Romantic Hausa Novels

A Dalilin Matar Uba Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: A_Dalilin_Matar_Uba_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 1 of 35

[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & ✍🏼WRITTEN BY```
*Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

✍🏼 _In the Name of Allah, the Most Beneficent, the most Merciful. All the praises and thanks be to Allah, the Lord of the 'Alamin (mankind, jinns and all that exists). The Most Beneficent, the Most Merciful._

*I SALUTE YOU ♻E W F gaisuwarku tada bance, baki bazai Iya furta yanda nake jinku a zuciyataba, kuna gaba sedai a biko a baya na gaisheku yan uwana masu kamshin humrah, kuyi naku kuyi na wani* ❤Zuciyata na tare daku a koda yaushe____ _One Love to you All_❤

*I will never forget you kawayen arziki*
_Xeey Haruna, my Asy Khaleel, Farida m Nasir, fati Axland And Mariam Tijjani_

```WANNAN LITTAFIN GABA DAYA SADAUKARWA NE GA_____```
*MARIAM TIJJANI ADAM* _NA BAKISHI KYAUTA HALAK MALAK NAKINE_

*Dedicated To My great FAMILY❤ One love kawai*

*1 ____ 2*

Mummy.....mummy kinga Zee_zee tana biyoni ko kice mata ta dena bina... Cikin wani tafiya na kasaita Naga Hajiya Halima Tana sakkowa daga upchair dauke da wani yalwatacciyar murmushi ta sama waje ta zauna a kan wani hadadden Kujera dake Pallon..

Da zamanta sega abba (usman) yazo da gudu ya kankame Mummynsu yana Hajiya kinganta ko,

"HAJIYA ce ta dakamai tsawa tana cewa Haba swthrt i told you several times akan ku dena wannan guje guje amma bakwaji ko?

____Zee dake labe Tana jin hajiyarsu na fada dan haka ta dakata bata shugo falon ba, Zee dai se leken brother dinta takeyi tana mai gwalo.

"Tun hajiyarsu bata luraba harta lura da leken Da XEE takeyi dan haka ta kirata

"Xee Ce ta tako sumi Sumi gabar hajiyarsu tazo ta zauna, Dukansu dukar dakai sukayi kamar basu suke guje guje ba "Hajiya Halima ce ta kalle yaranta cike da farin ciki da godewa Allah da ya bata yara masu kaunar junansu, sannan ta bude baki tace me nace muku? Ba nace ku dena guje gujen nan ba idan wani cikinku ya fadi fa?

"wata matace nagani ta kelo tace Aww hajiya ai da kin barsu sui wasansu idan basuiba dawa zasui? Naga gidan bakowa saisu kadai just leave them su shana wata rana bazasui ba

"Hajiya halima ce tace Uhum kinsansu se anayi ana taka musu burki tukunna if not ahaka zasu tashi da rashin ji ballema Zee tana babba amma wai ita take tsokanar

"Abba ne yai kasa kasa da murya yace No mum bazamu karaba, excercise mukeyi ko sweet sist, Zee dai ta daga Kai alamun da cewa Yeah,

Hajiya Halimace Tace to Naji adai dena banaso suka hada baki sukace *Okay MUM.....*

*TOSHEN LABARIN*

Alhaji Abdullahi dan garin kadunane, Babban dan siyasane dan sunsan komai da yake shiga da fita na gwamnati, suna yawo kasa kasa Inda Allah ya hadashi da matarshi ta Farko Hajiya sa'adatu, sunyi auren soyayya shuru shuru har sukai 10years ba yara shi kuma Alhaji Abdullahi nason yara sunje asibiti ance duk ba me matsala cikinsu Lokacine be yiba..dan Haka Kwasam se Allah yasa Ya kara aure Hajiya Sa'adatu tadanyi bakin ciki sosai da ya sake aure a aganinta zai juya mata baya setaga akasasin Haka... Kuma Ikon Allah matar daya aure bata mata raini tana bata respect sosai daidai gwargwado hakan yasa ta dan kwantar da hankalinta,

"Akwai wata rana kwatsam Bayan Alhaji Ya Auro matarshi ta biyu after 1year se gashi Allah ya azurtasu da Yarinya ta farko Mace, Alhaji yayi farin ciki sosai da kowama ya nuna farin cikinsa nan fa Alhaji ya daura Son duniyan nan wajen wannan Yar lelen Tashi Wato *ZEEE* dan kamaninsu daya da mamanta, fulanin gombe ne,

"ana haka komai na tafiya normal ba wani kishi ko Bacin Rai after Zee tayi 7 Years Allah ya kara azurtasu Da Yaro Usman (Abba) to nan fa Alhaji kwata kwata ya tare wajen yaranshi baya son wani abu dazai Tabasu, hatta uwar data haifesu sedai ta nuna ita ta haifesu amma cinsu chansu duk alhaji keyi, dan aganinsa sune farin cikinsa dan ba karamin Son yara yake kuma gashi Allah ya bashi....

Nan fa Hajiya sa'atatu ta shiga damuwa duk abun duniya ya isheta akwai wata rana tana zaune a daki tayi tagumi sega Alhaji ya shugo, ya kalleta yace hajiyata meke faruwane naga duk kin chanza kwana biyun nan

"Hajiya sa'adatu tace ba dole ba har yanzu ban haihu ba abun na damuna

"Alhajine yai smiling yace ki kwantar da hankalinki, haihuwa zakiyi just lokacine muke jira sai mu dage da addua, nima inason inga kin haihu uwar gidatah, yanzu abun da nakeso dake shine ki kwanta ki bacci tace okay saida safe, seda yaga ya lallabeta ta kwanta sannan Shima yaje yai Alwala yai sallah ya tsaya addu'oin neman wa iyalansa tsari....

*Ummiey Xeey*
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & WRITTEN✍🏼 BY```
*Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA_____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*

Where is *UMAR M SHARIFF FANS* _Wannan page din gaba daya nakune masoyan Umar, Ku taka Ku juya Jirgin *So* zai tashi so karki bari a tafi bake💃🏻💃🏻💃🏻_
*Jirgin so zaya tashi kaidai ake jira Dan gatah duniyar So Kaine da Sarauta..Umar👑*

*📄 Page 3 ____ 4*
The next day ne in the morning Alhaji Abdullahi da iyalansa suna kan dining table suna having break fast phone dinshi yayo ringing

Yana dubawa yaga one of his friend ne da suke aiki waje daya then yai picking suka gama magana sannan ya kalle matayanshi Tace huhh emergency tafiya zanyi kuma is like zaiyi taking time before na dawo kuyi shawawa yanzu plz dawa ya kamata na tafi?

Hajiya Sa'adatu tai kicin kicin darai Dan all her thought Alhaji zaice da hajiya Halima zai tafi but bari dai taji ayi shawaran

"Mum Din su zee tafara magana cikin fara'a Tace Alhaji Ku tafi da uwar gida mana, ni banga ta tafiyaba saboda yara suna zuwa school kuma kaga idan na tafi zan bar mata surutu Dan sata magana zasui tayi just ko tafi WATA rana inda rai da lafiya zai muje

___Alhaji Abdullahi ya kalle Hajiya Halima Dan ba karamin burgeshi takeyiba SBD saukin kanta, tanada dadin sha'ani Dan bata dauki duniya wani abuba yace Nagode Allah yai miki albarka, Tace ameen, sannan ya koma dubarsa ga hajiya Sa'adatu yace ki Shiga ki shirya zuwa 12pm flight dinmu zai tashi

Hajiya Sa'adatu jiki na rawa ko to bata cemai ba ta Shiga daki ta kira aminiyarta tana bata labarin ai zuwa anjuma zasubar Nigeria Alhaji da ita zai tafi kuma zasu kusan two weeks a chan

" Aminiyarta ta washe BAKI Tace wani hanin ga Allah baiwane, da yanzu kin haihu kin Tara yara badake za'ajeba

Hajiya Sa'adatu ta Dan hada rai Tace uhm kinsan dai inason yara sosai yanzu idan Alhaji ya mutu duk su zasu kwashe gadon

Kawarta Tace karki damu zamusan me zamuyi kema zaki haihu nan sukai sallama Amimiyata Tace Allah kaiku Lafiya Asha soyayya Allah yasa Asama tsaraban chan Lolz.... Itadai Tace Ameen

Misalin 11 ne Su Alhaji suka fito zasu tafi airport driver yazo ya kwashesu dukansu harda su Zee n abba yan rakiya da mum dinsu, Zee n abba se kuka sukeyi wai zasubi Dad dinsu but ba hali, se lallashinsu yakeyi dakyar suka hakura yace zai kawo musu tsaraba masu Yawa sannan Suka dan lafa da rigima,

"seda sukaga Tashinsu sannan driver ya dawo dasu gida, Suna dawowa sukaga gidan su kadai ba Dad suka fasawa Mum dinsu kuka wai suna missing Dad, Seda tai da gaske sannan sukai Shuru,

_____Around 4pm ne Suka isar kasar England an ware ma ko wanne a cikinsu bangarenshi kasancewar Kowa da matarshi Yazo, Hajiya sa'adatune bayan Sun huta sunci abinci takecewa Alhaji Tana missing din gida Most especially *XeeXee,* wai taji kawai tana son yarinyar ne Ko zai bar mata itane??

"Alhaji Yace ai ba komai Bari mu koma Gida Seta dawo dakinki kinga anyi One One kenan, Nagode Miki Allah yai maki Albarka kema Allah ya kawo Miki Naki Tace Ameen......

•••••••••••
Xeexee ce a Compound din gidansu Da kaninta suna Wasa, tasa wani Riga da wando kanta tayi parking amma a rufe yake da wani Hula, amma baya hana ganin gashin kanta, Daganinsu kasan hutu ya zauna musu a jikinsu dan har skin dinsu wani sheki yakeyi, Suna cikin wasansu Sega wani class mate dinta *Ismail* ya shugo kana ganinsa kasan Dan hutune, farine beda jiki sosai ga Idonshi me kyau, class mate din xeexee ne but ya girmeta ba sosai ba age dinshi zekai 19years haka while Xee kuma she's just 15yrs..

Da gudu taje zatai hugging dinshi chan kuma meta tina seta Fasa, Shidai isma'il kallonta kawai Ya tsaya yi sannan ya bude baki Yace Hmm ke bakyaji ko wai yaushe zaki hankaline, Abba kaninta kuma Se dariya yake mata Yace Sweet sist kenan, Ganin Abba na dariya ne dan he's just 8years besan ma wani abun ba dan kawai girman ne ba wani wayau...

Isma'il ne yace nazo ne fa Ki bani assignment din da aka bada kinsan ran Friday banje school ba gashi gobe monday... Tace Oh hakafa let's Go in kaje ma ka gaishe da Mummy tana ciki, Yace Okay, sannan suka kama hanya se cikin Pallow din nan suka tadda mummy tana Kallon TV, he greeted her then Tace Mai ina mum dinsa yace tana Gida, tace a gaida ta, yace Ok,

"Zeezee ce Ta fito da school bag dinta ta ciro mai book din Tace gashinan Nima banyiba please kai mana Tare, "Mummy tace me za'ai Dama an baku assignment baki fada mun ba

*Zeezee* tai narai narai da ido tace am sorry mummy na mantane,

"mummy tace sorry for yourself yarinya se wasan tsiya ace common assignment kin manta, Allah ya shiryeki Tace Ameen,

Then Isma'l ya Amsa book din, mummy tace yagaida mamanshi yace okay Hajiya, Zeexee ce ta fito raka isma'il ya kyalleta yace ke wai me yasa kike hakane? Look at you bakyajin kunya? Jifa shigan da kkeyi haba ba girmanki bane

"Xeexee ta kalleta tace haaa what's wrng with my dress kaifa ka cika sa ido ko incema ustaz, komai akai ba daidai ba nikam bye sai mun hadu gobe a school ta juya tai shigewarta Daki,

Shikam girgiza kai yayi yace tabbas hankalin mace da namiji ba dayaba, yai ficewarsa ya shiga gidansu

*Yours Ummiey Xeey*
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY &✍🏼WRITTEN BY```
*©Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻ EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*😍

_Dedicated This Page to you my dear Sweet Hearts_ *Aisha's*💋💋
*Aishan Umma and Aisha A Muhd* _I love you Guy's zama daku Akwai Sweet Irin sosai dinnan infact if am with you Guy's I forget my worries... Allah ya kara daukaku yasa Ku gama da duniya lfiya..._ *ummieyxeey* _cares a lots irin Ku kadai kuka sani dinnan😘_

*📄 PAGE 5_____6*

Shikam girgiza kai yayi yace tabbas hankalin mace da namiji ba dayaba, yai ficewarsa ya shiga gidansu

Ya na shiga room dinsa ya shige ya zauna abakin bed, se a time din Ya tuno wai fa dazu xee taso tai hugging dinshi ha'a whats wrng with this pretty girl ya fada a mind dinshi,

