Complete Hausa Novels

A Wani Masarauta Complete Hausa Novel

Reading file: A_Wani_Masarauta_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 15 of 25

Page1⃣5⃣

A Hankali ta Rintse ido Tareda duqar dakai Wasu Zafafan Hawaye Suka Gangaro Mata. A Haka Suka Qarasa Inda Amarya Zata Zauna. Saida Ta Zauna Sannan aka Fara Chashewa, Ganin Kawayenta da Yanuwa Yasa Tadan Saki Jiki tana Murmushi...

Haka Akaita Bukukuwa Har zuwa Ranar Daurin Aure. Parveen Ranar Daurin Aure Yini Tayi Kuka, Dakyar umma Ta Lallabata Ta Shirya Cikin Wani Hadadden Lace Light blue. Anmai Dinkin buba, Kayan sun Mata Kyau Sosai. Kana Kallan Idonta Kasan Tayi kuka, Hajiya Shuwa Ce Tai Mata Makeup ta Fito Princess Parveen dinta Sosai..

Karfe Daya da Rabi na Ranar Sati Aka Daura Auren Fardeen Kabeer da amaryarshi Parveen khaleed a Kofar Fadar Sarki Khaleed a Bisa Sadaki Dubu Dari. Daurin Auren daya Tara Manyan mutane Tun daga Kan Shugaban Qasa Har Zuwa Gwamnoni, ministers, Senators, Sarakuna. Babba da Yaro manya da Qanana. Ni Kaina Ummy Abduol Saida na kashe qwarqwatan ido na Baje kolin Hajata na Litttafai Inata Ciniki..lol chan na hango Umma Yahaya musa Da Ummiekhaleel Sunata Dambe akan takeaway..lol

Cikin gida ma Y cika maqil, Matan Manya neh anata Hidima Cikeda Farinciki, misalin Karfe Hudu Aka Tafi da Amarya Gidanta. Parveen Tayi kuka Kamar ranta Zai fita, Dakyar Ta Yarda Ta Shiga mota bayan Mai martaba ya Gama Mata Nasiha. Koda Suka Shigo garin Gombe, Gidan mai martaba taga sun nufa. A Tunaninta Za'a Kaita neh Fulani Tai Mata Nasiha, Saida Aka kaita Side din Fulani Tai Mata Nasiha Sannan Aka wuce da Ita Bangarenta. Bata Qara Tsinkewa bah Saida Akace Mata Nan neh Gidanta...

Deeza dake kusada Ita Ta Kalla Idonta cikeda Kwalla, Deeza Wanene Mijina?? Shiru Tai Nayan Seconds Sannan Tace
"Nima Bansani bah Parveen"
Qara Kallanta Parveen Tai Cikeda Mamaki
"Nanfa Gidansu Yarima Fardeen neh, Meh Nakeyi a Nan??"
Shiru ne Ya biyo baya. Ganin Deeza batada Niyan Magana Yasa Parveen ta Sulale ta Kwanta Kan Gado Tareda Lumshe Ido. Shin wa Zata Tambaya??

Yarima Fardeen koh Babban riga Yasa Fari Kar, Kayan Sun Amsheshi Sosai. A Wajan Daurin Aure sai Washe Baki Yake Yana Gaisawa da Mutane Kamar da Gaske. Shiko Bilal Har Ranar Mamaki Yake Wai dagaske Yarima Neh kuwa Yau Ya Yarda Zeyi aure?? Ana Gama Daurin Aure ko Walima Yarima bai Tsaya bah Ya juyo zuwa Gida. Yana Tsa Gida Ya Chanza Zuwa Black Trouser da White T Shirt ya Fito. Matan dake Haraban Gidan Sai mai Tsiya Suke, Murmusawa Kawai Yake Yahau motarshi yabar Gidan, wani hadadden Gida Ya nufa Wanda tun dawowanshi Ya Siya. Horn Yayi mai Gadi Ya bude Ya Shiga Yayi Parking ya fito. Cikin gidan ya Nufa Kai Tsaye, A Hankali ya bude kofan falon. Wata Kyakyawar Budurwa ce Daga Gani bah musulma bace Ta Taso ta rungumeshi Tana Mai murmushi, Shima Murmushin yake Mata Ya Dagata chak Sai Bedroom din dake Falon..

