Sanadin Caca Book 2 Complete Hausa Novels By Sadi Sakhna
Reading file: SANADIN CACA 2.txt
Chapter 19 of 42
Sashen hajiyah Mammah nayi bayan na kaiwa hajiyah maryam abincin danayiwa Ahmad,bataci sandwich É—in bama,iya kunun gyaÉ—ar kawai tasha.
A hanya naci karo da wani soja a ƙofar sashen,yana ɗaya daga cikin masu kulada security na gidan.
"Am gud morning,please can you send this to hajiyah Mulaifah?"
Yafaɗa yana miƙomin wani akwati irinna package ɗinnan.
Karba nayi kafin nace wani abun har yabar wajen. Banso ba haka na nufi É—akinnata,Allah yagani banason duk wani abu dazai dunga haÉ—ani da waccer matar.
Tura ƙofar ɗakinnta nayi bayan na shikenan sashen hajiyah Mammah,ko ƙwanƙwasawa banyi ba.
A buÉ—e kuwa yake bata rufe ba.
Wata irin kwanciya tayi akan gadon kaman wata Æ´ar bori,hararta nayi tareda ajiye abin akan drawerta,har na juya zan tafi naji maganar ta cikin magagin bacci.
"Ke rainin naki har yakai kishigomin É—aki kai tsaye kaman wadda muke sharing dake?"
Tsayawa nayi amma ban juyo ba,wai dama idonta biyu?
"Ga waÉ—annan kayan naÉ—eminsu kafin ki tafi"
Cije bakina nayi,amma ya zanyi,banason yazamo koyaushe muna samun sabani da itah.
Juyawa nayi wajenda take maganar,a hankali nake takawa har naje gaban wardrop ɗin,ina buɗewa kaya suka wani sako kai zuwa ƙasa. Saida na tsorita domin banyi zato ba. Zaro ido nayi ganin kusan duk ilahirin kayanta a cunkushe suke babu tsari.
Wai a hakan zata ƙira kanta mace,kuma maison mallakar wani namijin.
Fitowa nayi da kayan cikin tass nafara jerawa da É—aÉ—É—aya.
Wayar tace tayi ƙara,saida tayi ƴar ƙaramar tsuka kafin ta miƙa hannu ta ɗauka.
"Hii padush ykk"
"Ƙalau ke ya akayi jiyanne,abin yayi aiki"
"Hmmm ai nake faɗamiki fiyeda yanda kike zato ma,yace haka ne kam tunda abune da aka farashi,kuma yayi alƙwarin haɗashi yanzun bazai gagara ba. Yau ma zayyi magana da Ahmad akan zancen,zuwa gobe kowa zai shaida shirye shiryen aurena da Ahmad"
"Amma bakya ganin shi Ahmad ɗin ya ƙi amincewa"
"Nima nayi wannan tunanin amma hakan bazayyiyu ba,domin Abbah bazai taba daina yimasa zancen ba idan har ba auren aka yiba,shikuma kinsan wancan karon ma,baya iya tsallake maganar abban. Dan haka kisha kuruminki ki saurari mai zai faru"
Dariya suke sunata maganganunsu wanda sukayi amanna dasu kuma suke yi musu daÉ—i..
A yayinda gefe ɗaya kuma ni suke ƙonamin rai fiyeda yanda mai tunani zai tuna,wai dama matar nan da gaske take,mijina take son mallaka hakan ma kuma ta hanyar mallakar magani,bawai da son ransa ba?.
Rigar da take hannuna na jefar na tashi na tafi,kunnuwana bazasu iyah jin waÉ—annan maganganun ba,in kuma nace zan cigaba da saurarensu to za'a samu cikyakykyen mishkila.
Ina jinta tanamin magana amma nayi banza da itah nabar sashen.
Kai tsaye sashen hajiya Maryam nayi,saidai tun kafin na shiga nake jiyo maganar ta,da kuma muryar babban mutum,nasan babu makawa babansu Fatee ne.
