Trending Hausa Novels

Sanadin Caca Book 2 Complete Hausa Novels By Sadi Sakhna

Reading file: SANADIN CACA 2.txt

Chapter 22 of 42

Bayan ya fito daga wankan ƙaramar riga yasaka da kuma wando 3 quater,ganin bai ganta a ɗakin ba yasa ya fito falon,nan ma batanan,amma yana tsaye yaga ta fito daga kitchen hannunta ɗauke da kofi.
A gaban kujerar dayake zama kullum ta ajiye,itama kuma ta zauna a gefe.
Har tagama komai yana nan tsaye a bakin ƙofar ɗakinsa yana kallonta,shidai yasan wani abu yakeji gameda wannan matar a cikin ransa.
Da hannu ta nuna masa yazo ya zauna,ganin ya tsaya kaman wani soja (ohh dama sojanne ashe).
"Ciwon ƙirjinnaka ya lafa ne kokuma na samomaka maganin?"
Ajiye cup ɗin hannunsa yayi tareda yin ɗan ƙaramin murmushi.
"Idan nace ki nemo min maganin a ina zaki nemo?"
"A inda yake zan nemo"
"Wanne magani zakice a baki?"
"Uhmm maganin ciwon zuciya idan akayi mata abinda ba daidai ba"
Maganar tata ce ta bashi dariya,agogon É—akin ya kalla.
"Dare yayi yakamata ki tafi"
"Uhm amma zaka iyah........"
"Am not a child Sumaimah,nasaba da irin wannan yanayin zan kulada kaina. Nagode da kulawarki,amma kusancin mu yana yawa,kada ya wuce mizani"
ÆŠaga masa kai kawai tayi,domin batada tacewa a yanzun.
Rakata yayi har bakin ƙofa ta fita shikuma ya rufe.
Dare yafara kam,don goma ta wuce,saidai akwai farin wata daya haska gidan.

