Sanadin Caca Book 2 Complete Hausa Novels By Sadi Sakhna
Reading file: SANADIN CACA 2.txt
Chapter 30 of 42
Mun daɗe muna tattauna,wanda duk yawanci gargaɗi hajiyah Maryam takemin akan nayi taka tsantsan, lamarin,tunda yanzu yafi nada muni,ga zaman dazan ƙarayi a sashen hajiyah Mammah,domin inkana son kama damisa dole saika shiga sansaninsa.
A ranar Ahmad yadawo daga yankinnamu,anyi murna sosai da nasararsa ciki kuwa harda hajiya Mammah,kaman ba fadarta ya ruguza ba. Musamman A.M Aliyu ba ƙaramin farin ciki yayi ba da nasarar. Ana ta murna amma bandani,domin wajen zamannawa na kullum wato lambu na tafi na zauna. Zuciyata nason ganin Ahmad domin nayi kewarsa sosai,amma kuma ina tuna kashedin da yayimin na cewar kada na kuskura nasake nuna fuskata a gabansa.
∆∆∆
Bayan sati ɗaya da wannan nasarar da gen Ahmad yasamu nutsuwarsa ta ɗan dawo ba kaman da ba,saidai duk da haka yakasa tsintar kansa da jin komai ya ƙare. Koda yake dama yasan akwai sauran rina a kaba,tunda har yanzu bai kama shugabar ƙungiyar ba,amma tunda yasan macece yanzu zarginsa kashi tamanin a cikin ɗari yana kan hajiya Maryam ne,don abinda yake kwanannan kenan saka mata ido na shige da ficenta,domin ya kula tashiga cikin tashin hankali da abinda yafaru,sannan ta tsiri zama cikin busy.
Biron hannunsa yake dannawa yana É—agoshi,duk da hakan akwai wani abun da babu.
"Ohhh that girl why....meyasa nake missing É—in matar wani,kaddai na fara son matar da bazata taba zama mallakina ba kai,ahah no ba sonta nake ba,inajin haushi ne da kuma zunubin abinda na aikata mata"
Cije cije yake yace wancan yace wancan shi kaÉ—ai,a iya sati guda daya wuce gabaÉ—aya yaki ko gidan baya son komawa,domin yana shiga zaiji yana so ya ganta,wanda kuma yasan bazai gantan ba,shida kansa ya bata umarnin kada ya sake ganinta a inda yake.
Kai inaga barin ƙasar zayyi naɗan wasu watanni ko zaiji daɗi,dama abbah yabashi hutu tunda yasamu wannan nasarar.
Yana cikin wasiwasinne Eemran ya shigo office É—in.
"Eemran kayimin arrenging na zuwa hutu gobe"
"Ogah anya kuwa hakan zayyi wu,don an fitar da aiki daga headquater,kuma naga hadda kai a cikin wanda zayyi supervising"
"Supervising É—in me"
"Uhmm a cikin trainee ɗin aka dauka masu ƙwaxo zaku tafi dasu Russia na tsawon wata Uku"
Komawa jikin kujerar Ahmad yayi tareda sakin dogon numfashi.
"Yaushene tafiyar?"
"Gobene ogah"
"Ohk"
Abin yabawa Eemran mamaki,yayi tunanin zaice bazai jeba,amma saiyaji sabanin haka,kenan so yake yabar garin kota wacce hanya.
Washagari bayan an gama tsara zaman sojojin a jirgi sun tafi kafin manyan suka bisu a private jet,duk cikinsu Ahmad ne kaɗai ƙarami.
Lokacin dazai taho ko Æ´an gidan bai fadamusu zai tafi ba,iya Neelah ce kawai tasani sai Saleem.
Masauƙinsa aka kaimasa kayansa, bayan ya watsa ruwa yasaka riga marar nauyi ta shan iska.
Fitowa yayi wajen cin abinci,amma shi a hadene da sauran ƙananan sojoji.
Bayan ya zauna an saka masa abinci,har zai fara cin abinci yaga wani yazo ya zauna a opposite É—insa,mamaki abin yabashi,dan yasandai baizo dasu Eemran ba bare su zauna.