"Wata zuciya kuma tace mai Kasan wasu haka suke Tarbiya kowanne da irin tasu, yace dai Allah ya shiryamu kawai Ya bude assignment din ya Fara dubawa

Haka ya duba tsab yai musu assignment din Tare Yasa a school bag dinshi sannan ya dakko kayanshi yai iroing bayan ya gamane Ya zauna ya rasa ina zaije then ya tafi wajen mamanshi Tunda dama Shi Kadai ta haifa.. Yace Mum kinki samomin aboki ni kadai banajin dadin zama nan gidan ba abokin wasa

"Mum tace ina kawarka *xeey* take? "Yace oops daga gidan ma nake hajiyama tace in gaishe dake, tace dan Albarka se yanzu kke fadamun yace mum na mantane tace ina amsawa...

Chan kowa yai shuru sannan yace Mum Yauwa wani abu na damuna wlhi

"mamanshi Hajiya Maryam Tace zo sweet heart dina ka fadamun banaso abu na damunka menene relax and tell me "ismail Yace mum Wlhi inason frnd da xeexee amma halayenta basui mun ba setai ta abu kamar Ba hausa fulani ba as I'm yanayim dressing dinta

"Hajiya maryam tai smiling tace come on babyboy Just pray for her, Kasan an sangarta Ta kuma kasan first born ne so dole zakaga ba daidai ba and her father is a rich man kowa yasansa a kasan nan ba ruwanka

"ismail yace Rich man fa mum? Nima ai muna da kudi but why banyin Behaving Haka

"hajiya tace my Beloved Son It's okay zakazo ka cikani da surutu i said just pray for her ba shikkenan Ba "yace ok mum

Suka Fara wani hiran, misalin 9 pm Dad dinshi ya dawo yamai sannu Da zuwa mum dinshi ta kawomai abinci then sukaci gaba da hiran suna su uku Dan ba karamin soyayya suke nunawa Son dinsu ba se kusan 11 dad yace yaje yai bacci tomorrow is Monday............

Washe gari monday Tun asuba Hajiya Halima ta tashi ta fara aiki ta hada musu break fast

Ta shiryasu tsab sannan driver yazo Ya kaisu School, Bayan sun tafine ta shirya Gidan tsab ta daura abincin rana before su dawo...

*Xeexee* ne A class tare da sit mate dinta ismail,

Class teacher sune ya shugo yace ai summiting assignment, Sannan ismail ya Fito mata dashi sukaje sukai summiting, Tamai godiya dan dama in ta itace sedai a doketa, gata da kokari shap brain but matsalarta rashin Concentrating Wasa yai mata Yawa, She's lucky ma ta hadu da frnd din kirki..

Around 10am ne akai ringing Break Female friends dinta se Kiranta suke suje sui break but taki ta makalewa Isma'il hakanan suka barta suka tafi kowa se gulmarta yakeyi wai bata da frnd se Namiji, Ta fito da food flask dinta Tace mai yazo suci abinci yace Bazaici ba wai me yasa take hakane? Yace mata Why can't you go for your female frnds Dan taga yana biye mata ko?

Nan danan tasa kuka wai yana mata shouting itafa batason haka, Yana tsaye ya rasa me zaiyi just rungune hannuwansa yayi Yana kallonta yace Ikon Allah ahaka har Aka dawo break yan Class ganin zee na kuka ismail kuma na tsaye aka cika se ihu akeyi wai *Xeexee is In Love Lolz....*

"ismail ne ya hada Rai yace bafa haka bane ba wanda yasan abun dake faruwa kan kace meye har Romours Ya kai staff room haka aka kirasu staff room aka zanesu wai tun basu tafasaba zasu Kone,

Xee tayi kuka kamar ranta zai fita Duk tabi ta Kosa Ai closing taje ta fadawa mum dinta after sun dawo class ne, English teacher din daya basu assignment yace yaga hand writing iri daya ya bada names din aje a kirasu, suwa zasu gani Again *xee ce da ismail* nan dai aka kara tabbatar da soyayya Sukeyi alhalin karyane....

Ismail yaji duk school din gaba daya ya tsana balle kuma Ita Zee, tana ganin kamar dan dad dinta bayanan ne Ake mata haka anya ma sunsan waye ita da zasu dinga bata wahala,

after sun dawo class ne all eyes on them Ismail yake bata hakuri dukda dukansu sunsan kwata kwata ba haka zancen yakeba, tace bakomai karya damu... Haka dai suka Wuni a class dukansu basa wani Jin dadi

Anayin closing Abba brother dinta Yazo wajenta yaga her eyes looked Red alamun tayi kuka sosai yake tambayanta meke faruwa tace muje gida kawai bro, suna nufuwa bakin gate suka hango driver Dinsu sukaje suka Shiga shima yana son tambayar meya faru amma yana tsoro sbd yasan ba mai magana takeyiba.....

"Abba ne yace baka lura da xeexee bane, Se a time din yace meya Faru, nan ta kara fashewa da Kuka take bashi labarin Komai, ya bata hakuri Tace ai ba komai Allah yasan komai to ma in soyayya mukeyi ina ruwansu Damu tai kwafa, shidai driver se bata hakuri yakeyi har suka iso gida....suna shiga gida ta kwallawa Mummy kira mummmmyyyyyyyyyyyyyyyy,

mummy naji tasan ba lafiya an tabo *xeeynta* dan haka ta fito da sauri dan ganin me ya faru dan tasan kiran nan ba haka kawai bane..........!

*Ummiey xeee ce*
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & ✍🏼WRITTEN BY```
*Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*😍

👂🏻 *NASIHA TO ME AND YOU*

_Yan Uwa mudai kara jin tsoron Allah, Musan abun da mukeyi tun kan lokaci ya kure mana, wai yau hartakai ta kawo Saboda Novel yaran mutane suna lalace, subhanallah, ke marubuciyar batsa bazakiji tsoron Allah ba ki dena, mezakicewa Allah idan kina cikin rubutawa Allah ya dauka ranki, Sit down and think yar'uwa....Ke kuma reader ko kunya bakyaji ki wasting time dinki kina Karanta abun da ba temakanki zaiyiba sedai ya saki cikin wani halin da ke kadai zakiji...haba Yar Uwa......Wallahi it's not too late to repent kowa ya gyara halinshi...Allah yasa mu dace_ ~Atakaice dai kenan~

*Mudai yan â™»Exclusive mun hana rubuta batsa. Kuma duk wacce ta turo mana Book din batsa cikin group din mu....zamu cireta mubarta da Allah.... Thanks All*

📄 *PAGE 7____8*

A bakin Kofa Taci karo da Su Xeey, xee na ganinta ta kara fashewa da Kuka Tace mummy kinga kinga....... Bata sama daman Yin maganar Ba Saboda Kuka Ya riga yaci karfinta, Shikam Abba Yayi ciki dan yaga abun yayan Tashi Azimun,

"mummy ce ta riko hannunta Tace Let go in inji me akai Miki, suka Shiga dakin sannan Ta dago fuskar yarta Ta share mata hawayen dake Zuba a fuskarta ta dai lallasheta tai Shuru kannan Ta Ke tambayanta meke Faruwa,

___Nan Xeey taba hajiyarta labarin Komai From A To Z bata boye mata komai ba tun daga Kan Dukan da akai musu wai tun basu tafasaba zasu kone suna soyayya Har na Hand writing din da aka Gani iri Daya, Itadai Hajiyarsu bata hakuri tayi dan tasan Halin yarta Sarai bata san Komai kan soyayya ba kawai dai anci zalun sune, but kan Batun assignment Tasan sunyi daidai amma ya zatai? Ita ta jama kanta,

hajiya hakuri ta bata ta kwantar mata da hankali, tace Dad dinsu na dawowa Zai cireta daga school Din....

Xee Ce ta shiga wanka bayan ta fito ta shirya tsab cikin Wani riga da siket yar kanti yai mata kyau sosai sannan ta dakko abincinta Taci after ta gamane taji kawai tana missing Dad dinta dan haka ta dakko phone ta fara dialing Numbern Dad dinta, Ringing Daya ya dauka, Suka fara magana kamar Haka
Sweet dad Good afternoon,
Yace afternoon how ar you my love
"tace I'm fine am just missing you dad,
nan dai suketa hira kusan 30mins kudin wayan ya kare ya Sake Kira mum bata ce mata Komai ba dan tasan Idan suna waya da dad se sukai 1hr dan Shi indai kan yaranshine zai iya spending more than Hour suna waya,

Hajiya sa'adatu ne Taga abu yaki karewa tun bata damuba harta damu Tai tsaki tace wai kai har yanzu da yarinya kake waya haka, Nifa banaso, Ko sauraronta beyiba seda ya gama waya Yace Hajiyata ta Kaina,

Hajiya sa'adatu ta wani dan bata Rai dan Ita kwata kwata Bataso Mijinsu Na yawan Kula yaranshi haka, Dan gani take tamkar zama da ita kawai yakeyi amma yafison yaranshi da uwar yayanshi,

"ALHAJI Abdullahi yace yarkicefa nake waya da ita, Se ta dan wayince dan kar yace akwai wani abu aranta gashi Kuma tace Tana Son zee ta dawo wajenta sai yasa ta dan sake fuska tace Oh am missing them na kosa mu koma mu gansu, Lolzzz Mata kenan na ciki na ciki,

"Yace karki damu soon zamu Koma ai nima ina missing dinsu sosai sosai, Da yace sosai sosai dinnan Wani bakin ciki Taji kamar Ta kwalla ihu amma Ba yanda ta iya se ta dan wani ce Uhmm.......
••••••••

Bangaren Su xee kuwa komai na tafiya Normal ba wani abu sedai tun ran da aka Zanesu a school ta fito da wani Sabon Salo, Dan kara chusa kanta take wajen Ismail Dan ace eh soyayyan sukeyi amma Ina shi tsoro yakeji dan yasan halin babanshi idan yasan abun dake faruwa kenan shi yana baya baya da ita, ita kuma se shisshigemai Takeyi,

*1 WEEK LATER* Ana Gobe Su Alhaji Abdullahi zasu dawo sukaje babban Kasuwar dake Kasar England, Alhaji ba karamin siyayya yaiwa yaranshi ba, Hajiya sa'adatu kuwa ganin siyayyan ne hankalinta ya tashi Tace tab Alhaji ina zamu da wannan kayan,

"Yace na xee da abba ne, sa'adatu saboda bakin ciki kasa boyeshi tayi tace haba Alhaji wai me yasa hakane yan uwan naka fa, komai se kace yaranka, to Nima kaga banda Yara zanyiwa yayan yan uwa nasan ananan ansamun ido aga me zanzo dashi

"Alhaji Abdullahi Yasan inda Maganarta ya dosa be wuce tace itama da tanada yara da yanzu da ita ake cin wannan daular se be da muba yace To kema ki zaba duk kayan da kikeso ko nawane zan biya, nan ta yake baki ta faramai Godiya shidai Binta da ido kawai yayi dan tausayi yana tausaya mata amma idan tai wani abun kana Gani kasan bakin ciki ne,

"haka suka gama siyayya sannan suka dawo Gida, yana dawowa ya kira Matarshi (maman Su Xeey) yake sanar dasu Gobe in Allah ya kaimu zamu dawo, Tace To Alhamdulillah Allah ya dawo daku lafiya yace Ameen, Suna gama waya ta kira two loving children dinta take fada musu Gobe dad dinsu ze dawo, Aiko nan suka fara murna suna Tsalle Zeey da taji murnan ya mata yawa da gudu ta shiga neighbour dinsu gidan su Ismail, yana Daki a kwance Kawai yaga an fadomai dakin Bako sallama ta haye gadon tana *my Ishmail* sunan da take kiranshi kenan, Tace Gobe Dad zai dawo, gobe dad zai dawo ka tayani murna...

"Tashi yayi yace hoohoo xeexee to Naji Allah ya kaimu gobe... Tace Amin but lafiya naga kamar you're not in the mood,

"Yace to ba doleba kinga Ya kamata ki kara hankaline ni namijine ke ta macene be kamata kina yawan shugomin any how ba.... Tace tooo bari na ware naga zaka fara mun preaching din da ka saba Aikam kan kace me, xee ta fita a dakin Se cikin gidansu taje ta sama waje Ta zauna kamar wacce akaima Rasuwa. Allah Sarki xeey...

Mum ce tazo wucewa taga Xee ta natsu tasan Da alama Abokin natane ya tabota dan haka batace mata Komai Ba, mum ce tazo fitowa Zata dakko Wani towel da take goge goge a kitchen Taci karo Da Ismail a bakin kofan Ya gaisheta yace Mum ina Frnd Take Tace Tana ciki, Yai maza ya shiga yana Xee xee xee, Tanajin muryanshine Ta wani bata Rai tace who is calling My precious Name,

Tana magana tana wani Yatsina Fuska sannan ta fito sukai 4eyes... Yace Xee haba Xeey... Itadai mummy ko bin ta kansu batai ba Ta ci gaba da abun da takeyi....

*Ummiey Xeey*
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & ✍🏼WRITTEN BY```
*© Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*😍