"Kinƙirani mommy,shin mai yake faruwa?"
Neelah ta tambayi hajiyah Maryam wacce take zaune ta haÉ—a kai da gwiwa.
Magana neelah tacigaba dayi mata,amma kuma babu wanda ta amsa mata a ciki,hasalima ko É—agowa batayiba daga tsugunnen.
Zama tayi a bakin gadon kusada itah kana ta sauƙe wani gwauron numfashi.
Sun daÉ—e a hakan kusan awa guda, hajiyah Maryam batace komai ba,itakuma Neelah ta gaji da tambayarta.
"Sumaimah batazo ba,baki haÉ—u da ita a hanya ba"
"Uhm banganta ba"
"Ta zabeshi kenan,banyi tunani ba amma tayi zabi mai kyau,takan tsallake duk abinda bana zato"
"Mai ya faru ne a gidan?"
"Duk da a idonta akwai tsananin buƙatar son jin abinda yake faruwa,amma ta zabi kasancewa dashi."
"Wa kike magana akai?"
"Sumaimah"
"Gata nan tashigo fah"
ÆŠagowa Hajiyah Maryam tayi daidai shigowar Sumaimah cikin É—akin,wato ba É—aya ta zaba ba,ta yanke shawarar zuwa kowanne bangarene.
Takowa tayi har zuwa gaban hajiyah maryam ɗin,fuskarta a dake kaman wata soja a fagen yaƙi.
"Meyasa?"
Shine tambayar data samu ikon furtawa hajiyah Maryam,duk da kuwa a cikin ranta ba iyah hakan taso ta tsayaba.
"Meyasa me?"
"Ba É—anki bane? Meyasa zaki masa haka,ko meyasa kike masa haka?"
"Saboda shiÉ—in É—ana ne shiyasa nayi masa hakan,idan ba É—ana bane bazan damu dashi harna bada rayuwata akansa ba"
"Amma abinda kikayi a cikin bainar jama'a hakan kaman ba taimakonsa kikayi ba,saima sakashi a cikin wani tsatstsauran yanayi"
"Taimakonsa nayi Sumaimah,saidai shi taimako kala kala ne da kowacce uwa da irin hanyar da takeyi akan ƴaƴan ta. Ni tawa ƙaddarar kenan taimakonsa a ta hanyar dazai ga kaman cutar dashi nake,kokuma wani daga gefensa"
"Taimako??? Menene dalilin yin wannan maganar toh,shegantashi kikayi fah a gaban kowa,kince shi ba É—an Alhaji Aliyu bane,to É—an waye kenan baki faÉ—aba?"
"Batun É—an waye karki damu kanki,yanada uba wanda ba kowanne É—a ne ma yake iya dacen samunsa a uba ba" dalilina nayin hakan kuwa ke baki san komai ba.
Siddabarun da Mulaifah tayi masa,tayine akan Alhaji Aliyu,amma kuma ba iya nan zai tsayaba,shima Ahmad anyi asirin da idan Alhaji Aliyu ya tambayeshi to dole sai ya amince,a matsayinsa na mahaifinsa.
Sai yana ganinsa a matsayin mahaifinsa tukunna asirin zayyi tasiri,wanda bazai karyeba har sai anyi auren.
Hakanne yasa nayi amfani da gaskiya na farfaÉ—o dasu daga tarkonta. Yanzu da Ahmad ya daina ganin Alhaji Aliyu a matsayin mahaifinsa to asirin ya karye akansa"
"To amma sai kinbi ta wannan hanyar kafin ki karya abin jikinnasa,abinda kika faÉ—aba i think ya tona abinda bai kamata a tona ba ne na tsawon lokaci,kinaga hakan bayyi yawa ba"
"Yawa?? Hmmmm Sumaimah kenan!! Abinda nayi a yau É—in shine ya dace ayishi tun shekara talatin baya,dan haka banji wani É—ar ko jin babu daÉ—i akan abinda nayi,hasalima tsuntsaye biyu na jefah da dutse É—aya. Shin kinsan mai zai faru idan banyi abinda nayi yau ba?"
Jijjiga kai Sumaimah tayi,harda Neelah wacce ta tsaya ƙyam tana kallonsu su biyun,kuma ta fara ɗago mai yake faruwa.
"Nafarko zan mutu,Mulaifah zata mutu sannan shima Ahmad bazata barshi ba zata kasheshi. Wannan shine kaÉ—an daga abinda zai faru,to kinga banida zabi face yin hakan,duk da raina dana Ahmad zai sosu akan hakan"
Mutuwa kuma,abin har yakai hakane,to waye mai ƙullah hakan,waye ya hana gidan gabaɗaya zama lafiya,idan har zancen da hajiyah Maryam ta faɗa gaskiya be,cewar ba itace takeyin abubuwannan ba?.
"Hajiyah Maryam shin idan nace na yarda dake har raina,zaki bani labarin abinda yake faruwa?"
"Bazan baki ba,saboda baki yarda dani É—in ba,saidai zan baki dan wani abun daban"
"Menene?"
"Saboda ke ɗin kin zama ɗaya daga cikin a halinnan,ko ki yarda ko kowa ya yarda,ko kiƙi yarda ko kowa yaƙi amincewa,keɗin kece surukata kuma matar ɗan gidan na farko,wanda shine magajin dukkan komai. Uwa uba kuma gashi hadda ɗa,wanda shine jika na farko a wannan generation ɗin. Dan haka a matsayinki na mahaifiyar jikana,kuma matar ɗana zan faɗamiki mai yake faruwa a ahalinnan tun daga farko har ƙarshe a taƙaice.
Barina je banÉ—aki na dawo,ki shirya kwana a zaune yau"

To kuma zaku kwana a zaunen mu fara,kokuma zakuyi bacci inyaso gobe sai mu cigaba.

SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.

*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)

Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150

Bismillahir-rahmanir-raheem

Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na É—aya yayi min magana zan bashi shi kyautane.

Sister's duk wacce batayi anfani da sabulun mg's ba ko kit dinsu inamai shaidamuku anbarku acan baya domin duk wnd yajaraba mg's sai sanbarka duk wani Mai tantama Akan kayan gyaranjiki toh tabbas yacire sabulun mg's domin yahadu bakarya zegyarajiki yafidda dattin fata Dama duk wani matsalan fata duk Wanda kefama da matsalan fata walau pimples ko spot, sunburn acne,stretch mark dama dukkan wani prblm yajaraba mg's bi'iznillah komai zaizama labari bayan jikinku yy fresh zaisa jikinku yy smooth yadinga glowing,gawanda basa San anfani da Mai zaku iya using mg's batare da kunbukaci wani Mai b🤗nd wnn new soap din💣ne,😯 bama cika Baki kujaraba kugane ma idanku domin ance gani yakoriji Kuma siyan daya maida kudi gida
You can check pic👇for the soap reviews🥰
Soap price:4k
maiso yy mgn
08062991549
07046881166
07067210195
Call 08064532391
Instagram:glow_with_mgs
Facebook: mg's skincare

Masu bukatar cream Shima munadashi harda ma complete set nagyaranjiki
Small 14k
Babba 16k

Munatura Kaya kowani gari dayardar Allah Amma delivery is not free

Be part of the glow team😍karkubari abaku lbr👏

*BOOK 2*
...20...