Ɗagowa yayi suka haɗa ido da wani matashi,zaiyyi shi a haife,kallon rashin sani yake masa,amma kuma sai yaji kamar ya taba ganinsa. Shima kallonsa yake ko ƙiftawa bayayi,sai can kafin yace.
"Goje mai kakeyi a nan,bayan batanka kaima soja ka shiga,amma meyasa baka faÉ—i inda kake ba,kasan kuwa halin da Sumaimah tashiga a sanadiyyar rashinka?"
Maganar da bawan Allahn yayine ta dakeshi da ƙarfi,zaro ido yayi tareda ajiye cokalin yana kallonsa.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na É—aya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...28...
Number dakinsa kawai yabashi tareda yimasa alamar ya sameshi a can É—in,
Yagane mai yake nufi kuwa,sai yayi shuru da zancen akan zai sameshi a É—akin.
A zaune yake da labtop akan cinyarsa lokacin da musbahu yayi sallama a É—akin,bayan ya zauna shuru sukayi babu wanda yace komai,saida suka É—an ja kaman mutuna kafin Ahmad yayi masa magana.
"Naji kana magana akan goje,ga dukkan alamu kasanni lokacin ina a matsayinsa,kuma kasan inda na zauna"
Kallom mamaki Musbahu yabi Ahmad dashi kafin yace.
"Ya kake magana kaman ba kaine goje ba,shin mai yake faruwane,ka rasa hankalin ka ne a hatsarin dakayi,shiyasa ka manta komai,amma bakayimin kamada wanda ya rasa hankalin sa ba"
"Eh ba hankalina na rasa ba,nayi recovaring hankalina ne,saikuma na manta rayuwar danayi a wanda kake faɗa. Kafin muce komai zanso nasan wanene kai kuma menene alaƙata dakai a rayuwar bayan.
Sunana Ahmad Aliyu,General under Investigation division"
Zaro ido Musbahu yayi jin matsayin da Ahmad ya faÉ—a.
"Shin mafarki nake kokuma idan har kaine goje yaushene kayi karatu haka,a sanina dai dabanci kakeyi da kuma aiki ma Æ´an siyasa. Sannan kana nufin baka ganeni bane,nine fah Musbahu yayan Sumaimah matarka,duk da bakaje wajen É—aurin aurenba amma ai muna haÉ—uwa a gari san......."
"Bangane wanne labari kake min ba,kaine yayan matata,kuma banje wajen ɗaurin aure ba,meyasa toh? Barina baka labarin abinda yasa bansan kokai wayeba,sannan inaso ka bani labarin abinda yafaru daga farkon rayuwata a wannan gojen dakake faɗa har ƙarshe,harma da labarin ita matar tawa."
Bayan yabashi labarin abinda yasameshi ya rasa hankalin sa har yayi rayuwa a matsayin goje,ba ƙaramin mamaki yabawa Musbahu ba. Shima labarin rayuwarsa daya sani a matsayin goje ya faɗamasa,da yanayin aurensa da kuma yanda Sumaimah tasha wahalar zaman aurensa harda tafiyar dayayi ya barta.
Abin ba ƙaramin tayarwa Ahmad hankali yayi ba sosai,shin dama haka yake a rayuwar,a ina zai samo wannan baiwar Allah,mai zaice da ita irin wannan abun daya jawo mata.
Kama kai yayi tareda jan numfashi,tsawon lokaci ya É—auka yana jimamin abinda ya aikata.
"Zan shirya komawa gida gobe,zamu tafi ka nuna min itah"
"Ahah hakan bazai yiyu ba general,duk da nasan kai ogah ne,amma inna bika zan samu matsala a nawa training,nayi ƙoƙari sosai kafin na samu wannan matsayin.
Sannan kuma ita kanta wacce kake son zuwa wajenta bata nan,ta tafi garin abuja aikatau,saboda bayan tafiyarka hatta makarantar daka biyamata kuÉ—inta had ta gama sun hanata certificate,duk wani abu mutane sun washe ganin an É—au shekara baka dawo ba,shiyasa ta tafi neman abinda zata rufamusu asiri"
Wani irin sanyin jikin Ahmad ya sake jin wannan batun,gabaÉ—aya ya rasa mai yake masadaÉ—i.
Wunin ranar gabaɗaya ƙareshi sukayi Musbahu yana yimasa labarin goje,batun zuwa wajen Sumaimah kuwa sun barshi akan suna komawa zasu nemi inda take yaje.
