A Gidanmu Take Complete Hausa Novel
Reading file: A_Gidanmu_Take_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 5 of 28
Page 9&10
Washe gari bayan sun gama breakfast ne,
Habeeb yake cewa Ahmad
"To kaga ni yau zan tafi kuma bazan dawo nan dawuri ba"
Saboda wannan zuwanma dakyar mommy tabarni.
Acewarta bataso nayi nesa da ita
Dan Allah Ahmad kada kasa tinani a ranka
Sannan kuma karka gaji da Zuwa gidanku neman tuba a wajen
Mommynka
"Aa Habeeb bazan iya zuwa inda mom take ba gsky"
Sabida mom idan taganni bacin ranta karuwa yake
Har Tana barazanar Zata tsinemin idan harna sake zuwa inda take
Ba tareda Fateemah ba
Kai innalillahi wa'inna ilaihiraji'un abun haryana kai da hakane Ahmad
Wlh Habeeb shiyasa kaga damuwan sunyi min yawa narasa yanda zanyi
Yanzu ma tafiyar da zakayi banso ba
Koba komai kana debemin kewa.
Amma yana iya, idan kaje ka gaida mommy
Da kannan ka duka
Nagode Allah yabar zumunci
Habeeb yace Ameen
Ahmad yace "Kashirya nakaika airport karkayi missing flight"
Ok
Bintu kinga yau broh ze dawo
"Kizo mushiga kitchen dakanmu muhada mishi delicious"
Bintu tace "Ok sis karki sami damuwa muje"
Suka tashi suka shiga kitchen suna ta hira
Mommy Tana kallonsu Tana Mejin farin ciki a zuciyarta
tace "Allah yasake hada kanku my twins"
*AHMAD*
Tafiya suke a mota suna hira shida Habeeb.
Nan Habeeb yake kara jaddada masa akan yakula da kanshi yadaina yawan tinani.
Ahmad yace "kaga karka dameni tin jiya kana ta maimaitamin kalma daya kamar karatu"
Ohh "dama nasan bazaka taba canza haliba Ahmad"
Eh naji bazan canza ba
Dahaka har suka isa airport
*BINTU*
Bintu kuwa anata aiki a kitchen bebba se surutu take zubawa.
Banda eh, aa, to,
Ba abinda Bintu take cewa har suka gama hada frid rice da kaji
Bintu tahada sobo me cucumber
Mommy tace "yanzu natura driver yaje dauko shi a airport
Wai ya karaso"
Yeeeee mommy "Aida kin fadamin da tare zamu tafi dashi"
Kai Beebah kin fiye gaggawa
Haba mommy "yabazanyi gaggawa ba yaufa kusan 2weeks ban ganshi ba sede waya"
Bintu kuma murmushi kawai tayi
Horn sukaji abakin gate
Nan Beebah tafita da gudu Tana oyoyo yaya oyoyo
Kafin driver yagama parking harta fara
Bubbuga motan
Seda yafito da sauri yana oyoyo my sis
Nan ta rungumeshi kamkam Tana murna
Yace ina dayarki? Tana falo itada mommy
Ok mushiga daga ciki
Suna tafiya Tana rike da waist nashi har suka shiga falon.
Tana cewa "yaya kadauko tsaraban toh"
Mushiga de tukun kinsan tsarabarki ta daban ce.
Mommy tace "oyoyo my son sannu da zuwa nan itama ta rungumeshi tana murna"
Bintu ta tsaya Tana tayi mishi murmushi
Yace "kekam meyasa bazaki Waye ba Bintu"
kullum kina cikin rashin sabo da mutum.
Cheww Allah yakyauta halinnan naki.
Kina gani fa 'yar uwarki tazo tayi min oyoyo
Amma ke kina tsaye
Daga nanne Bintu taje ta rungumeshi
Yahada su duka uku ya rungume sunata murna
"Ahmad yana komawa gida ya kwanta agado yana tinanin mommynshi
da kanwarshi"
Wai yau shine Kanwarshi wanda yafi so aduniya take gudunshi?
"Yau shine mommynshi take ikirarin tsine mishi"
"Idan yatuna rayuwarshi na da se yayi kuka"
*WANENE AHMAD*?