Sunana Maryam A.M Abubakar Rimi,ni kaɗaice ɗiya tall a wajen mahaifina mace,sai ƙannena maza guda biyu.
Duk da yanda na faɗamiki wannan muƙami da mahaifina keda shi,amma sam mu a wajenmu tamkar da babu yakene,domin bamuda yawan haula na dangi,ga mahaifiyarmu ta rasu a haihuwar Mujaheed ƙanin Taheer,tun bayan rasuwarta abbanmu bai ƙara aureba,haka ya zauna dagamu saishi sai kuma Wata mai kuladamu Anty Mommy.
Cikin kaɗaici muka tashi da rashin iyaye,domin abbammu baya zama a gida,saboda babban muƙamin daya samu a ƙarancin shekaru,sannan aikine na sojoji,shiyasa baya zaman gida sosai. Domin wani lokacin sai yayi sati uku ma baya ƙasar.
Rigima irinta yara duk bamuyi shi ba,koyaushe daga makaranta sai makaranta,in kinganmu a gida to da daddarene.
Ta inda Allah ta taimakemu shine da muka samu nanny mai mutunci da kuma tausayi a garemu.
A haka kwanci tashi cikin wanann halin har nayi graduation a secondry,lokacinne kuma aka kai Taheer makarantar sojoji bayan ya gama juniour school,shikuma Mujaheed yana jss one.
Kasancewar inada ilimi sosai mashaallah,kuma dama tsawon zamannawa a gidannamu karatu kawai nakeyi har na girma nayi wayo.
Saina roƙi abbanmu akan yabarni na tafi law school,bai hanani ba,hasalima yaji daɗin hakan sosai.
Cikin ƙanƙanin lokaci aka shiryamin komai da komai na tafiya law school a nan abuja.
Kasancewar abbah baya zama sosai,kuma yanzu na tafi makaranta,kuladani zayyiwa anty mommy wuya,sai abban mu ya tamƙa kulawata a hannun Gen Hammah,wanda shine mataimakin abbanmu,duk da cewar yafi abbanmu a shekaru,kaman yanda na faɗamiki ɗaukaka ce tasameshi a ƙarancin shekaru.
Abbah Hamma a lokacin yanada Æ´aÆ´a guda biyar,akwai Muhammad,sai Aliyu sai Aina'u,sai Mariyah da Zainab.
Muhammad shine babba,kuma ɗan hajiyah Fatima,ƙanwarsa ɗayace Zainab.
Saikum Aliyu shine mai ƙanne biyu,Aina'u da Mariyah,su kuma ƴaƴan hajiyah Mammah ne,kuma itace amarya a wajen Abba Hamman.
Zaman lafiyar dana gani a gidan farkon shigata da kuma yanda yaran suka tashi abune da zai burge duk wanda yagani,musamman ma irina da sukayi rayuwa da ƙaɗaici da rashin iyaye.
Bayan shekara Biyu da fara makaranta ta,abbanmu ya ɗebe Taheer da Mujaheed suka koma England da zama,babu yanda banyi ba akan ya tafi dani,amma firr yaƙi,a cewar sa ina mace bai kamata na bishi ba musamman da lokacin karatuna yafara ɗan nisa.
Haka dole inaji ina gani na hakura suka tafi,wanda kuma nasan bazai wuce da saka hannun Hajiya Mammah ba,don lokacin dana fara zuwa gidan ta jani a jiki sosai,amma ni ban fiya shiga sashenta ba,saboda bama shiri da Aina'u,nafi shiri da zainab. Ita kuma mariya lokacin ƙarama ce.
Kayana na tattara daga hostel na koma gidan Abbah Hamma da zama,hajiyah Mammah taso na zauna a sashenta amma naƙi,badan komai ba saidan abu biyu,. Na farko Banason faɗan da muke da Aina'u,duk tsiya ita gidansu ne,bai kamata ace nazo ina faɗa da ƴar masu gida ba kullum,sai kuma magana ta biyu Aliyu yana sona,nikuma har sannan ban bashi amsa ba gaskiya,bazance bana sonsa ba,bazan kuma ce ina sonsa ba,irindai kaji mutum yana burgeka amma ba so ba.