```Dedicated this page to All ♻exclusive writer's Fan's💋💋💋 ```

*📄 PAGE 9___10*

ISMAIL ne ya sake kallonta for the 2nd term Yace Haba Xeey, why are you behaving like this, "Itadai Mummy ko bin ta kansu batai ba taci gaba da abun da takeyi Dan Tasan Sun saba irin wannan ai fada wannan ya Biyo wannan,

"Ishmail dintane ya Kara Magana Yace am talking To you ne fa kin wani banza da mutane, se a time din xee ta dago fuskarta sharkaf da hawaye tace to bansan ya kakeso ina maka ba, komai nayi se kace ba daidai ba seka ganar dani, Nikam banga Wani abu ba dan ina shugoma Daki any how you're my frnd, my sitmate infact my everything, bantaso naga kowa ba se kai, sanin kankane banda frnd sbd a tinanina mata basu da Wani abu se gulma and so On,

"Yace Eh Hakane But i want you to understand Something My Xeey, kinfa........ Se kuma Yai shuru dan Yasan kome zaice mata ba ganewa zatai ba saboda ba zama da mata takeyi ba inma wani abun ne shi yafi kowa Sanin wacece Zee sai yasa yai shuru,

"Tace naga zakai magana kuma kayi shuru yace Eh zancene Kinga Kiyi hakuri ki share hawayenki kar idonki su kumbura kinga gobe dad Zai dawo, Tace bazaka sharemun ba kai,

"ismail Yadan waiga yaga mum bata Kusa ya ciro handkachief ya goge mata yace mata zai tafi to hpe ta dena fushi dashi, Tace yeah ta rakashi Har bakin Gate sannan ta dawo cikin room,

___Wanke fuskarta tayi tama chanza kaya dan ma'abociyar tsabtace sannan taje kitchen ta taya Mum dinta abun da zasui dinner dashi, Sunyi Sun Gamane after kowa yaci Suka gyara ko Ina dan gobe da wuri zasu tashi su fara shirye shiryen Abincin tarbon Su DAD....

