Ni Da Aminiyata Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Ni Da Aminiyata Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 15 of 40
💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 23~October ~2016
🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷
NA BILKISA IBRAHIM💞
🔶🔸2⃣3⃣🔸🔶
..........kwance take bayan ta gama shanruwa, tayi zugum dan kuwa tana duniyar tunanin abinda yafaru d'azu, tsakaninta da uncle G!, ta tuna yanda yake magana cikin gadara da bada umarni.
"Toni na shirya yin aure safiyya, domin matata tarigaya ta iso, bawasa nazo dashiba, domin inada buk'atar yin aure yanzu,"
Tayi murmushi, tareda sake tuno wata maganar tasa.
"Dan inason muyi aure ba soyayyaba, idan kinje gidana zan nuna miki dukkanin soyayyata".
Taja numfashi tareda gyara kwanciya, wato shi baya lallashi, kai tsaye yake magana babu wani kwala kwala, to amma shi baisan ba'a umarni a soyayyaba ne?.
Ta tuna inda yake fad'in, daga yau karna sake ganinki da zaliha dan batada tarbiyya, nasan bakya kula samarin makarantar nan, to karki fara domin inada kishi mai tsanani, zan iya komai yayinda naga abinda zai tada min kishina".
Ta murmusa, su uncle G! Masu kishi, to ina ruwana da kishinka, ni nan dakake gani maza duk d'aya na d'aukeku, a kan mizani d'aya nasakaku, taja ajiyar zuciya domin jin an kwala kiran sallar isha'i, tamik'e domin gabatar da sallah.
Saida ta kammala komai na al'adar rayuwarta, sannan tazauna domin duba book d'in da uncle G! Yabata, ga gajiyar azumi, tazauna tana fad'in wash ALLAH!! aii duk gajiyar danayi bazata hanani karanta book d'innan ba, tai saurin kallon wayarta datake wringing sabuwar nomber ce, dan haka ta share, saida aka k'ara kira sannan tad'auka tana mita, tai shiru batareda ta amsa ba, daga camma ank'iyin magana.
Ta daure ta ce, "kowaye idan bazaiyyi maganaba tofa zan kashe".
jitai wata sassanyar murya ta ce, "assalamu aliki?.
Sopy taja ajiyar zuciya domin tagane mai maganar, ta amsa da wa'alaikassalam, ta d'ora da fad'in good evening sir.
Yay murmushi mai sauti, ya ce, " evening, kinsha ruwa lafiya?
"Lafi law, sopy tafad'a"
Ya ce, "masha ALLAH", Amma a canja min wannan sir!! D'in.
Tai d'an murmushi, to aii kai malaminane, in bance maka sir!! Ba mixan ce maka?
Ya ce, "hummm, ga sunaye nan masu yawa, darling, honey, dear, my love, prince, gasunan dai dayawa.
Hannu tasa ta rufe fuska tamkar yana gabanta.
Jin tayi shiru yasashi fad'in ya dai?
Nanma shiru tayi.
Ya ce, "okey, sarkin kunya, amma yakamata arage kunyarnan ko? Dan zata d'an cutar dani, in tambayeki mana??
Ta ce, "to, tambayeni?
Okey ince dai kinyi mana addu'a?? yayinda zaki sha ruwa, dan kinsan ana karb'ar addu'a a irin wannan lokacin.
Sopy ta gyara zama, ta ce, "e, nayi.
To, mikika rok'ar mana?.
"Komaima, na rok'a" sopy tafad'a, asanyaye.
Ya ce, "nice, "to d'an fad'amin mana naji.
Cikin shagwab'a ta ce, "ni dai basaina fad'aba.
Uncle G! Yay dariya, ya ce, "nice, my sopy karki damu wataran zaki fad'a, bari nabarki kiyi barci, goodnight.
Kafin ta ce, "wani abu ya sumbaci wayar, ya kashe, sopy ta rintse idanu tabud'e, ya salam ta fad'a tana kwanciya, dama maza basuda kunya, duk jan ajinsu dawani jijida kai, idan akazo fagen soyayya saisu canaja, duba dai kiga uncle G!, ni wlhy mamakima yake bani, ta lumshe ido tana murmushi, wanda itama batasan dalilin saba.
Ta dafe k'irjinta tana fad'in oh ni safiyya, waiy mike shirin faruwa dannine?? Miyasa nike shiga farinciki aduk lokacin da uncle G! Ya kasance danine?? Idan ban ganshiba nakanyi kewarsa? Shin miye dalilin hakan??.
Zuciyarta ta ce, "kin kamu da sonsa ne.
Ta girgiza kai tana fad'in ban yardaba, alokacin dana keson Abdul bahaka nakejiba aii, akwai dai dalili, to amma miye dalilin??
