Sanadin Caca Book 2 Complete Hausa Novels By Sadi Sakhna
Reading file: SANADIN CACA 2.txt
Chapter 29 of 42
Ban nufi sashen hajiyah Maryam ba saina nufi namu,yanzu dole na rage shiga wajen hajiyah Maryam É—in,idan har inaso nasha lafiya.
∆∆∆
Su Ahmad har sunyi kwana uku a cikin sansanin barayi,yauÉ—inne kuma suke saka ran zuwan shugaban kungiyar na biyu wato Don 2.
Abubuwa da dama da suke shirin yi da kuma wanda sukayi babu wanda basu sanar da Ahmad ba,hakan ba ƙaramin dadi yayi masa ba,ganin ya samu dukkan labaran dayake buƙata cikin sauƙi.
Abu ɗayane dai har yanzu bai sani ba shine sanin shugaban ƙungiyar na ɗaya da kuma na biyu.
Wannan kaf cikinsu babu wanda ya sani.
Dare ya fara,kowannne lokaci Za'a iya ƙiran Ahmad su gana da Don 2,a zaune yake shida su Eemran suna plan yanda komai zai kasance.
"Ka gane Eemran ku tabbatar kun saitasu dukka bindiga,sanann gurnet dayake kakkafe yazama cikin ready,so nake mu tashi wajennan a yau bayan munkama shugaban,kada kowa ya tsira da ransa a cikinsu.
"Angama shugaba"
Suna gamawa aka zo ƙiransa ya fita.
Wani É—aki aka bi dashi,wanda tsawon kwanansu uku na gidan basu taba shigaba.
Yanada matsakaicin girma kuma yasha ado kamar ba'a cikin kogon dutse ba.
Wani mutum ne a zaune yasha suit baƙaƙe,ɗan dattijo ne domin yafara manyanta,magana yake a waya lokacin da suka shigo,sannan fuskarsa da wata baƙar mask tana sheqi.
Bayan ajiye wayar cire mask É—in yayi tareda juyowa cikin taqama.
"Barka da dawowa jaki na mijin gaske goje,naji daÉ—in cewar kana raye,domin ko babu komai nasan jakar da muke nema tana hannun ka,sannan........."
Caff ya tsaya da bayanin ganin wanda yake tsaye a gabansa.. Yana zare ido.
Shima Ahmad É—in a bangarensa tun lokacin daya juyo É—in kafeshi da ido baya ko motsawa saboda razanar ganinsa a wajen.
"Gen. Buhari Bello wanda suke cewa Uncle BB,Aminin mahaifinsu ne tun suna ƙanana,suma tare suka tashi suka gansu. Komai da AM Aliyu zayyi sai yayi shawara dashi,amma.......what yana ɗaya daga cikin wakilan ƙungiyar datake maƙiyarsu a barikin sojoji??
"General mai kake anan badai kaine goje ba??"
Kafin yagama tantancewa Ahmad ya saitashi da bingida,yayinda ya danna wata makunna a hannunsa,aikuwa wajen ya kaure da ƙarar bindigu da tashin gurneti.
SADI-SAKHNA CEH
09035784150
ku tuntubeni domin biyan kuɗinku ko ƙarin bayani.
*SANADIN CACA*
-BOOK 2 (PAID)
Mallakar *SADI-SAKHNA*
09035784150
Bismillahir-rahmanir-raheem
Ki biya kan ki karantamin na biyu dan Allah. ga number ta nan mai son littafi na É—aya yayi min magana zan bashi shi kyautane.
*BOOK 2*
...27...
Duka da naushi Ahmad yake kaiwa Gen Buhari Bello,shima ramawa yakeyi kasancewarsa tsohon soja,ga Don 3 ya buge bindigarsa tun É—azu.
Ganin faÉ—an ya É—auke musu hankaline yasa don 3 É—auke wayar Gen BB ya fita.
Sun daÉ—e suna faÉ—an kafin Ahmad yasamu nasara akansa,ta hanyar É—aukar bindigar tasa,saita shi yayi da ita yana haki.
"Miye alaƙarka da wannann kungiyar,dama tsawon lokacin nan amanar sojoji kake ci,irinkune kesa a dunga yiwa jami'an tsaron ganin marasa gaskiya koh.......(kwafɗama sa ƙasan bindiga yayi saida ya faɗi)........kaine don 2 to wanene shugaban ƙungiyar,inaso ka faɗamin yanzunnan kokuma na jajjage kanka da bindigar nan"
Cikin ƙaraji da tashin hankali yake maganar.
Wata dariyar baka isa ba gen BB yayi wa Ahmad,cikin sauri yasaka ƙaramar wuƙa ya yanke wuyansa da itah,yana kakarin mutuwa Ahmad ya jefar da bindigarsa ya ƙarisa wajensa da sauri.
Tallafoshi yayi a razane,ga jini yanata zuba a wuyansa,abin har yakai ya kashe kansa akan yafaɗa masa wanene shugaban ƙungiyar nan?
"Yaaa....rrro kenan,mai amfanin na faÉ—amaka tunda nasan dama mutuwa zanyi idan ta gano kasanni........bazaka taba sanin wacece itttt.......ba"
"Dama macece ka faÉ—amin, wacece w......"
Shuru yayi tareda sakinsa ya koma gefe,ganin ya riga ya mutu,abin yayi matuƙar razana shi sosai.
Wayarsa ce tayi ƙara,hannunsa yana rawa ya ɗauka ganin Eemran ne.