*WASHE GARI*
Tun 5 da mummy ta tashi bata koma bacci ba, Taje ta Gyara side din Mijinsu, Sannan sukazo sukai break fast atsartsaye, tun daganan hajiya Halima bata zauna ba tayi wannan tayi wanchan, ta gyara ko ina abinci kam ba'a magana tayi kala kala, Around 11pm ne sukaje Airport taren Baki...

"suna Zaune suna shan ice cream ne Jirginsu Ya sauka, Mum tace su tsaya a fara fitowa sannan, Aiko suna tsaye sega Dad da hajiya sa'adatu a gefensa da gudu Sukaje sukai Musu oyoyo, Hajiya sa'adatu harda wangale baki tana oyoyo my xeexeey,

Dad ne yace plz mu Shiga cikin motar gaggaisa, na gaji Nan driver ya kwashesu da jakokunan Su se gidan Alhaji Abdullahi, Nan Fa aka baje a Pallow, Hajiya Halimace Ta dakko Musu Abincinan Datai Musu, Tana budewa ta fara serving Dinsu nan fa kamshi ya turare ko Ina,

hajiya Sa'adatu jiki na rawa ta amsa dan ta manta rabon da cin irin abincin nan, Shinkafa ne fara se taliya taji Su latas se Dan sauce din miyar da taji kifi ta zuba musu, Sukaci sukayi nak,

Su xee kuwa baki yaki rufuwa anga Beloved Dad tana makale dashi, Nan fira sukai sosai sannan dad ya shiga ciki ya watsa Ruwa ya Samu ya kwanta ya huta gajiya.....

__Misalin 5pm ne dad ya Tashi daga bacci yaje Waje ya gaggaisa da frnds dinshi da suka kwana biyu basu haduba...

Around 8PM ne Bayan anyi sallan isha'i Dad Ya kira yaranshi pallow, Dad ne ya janyo manyan jakunkunan da yazo Dashi Ya bude ya ba kowa tsarabanshi, Tun daga kan yaranshi har da masu gadi da drivers Na gidan...
Su Xee sunji dadi sosai dama burinta itama be wuce taganta kusa da Dad dinta, sun mai godiya sosai se atime din hajiya sa'adatu da lura da yawan kayan da yasai musu, daki ta shige ta tura kofa tana maida nunfashi tana tabdijam Allah na godema da banyi k'auran bakiba da yanzu Wannan kayan banawa a ciki balle naba yan uwana tunda ni ba haihuwa nakeyiba Tabdijam... Nan ta ciro waya ta kira kawarta taka sanar mata da cewa ai Ta Dawo, Kawar ta tace To Inanan Zuwa gobe Hope dai an mana tsaraba, Tace Uhm kedai Allah ya nuna mun randa nima zan haihu, dan ko ba komai Na samu gado Subhanallahi, kawarta Tace tab he har tsayawq zaki ya mutu, hmm zamui magana anjuma nan sukai sallama

Ita ko Xee badan dare yayi ba da taje wajen Frnd dinta ta nunamai Kayan da Dad inta ya siyo mata Hakanan ta hakura se goben..

Washe gari Nayi Tun 8 after dad dinta sun tafi Abuja xee ta je gidan Su Ismail yana bacci ma tunda ranar Sunday ne kamar daGa Sama yaji ana Knocking kofanshi,

Mum din shine ta fito ta Ganta ta gaisheta, Tace Aww Xee ce da safen Nan, gashi yana bacci,

"ismail Na juyosu da sauri ya bude kofa Yace Na tashi dan yasan yanzu se Xeey tai Fushi idan taji ance yana sleep kuma be bude mata kofar Ba..

"Tana ganinsa ta fara dariya Tace Come lets Go muje kaga kayan da dad dina ya siyomun, Yace Ok bari nayi brush Ko najene haka,

Ta kyalkyale da Dariya, "Mummy tace Uhm bari nai gaba dan kunfi Kusa, XEE CE ta jirashi a pallow Har yaje yai brush dan har wanka ma yayi ya shirya shap shap sannan ya Biyota suka Fito yace xee rigima this early morning kinzo Kin tasheni da kece da yanzu kin fara zumburowa mutane Baki,

"Ta kyalleshi ta murgudamai baki tace eh naji dai muje, Suka shugo ya sama su mummy a pallow Ya gaishesu Nan ta fitomai da kayan Ta raba wasu kashe biyu ta bashi yace No bazai karba ba, dakyar dai Ya amsa wasu kayan a ciki sannan Ta rakashi yakai gida harda mum dinshi ta biyosu Godiya.......

Nan dai suka zauna se Hira sukeyi da xee da ismail, Shima abba Se Wasa da ball yakeyi tsakar gidan...

*Ummiey Xeeey*
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & ✍🏼WRITTEN BY```
*© Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*😍

*📄 PAGE 11__12*

Misalin 11am Hajiya yalwa Aminiyar Hajiya sa'adatu tazo gidanta, tai mata sannu da zuwa nan fa suka baje a dakinta, Hajiya Sa'adatune ta kawo mata su Apple, lemu da Kankana, taci ta koshi ta mike kafa sannan ta kalle sa'adatu tace kai Hajiya kina shanawanki fa wannan Kayan dadi haka gaskiya kina jin dadi sosai,

"sa'adatune tace Uhm sannan ta tura kofan dakinta tace aminiyata wani dadi kina ganin har yanzu ban aje kwai a gidan nan ba balle nai tinanin jin dadi nan gaba, Bazan boye mikiba rashin haihuwar nan nawa na damuna, Ita kuma wanchan (Mamansu Zee) Yaranta fa biyu, Gasu har sun girma ni yazanyi yanzu se kuma taI tagumi,

"Aminiyartace tace haba Kawata ki kwantar da hankalinki abun da nakeso dake Shine, ta matso kusa da kunnan Kawarta ta shafa mata wani tsegumin da ni kaina banji me sukaceba, Tana cire bakinta wajen kunnanta naji Sun wani tafa suka hada baki sukace Mun kusan shiga Gari......!

Bayan sun gama yan Surutansu na kawaye ne Hajiya sa'adatu Ta kwaso kayan da tai tsaraba nan ta nuna mata, Hajiya yalwa tace kai amma kinyi daidai, tunda baki da da ko jika dole a gwangwaje yan uwanki da kaya, nan dai suketa firfito da kayan har suka gama Itama yalwan Ta sama rabonta sukai sallama sannan Ta tafi gida.....

"life goes on haka abubuwa suketa gudana; akwai wata rana da ya kasance Ranar Bakin Cikin Xeexee Suna Zaune a Class time Din Suna SS 1, Ismail ne ya kalla Xee yaga se Design takeyi a wani paper,
Ismail yace ki tashi i have something to Tell you,
Zee ce ta ajiye abun da takeyi ta fuskanceshi tace Ok bro i'm all ears,

Yace Soon to miss you my lil Sister,

"Tace Amm banganeba ina Zaka ba,

Yace Kinsan time yayi da zan zana waec dina so by next week zan bar zuwa school dinnan sedai mu dinga haduwa a gida....

Nan take xee ta fara kuka, wai ita dan me ze fada mata haka, Kuka takeyi ba sauki, Dakyar ya lallasheta tai shuru ana yin closing kam tun da tazo gida ta kwanta bata kara fitowaba, Kowa se tambayanta yakeyi what's Wrong setai banza da mutane, mummy kam bata damuba dan tasan ita da ismail ne duk yanda akayi, ranar Wuni tai a room dinta har Dad ya dawo ya sameta a kwance sannan ya tambayeta meke faruwa ta fadamai,

"Dad ne yai smiling yace Oh my baby lalle kun shaku da wannan yayan naki, in banda abunki ai ba Age mate dinki bane balle a ace zaku zauna Class daya,

"tace Dad wlhi i so much like ismail, guy din beda prblm and he knows what he's Doing, daddy dai ya bata hakuri akan Dole fa ta hakura tunda zaman mace da namiji ba zai taba Yuwuwa ba ko yan biyune dole sai daya yabar daya wata rana, Seda taji kalaman dad sannan Tai hakuri tace It's Ok,

ranar dai ba wani bacci tai ba se tinane tinane takeyi Na Ismail.....

*ONE WEEK LATER* Rana bata karya
Yaune Ismail ya dena Zuwa School.

Xeexee kam hankalinta a tashe yake koda taje school taga She's Alone ba abokin hiranta kwantawa tayi akan Desk Se tinanin her frnd takeyi,

Wata Safiyyace yar Class dinsu Tace Haba Sist, karki damu zan zama me share miki hawaye, Muma nan da kike ganin mu one day zamu rabu, no condition is Permanent....

"Xeey ce ta dago kai ta kyalletace Ta sake wani murmushi tace yes hakane sist, Ngd Yanzu na sama frnd kenan dama ni banson tarkacen kawayene sai yasa ban ciki bin Kowaba...
"Safiyya Tace yeah like me kenan naga rayuwarmu zatazo dayane sai Yasa Nazo mu kulla frndship...