∆∆∆∆
Sumaimah {POV}
Bayan wata biyu.....
Yau tun safe na tashi da tashin zuciya,abu kaÉ—an sai naji zanyi amai,da sabuluna nafarayi a banÉ—aki.
Bayan rana tayi har sannan ban saka komai a cikina ba,saboda banajin son komai.
A zaune muke nida ummi bayan mun gama aikin ranar,inata magana niban kulaba ashe kallona takeyi,É—aga mata gira nayi da alamar lafiya.
"Lafiya kalau,kawai naga kin sauyaminne kwanannan,duk da ke farace amma ƙin ƙara fari,ga wayan bacci dakikeyi,komai inkin fara saikice kin gaji"
Maganganun da ummi tayi dukka nima na kulada su,amma babban abin tashin hankalin shine abinda na zarga,wanda ban kawo shiba sai yanzun.
Wani zabura nayi nai banɗakinmu da sauri,a gaban madubi na tsaya ina kallon kaina,mamana na kalla wanda naga sun ƙara girma,rabonsu da haka tun inada cikin Sayyid.
Zaro ido nayi tareda shafa cikina,rabona da al'ada wata biyu kenan,wayyo mai nake tunda ban kulaba sai yanzu.
"Innalillahi yanzu ya zanyi kenan,kenan ciki na samu a ranar? Mai yasa dukka biyun suka faru a rashin saninsa,nasan wannan zaisan nasane,amma da wanne zai kalleshi shine tashin hankalina,ahhhhh"
Ƙarar danasaka ne yasa ummi yin magana daga cikin daki.
"Sumaimah lafiyarki kuwa?"
"Ba komai ummi"
Fitowa nayi daga bnaɗakin ina rarraba ido,yanzu wazan tunkara da wannan zancen kenan,nasan hatsarin danake ciki nida wannan cikin Allah ne yasan iyakarsa. Don yanzu su hajiyah Mammah babban burinsu shine gano ni wacece,tunda yanzu babu komai ya ruguje. A bangaren hajiyah Maryam kuwa kullum ƙara rauni takeyi,Neelah kuwa batada lokacin kanta tunda Ahmad ya tafi ya barmata ragamar hidimominsa.
Hanyar sashennasa na nufah,haka kawai na tsinci kaina dayin hakan.
Buɗewa nayi na shiga,alamun rashin mutum duk sun nuna a wajen,har ƙura ta taru a falon.
Ina shiga naji wani ƙamshi a falon,wannan wanne turarene haka dayaƙi washewa tsawon wata biyu.
Ɗakin na bude na shiga,nan kamma har yafi falon,dan ji nayi wata nutsuwa tana sauƙamin.
Duddubawa nakeyi ina neman turaren,saida na shinshina dukka turarensa amma ban jishi a ciki ba.
Wardrobe ɗinsa na buɗe,inda ya lanƙaya kayan daya saka a gefe,a jikinsu turaren yafi yawa,ɗakkosu nayi ina shinshinawa,na daɗe ina abu ɗaya,sai daga baya nagane ina abu tamkar kuliyah. Kuma mai wai tsaya,kenan ba turare hancina yake shinshinowa ba,guminsa ne,yaushe na zama mai iya shinshino yanda gumin mutum yake?.
Ajiye sauran kayan nayi na É—auki riga É—aya na boye,kan gadonsa na faÉ—a,ahhh nan ma jinayi kamar yana kai. Nice nake kewarsa kokuma É—an cikina duk bai shafen ba,tunda naji daÉ—in kwanciyar bacci zanyi kawai.
Bacci nayi na ƙoshi sai don kaina natashi,amma duk da haka banji ya wani isheni ba,mitstsike ido nayi,sai sannan na hango gari ta window yafara duhu.
What bacci nayi na kusan tsawon awa shida ko biyar.
BanÉ—akin sa na faÉ—a da sauri nayi alwala,mayafin kaina na yaye nayi sallah kafin na fito zuwa kitchen É—insa ko zan samu abinda zai iya shiga cikina.
Tundaga lokacin dana gano inada ciki,sai yazama kamar hurashi akeyi,tsorona É—aya nasan zayyimin girma fiyeda na sayyid,dan daga ganinsa ma.
