,ko a bani cefane ko ba'a baniba sai nayi tuwo,akwai wanda yake taimakata da ƙwandala a gidannan ne?
Da nace tayi na kwana É—aya,to yanzu na fasa,wanke wanke da shara kullum ita zata dungayi a gidannan,indai har wasu suna so na dungayin abinci dasu"
Tana gama faÉ—in hakan ta zefamin soda da soson wanke wanken.
Wayyyo Allah nah yanzu da soda zan dungayi,ni wanke wanken bai dameni ba kaman sodar,jikina kwata kwata baya sonta ko kaÉ—an,nan da nan hanni na sai É—aÉ—e ya tsatstsage..
Wani tarin abune yazo ya tarimin a maƙoshi,wato inna kula inaga ƙalubalena na gidan ba goje bane kenan gaji ce.
A hankali nake yi ina duba hannuna ko yayi wani abun har na gama tsaff,Alhamdulillah bai tsage ba amma yayi za sosai,to yau kenan nasan nan da wani É—an lokacin zai fatattakema.
Bayan nagama barandar inna Mairo na koma na zauna,ido na tsurawa yanda take tukawa nayi,abin abin sha'awa,inaso naga mutum yana sana'a.
Da farko taso bani haƙuri akan abinda yafaru,nice naƙi na ɗauko wani zancen,zamane da allah kaɗai yasan ƙarshensa,idan yazamo kullum sai ta bani haƙuri to abin bazai tafi daidai ba..
Hira muke jefi jefi,tana bani labarai na zamansu a garin da baban goje yayi aiki,wani nayi dariya wani na jijjiga kai.
Ƙarar buɗe ƙofar goje nayi,hakanne yasa na juya da sauri wajen,wash ashe yana nan,harga Allah ni manta ma dashi..
Nufo idan muke yayi kamar kullum da riga da wando a jikinsa ƙanana masu duhu,Allah ne kaɗai yasan yaushe suka ga ruwa..
"Innna ykk"
YafaÉ—a yana zama a bakin barandar.
"Kalau mana nake,kaman yanda ka sanni,ina ka shiga kwana biyu,sai kuma ka koro matarka jiya da daddare koh"
Runtse ido nayi ƙirjina yana lugude,inda inna tana ganin zuciyata da batayi wannann maganar ba,na samu bai kula dani ba a wajen,yanzu ta saka ya juyo da idonsa inda nake.
Wani kallo yayi min kaman yaga dutse kafin yace.
"Kwana biyu naje wani wuzilinne shiyasa kika jini shuru,batun wannan kuma dama fah tun farko na faÉ—amiki,zuwa tayi tai abinda yasaka tazo,ke na kawowa ita,in bakyaso ta tashi ta tafi ubanta yabani kuÉ—ina. Amma batun ta zauna a sashe na ban yadda da wannan ba sam."
"Hmmm kaidai kace haka,zata zauna a wajena na É—an wani lokaci,idan kun shirya saita koma É—akinta"
"ÆŠakinta kuma,akan idonki fah mukaxo nida yarana muka gina É—akinnan,yanzu rana tsaka lokaci guda kin bata shi?"
Ganin yafarajin haushin abinda inna ke cewa ne yasaka ni yimata alama da ido,kaman kuwa ta gani saida sanja zancen. Amma kuma tasake kwafsawa.
"Sabo dayi gawa da gatsine,saida ranar Allah tayi kafin ka fito,ita matar taka inka fita karyawa saika kawo mata nata,tunda kasan a ƙarƙashinka yanzu take koh"
"Wajen Iliyah zanje nasan ya ajiyemin,daga can zan wuce saina juyo kuma"
Huhhh na sauƙe ajiyar zuciya,ganin bai ɗaga zancen da innan tayi masa ba,da alama bayason duk wani zance daya shafeni ne inaga.hmmm niyafimin ai,gaba takaini gobarar titi a jos.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.