"Xeexee tace well it's Ok Allah yasa mu dace Safiyya tace Ameen, "xeexeece ta ce to baki fadamun Ke wacece ba,

_Safiyya ta gyara zama Tace Uhm kamar yanda kika Sani sunana Safiyya, Muna Zaune a Ung Sarki, Mu ukune wajen Babanmu, nice yar auta, kuma inason kasancewa da mutun me gaskiya me rikon Amana bansan gulma...._

"Xeexee ce tai wani irin Ihun dadi Tace Wow, Lalle rayuwarmu zatazo Daya, Nidai sunanan xee, matan dad dina biyu, mamanmuce ta biyu kuma nida brother na Abba kawai ta haifa...

"Safiyya Tace Wow Nice family Allah yasa mu rike junanmu da Amana, Xee tace Ameeen

*Bangaren Ismail kuwa.* ...

_Lolz Ku tara a next page Love you All_

*Ummiey Xeey CE*
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & WRITTEN BY```
*Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*😍

This page is dedicated to my dear sweet Heart *Herlieymer Ameen* ```I love you so much, Allah ya kara daukaki da kungiyarku na``` *TWF* 💦💦

*📄 PAGE 13____14*

Bangaren Ismail Kuwa. Ranar Da ya dena zuwa School kamar mara lafiya dan missing Din Xeexee yakeyi, yana kwance a daki pillow ya dakko ya rungume, Naji yana wani surutai nasan be wuce Missing Din Xeexee, chan naga Ya sake pillow din Ya zauna a bakin gado, Kana Ganinshi Kasan Tinani yakeyi, Wani dan Memo naga ya dakko yayi rubutu,

"tashi yayi ya nufa side Din Dad dinshi ya Ajiye wani write Up din da yayi, Dawowa daki yayi amma Jikinshi Be bashiba dan gabanshi wani Fadi yakeyi Kome ya

"rubuta Ohon mai.... Around 10Am ne Dad din Ismail ya Tashi after yayi wanka ya shirya zai fito daga Room dinshi kenan Yaga wani dan memo a Side Bed dinshi ya dauka ya fara karantawa kamar Haka....
_Dear Dad Please ina rokon Wata Alfarmane Nasan Zaka iyamun, Nasan nayi karami amma Dan Allah Dad Kai Mun Aure yanzu, A auramun Xeey Inasonta inyaso sai inci gaba da karatuna_

Dad Ne Ya kara kura ido Yace WHAT? Ismail ne da wannan rubutun! Pallow ya Nufa ya zauna Akan Kujera sega Mahaifiyar Ismail tazo itama ta zauna, Dad din ismail ne ya mika mata write up din da yayi itama ta karanta gabantane yai wani mugun Fadi tace Aure, He's Just 21years Fa Subhanallah,

"Baban ismail ne yai wani murmushi yace ki barni Dashi Jeki kiramun Shi, "Hajiyace ta tashi ta nufa room dinshi knocking biyu ya bude tana kallonshi Maida kanta gefe tayi Tace Alhaji na kiranka,

"Gabanshine yadan Fadi but wata zuciyan nacewa Yo ai ba karya kayiba kaje kawai kaji, Tafiya kadan segashi a Pallow, Waje ya sama ya Zauna a Kasa ya gaishe da Dad dinshi

"Alhajine Yace Naga Sakonka Amma abun da nakeso dakai Shine ka Daga Kai ka kalleni ka fadamun Da bakinka aure kakeso,

Ismail ya kasa daga kai ya kalla dad dinshi balle ya furta WATA magana ,

"Alhaji yace badakai nake maganaba Nace Ka daga Kai ka kalleni Nan ma shuru seda Yace ya kalleshi sau Uku amma Duk ismail ya Kasa...

Dad ne yai murmushi Yace To baka Isa aureba tunda ka kasa daga kai ka kalleni, Haba Ismail saurin me kkeyi kaifa dayane a gidan nan, Karatu nakeso kayi sosai wanda kasa zasui alfahari dakai Amma Kanaso Ka kawo maganar Aure? Nan Ismail yaji duk wani kunya ta isheshi shima Me yasa yai rubutun Oho..

"Yace I'm Sorry Dad, "DAD yace Sorry for urself inma zaka cire wani maganar aure ma To ka Cire dan By Monday computer school zaka Fara zuwa a *DIALOQUE* idan ka kammala By next year Kuma Kasan waje zakaje Kai karatun doctor ko wani abun. Aure time ne zakayishi ko bakaso.

"Ismail To Kawai yace dan dad ya rusa mai plan but ba yanda zaiyi hakanan ya hakura, "hajiya kam tunda suka fara magana Ko A batace ba dan abun yaron nata ya girmama... Alhajine yace ya tashi ya Tafi dan haka ya mike sumi sumi jiki ba kwari ya nufa daki,

"yana Zuwa fadawa gado yayi Ya fara Imagining yanda rayuwarsa zata kasance ba tare da Xeey Ba...Pillow ya dakko ya fara chusa kansa a ciki yana i love you my xee, my hrt beat... Wata Xuciyan kuma Tana Cewa ka manta da zancen Dad kenan na ba yanzo ze maka aureba

Wani bakin ciki yaji A tare dashi Kawai Yace Nama Hakura da xee nasan baza a bani itaba da wannan tinanin bacci yai gaba dashi...

"Alhaji kam Bayan tashin ismail Hajiya ya kalla yace kinga yaronki ko, yanaso Ki tsufa da wuri wai aure ni dariyama ya bani wallahi.

"Hajiya tace hmm Nasan be wuce zeey zaice yana So dan ita kadai ne Suke Tare, Ni na rasa gane kanshima aure at this early age of him, Alhaji yace kema kya Gani, Allah dai ya tsare mana Zuri'an Mu gaba daya tace Ameen, nan ta kawo mai breakfast, yaci yasha sannan ya tafi office itama ta tashi tai gyare gyaren Ta...
°°°°°°°°°°

Around 2Pm ne Xee sundawo daga school kenan ana droping dinsu a bakin Gate ko gida bata shigaba Gidan su ismail ta shiga, Ta sameshi yana wanke Singlet dinshi da wasu kayanshi, Beji tafiyantaba dan yayi nisa a tinani kawai hannu yagani a cikin bukitin da yake wanki, Yaji tsoro dago kai yayi dan ganin waye, Kawai sukai ido hudu da xee wani murmushi ta sakar mai shima ya maida mata,
tace weldone bari na tayaka,
yace no Karki bata kayanki da ruwa,
"ki barshi yanzuma zan Gaba bazanyi taking time ba kije ki zauna kafin Na Gamaa

Tace tab Bari dai naje gida na cire uniform na dawo yau akwai labari yace Ok sist, Tana tafiya ya bi bayanta da kallo Yace Damn...this girl is Pretty, Seda yaga ta fita a gidan sannan ya duka yaci gaba da Wankinshi shap shap ya gama yai wanka ya shirya,

"xee kuwa tana shiga gida tai wa mum dinta Sannu da gida ta shiga toilet ta watsa ruwa sannan ta dakko kayan da ta sama sawa Gida da wando tasa, Ta dakko abincinta taci tacewa mummy Bari taje gidan Su Frnd ismail, Da mummy kamar zatace kartaje amma seta barta tace to sai kin dawo karki dade tace Ok Mum.....

Tai ficewarta Zata shiga gidan Su ismail kenan segashinan sun hadu a bakin Kofa, tace laaa da fita zakai ko inzo bansamekaba, Yace aa dama wajenki zani najiki shurune tace tom Ganinan....Yace yanzu ina zamu gidanku ko gidan mu, Tace Noo mu Zauna a waje kawai mui hira nan suka sama Waje Suka zauna a kasan wata bishiya suna shan Iska.......

Ummiey Xeey Ce
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & WRITTEN BY```
*Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*😍

*Dedicated To my Yar gatah°°°°🌹 Real Khady*
_Masha Allah for d completion of ur amazing and fabulous novel called *"Suhailat"* the most amazing and sweetest novel ever.​​ Congratulation one again_💋
_​My Love For you is deep and True baby....i Love You with all my and i always will Honey... I Love You so Much... I love you so Much...... I love you So much........._💓💓💓

*📄 PAGE 15____16*

Waje suka samu suna Shan Iska, nan suka fara Hira sosai tsokana tsokana, Soyayya soyayya gashinan dai dan hiransu bame tantance inda suka Dosa...