Nashiga damuwa sosai da lamarin,ga banida waya ta faɗi a ruwa bare na ƙira inna na faɗa mata.
Kullum inna tashi da safe sainayi shiri mai kyau,gashi na tsiri saka hijabi da kuma É—aurin zani akan cikin. Sati uku da fara laulayin har na rame na yi fayau.
Fitowa nayi daga wanka kware kwaren danayi,to wankane babu sabulu,towel ne a jikina ina gogewa ruwan,kullum a banÉ—aki nake shiryawa,amma yau dayake naji su ummi suna aiki a babban falo shiyasa ban yi a banÉ—akin ba.
Motsin tafiya naji,hakan yaa na rarumi hijabina na saka.
"Dama kin ajiye hijabin,wannan boye boyen ya isa haka,nariga nasan cikine dake malama,inna tacemin wai ai mijinki ya kawoki ziyara,shine daga bada tsarabar ciki sai ya tafi,bazai tsaya a gaisa ba?"
Sauƙe ajiyar zuciya nayi bayan naji bayanin ummin,kenan daman sunsan inada ciki,musamman abinda inna ladiyo tafaɗawa ummi,yayi min daɗin matuƙa,kuma ya kareni daga amsa tambayoyi.
"Miye kikayi wani tsaye kamar gunki,kije sashen hajiyah Maryam wai tana nemanki,inna ladiyo ce tace na faÉ—a miki"
Karisa shiryawa nayi cikin doguwar riga ta atamfa,nasaka hijabina na tafi.
Kafinnan saida nabi ta wajen inna ladiyo tukunna tana kitchen.
"Inna dama kinsan......."
"Haba Æ´ar nan,muna tare a É—aki É—aya har mu kasa gane halinda kike ciki? Abinda zan faÉ—amiki shine ki daina wannan boye boyen haka,wanda yasani yariga yasani,wanda baisani ba kuma zaki jawo hankalin sa ne yasaka ayar tambaya"
ÆŠaga mata kai kawai nayi batareda nace komai ba,kuma maganar tata haka ne.
"Kije hajiyah Maryam tana nemanki a sashenta"
"Toh"
Shine kaÉ—ai amsata kafin na wuce can din,sai a lokacin naji rashin kyautawa ta,don rabona da sashen nayi sati biyu,wasan buya nayi tayi da Æ´an gidan,saboda karsu gane inada ciki.
Magana naji sunayi tun kafin na shiga,da waye haka suke surutu.
tura ƙofar nayi na shiga,wani saurayine amma ba zai wuce shekara sha bakwai ba.
Daga yanda suke maganar zaka gano cewar É—an uwanta ne.
"Wai huzaif yayar babanka nake fah ba kakarka,tashi to ku tafi gatanan ta shigo"
Dukkansu kallona sukayi itada shi,kallo É—aya mutum zayyi masa ya gano kamar da suke da hajiya maryam,tunda tace yayar banbansa to É—an Taheer ne kenan,babban dansa.
"Okay ni barina je waje,ki sameni a mota"
Rabawa yayi zai wuce tagaba na hajiyah Maryam tayi masa magana.
"Kai banason sakarci,bata girmeka bane da bazaka gaisheta ba"
Cikin ɗaɗɗagawa irinta masu sabuwar samartaka ya gaisheni,nidai na amsa a taƙaice ya fice. Ƙarisawa nayi muka gaisa da hajiya Maryam,sunkuyar da kaina nayi,don naji kunya sosai.
"Hhhh yau kuma kunyata kikeji,kijr zai kaiki gidansu ne akwai wanda zaki haÉ—u dasu,bansan ko ki kwana ba ga wannan ki riqe,amma ki tabbatar ki dawo gobe. Kije maza Allah ya tsare,ki kula sosai dan yanzu ba kaman da ba,na fadamasa
kada yayi tuƙin ganganci"
Nidai da toh na amsa mata dakuma godiya. Saikuma kaina a É—aure shin dawa zan haÉ—u a gidan da ban taba zuwa ba..
A haka dai na bi bayan wanda taƙira da huzaif ɗin zuwa motarsa. Ina shiga ya tayar da itah ya hau hanya ko magana bayyimin ba.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.