Saidai shikuma a nashi bangaren soyayya yake nuna min a gaban kowa,hakan sai ya fara takurani,shiyasa na sauƙa a sashen hajiyah Fatima dana dawo gidan da zama.
A tsawon dawowata gidan bamu haÉ—u da Muhammad ba,saboda shi yana England wajen abbanmu a can yake aiki a wajensa,yawanci mutane ma cewa suke shine mai gadon abbanmu a wajen aiki,domin yasha cewa Abbah Hamma ya bashi shi,saidai kawai yayi dariyah.
Bayan shekara huɗu da fara makaranta ta Allah ya kawomu gamawa,a lokacinne na roƙi abba yazo shida ƙannena dukka.
Duk da cewar dama yana xuwa wani lokacin,kokuma in anyi hutu nina je,amma hakan baikai a ce dominni zasuzo ba.
Tareda dukka gidan aka haÉ—u ana tayani murna da kuma shirye shiyen gamawar tawa.
Zuwa lokacin na zama Æ´ar gida sosai,tun inajina tamkar ba É—aya daga cikinsu ba,har yazamto yanzu in ba mutum yasani ba bazaice niba Æ´ar gidan bace.
Sauri nake hadda gudu gudu na nufi Wajen Zainab,saboda ance min ta karbo mana dinkinmu da zamu saka.
Jinayi na bugu da mutum,ɗagowa nayi muka haɗa ido da Muhammad,ƙifta ido nayi shine kuwa,kuma fah shine.
To ko su Abbah yabiyo shima domin zuwa murnar gama makaranta ta kai,kai anya kuwa.
Mutum ne shi mai sauƙin kai da kuma mutunci,amma fah akwai miskilanci dayin sha'aninsa daya shafeshi,bai fiya shiga harkar mutum ba in bawai an tsoma shi ba.
"Ahh yah Muhammad tare kuka......."
Tun kafin na gama maganar ya ɗagamin kai yana murmushi,nasan ba lallai yabani amsa ba,murmushin shine amsar,kai mutuminnan yana bani a jikina,duk sanda na ganshi rasa nutsuwata nakeyi da kuma guntun hankalina. Duk da ma saina ɗaga ido nagano shi,saboda yanada tsawo,nikuma ga ƙanƙantar jiki kaman ruwan aski.
Daƙyar na janyo ganina daga kansa na rabashi na wuce zuwa wajen abba nah da ƙannena,nabar batun ɗinki tunda naji ance sun iso.
Da tsalle na faɗa kan abban ina kuka,wanda kowa yasan na farincikin ganinsa ne,a tsaye suka a ƙofar gidan da Abbah Hamma,ina jinsa yanamin dariya sai sakaliya,nidai shuru nayi,Allah yaga ai ina ƙoƙari,ace mutum yana rayuwa wai kuma ƴan uwanshi suna wani wajen daban.
Gaisawa mukayi da sauran Æ´an uwannawa, kafin daga bisani muka shiga ciki anata murna.
Mun zo shiga cikin gidan naji zainab taja hannuna zuwa garden,tambayar ta nake mai yake faruwa amma sai jana take tana dariyah.
Bayan mun isa sakinta nayi tareda buÉ—e baki saboda mamakin abinda nagani. Da balloo akayi amfani wajen haÉ—a sunana da kuma murnar gama makaranta ta..
Abin ya burgeni matuƙa,har bansan lokacin da yah Aliyu yazo inda nake ba.
"Ina miki murnar gama karatunki maryam,sannan kuma dan Allah a yau É—in ki karbi so........."
Tun kafin yagama naji mai zaice zainab tazo akan wai ana kirana a cikin gida,da alama sun gama shirya walimar kenan.
Haka na juya batareda naji mai zaice ba nabi bayanta.
Riga ta da aka ɗinka saboda ranar,babu taron mutane sosai,amma wajen yayi kyau babu magana,a dai irin dai zamaninmmu kam abin ya ƙayatar.
Bayan an gama komai magana abba nah ya farayi,ganin yanada muhimmanci sosai yasa dukka kowa yayi shuru domin muji mai zaice.