Xeexee ce tace Kasan meye Yau nayi frnd safiyya a school kai tanada kirki sosai walhi, tasan abun da takeyi. "ismail ne ya wani hada Rai yace frnd bayan Ni? Amma bana hanaki yin kawaba,

"xeey ce tace baka gantaba wlhi kaima da zakaso ace frnd dinkane, Taba baki yayi yace tab akai kasuwa, dan shi ganinshi yakeyi kamar frnd indai ta wuce Xee to Gaskiya se ahankali dan wani irin tsakuwa sukai Sosai,

"Tace Ya naga ka wani bata rai Frnd fa nace ba Saurayiba, kara bata rai yayi yace to ina ruwana da frnd nidai kisan frnds din da zaki dinga kulawa, dan da bakinki ma kina fada ki ba wata frnd da zaki after ni se gashi Ke kinyi, Nan dai suketa abunsu akarshe ma Fada Sukai kowa ya Tafi gida babu dadi a Ransu, gashi duka in suna tare basasan rabuwa amma Hakanan kowa yai xuciya ya tafi Gidansu...........
××××××××××

*AFTER 3 Months*

Hajiya halima ce kwance a daki yau ta tashi batajin dadi ko kadan dan ko Pallow ta kasa fitowa Takai kwana 2 a haka, yaudai abun yayi worst Ne. Alhajine ya Shugo dakinta yaga ko ina ba a gyareba Yasan ba lafiya ne tunda 2days da suka Wuce ba a dakinta yakeba, Rawar sanyi yaga tanayi ya taba jikinta yaji zafi dau, Subhanallah yace tare da fadin Halima meke damunki, Kasa magana tayi dan ba karamin Jin jiki takeyiba, Temaka mata yayi ya dagota Ya kira driver Da sauri ya bude mota aka Sata,

___Jin tadar motar ne Yasa Hajiya Sa'adatu Ta leko ta window dan ganin waye zai fita ko Alhajine ba Sallama, Kawai taga Alhaji na kokarin Sa hajiya halima A mota, Da sauri ta fito tana subhanallah, Meke faruwane, Alhaji yace asibiti zan kaita batada lafiyane zamuje a dubata meke damunta,

Hajiya sa'adatu a xuciyanta tace senaje jin kwakwaf dan haka tacewa Alhaji a jirata Taje ta dakko hijabinta su tafi tare, Yace to ki sauri, dakkowa tayi dan gulma a cikin motan Ta karashe sa hijib din driver kam yaja mota sai Wani babban *Ummiey_Xeey specialist Hospital* Nan aka fara gwadata akace admitting dinta zasui dan akwai wani Blood tests da zasui mata Alhaji yace badamuwa Ko nawane Ai mata, Hajiya halima kwata kwata batasan ma Inda Kanta yakeba,.... Koda su Xee suka dawo gida akace mamanmu batada lfiya Kuka Take tayi Dan har seda dad ya Dawo kenan zai kwasa wasu kaya yaganta ta takure se zabga kuka takeyi Abba kuma yana gefe shima yai tagumi

Dad ne ya karaso Inda suke yai hugging dinsu yace su kwantar da hankalinsu momman Su zata Sama lafiya

Nan ya temaka musu suka Shirya sannan driver ya jasu basu tsaya ko inaba se wani babban shag, nan yai musu siyayya suma na kayan dadi sannan yai wa mamansu siyayya itama then suka wuce specialist hospital
Suna zauna ne time din hajiya Halima ta Dan farfado ta samu taci wani abun tai wa kishiyarta godiya

Alhaji Abdullahi ne yace basu kawo texts din ba be gama rufe bakiba se ga WATA nurse ta Shugo dauke da murmushi ta gaisheshu Tace mika da Alhaji result din tana cewa Congrats

Dubawa yayi yaga matanshi Nada cikin WATA Biyu, Yace Wow..Masha Allah

Halima Ashe cikine dake baki fadamunba har tsahon WATA biyu

Tace haba dai Alhaji wani irin ciki yace gashinan dai ai ba karya zasui ba

Zee CE Dan murna ta kwalla ihu Tace wow Alhamdulillah,

Hajiya Sa'adatu kuwa tsit kake jinta Dan jikinta gaba daya mutuwa yayi

Gabantane yai wani mugun fadi Tace Halima ciki, Ikon Allah Alhaji yace eh wlhi ya mika mata result din ta gani wani bakin ciki taji ya mamaye mata Zuciya ohhhh Allah ta fada

Tofaaaa

*Muje zuwa kuyi hakuri ba yawa*
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & WRITTEN BY```
*Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*😍

*the whole page is dedicated to you Miss_Xarah_Mansur❤ “Thank you for your love that you show me regularly. I love you Sweet Heart*❤

*📄PAGE 17___18*

Alhaji Abdullahi Murna Yakeyi Kamar wannan Karon Ne cikin Fari, Ita ko HajiyA Halima Tana fama da Kanta Hamdala Kawai takeyi a zuciyanta....

Sa'adatu ne fa nan abun duniya ya isheta, Kasa sukuni tayi amma Setaita wayincewa, Tace Dai bari Taje Gida Ta dawo Tayi mantuwan Ruwan Zafi a heater, Alhaji ne yai mata wani Kallo Irin taya zata fito akwai heater a gida ba ya hanasu ko ina zasu Su dinga kashe Komai ba, Tace yi hakuri Alhaji, Ta tashi da wani jikinta duk a sanyaye tai musu Sallama Ta kama hanyar Gida,

Tana cikin Napep ne ta kira aminiyarta Yalwa Tace su hadu a Gida Dan Allah Zata dau mataki, Tace namefa Hajiya, Sa'adatu Tace Sai kinzo Kawai Kawata, Me napep kam se satan kallonta yakeyi ta madubi amma ba halin magana,

********
___ Bayan Tafiyar sa'adatu Ne Alhaji ya kalle matarshi Halima da yaranshi Yaji wani Irin Nishadi kawai yakeji, Nan yaketa godiyawa Allah Daya bashi Yara, Duk tinaninshi daga Abba Bazata kara haihuwaba dan Se After 7years Take haihuwa wannan karon Kam Har Ya Shiga kusan 9 shuru, Ikon Allah kenan dama ko wace haihuwa da yanda take zuwa Maka.....

"halimace tace Alhaji ka kira kanwata Mariam Tijjani Ka sanar mata Da ina Asibiti, Yace ok Yauwa dama ina so indan Fita nan take ya kirata tace Tana ma hanya zata wani wajen ne Amma Gatanan Zuwa, Ba ai 10mins ba segata Ta Shugu, nan ta sama waje ta zauna Tai mata Sannu Sundan taba hira Kadan da yake mutuniyar Alhajine, Sannan Alhaji Ya fita zaije inda zaije,

"Su xee kam makalemai sukai Seda Ya fita shan ice cream Dasu, Nan dai Hajiya halima da kanwarta Suketa Hira dan zuwa yanzu Ta wartsake...

""Hajiya sa'adatune ta rasa meke mata dadi yanzu dai ta zama Juya Kenan ba Haihuwa se yawo takeyi a tsakar Gidan Tama kasa Zama Gaba Daya, knocking Taji Me gadi yaje ya bude Dama Tasan ba kowa bace se Aminiyarta YALWA....Rungume ta Hajiya sa'adatu tayi irin Taji dadin Zuwanta Dinnan, Daki Suka Shige, sa'adatu Ta zauna ta hada kai da gwiwa

Yalwace Tace Meke faruwane Ki natsu ki fadamun Yar uwa ko zan temaka Miki, Hajiya sa'adatu ta dago jajayen idanuwanta Tace yar uwa dole ki temakamUn, mamansu Xeexee Fa tana asibiti wai Cikin wata Biyu,

"Hajiya yalwa Ta wani zare ido tace Ci me?? Sa'adatu tace Yanda kikaji Ciki gareta Har na tsawon Wata biyu Anan Gidan...

Yalwa Tace Tabdijam Lallekam Bazaki Zaunaba, Yanzu Meye Shawara, Tsakaninta dake kafin tazo nan Gidan Shekara 10, yanzu Da auranta Kusan 17kenan Fa 27years Kenan kinanan Godan baki ajiye Komai Ba, gaskiya dolene musan matakin da zamu dauka da gaggawa Inba hakaba ai na shiga Uku Inji sa'adatu kenan,

"Yalwa ma Tace har tarama sai kin shiga tunda yanzu yana mutuwa yan uwanshi da yayanshi zasufiki gado, _subhanallah_

"Hajiya sa'adatu Tace tun muna england Nayi shawaran Zan amsa Xee amma yanzune Right time din daya kamata Na amsheta Inyaso......seta matso kusa da kunnanta Ta fada mata wani zance.... Tafawa sukayi Yalwa tace Aikinki nakyau yar uwa yanzu ki sakar musu komai ki nuna irin Bakyajin haushinsu inyaso..........

_Nasan readers kun kosa kuji me wa innan matan biyu suke Shiryawa Karku damu inanan daku, kuci gaba da biyoni zakuji komai Har End..love you All_

Nan suka wani kwashe da dariya, Sa'adatu tace kiyi hakuri ko ruwa ban kawo mikiba, Yalwa tace haba Ba komai Nan gaba idan komai ya kankama Ba ruwa Ma kadai zaki kawomun ba har wani abu me kala na roba....,

Sa'adatu tace sai yasa nake Sonki yanzu to Ki tashi muje mu gaisheta nan suka shirya Suna fitowa suka sama napep se *ummieyxeey specialist Hospital* Room din suka Shiga suka sametama tana bacci se sistern ta Mariam tijjani tana daddanna wayarta da alama Chat takeyi a group din taurarin Mata,

gaishesu Tayi Suka tambaya yame Jiki tace da Sauki Alhamdulilah, Sukace Allah kara sauki Tace ameen; taci gaba da chat dinta abunta.......