AHMAD KABEER yarone awajen alhaji kabeer.
Alh kabeer shahararren dan kasuwane
"Wanda yayi suna a duniya"
Alhaji kabeer de dan asalin garin adamawa ne
Shi asalin fulani ne
Wanda yafara harkar kasuwanci tin yana saurayi
Allah kuma ya buda "mishi sabida yanda yake da kyauta da taimakon talakawa"
Alh kabeer yabude gidan marayu tin yana saurayi,
sabida yadda Allah yasa mishi tausayin marayu a zuciyarshi.
Dan hakane har yaki yin aure
" dan yana gudun kar ya auri matar dazata hanashi taimakon marayu"
Iyayenshi ne suka nema mishi aure Agidan marayu Wanda shiya bude da kanshi
Acewarsu zatafi jin tausayin marayu 'yan uwanta
"Inda suka nema mishi wata kyakkyawar yarinya me Suna mariya"
"Ba matsala a auren mariya da alhaji kabeer sabida mariya Yarinyar kirkice"
Bayan shekara hudu Allah be kawo musu haihuwa ba
Har abun yafara damin mariya
Inda alhaji kabeer yake cemata
"karki damu mariya haihuwa na Allah ne"
"Idan ma Allah be bamu b! Baga gidan marayu ba, semu dau daya murike kaman mu muka haifa
Mariya tace "haba Alhaji kasan fa akwai banbanci tsakanin É—a da kuma É—an riko"
Aa mariya É—a na kowa Ne!
Ganin yahau matsifane mariya tayi shiru
"To dahakane har Allah yakawo ranar haihuwanta inda aka sha shagali akayi murna"
Akasawa yaro sunan baban alhaji kabeer wato AHMAD.
Ahmad de yasamu gata dan kota ina anaji dashi
"Ahmad kyakkyawa ne"
Fari Ne shi, dogo, da dogon hanci, ga karamin baki, Atakaicede shi yayi kama da larabawa.
Sede kuma matsalar shi nada yawa
Yanada girman kai sosai
Ga kallon banza
"Ga zama da abokan banza"
Wasu abubuwan dayake yi abokai ne suke zigashi
"Sai yayi ta tsula rashin kunya son ranshi"
Dafarko yasamu daurin gindi awajen iyayenshi
Se daga baya abun yafara damunsu
*bayan wasu shekaru*
"Dahakane har allah yasake basu haihuwa"
"Yarinya taci sunan wacce take kula da gidan marayu na mahaifinsu wato FAREEDAH"
Fareeda de kykkyawa ce tana Kama da Ahmad sosai.
"Sannan kuma tinda aka haifi fareeda Ahmad yakara bude sabon rashin kunya"
Shi adole yana da kanwa
Bayan haihuwar fareeda fareeda ne Alhaji kabeer yafara diban yaranshi suna zuwa gidan marayu kai tallafi.
Acewarshi idan sun girma suma zasu taimaki marayu.
"Ranar farko dasukaje gidan marayun"
Ahmad yasa fararen kaya masu kyau yanata Hada rai danshi beso zuwa ba.
"Bayan an tara yara ana raba musu kudi ne"
Alhaji kabeer yahango wata kyakkyawar yarinya.
"Tana zaune a gefe tana kallonsu tana murmushi"
Alhaji Kabeer yaÉ—an tsaya da rabiyar yana kallonta.
Se ya yafito ta da hannu yace zo!
Yarinyan ta tashi a hankali tana tafiya
Harta iso su, seta durkusa tace gani.
"Alhaji Kabeer yayi mamakin wannan yarinya batafi shekara goma ba"
Amma take da natsuwa haka gata dakyau.
Shi kuma Ahmad se harara yake tayi wai ana bata mishi lokaci
Alhaji yace "ya sunanki?"
Ahankali tace "sunana Fateemah"
âœÂï¸Â🗒︠*JIDDAH S MAPI*
[6/23, 12:45 PM] Ummi Tandama: 🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
*A GIDANMU TAKE!!!*
🌸🌸🌸🌸🌸🌸🌸
Story/written by
Jiddah S mapi
_dedicated to walidation S mapi_
Wattpad
Jiddahpretty
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.