Uncle G! Yana burgenine kawai, amma bawai ina sonsa bane, zan iya cewama har yanzu ban amince da batunsa na d'azuba, domin kuwa Abdul yasa nayima dukkan maza kud'in goro a fannin yaudara, bana tunani zan sake shiga tarkon son wani namiji ahalin yanzu, nariga na shafe babin soyayyar wani namiji arayuwata, nasan ban isa nace, "bazanyi aureba, tunda nima saida akayi aure aka haifeni, amma koda nayi aure mijin dana aura bazai samu wata soyayya agareniba, sai dai kuma bazan iya nuna hakan ga uncle G! ba, saboda yanada girma a idona, malaminane abokin uncle d'inane, sannan koba komai ya girmeni, ta jawo book d'in domin karantawa.
Kubiyoni masu karatu, dominjin tarihin, youseef hussain Ahmad, wato uncle G!!!....................âœðŸ»
💞Bily💞
💞💞Mrs Abdus'salam💞💞💞
💞I LOVE YOU MY FAN's💞💞
[12/19, 7:25 PM] mrs bilkisu: 24~October~2016
🔷🔹NI DA AMINIYATA!!!🔹🔷
NA BILKISA IBRAHIM 💞
🔶🔸2⃣4⃣🔸🔶
.............TARIHIN UNCLE G!!!.
uncle G!, kona ce youseef hussain Ahmad, d'an asalin garin gurum ne, a k'aramar hukumar tsanyawa.
Malam hussain shine mahaifinsa, suna kiransa da baba, sahura itace mahaifiyarsa suna kiranta da gwaggo, su hud'u iyayensu suka haifa, hafsat itace babba tana aure anan cikin gurum harda yaranta, yusif shine nabiyu uncle G! Kenan, sai Libabatu itama tayi aure tanada yara, sai auta Aysha tana karatu yanzu tana (jss, a secondary ).
Gidan su uncle G! Talakawane sosai, saidai mahaifinsu yana son karatun boko sosai, wannan yasa ya tsayama 'ya'yansa sukai karatu, duk da matan daga secondary ake musu aure, amma sun tsayama uncle G! Yayi karatu mai zurfi, dukda kwakwalwarsa ta taimaka masa wajen kaiwa ga matakin dayake a yanzu, bak'aramar gwagwar maya akashaba wajen karatun uncle G!, amma idan ALLAH ya ce, "kaine tofa kaine".
Bayan ya kammala deploma d'insa ya samu aiki a primary school d'in Gurum, wannan ma ya taimaka masa wajen cigaban karatunsa, dan yana koyarwa ya rubuta takardar izinin komawa k'aro ilimi, da taimakon wani bawan ALLAH yasamu shiga (Ado bayaro university kano) anan ne ALLAH Yahad'ashi da uncle kabeer, duk talaucin gidansu sopy! Sunfi su uncle G! Arzik'i, dan haka uncle kabeer yataka rawa mai yawa arayuwar uncle G!, tab'angaren kud'i da wasu abubuwan, sun shaku da juna sosai shida uncle kabeer.
Uncle G! Bashida aure, dukda iyayensa suna damuwa da zamansa haka, akullum yana fad'a musu aure lokacine idan lokacin yayi zaiyi aure, yaso auren wata yarinya anan cikin garin gurum, amma sai ALLAH ya d'auke kayansa tarasu tunda ga nan bai sake yink'urin aureba sai yanzu dayaga sopy.
Uncle G! Yazama wani tauraro mai haskawa agarinsu, dan mutumne mai girmama manya, dakuma son cigaban matasa, har k'ungiyar taimakon matasa gareshi a k'auyensu, dukda bawani kud'ine dashiba saidai rufin asirin ALLAH,
Wannan shine tarihin uncle G!, atak'aice, nan gaba zaku rink'a jin sauran bayani akansa.
Sopy taja ajiyar zuciya, fuskarta d'auke da murmushi, lallai uncle G!, Ansha gwagwar mayar rayuwa, gsky yabata tausayi, dama ance babu maraya sai rago.
Tarungume littafin tashiga barci.
Dak'ar ta iya tashi da asuba tayi sallah, shed'an yaribace ta ta hau barci, wannan yasata makara gashi tanada lecture d'in safe, agurguje ta shirya tanufi aji.
Duk da haka saida ta makaro domin kuwa uncle G! Yarigata shiga, taja tunga ak'ofar class d'in, inda sauran d'alibai makararru suke irinta.
Tsaye yake yana gabatar da lecture, jikinsa sanye da blue d'in shadda d'inkin boda, bawata mai tsada bace, amma yayi k'yau, domin dama mai k'yawunne, babu abinda kakeji sai k'amshin turarensa, jiyay hancinsa yana shak'o masa kamshinta, yad'an juyo inda yake zatonta, kallon ido cikin ido sukayima juna, dukda idanunsa suna cikin gilas wannan bai hanata jin wani yarrrrrr! Ba, tai saurin kauda kai daga kallonsa, ya gyara tsayuwarsa yana wani d'an murmushin mugunta, yacigaba da gabatar da darasi.
Su sopy suna tsaye tareda suran maka rarrun d'alibai, har yagama lecture yafito, kallo d'aya sopy tai masa ta kauda kai, shikuma yawuce yana murmushin mugunta, wanda yabama sauran d'aliban mamaki, wasu kuma yabasu haushi dan aganinsu ya raina musu hankali, tunda akwai sa'aninsa agurin.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.