********

Bangeren Ismail Kuwa Yau wuni chur bega Beloved Xeexee Dinshi Ba ya kasa zama ko abinci ya Kasa chi da yaji Moto ya wuce seya leko gate ko su xeexee Ne, Yayi hakan Kusan 7 na karshene yace bazai koma Ko inaba Dan haka Yai Lamo A gado ya fara tinaninta chan ya hango wani cardboard Paper ya tashi ya dakko hade da wani dan table yazo ya zauna a bakin Gado ya ajiye Cardboard din Kan table dinnan Ya dakko pencil ya fara zana Xeexee (Drawing) Beyi Taking Time ba ya Gama Drawing ne Amma Tayi kyau sosai kyanta ya fito dan har wani smiling Yasa Drawing din yakeyi, Dauka yayi ya kwantar dashi a chest dinshi Kawai wani nishadi Yakeji Daya kalla Drawing din Se shima Yai murmushi Yace I love You my xeexeeeeeeeeee!!

Karar moto Yaji.......

*Kuci gaba da kasancewa Dani*

TEAM XEEXEE
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & WRITTEN BY```
*Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*😍

_Dedicated this page to you my beloved frnds..I love you so much_
Hummyluv
Armeenat
Ameemee
Fresh khady..

*📄PAGE 19___20*

Karar Moto yaji ya ayyana a ranshi Yace nasan ma basu bane ba Inda Zanje, Yaci gaba da Kallon Drawing din da Yayi,

"Su Xee Dad na droping dinsu, Usman yayi Gida Ita kuma dama Throughout itama tayi missing frnd dinta dan Haka gidan su ismail Ta Shige, Mum dinshi ta samu a Tsakar gida ta gaisheta sannan ta nufa Room Din Ismail Din, Shiga tayi bemasan da mutun Ba se Hugging din Drawing din Da yayi yakeyi, Ita ko Xee tsayawa tayi tana Ganin Ikon Allah, Kusan 10mins tayi bemasan Tana wajen Ba,

"Takawa tayi ahankali Ta isa wajen Bed Din ta fara Zaro cardboard din da ya rungume Kamar daga sama yaji ana Zare a abu a jikinshi, batakai Ga zarewa ba, firgita Yayi Hade da juyuwa yaga Waye Zee ya Gani a Tsaye;

Tace Sannu Da Aiki, Ya wayince yace Uhm Tun yaushe kike nan Tace 10min ago, Murmushi yayi yace Myxeexee. Tace To muga Meye ka Zana ni ka hanani gani ma,

Yace no bana hana ki bane itace farin cikina Kuma Zan faranta mata rai banaso wani abu ya dameta infact bazaki ganiba dan Sirrinace, Tace Ohh Ashema sirrinkane nima zan fara boyema Nawa kenan,
Yace Eh Naji,
Tace Toh madallah,
Tana magana Tana shirin hawa Gadon...

Ismail ne yace kar ki hau, Itakam xee inama ta saurareshi Tuni ta haye Gadon Ta janyo pillow ta kwanta Tace Huh gaskiya na gaji bari nadan huta Anan,

"ismail ne Ya zare ido yace lalle you're Serious Kinga Zo Ki fitan mun a daki tundake Bakyajin Magana, Ko kallonshi batai Ba, Ya sake magana, Tace haaa Waikai ina ruwanka danine, Ba dama nazo kusa dakai sekaita Wani dan karamin wa'azi to yau ba Inda Zani,

"ismail ne Yace ba wani karamin wa'azi Gaskiyace ke kin taba ma ganin Inda Mace da namiji suke kebance ba tare da shaidan ya shiga tsakaninsu Ba, Kee zeee ina baki cronic warning akan cewa Ki dena shigan mun daki Anyhow Ko.

"Tace Shaidan fa Kace To ina Ruwana Ta janyo bargo ta rufa Ya rasa ya Zaiyi Da Ita Dan kome Ze ce mata ba fita Zatai Ba, Shima hayewa Gadon yayi Yace Nasan me Kike Bukata, Zaki gane ne Yau kuma kikaimun Ihu Zaki Sani, Yana shirin.......... Da gudu ta Sauka Tana maida numfashi Ya zo kusa da Ita Yace Shiiiiii kar ki sake kiyi magana, Nan danan Ya chanza Face kamar Ba shiba

********** 2DAYS su Hajiya Halima sukai Aka sallamosu daga Asibiti, Nan fa Hajiya sa'adatu bakuga kirkiba Kamar Me, kusan aikin gidan rabi duk ita takeyi, Shima Alhaji ba karamin Farin Ciki yayi Ba da yaga Matar Tashi tadan sauya, dan da dane Setayi mai Magana akan tunda bata haihuwa ya ajiye mata dubu dari biyu ko uku, haka suke zama duka hankalin Kowa a kwance.

*One Week*
da dawowar su daga Asibiti time din Hajiya halima Taji Sauki sosai, Alhaji Abdullahi Ya dauketa sukaje Kasuwa siyayyan Kayan Baby, Hajiya sa'adatu Harda Rakiya bakin gate, tana ganin sun Tafi Tace ina Su xee da Abba, Sukace gasunan, Tace yauwa yarana ku zauna anan banda yawo kunji Xee tai smiling tace ok hajiya, Ta kunna musu TV ta kawo musu fruits Suna sha suna kallo sunji dadi Kam sosai, Ita ko ta Shiga Daki ta kulle Ta kira Wani mutum Bansan nima me suka ceba Naji Tana Cewa Very Soon ne Ai...Nan dai sukai Sallama...

"Xee kam Kura mai Ido tayi dan yau Ya kusan bata Mamaki, Tace ismail dama Dan Iskane. Bazan kara shigar Mai Dakiba da yau, Seda yaga Nunfashinta Ya dawo Normal Ya bude mata kofa Yace Maza Ki fita. Tana Fita In banda Innalillahi da takeyi a zuciya ba abun da takeyi seyau ta fara Tsoron Ismail,

"shikam tana fita wani Dariya Ya sake Yace kaji mun yarinya Zatazo Ta batani, Irin matan nan hmm Ba wuya sunsa ka karya alkawarin da kayi yace Allah ya kyauta, Cardboard ya dakko ya kalleta Ya kara Wani Murmushi Sosai

Ita Kuwa Mum Din Ismail tun da taga Xee ta shiga dakin hankalinta ba a kwanceba Dan Tsoro takeyi kar Danta Ya janyo mata abun magana Balle Kuma Yace ai mai aure...Mum ce ta fito ta nufa Dakin Ta kwankwasa Yaqi budewa, Ta kara still shuru, Shi Duk daukanshi Xeee ce sai yasa beda muba, Mum ce ta banko kufan idonta ciki ciki tana tsoron abun da zata Gani, Ismail ta gani a zaune hankalinshi kwance, sannan itama hankalinta yadan kwanta, Tace Ina Xeey yace kai Ai tana shugowa bata dde ta fitaba sannan hankalin mum ya kwanta Tace My Son yace Na'am mum Se kuma ta fasa maganar da zatai,

fita Tayi taje tai alwala ta Kara neman wa danta Shiriya da dukkanin musulmai, Allah ya kara tsare mana Imani ya hanemu da Aikin dana Sani......

**********

Ummiey_Xeey
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR​*
*UBA​*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```​​​STORY & WRITTEN BY​​​```
*​Ummiey_Xeey Abakson​💋*

*​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

LIKES AND DROP YOUR COMMENT👇🏼👇🏼👇🏼👇🏼
#https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/
👆🏼👆🏼👆🏼👆🏼
*HAKA ZALIKA NAN ZAKA SHIGA DOMIN SAMUN LITTATTAFANMU*