Fardeen bai dawo gidan bah sai washe Gari da Safe, Fulan ta tareshi rai bace.
"Daga ina kake Yarima??"
Sosa Keya yayi
"Wallahi Na...Umm Naje wajan mahdi neh jiya da Daddare Sai Barci ya kwasheni a Chan"
Kallanshi kawai Fulani tai tareda Girgiza kai
"Shiknan jeka. Ka Shirya Anjima Akwai Dinner"
Dan Tsuke Fuska Yayi baice Komai bah Yabar wajan
Mamaki neh Sosai a fuskan Fulani. Binshi tai da Kallo tai Har yabar Wajan Sannan Ta Wuce...

Amarya Nachan Side dinta ita da Qawayenta da Yan Uwanta. Fulani ce Tareda Kuyanginta Sukai Sallama, Duka mutanen Falon Suka Amsa, Gaidata Sukai Ta amsa Fuska A sake Sannan ta Nufi inda Amaryan Take.
Kwance ta Sameta, Qawayenta Sun Zagayeta, Tanajin Muryan Fulani ta mike ta zauna. Saida Suka Gaida Fulani Sannan Suka bar dakin. Fulani Ta Matso kusada Ita Tana Murmushi
"Amarya Kinsha Kamshi"
Turo Baki Parveen Tai
"Nifa Fulani Har Yanzu ban Gane bah"
"Menene Baki ganebah??"
Tsintan Kanta tai da Kasa fadama Fulani Rashin Sanin waye Mijinta
Fulani ta kalleta
"Ina jinki"
Shiru Parveen tai ta Dukar dakai tana wasa da zoben zinarin dake Hannunta..

Cikin Tsa Fulani Ta soma kiran Kuyanganta
"Ladi! Ladi!!"
Ta amsa ta shigo dasauri dauke da Wani Hadadden Trolly. Ajiyewa tai ta Fita
Fulani Ta kalli Parveen
"Anjima Akwai Dinner, Wannan Kayan nakeso kisa Kinji my Daugther??"
Kai Parveen ta Gyada Sannan Tace
"Nagode Fulani"
Shafa Kanta Tayi tana Murmushi
"You dont hav To"
Itama Murmushin Tai. Fulani ta mike ta mata Sallama Tabar Dakin...

Karfe Bakwai da Rabi dai dai Aka Gama Shirya Parveen Cikin Hadadden Gown. Kwalliya Aka Mata Ta Fito tai Kyau Sosai, Deeza Dake gefenta Sai Kodata Take. Parveen Koh Sai Bata Fuska Take Kamar zatai Kuka...

A Bangaren ango shima Shigan Hadadden Shadda Yellow Yayi, Sai Farin Hula Da Takalmi. Abinka da Farin Mutum, sai Yellow Shaddan Ya Haskashi Sosai. Mahdi dake Gefenshi ya kwashe da Dariya.
"Menene na Dariya"
Qara Tuntsirewa da Dariya Mahdi Yayi
"Allah mutumina Kaji Tsoron Allah, Duk wanda Ya ganka Zai dauka Auren Soyaiya Kayi. Nanko Bah Haka Baneh"
Baice Komai Bah Saima Qara Hade Rai da yayi
"Nifah Wallahi Badan Fulani ta Matsa Bah dah Yanzu inachan Eneh na Jirana"
Zaro ido Mahdi Yayi har ya bude baki zaiyi magana Bilal ya Shigo.
"Ango Kaifa Ake jira Ka Fito"
Tsaki Yarima Yayi ya kwashi wayoyinshi ya fita, bilal da Mhdi Suka bishi a Baya...

Yana Fita Yaga Mota a Qofar Side dinshi, Baiyi wata Wataba Ya Shiga drivern Yaja Sukabar Wajan. Ganin Sun nufi Cikin Gidan Ya Kalli Drivern
"Ina Zamu kuma??"
Sarauniya Fulani ce Tace idan na daukeka Naje Na Dauki Amarya, Tace a Mota daya zamu.
Dogon tsaki yarima Yaja Ya Juyar dakanshi yana kallan Window...

Ummy Abduol✍🏻
πŸ€πŸ€πŸ€πŸ‘‘
*A WANI MASARAUTA*
🏀🏀🏀 πŸ‘‘

By *Ummy Abduol*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.