Trending Hausa Novels

Sanadin Caca Book 1 Complete Hausa Novels By Sadi Sakhna

Reading file: SANADIN CACA.txt

Chapter 26 of 40

Littafi na É—aya ne dana biyu kaman yanda na sabayi,na É—aya bati siddan,na biyu kuma Naira 300 ne dan haka zaka iya biya tun yanzu kafin a shiga kashi na biyu.

3131951977
Auwal Sadiya
First bank

Ko katin mtn ta nan
09035784150

VTU ta nan
2347068390570

Shaida kuma ta nan
09035784150

Ƴan niger ku tuntubi wanann number.
+227 97 21 16 15
----------------------------------------------------

Sadi-sakhan ceh
09035784150
Share please

*SANADIN CACA*

Mallakar SADI-SAKHNA

PROFICIENT WRITER ASSOCIATION

*USERNAMES*
FACEBOOK PAGE:Sadisakhna
WATTPAD:@SAKHNA03
AREWABOOKS:@sadeesakhna
PHONE NO:09035784150
________________________________
*Book 1*
Chp[20]

Zamana na gyara a tsakiyar gadon na saka wannan kayan daÉ—in a gabana,saida na cinye indomien tass kafin na buÉ—e peak É—in,itama gamawa nayi da itah na É—auko itama maltinar. Saidai ita ban sha dayawa ba na ajiye,dan batayimin daÉ—i sosai ba kaman wancan madarar.
Wata nurse ce ta shigo É—akin hannunta É—auke da littafi tana rubutu.
"Mrs goje ruwanki ya ƙare koh?"
TafaÉ—a tana kallon hannuna na hagun,oh ni na manta da ruwan dayake shiga jikinnawa ma.
Matsawa kusa dani tayi ta zare ruwan,iyah canular kawai tabari a jiki.
Murmushi tayimin da muka haÉ—a ido.
"Hhhh kin burgeni wlh,bakida lafiya amma kin cinye abincinki tass"
Kunya ce ta kamani,hakan yasa na sunkuyar dakai,hmm batasan rabona da abinci ya isheni bane shiyasa.
"Karki damu babu wata matsala,tunda kina cin abinci basai an sake saka wani ruwan ba,ga magunnan dazaki dunga sha da shafawa duk ya siyo ɗazu,saiki dunga kulawa sosai karki ƙara taba abinda jikinki bayaso"
ÆŠaga mata kai nayi alamar na fahimta.
Har tazo fita saita sake dawowa,
"Yawwa ya kawo kaya akan ki sanja,dan haka idan kin gama kizo office É—inmu daga kin fito ta gefennan kiyi wanka,yace yana zuwa yanzu"
"Ohh nama gama bari kawai mutafi"
Binta nayi a baya a hankali har muka isa office É—in nasu da tace,a matsayina nasan bankai har a kaini wajen ma'aikatan jinya nayi wanka ba,ya danganta ne da wanda ya kawonin shiyasa ka.
Bayan nafito daga wankan bandegi da sake sauya min na hannunsa,wanda na ga ashe sun cire fatar jikin hannun ne. Doguwar riga ta miƙomin maroon mai kyau da mayafinta,sai pad dakuma pant.
Karba nayi na koma banÉ—akin na shirya kafin na sake fitowa.
Kasancewar ban iyah surutu ba musamman da wanda bansani ba,shiyasa na zauna nayi shuru.
Muna nan zaune kaman kurame naji muryar gojen suna magana da wata nurse,lokacin ana ƙiran magriba a wasu masallatan.
Yana shigowa dani muka haɗa ido,nayi saurin sauƙar da kai,wai karfa in mukaje gida ya casa ni,dana tuno rashin kunyar danayi masa jiyah.
"Oh sainace ki fito tukunna zakizo mu tafi,ko baki ganni ba kai"
"Uhm naganka"
Binsa nayi kaman jela a baya ina ta kakkare jikina saboda mayafin bashida girma,dan ma dare ya É—an fara shiga.
Wani mashin naga mun nufah sabo irin bajaj É—innnan mai babban mazauni a baya.
Saida ya hau yafara diri kafin na hau bayan,dadumeshi nayi ƙanƙam,saboda ban taba hawa mashinba.
Nasan yajini dan har Æ´ar tsuka yayi amma baice komai ba.
A hankali yake tafiyah wanda nasan saboda nine har muka iso gida.
Sauƙa nayi daga kan mashinɗin ina rarraba ido.
"Nagode"
NafaÉ—a a hankali,bai kalli inda nake ba ballantana ya amsa,duk da nasan yajini sarai.
Kafe mashin É—in yayi ya nufi cikin gidan,nima binsa nayi a baya,mamaki yabani ganin ba hanyar É—akinsa yayi ba.
ÆŠakin ya shiga ya tattaro kayansa wanda ya juyemin su a jikina,harda zannuwan gadon wanda ya nabata da jini da kuma ruwan daya zuba duk ya tattaro ya fito dasu waje.
