Sanadin Caca Book 2 Complete Hausa Novels By Sadi Sakhna
Reading file: SANADIN CACA 2.txt
Chapter 35 of 42
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na É—aya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...33...
Sumaimah ce tafara shiga ɗakin,hajiya Maryam na zaune a bakin gado,hannunta na riqe da ƙirjinta,sai tari take wanda kana gani kasan wahala take sha.
Da gudu ta isa gabanta tareda riqe É—aya hannunnata,
"Hajiya yadai jikinne ko zamu koma asibitinne"
"Ahah bazan komaba Sumaimah,kozan koma ma yanzu bazayyi ba,jikina yanzu ya daina regulating baƙon jini,is no more lokaci na yayi haka,ki kulada kanki da kuma mijinki Sumaimah,yanzu na maida komai kanki ina miki fatan ki samu nasara ke.
"Ahah dan Allah karki ce haka,zamu samu mafita,nasan abinda yake saka miki wanann matsalar,wannan akwatin nata ne,in muka wargazashi shikenan"
Duk abinda suke Ahmad na tsaye yana kallonsu,inda Sumaimah bata bashi labarin abinda ya faru ba da bazai san mai suke faÉ—a ba.
Hajiyah maryam ce ta fara É—aga ido ta ganshi,sai kuma Sumaimah.
A razane da kalleshi,domin tunda take dashi bai taba shigowa ɗakinta ba,maida kallonta tayi ga Sumaimah,tareda alamar biɗar ƙarin bayani..
"Sumaimah mai...,..."
"Eh yariga yasan mai yake faruwa,yasan matsayinki da kuma matsayina a wajensa"
"Meyasa meyasa kin kuwa san kasadar da kikayi, abubuwan suna tafiyah ba yanda muka tsaraba,the more mutane na shigowa the more hatsarin hakan yana ƙaruwa"
Matsowa Ahmad yayi kusada Itah tareda tsugunnawa.
ÆŠauke kanta tayi idonta yana zubar da hawaye,tayaya ne zata iyah haÉ—a ido dashi ita kuwa,bayan abinda tamasa da bazai misaltu ba.
"Um.....mmeee"
Runtse idonta tayi jin kalmar daya kirata da ita,abinda bata taba zato ba a rayuwarta. Ita kanta Sumaimah tayi mamakin furucinnasa sosai.
"Shin bazaki amsa ba,wannan shine sunan danake ambaton mahaifiya ta dashi a cikin Addu'a ta,yanzu kuma tunda ga mai sunan a gabana shiyasa na ƙirayeki dashi,shin bazaki amsa ba?"
Kuka hajiyah Maryam ta rushe dashi.
"Bazan amsa ba bazan iyah ba,bai dace dani ba sam,nagaza nakasa,nayi zaton zan iya amma ashe ba haka bane"
"Ke kuwa kika kai ummeee,abinda kikayi ba kowacce uwace zata iya ba,ko a da dabana ganinki a matsayin mahaifiya ta,amma nasan keÉ—in jajirtacciyar mata ce. Nine na gaza na kasa,da har ban iya kallo soyayyata a idanunki ba,sai yanzu nagane da kinada niyyar cutata da tuni kin cutar dani ina yaro,saidai kullum ki dunga treating É—ina. Dan Allah ki juyo ki kalleni."
A hankali take juyo da kanta har suka haÉ—a ido,da alama bataso hakan ba,amma roqon da É—annata yake yi mata abune da bazata iyah riqewa ba sam.
Kafeshi tayi da ido har sannan bata daina kuka ba,hannayenta takai kan kumatunsa,tamkar tasaka ƙaramin yaro a gabanta.
Shafah kumatunsa takeyi wanda rabonta data taba tun yana jinjiri.
"Ah...ahhmadd kayi haƙuri ka yafemin,shayarwa iyah na wata biyu kawai nayi maka,girman da yaro yake a gaban mahaifiyarsa duk baka samu ba, saboda wani yankyakykyen hukuncina".
Duk kasancewar sa namiji mai dauriya,amma ganinta a gabansa tana roqonsa sai ya tsinci kansa da kasa riqe kansa..
Rungumeta yayi kaman zai shige cikinta inda ya fito,wata soyayyarta ne ke shigarsa Tamkar an jonawa tanki bututun ruwa.
Sun daÉ—e a haka Sumaimah ta zuba musu ido. Hawayen idonta ta share,data tuna cewar itama bata san tata mahaifiyar ba,kuma tasan bazata taba ganinta ba,tunda ta koma ga mahaliccinta.
Jikinta ne ya shika,hakanne yasakashi É—agota domin yaga menene,idonta a rufe tamkar bata numfashi..
Jijjiga ta yakeyi amma shuru,waigawa yayi inda Sumaimah take.
"Sumaimah ya zanyi bata motsi fah"
"Jinin jikinta ne ya ƙare,inaga muyi gaggawar kaita asibiti yanzu"
Tashi tayi shikuma ya É—auketa irin bridal style É—innan suka fitah,tashin hankalin daya shiga ya dade baishiga irin sa ba.
