Ni Da Aminiyata Part 1 Complete Hausa Novel
Reading file: Ni Da Aminiyata Part 1 Complete Hausa Novel.txt
Chapter 7 of 40
Abdul yazagayo tabayan sopy yace" mai b'uya aii gani naganki.
Sopy tayi saurin juyowa danjin maganar habibinta,, tai murmushi to waya gayamaka ina nan?? Yay d'an murmushi aii basai anfad'a minba zuciyata ma zata iya ganoki,, barema ina kallonku keda fareeda kuna kullawa.
" sopy tai dariya sosai tace" to naji ina ka kaimin k'awata ne?? Yace" taje sayo muku gyad'a ne, yanzu zata dawo,, tace" okey tokai mike tafe dakaine?? Ya murmusa nazone kawai naganki gimbiyata,, ya d'akko kud'i har dubu goma ya mik'a mata ga wannan kiyi hidimar biki dasuko, saidai kiyi hak'uri babu yawa gashi kuma sunzo miki ak'ure.
Sopy tace" to ngd saidai karage domin kud'in sun yimin yawa, dan mun gama komai,,, Abdul ya girgiza kai kinsan bana son musu kuma babu k'yau maida hannun k'yauta baya.
Bayanda zatayi dole ta karb'a tai masa godiya.
Ya harareta batare data ganiba azuciyarsa yace" ' yar son banza.
""kud'inda Abdul yabama sopy fareedace tabashi yabata tunda tasan kud'in zasu dawo hannunta ne.
Fareeda tak'araso sukad'an sake tattaunawa sannan Abdul yatafi,, bayan tfyr Abdul suma suka nufi gidan aunty zainab sopy tamik'awa fareeda kud'in my sis ga wannan habibine yabani ki ajiyesu awajenki ko wani abu zai taso mana.
Fareeda tace" ALLAH yasaka masa da alkairi.
RANA BATA K'ARYA SAIDAI UWAR D'IYA TAJI KUNYA:- yaune aka d'aura auren fareeda d'ahiru da Abdullahi Abubakar mai fata,, d'aurin auren dayabawa mutane mamaki, domin mutane dayawa sun san Abdul da k'awar fareeda yake soyayya,, amma gashi yanzu ya auri fareeda, dan danan surutu yafara yawa acikin anguwa.
Su sopy suna makwafta gidan wata saddik'a anan suke zaune,, sopy tagama shirinta cikin ankon dasukayi itada fareeda kawai,, saidai ta manta sark'arta agidansu dan haka tamik'e tana cema fareeda bari ta d'akko, sopy ta fito tana gaisawa da mutane,, amma sai mamki yakamata dataga anata nunata ana kus kus, bata kawo komai arantaba tayi wucewarta.
Da daddare aka kai fareeda d'akin mijinta dake cikin gidan su Abdul,, dukda darene lamarin yayi matuk'ar bama sopy mamaki,, saikuma gabanta yashiga yawan fad'uwa da sauti da sauri,, bayan raguwar mutane 'yan kai amrya fareeda tacema sopy dan ALLAH ta samomata ruwa tasha,, sopy tace to amrsu ta ango mai dad'in suna aii dole naje neman ruwansha,, bayan fitar sopy fareeda ta d'auki wayarta takira Abdul,, dan dama shitakeson kita shiyyasa ta aiki sopy.
Sopy tana tsaye a k'ofar gidansu Abdul tanata kalle kalle zuciyarta cike da fargaba,, can saitaji muryar adam yana fad'in Abdul kana ganin hakan dakayi shine dai dai tun d'azu nakeson muyi magana kanata min hanya hanya,, yanzu kai kana ganin idan sopy tagano kaine ka auri fareeda mi kake ganin zai farune???
Abdu yay magana cikin tsawa kaga adam kafita hanyata wlhy to miye idan sopyn tagane nine na auri fareeda,, ita uwatace kokuwa zata tsirenine???
Bazata tsirekaba amma tabbas sai ALLAH ya saka mata kuma karubuta ka ajiye ranar nanan zuwa gareku daga kai har fareedar daka aura.
Tun sopy najin abinda suke fad'a harta dainaji,, garin yafara juya mata kafin kace me ta yanke jiki ta fad'e awajan,, dan dana hankalin mutane yadawo gurinta,, Aka fara fad'in "inna lillahi wa inna ilaihirraji un." Wanine yay k'arfin halin fad'in ad'auketa mana atafi asibiti dan asume take...................âœðŸ»
💕Bily💕
💕💕Mrs Abdus'salam💕💕💕
💕I LOVE YOU MY FAN's💕💕
💕
[12/19, 7:24 PM] mrs bilkisu: 12~October ~2016
🔷🔹NI DA AMINIYATA🔹🔷
NA BILKISA IBRAHIM💕
Assalamu alaikum masu karatu,, ina mai baku hak'urin canja sunnan wannan book,, domin bansan an rubuta book d'in NI DA K'AWATA ba sai yanzu,,dan haka yanzu zai koma NI DA AMINIYATA,,, sannan ina k'ara bawa marubuciyar NI DA K'AWATA hak'uri. Ngd acigaba da gashi.