"Wai bakida lafiyane naga duk kin sauya,kin rame ba kaman da ba"
"Ohh dama ka damu da hakan,sai yanzu kasani? KafaÉ—amin menene yake tafe dakai da har kazo sashena i yanxu?"
Shuru naji ya gibta,har zan juya na tafi saboda bai dace na zama kullum mai jin abinda wasu zasuce ba,hakanma kuma sabgar ma'aurata wanda bai shafeni ba.
Turus nayi tareda komawa baya,abinda naji ya faÉ—a ya shafeni.
"Akan maganar auren Mulaifah da Ahmad ne,tazo tasameni akan maganar jiya da daddare...kinsan kuma daman abune da har an farashi wancan tsautsayin ya gibta. To yanzu tunda komai yalafa yakamata a yi auren.
Yanzunnan daga office nake,nazo É—aukar abune nace barina yi miki maganar,shima Ahmad munyi magana dashi É—azu kuma ya nunamin amincewar sa."
"To mai yasa kake faÉ—amin,a matsayina nawa a wajensa"
"Maryam mai yasa kike hakane,wainikam yaronnan mai ya taremiki ne,da kullum kike nuna haka?"
"Abban Fatee mai nayi kuma,shin nasake ƙoƙarin kashe maka ɗa ne yanzun,da kake min wannan zancen. Naji abinda kace,Allah ya taimaka ya kaimu ranar auren,yaushe ka saka?"
"Wani satinne idan komai ya daidaita,yakamata yayi aure zuwa yanzu,kuma babu amfanin sake wani shirye shiryen bayan wanda akayi a baya"
"Uhm"
Shine kawai abinda na iya faÉ—a kafin nabar wajen,nikam mai yasa kullum kunnuwana sai sun jiyomin zancen wasu ne wanda zai tabamin zuciya?.
Dafa bango nake jikina yana rawa na bar wajen. Itama ta yarda da auren,shima uban gayyar ya yarda da auren,shikenan daga ƙarshe sun zabi jininsu zasu haɗashi da ita,dama nasan yafi ƙarfina tun ranar danagano wanene shi,kawai son zuciyane da yarda da abinda bazai yiyu ba yasa nake ganin watarana zai waiwayeni.
Kukane ya kufcemin mai matuƙar ƙarfi a corridon da zai fitar dani zuwa sashenmu.
Kasawa nayi,na kasa ƙarisawa na gaza,komai yayimin duhu. Nakasa dawowa dashi a cikin rayuwata,shin dama bana cikin ransa tunda ko kaɗan,da gushewar tunani kaɗai zai shafeni tass daga cikin kansa?. Dan ban faɗamasa ni wacece ba shikenan koda da sau ɗaya bazai iya cankar wacece ni ba? Idan ta ɗaukeshi wane uba zan bawa ɗana kenan,shikenan yanada uba amma kuma tamkar bashida shi_? SANADIN CACA ne yahaɗani dashi, na tsorata dashi,na ƙyamaceshi amma kuma na daure na amince dashi,na yarda dashi na taimakeshi na kuma bashi kaina da amanata,batareda na duba mai yayimin a baya ba kokuma waye shiba a baya. Amma shi mai yasa yanzu yakasa gani na,ya kasa tuno ni,yakasa karbata a rayuwarsa. Shin mai zanyi nan gaba wanda zai dawo dashi cikin rayuwata?.
"Wayyo Allah mijina,Allah ka dawomin dashi bada wayona ba kokuma dabarata, zan iya bin son zuciyata na faɗamasa ni wacece kai tsaye,amma hakan mai zai faru......zan rushe abinda hajiyah Maryam ta daɗe tana ginawa,zan bayyana ni wacece a idon maƙiyina. Sannan shima zan sakashi cikin ha'ula'i.
Amma kuma idan na kawar da zuciyata gefe shin zan iya rarrashin zuciyata taga masoyinta tareda da wata?? Ohh ni Sumaimah naga ta kaina.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na É—aya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan daya maida kudi gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso yy mgn
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.