A hanyar fita suka haÉ—u da Maimuna tana magana da Fatee wacce tafito daga motar Saleem sun dawo daga É—akkota a makaranta.
Ganin Ahmad É—auke da hajiyah Maryam kaman bata numfashi yasaka su sakin baki suna kallonsa.
Abu É—ayane yazo ransu shine wani abu ya aikata mata.
Saleem ne yasha gabansa cikin bacin rai.
"Yah Ahmad mai kayiwa mommy"
Kallonsa yakeyi da idanunsa wanda ya kaÉ—a yayi ja. Ya kasa bude bakinsa balle ya bashi amsa.
Ganin hakanne yasa Sumaimah shiga tsakiyar su tace.
"Babu abinda yayi mata dama bata da lafiyah,kaita asibiti zamuyi kubiyomu a baya,amma bayan Sameer kada ku faÉ—awa kowa mai yake faruwa a gidannan"
Maganar da Sumaimah tayi ne cikin alamar roqo yasaka Saleem matsawa Ahmad ya wuce da hajiyah Maryam a hannunsa.
A gidan baya ya ajiyeta inda Sumaimah tashiga,sai kuma shi ya shiga wajen driver.
Sai bayan sun fita daga gidan kafin su Maimuna suka bi bayansu.
Asibitin gidan marayunta suka nufah,amma a hanya saida suka ƙira babban likita tukunna,wanda suka yayi mata magani na ƙarshe.
ÆŠakin karbar mutum na gaggawa aka shiga da itah suna isowa,daidai lokacin kuma su Maimuna suka iso,harda Sameer wanda sukayiwa bayani dama yana kusada wajen.
Babu wanda yake magana a cikinsu,amma kana ganinsu kasan suna buƙatar ƙarin bayani.
Likitanne yafito daga wajen cikin sauri.
"Am duk da jinin ta A+ ne bashida wuyar samun donor,amma kasancewar an daɗe ana bata jini dayawa,yanzu jikinta bazai ƙarba ba sai wanda DNA yayi ɗaya wato jininta"
Yana gama bayanin Sameer da Saleem sukabi bayan sa,Sumaimah tana ganin haka ta kalli Ahmad akan yaje.
"Kaje mana dan Allah,wataƙila sai naka yafi kamancece niya da nata"
Su Maimuna suna jin abinda take faÉ—a,amma basu fahimce ta ba..
Shiga yayi wajen É—aukar jinin yabada sample É—in nasa shima ya fito.
Suna nan tsaye bayan an karbi sample É—in Sumaimah ta riqe kunkuminta,wani irin kamawa taji yayi mata.
Duk abinda take Ahmad yana kulada itah,cikin wani É—aki ya shiga ya É—auko kujera,wajen babu gun zama,yasan kuma in yace taje wajen zama bazata tafi ba.
A gabanta ya ajiye kujerar tareda kama hannayenta ya zaunar da itah.
Da mamaki take kallonsa,kenan yasan ta gaji,hakan yayi mata daÉ—i sosai,amma taji kunya ganin su Saleem suna kallonta.
"Yah Ahmad matar wani ce fah kake taba jikinta,yanzu kai......"
Wani kallo yayi mata dole ta haÉ—iye abinda yake bakinta.
Wata nurse ta fito da wata takarda a hannunta.
"Ana ƙiran Ahmad Aliyu,ka shigo wai naka yafi zama iri ɗaya da nata"
"Ohk"
Daga haka ta koma ciki.
Da Murmushi Sumaimah ta kalleshi wanda shima ita É—in yake kallo.
"Kaga abinda nake faÉ—amaka koh?"
"Uhm nagani,barina shiga kada ki tashi ki tsaya,ki zauna yanzu zan fito. In kina jin kishirwa Saleem ya nemo miki wani abun uhm?"
"Uhm naji ka shiga Allah ya taimaka yavata lafiya"
Ahmad yana shigewa Fatee ta matso inda Sumaimah take.
"Ke bangane ba mai yake faruwane,shine zai bawa mommy jini a wanne dalilin,wani shirin kuke haɗawa saboda ku kasheta koh? Ke kuma mecece alaƙarki dashi kina matar wani,nake ganin kaman ta Allah ashe........."
"Ke Fatee miye kike hakane,meyasa duk abinda yazo zuciyarki shi kike faÉ—ane. Mahaifiyarki na ciki batada lafiya amma kin gulma"
"To laifinta ka gani,ai dole ta tambaya,nima abin ya É—auremin kai,miye tsakanin mommy da yah Ahmad da har zai bata jini,wai kuma kuda kuke Æ´aÆ´an ta naku bayyi daidai ba sai nata?"
Maimuna ce tayi maganar cikin kasa gane mai yake faruwa.
Duk abinda sukeyi babu wanda Sumaimah tasaka baki,da abin yayi yawane ma tace musu waƙa a bakin mai ita tafi daɗi.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.