ÆŠakinsa ya sake nufah sai gashi da bargonsa da zanin gadonsa nan ma.
Dukka zubasu yayi a gabana,nidai ina nan tsaye ina kallonsa,jikina har yafara karkarwa,kaddai yana nufin a darennan zan wanke duk uban kayannan kai?.
Wuceni yayi ya shiga ƙofar gaji,can sai gashi ya fito Atika tana binsa a baya, itada kursiyyah.Taci kwalliya da alama fita zatayi a daren.
A tsayawa suka yi a gefe dani suna kallonsa.
"Ku É—auki wannan kayan ku wanke su a darennan,idan har suka kai gobe baku gama ba wlh kunji na rantse sai na É—aureku na tsawon satin bakuga rana ba.
Sannan idan kungama ku cikamin randa ta da ruwa"
Sakin baki mukayi haddasu muna kallonsa,hanyar ƙofar sa ya nufah hankalinsa kwance.
Bayan ya tafi juyowa atika tayi tana kallona.
"Wannan aikinkine ko,kema nan tantiriya ko,wato bari ki juyashi shikuma ya juyamu,toh baki isa ba,dan kuwa ke zaki sha wahala ma idan hakan za'ayi,ina zai tafi ya barki a gidan"
"Menene me naji ana cewa ne? Kekam ba fita zaki bane mai kike anan,ko ta dawone dama ba mutuwa tayi ba da mukaga ya fita da itah"
Kallon gaji nake tasaka wani figalallen hijabi,da wani zaninta mai kama da three quarter na wando,wai a hakan sallahr magriba da dungura,wato da suka ga yafita dani É—azu so sukayi ace na mutu.....hmmm mai nayiwa waÉ—annan mutanen suka tsaneni ne?
Ganin gaji tafito yasa Atika rushewa da kuka tana bubbuga ƙafa,kaman ba itace take magana yanxu ba cikin tsiwa..
"Gaji kiji wani sabon salon iskanci,ɗazu da kikaga yafita dai itah,ashe suman ƙarya tayi,suka fita taje ta kitsa masa munafurci,yana shigowa ya jibgo wannan uban wankin wai mu yi shi a darenann,nida ko nawa ma bannayi shine zaice wai muyi mata wankinta da nasa??? Nikan wlh gaji bazan iyaba,Allah gaji ki ɗau mataki"
Atika ta faÉ—a tana rushewa da kukan munafurci.
"Ke Æ´ar nan mai kikecewa,ayi mata wanki,akan uban me za'a maida Æ´aÆ´ana bayinki,Æ´ar gwamna ce ke ko Æ´ar sarki,toh wlh baxai yiyuba komai za'ayi saidai ayi,kuma kwanon abincin ki a gidannan babu shi,idan yunwa zata kasheki ma saidai ta kasheki"
Nidai ina nan tsaye in jinsu,ganin jiri yana É—ibana yasa na juya zan shiga É—aki.
Gaji ce ta jawoni baya ina shirin faɗuwa,da ƙyar na tsaya akan ƙafafuna. Hannu ta ɗaga zata shararamin mari,da sauri na rife ido ina jiran naji da wanne waje zai saƙƙo.
Naji ƙarar marin amma kuma banjishi a kuma tu na ba.
"Kambuuu nika mara goje ina matar kawunka zaka mareni,saboda kai......"
Wani marin yasake kifa mata ta É—aya kuncin daidai buÉ—e idona,kutt dama goje gaji yamara,kai matar kawunnasa?..na faÉ—a a raina ina zare ido.
"Kona daɗa miki ne,kukuma saboda kun rainani nasakaku aiki maimakon kuyi shine kuka tsaya kuna zage zage koh,ku faɗamin Nida na sakaku kuke zagi kokuma itah. Duk ina sane da abinda kuka aikata bananan,har kayana kuka ɗauka kuka saka a wajen kashin shanu ko?....daga kyau aikin gidannan kaff nasake ganin wanda yasakata tayimasa,saina cire masa ƙafafu da hannaye,in yaso ayi masa aikin da dalili"
Ƙwafah yayi mai ƙarfi yafita waje yana huci.
Oh ni inaganin ta kaina a gidannan,ko ina ba sauƙi.
ÆŠaki na wuce na barsu a wajen,duk yadda zasuyi ma suyi.
Can wajen goman dare har nayi bacci naji ana buga ƙofar tawa.
Buɗewa nayi muka haɗa ido dashi,ledar dayake hannunsa ya miƙomin,hannu nasaka na karba ya bar wajen..
Bayan na koma ɗakin zama nayi na buɗe ledar,soyayyar doya ce da ƙwai sai balangu,ikon Allah mai ya shiga kan gojene yake siyomin waɗannan abubuwan.
Bandai sake kawo tambaya tabiyu ba nafara kaiwa cikina.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.