"Hello sir mungama dasu,saidai wannan shugabannasu mun sameshi yana waya da wani"
"What definitely shugabarsu yake faÉ—awa mai ya faru"
"Eh nima nayi tunanin haka,na harbeshi a kafaÉ—arsa da dama"
"Ohh yakamata mu tafi,abin bai tafi yanda ake so ba,amma dai Alhamdulillah hakan ma mukeda nasara"
∆∆∆
"Ina jinka ka faÉ—amin mai yake faruwa a wajen Gen?"
"Hajiya an samu matsalane ba Ogah bane,Goje ashe sojane yayi mana baɗɗa kama,yanzu haka ya gane ogah kuma ya kamashi,na samu wayarsa ne na ƙiraki"
"Wayeshi ka faÉ—amin"
"Gen ........"
Kafin yaƙarisa aka katse ƙiran,kuma da alama harbeshi akayi don taji ƙarar bindiga.
"Waye ka faÉ—amin wayeeeeee......"
Ƙara ta saka tareda yin wurgi da wayar, kaltum ce ta tsugunna ta ɗauke wayar jikinta yana rawa.
Kallon fuskar hajiyah Mammah nakeyi,idan ka ganta zakace bazata wuce shekara talatin ba a duniya,babu wannan sunkuyawar da yamutsewar fuskar.
Mamaki abun ya bani,mai ta shafa haka ta sanja lokaci guda.
Masifa tacigaba dayi tana zuwa tana dawowa,ganin abin bazai mata ba ta jawo wani akwati a ƙarƙashin gadonta,ja ne yana glowing,kana gani kasan abun tsafi ne.
Hannunta ta saka ya buɗe,wani aljana ce ta bayyana a gabanta da baƙaƙen kaya,kamarsu ɗaya da itah,amma kana gani kasan ita ba mutum bace,to wacece kenan.
Jikina rawa ya fara daga inda nake labe da jikin ƙofa ina leƙawa,dan karfin hali bana tsoron ma ta ganni.
"Ruhina inaso kayimin bayani shin mai kasani gameda abinda yake faruwa,ƙungiyar dana kafah wadda da ita nake control na manyan ƙasar nan ta rushe,mai yasa abubuwana suke rushewa"
Muryarta da bibbiyu take fita kamar wata na'urah.
"Hakan dama dole zai faru,tunda dodo ya baki kashedi akai,matar da kike gudun kada ta bayyana harta haifi magajin wannan matakin tariga ta bayyana,kuma itace sanadiyyar karyewar alƙalaminki,indai ba kasheta kikayi ba to bazaki ƙara nasara ba"
"Kaman ya yarinya,ni banga kowa a tareda shi ba,Mulaifah ce itama kuma yanzu sun rabu"
"Hhhhhhhh duk da a zahiri kina kulada yarintarki amma hakan baya aiki a hankalin ki,shiya riga ya tsufah"
"Ruhuuuuuu karki ƙara magana akan tsufah na,bazan tsufah ba bazan taba tsufah ba,wannan fatar tsufan ina nuna ta ne kawai da iyalaina,suma in suka isheni dukka zan gama dasu nayi rayuwar ƴan ci na"
"To inba haka ba mai yasa kika kasa gane cewar Ahmad yayi rayuwa ba'a gabanki ba na tsawon shekara shida,bai kawomiki anan ya gamuda itah ba,sannan kuma yayi rayuwa a cikin ƙungiyar da kike karewa. Sannan ya bar mata da kuma ɗa a rayuwarsa ta baya.......munkasa gane hakanne a da dayake ta Addu'a a lokacin,yanzu dayake kan aikin ruguza ƙungiyarki bayayi sosai shiyasa muka gani......amma duk da haka bamuga hoton madubin rayuwar ba har yanzu"
Jikin hajiya Mammah rawa yafara bakinta yana fitar da wani hayaƙi,ganin Kultum zata fito yasa nayi saurin barin sashen nima nawa jikin yana rawa.
Me suke nufi,kenan nida É—ana mune sanadin karyewarta a yanda ta yarda,in hakane to kuwa muna cikin hatsari,sannan dole kada tasan koni wacece, matar nan ta wuce yanda nake zato.
Ina cikin tafiya ina tunani naji na bangaji mutum,saurin dawowa hankalina nayi tareda kallon Fatee.
"Ke ina kike gani haka, kaman wata sabuwar makahuwa,kije mommy tana nemanki "
Daga haka ta wuceni tana karairaya,nidai binta nayi da ido kafin na wuce sashen hajiya Maryam.
A zaune na gansu itada Neelah suna magana,ita kuma yaushe ta dawo,da alama yaune.
Saida na giashesu kafin na zauna a akan kujerar,Neelah ce ta kalleni tareda cewa.
"Miye ya faru haka Sumaimah naganki kaman wacce taga fatalwa,ko kema kinji labarin nasarar da Ahmad yayi akan ƙungiyar BC?"
"Uhm yayi nasara amma kuma yasake buɗe ƙofar gane shirinmu,domin a yanzu haka hajiya Mammah tasan da labarin yayi rayuwa a cikin ƙungiyar BC,kuma yanada ɗa da mata,duk da batasan sunanmu da fuskarmu ba amma nasan bazata zauna ba saita gano hakan"
Abinda nagani a É—akin hajiyah Mammah na sanar dasu,duk da basu wani razana ba,amma sunyi mamakin yanda takai har haka a shu'umanci.
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.