Bayani akan murna da kuma farincikin gama makaranta ta,sannan ya miƙa gaisuwa ga Abbah Hamma,bisa rikeni dayayi amana har zuwa lokacin.
Bayan nan kuma hannun Abbah Hamma ya riƙe kaman mai shirin roƙonsa wani abun,abinda ya faɗane yasaka dukkan mutanen wajen zare ido,bama kamanni da kuma zainab da Aliyu.
"Abokina komai dana roƙeka kayimin harda wanda banyi zato ba,samun amini irinka sai an tona,nagode nagode da karamcinka a gareni."
"Haba Abbakar miye kakeyi hakane,a tunanina kaman mun wuce wannan abin an zama É—ayah."
"Ehh to in hakane,ina neman alfarmar kabawa É—ana Æ´ar taka mana aure"
Abbana yafaÉ—a yana nunani da kuma Muhammad.
Dukka wajen kowa shuru yayi cikeda mamaki,amma babu wanda yace komai ana jira aji ta bakin Abba Hamma.
"Indai hakane babu matsala na bawa Muhammad Æ´a ta Maryam,Allah ya sanya alkhairi a aurensu ya basu zuri'ah É—ayyaba. Kenan itama zaka janyeta can wajenka koh"
Dariyah abba nah yayi tareda cewa,
"Ba komai saina bar maka Taheer anan ai,dama shine mai son yin aiki anan"
To shikenan abu yayi kyau Allah ya ƙara haɗa kanmu dana ƴaƴan mu."
Haka taron ya ƙare,wasu yayi musu ɗaɗi,wani yayi musu bazata,yayinda Aliyu shida hajiyah Mammah da ƙannensa duniyar tayi musu duhu,yazamana gani suke tamkar an ware sune a rayuwar gidan. Amma banda Aliyu,shi abinda yasakashi cikin wani yanayi ganin yanda soyayyarsa ta subcene akan idonsa,kuma hakanma ba mallakin kowa nake shirin komawa ba sai dan uwansa na jini.
A bangaren hajiyah Fatima itama taso ƙin amincewa,saboda ta kulada Aliyu yana sona,amma kuma batada ikon hakan musamman ma da su Abbah sun riga sun yanke hukunci,nima kuma a lokacin naso kaina,ban kulada halinda Aliyu zai shigaba,nabi zabin zuciyata wato Muhammad ɗin.
A ƙurarren lokaci aka saka bikin,sai murna nake zan koma kusada mahaifina da zama,shikuwa Muhammad da akayi masa zancen babu yabo ba fallasa ya amince.
Shirye shiryen biki aka fara,inda a ranar wata juma'a aka ɗaura aurenmu nida Muhammad. Aliyu bayanan aka ɗaura auren,a cewarsa an turashi aikine ƙasar spain,amma a zahiri kuma shine da kansa ya cika neman aikin saboda yayi nesa da gida,a lokacin danaji ance zai tafi ana gobe ɗaurin aurenmu naji tausayinsa sosai,saboda ni shaida ce irin son dayakemin. Amma kuma bazan iya tsaidashi ɗin ba saboda banada abinda zan bashi,kai na kokuma wata soyayyar,babu mai yiwuwa a ciki.
Wanda suka san soyayyar da Aliyu yakeyimin haka suka manta,aka cigaba da hidimar bikina.
Bayan an É—aura auren bamu tafiba sai a washagari tukunna..
A lokacin nafara kunyar hajiyah Fatima da kuma Mammah,ganin da gaske fah matsayina ya sauya a gidan,nazama surukarsu.
A daren mun É—au lokaci da tsawo muna kuka nida zainab,ganin da gaske fah rabuwa zamuyi na tafi.
Kyauta mai tsoka matan gidan sukayimin,harda Abbah Hamma ma. Tareda Mujaheed muka tafi,aka bar Taheer anan.
Shikuma Abbah da mijinnawa jiya suka tafi,akan za'amin cuku cukun wajen aiki da kuma cigaba da karatu.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.