🔶🔸1⃣2⃣🔸🔶
..............Asibiti mafi kusa aka nufa da sopy,, sannan labari yakai gidansu sopy,,, ALLAH ma yasa uncle kabeer yana nan,, shima yazo d'aurin auren fareeda,, babu b'ata lokaci suma suka nufi asibitin da aka kai sopy,, wadda likitoci suka rufu kanta,, amma ko motsi batayi kwance take tamkar gawa.
"Ganin dare yafarayi likitoci sukace su inna suje gida abarwa gobe,, aga abinda ALLAH zaiyi kuma,, inna tace" babu inda zataje tananan tareda sopy,, dak'ar aka lallasheta suka tafi akabar uncle kabeer awajenta.
Awannan lokacin kuwa amarya da angonta suna can ana ragargazar amarci,, dan ango bai d'agawa amaryar tasa k'afaba,, dukda yalura tana cikin damuwar abinda yafaru da AMINIYARTA,, itama dai tabada gudummawa dan tasan wannan shine zai k'ara kusanci tsakaninta da Abdul,, zai kuma k'ara zama dalilin da dole iyayensu su barta tazauna tareda mijinta,,, ba k'arya tasha wahala amma ta daure sosai dan tana son Abdul,, to fareeda saimuce ALLAH Yasanya alkairi yakuma shirya masu irin halinku nacin amana da yaudara. Amin
A asibiti kuwa har yanzu sopy bata farfad'oba kuma likitoci sun dage akan tanada rai bata mutuba,, to ALLAH yasa haka, dan gsky masu karatu indai sopy ta mutu to nimafa 'yar rahoton taku bazan sake kawo muku rahotoba,, ALLAH dai yasa da ranta.
Shagalin biki yakoma zaman jigum jigum,, dan maman fareeda sai kuka takeyi tana fad'in wlhy saita kashe auren fareeda,, tunda har taci amanar safiyya,, in kuma ba hakaba zata tsinema fareeda inhar bata rabuda Abdul ba.
""Tofa turkashi kunji wata sabuwa masu karatu.""
Har zuwa yamma sopy bata farfad'oba,, dayawa mutane sun fara yarda tama mutu,, dan ko mahaifinta ma cayayi likitoci suyi hak'uri subada gawar safiyya aje amata suttura.
"Wani likita yace" way baba wayace maka ta rasu?? Yarinyar nan tanada ranta dan ALLAH kubarmu muyi aikinmu.
Sai wajen k'arfe 4:46pm sopy ta farfad'o saidai sun hana kowa ganinta,, dansun yimata allurar barci,, saboda ta sami hutu,, dukkan 'yan uwa suna asibitin kowa ka kalla baya cikin walwalarsa,,, labari kuwa sai k'ara baza anguwa yakeyi,, kunsan dai mutane da gulma,, dan yanzu gulma maza da mata kowa ya iyata,, ALLAH dai ya shiryar damu jama'a.
Mahaifin fareeda ya aika hargida aka kira masa Abdul da fareeda,, bayan d'an wani lokaci suka iso,, dukkan dangi sun had'u, mamar fareeda da babanta sai yayunta biyu yaya lawan, da yaya saminu, da zainab, sai k'anin babanta.
Sai baban sopy da inna, aunty Nafisa da hauwa'u,, sai uncle kabeer,, fareeda duk tabisu da kallo azuciyar ta tace" tofa wannan gangamin namiye?? Zuciyarta tace mata duk anyishine saboda "k",, tai wani d 'an guntun murmushi aiko sama tarwatsashi dan fad'ansu ko wani hargaginsu bazai tsorataniba,, tuni nashiryama fuskantar wannan matsalar.
Yaya lawan yadaka mata tsawa to mara kunya idan kin gama yimana kallon rainin arzik'in saiki zauna ko,, mara mutunci kawai.
Fareeda tad'an tab'e baki sannan ta zauna kusada mijinta,, babanta yay gyaran murya, yad'ora da fad'in assalamu alaikum!!! Kowa ya amsa,, yabi fuskokin kowa da kallo sanna yagyara zama yace" Abdullahi!!! Abdul ya amsa kansa ak'asa.
Baban fareeda yace" miyasa ka auri fareeda bayan kuma da safiyya kuke tare??? Kuma har munyi maganar aurenka da safiyya harda iyaye aciki???
Abdul yagyara zama, baba ku gafarceni dacan safiyya nakeso amma yanzu fareeda nakeso kuma gashima har kun auramin ita.
Baba ya k'ara d'aure fuska, to miyasa lokacin da maga batanka suka zo basu fad'i hakaba??? Saima sukace mana yayanka ne zai auri fareedan??
Abdul yace" nine nace sufad'i haka dan karka hanani auren fareeda.
Baba yaja tsaki to aii har yanzu bata sake zaniba domin dolene kasaki fareeda yanzu anan wurin,,, gaba d'aya wajen saida suka d'ago suna kallon baba banda mama da tace" wannan batu kam tilas ne dole kasaki fareeda ka auri safiyya.
Baban sopy yay saurin tareta amma dai ba haka mukayi dakaiba malam d'ahiru,, gsky karku raba musu aure.........baban fareeda yay saurin katseshi, saidai kayi hak'uri malam ibrahim nariga nagama yanke hukunci.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.