*​OCTOBER 2017​*
~​SHORT STORY​~

```​​​SADAUKARWA GA____​​​```
*​MARIAM TIJJANI ADAM​😍*

_QUOTE: ​In the end you will see who’s fake, who’s true and who would risk it all for you. And trust me, some people will totally surprise you!​_

*📄PAGE 21___22​*

Haka Dai rayuwarsu ta kasance cikin jin dadi da kaunar Juna, akwai wata Rana family din Alhaji Abdullahi suna zauna Kan dining table, Yace To Alhamdulillah, Insha Allah Wannan karon Dukanmu Zamu Umrah Harda Su Zeee, xee ce ta kwalla wani irin Ihu dadi taje tai hugging dad dinta dama Already ya mata alkawari Time kawai ake Jira yau Gashi Zasuje,

Abba ma kaninta Shima murna Sosai Yayi su Hajiyas kuma in banda smiling ba abun da Sukeyi, Hajiya Halima ce tace Aww Harda Yaran To Masha Allah, Allah ya kara budi Alhaji Yace Ameen maman Baby.

"Hajiya Sa'adatu kam taji haushi amma ba yanda zatai Seta boye nan itama tamai godiya Yace ba Komai Zuwa Nan da kwana uku zasu tafi;

Sukace Allah ya kaimu su xee Kam Murna sukeyi tayi,

Tun Rannan Raban da Xee tasa Ismail a Ido shima Haka, Gashi tanaso taje Ta Fadamai Zasu tafi umrah amma tana Tsoro ta kira abba tace yazo ta aikeshi, Tacemai yaje yacema Ismail Tana gaisheshi, Intamai abune ya yafe mata Zuwa gata Zasu tafi umrah,

"Abba yace to ya kama hanya Ya Tafi gidan ya sameshi ma da mum dinshi a Pallow suna kallon wani Movie ya shiga da natsuwa ya fara gaishe da Mum sannan ya gaida ismail Yake sanar dashi Sakon da Xeexee ta Bashi,

"Yace wow Masha Allah zo muje, Suka nufa Dakinshi Yadan rubuta short note kamar Haka... ​Congrats My dear i'm happy for you ALLAH yakaiku lafiya ya dawo daku lfiy aimun tsaraba irin sosai dinnan ki cika Jaka, Bazakizo bane inganki kafin ku tafi i'm missing you fa​

Ya mik'a Mai abba yayo gida ya bata Sakonta, Tana fara budewa wani kamshi taji Ta tsaya kallon rubutun dan ya iya hand writing, Fara karantawa tayi a natse harta Gama sannan itama Tai mai reply kamar Haka ​peace be upon to you,....I'm missing you more and More, Karka damu indai tsarabane seka Ture, But nifa yanzu bazan iya zuwaba Tsoronka Nakeji tun ranan nan, byeee​

ta ce Bro gashi ka kai mai please, Dama yana bakin gate yasan comfirm zata aikoshi dan haka, Abba na fita zai shiga gidan suka Hadu dashi, ya mika Mai ya karanta wani murmushi Yayi yace ok Muje ka kiramun Ita kar mu dameka da Aike ko Little bro

Abba Dariya yayi yace anty Xeey din yaya Ismail.....ismail yace kai, Kama hannunshi yayi sukai wajen gidan su, abbane ya shiga ya cewa xee ishmail dinta na kiranta,

wani dadi taji sosai dan dama abun da take expecting kenan, Hijab dinta ta dakko ta saka har kasa, tai kyau sosai abunka ga Farar mace....tazo ta sameshi a wajen ta gaisheshi yaqi amsawa, shi just ma ya shafa'a da kallonta dan 2days dinnan da sukai ji yake kamar Ankai month, magana na farko dayai mata shine You look so gorgeous my dear,
"tace uhmm, nan dai suka sama wajen da suka saba zama under tree suka, hira sukai sosai har yake tambayanta meyasa bata kara zuwa ba, Tace hmm kafi kuwa sani dama ya Ismail kai dan iskane da raping dina zakai,

"Ismail dukar dakai yayi wasu hawaye suke zubamai a ido, yace look xee wlhi tunda nake ban taba iskanci ba, Allah yagani nayi hakane dan ki natsu ki shiryu, ke look at you, shigan nan da kikai saboda nine na sani badan na miki hakaba da yanzu dagake se Wani riga da wando ko siket se dan karamin gyale, ya kara da cewa ba ko wani namiji zaki dinga shigamai Daki hakaba ba tare da yayi wani abu dake ba, ko hannu ya rike maki idan yaje gaba zai kara yace yayi kaza, babban dalilin da yasa kenan banaso ki saba da mu'amala da maza, sbd they are very dangerous, Kinga tafiya zaki ki yafemun tunda haka kika daukeni, Nagode ba laifinki bane Bye......

"Tun da ya fara magana xee shuru tayi dan tabbas maganar da ya fada gaskiyane, mikewa yayi yabarta a wajen ya fara tafiya kenan ta janyo riganshi ta baya tana cewa i'm sorry My love i don't mean to hurt you please come back to me I love you, Tsayawa chak yayi ya juyo yace kar ki sake tabani nagode Xee ya cigaba da tafiya,

"XEE Durkusawa tayi tana kuka ko juyowa beyiba dan shima hawayen yakeyi...Gida ya wuce yana shiga ya wanke fuskarshi ya zauna bakin gado yana tinanin maganar wato shine dan Iska, Wata xuciyan tace karka damu tunda ba haka kakeba..... Xee kam kuka tai taga be bawoba tasan ta batamai rai sosai dan Haka ta tashi ta nufa gidansu daki ta shige ta kwanta nandanan kanta ya fara ciwo zai zazzabi dan har rawar sanyi takeyi,

hajiya sa'adatu tazo zata shiga Kitchen taji kamar Ana kuka ta leka dakin Xee taganta kudundune a bargo se rawar sanyi takeyi, subhannallah Tace Ta shiga dakin Ta taba jikinta Taji Zafi sosai, Nan danan ta kira driver Yazo takaita asibiti dan Hajiya halima Laulayi yasa duk bata wani abubuwa Sosai,

Asibiti sukaje aka dubata akace Zazzabine, Allurai Akai mata then suka bata magunguna

Ummiey_Xeey
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*​A DALILIN MATAR​*
*UBA​*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```​​​STORY & WRITTEN BY​​​```
*​Ummiey_Xeey Abakson​💋*

*​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*LIKES AND DROP YOUR COMMENT👇🏼👇🏼👇🏼👇🏼*
#https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/
👆🏼👆🏼👆🏼👆🏼
*HAKA ZALIKA NAN ZAKU SHIGA DOMIN SAMUN LITTATTAFANMU*

*OCTOBER 2017​*
~​SHORT STORY​~

```​​​SADAUKARWA GA____​​​```
*​MARIAM TIJJANI ADAM​😍*

​Dedicated this wonderful Page to you my abokan aiki, zama daku Akwai sweet irin sosai dinnan​ *​Nabilancy, Jameelah k Mashi, Maman Ussy And mmn khairat*

​📄PAGE 23___24​

Sundawo daga asibitin ne Mummy Tai mata godiya akan hidiman da Takey, Hajiya sa'adatu Tace ah Ai ba komai Nima yatace ko? Zee dai ita kam Gyada kai tayi amma Zuciyanta nachan tinanin Ya Ismail Dinta,

Around 8PM ne Dad ya dawo Yaji xee shuru yasan ba lafiya kiranta yayi amma Dakyar Ta iya zuwa dan wani irin ciwon Kai da ke addabarta, Zuwa tayi ta sameshi Ta gaishe dashi nan ya lallasheta Taci abinci Tasha magani, Suna Zaune a Pallow ne Hajiya sa'adatu tace dan Allah Ina neman Alfarma,

"Alhaji Abdullahi yace ok ina jinki, Tace dama maganar Zainab Ce Ina so Abani ita halak malak inba damuwa, tun kan Alhaji yayi magana Hajiya Halima dake kwance kan 3seater Tai murmushi Tace Haba Yaya Sa'adatu Indai Zainab ce an baki Ita, Jin dadin Maganar ne Alhaji besan Sanda ya zunduma wa Halima Albarka ba dan Komai tana yinshi cikin tsari da Hankali...... ​Lolz Masu suna xee se a tattaro kaya azo dakin Hajiya Sa'adatu muga wani Wainar za a toya​

kwanan Xee daya taji sauki Nan fa aka fara shirye shiryen Zuwa Umrah...ana Gobe zasu Tafi Dukda Xee da ismail Sunyi Fada Be hana Ta shiga Gidan yimai Sallama ba, har gate ya rakota bame cewa kowa komai tace Toh nidai Bye sai mun dawo. Binta da kallo yayi dan yasan He will surely Miss Herrrrrrr....
*******
​M​isalin Karfe 4 na Yamma Suka isa kasa me tsarki, Nan fa bakuga murna Wajen su xeey ba ​Allah ka bamu Ikon Zuwa Kasa me tsarki.....Ameen​

Dad ne yace suzo suje ya shiga dasu Wajaje sai kallo Abba yakeyi banda xee da gaba daya hankalinta baya wajenta Tana chan se tinanin Ismail takeyi dan imagining take yanda rayuwarta zata kasance na Two_weeks dinnan without Him,

"Alhajine ya lura da ita yace My baby Xee Ko dai jikin nakine, naga bakya walwala, kai kawai ta daga Alamun Eh yace sannu ko mamana tace yauwa abbana.....

"Bangeren Ismail Kuwa Duk dauriyanshi seda yai kuka, Dan betaba tsammanin Rana daya bazaiga Xee ba se gashi yau Wai ba ita gashi ba gobe zai gantaba ba jibi ba sai wata rana kawai dan idan ta dad dinsune zai iya cewa daga Makkah su tafi Wani kasar hutu tunda dama hutun school akeyi, kuka yaci sosai sannan Ya dakko Wani Diary Ya fara rubuce rubucen shi, amma kuma idan ya tino da furucin da ta mai na dama shi dan iskane sai yace mtsww gwandama da Mukai Nisa da ita but deep into his heart yayi missing dinta irin sosai dinnan...

​Kamar yanda nai missing my *emnoor Ahmerd..my Twin Sis​ Lolx*

Haka dai Itama Xee kullun tinani dan har rama tayi amma bataso Asan Saboda Ismail ne amma ina duk wayonmu iyayenmu kallon mu kawai sukeyi Hajiya halima mamanta ta gane duk Rashin Ismail ne ya maidata haka sedai Kawai tai ta mata Addua Allah yai mana zabi mafi alherine Shine Kawai...

Satinsu Biyu chur Suka dawo xee ba karamin tsaraba Tai wa Dan uwanta Ismail ba, Shima yanajin labarin sun dawo yajishi kamar an ciremai kaya a jiki dan har wani nishadi yakeji atleast zega pretty Frnd dinshi, XEE ma Da suka dawo Gaskiya tajita confortable dan tasan Itama zata Ganshi, Ta so ta ganshi suna dawowa amma ba yanda zatai dole se washe gari dan dare yayi kuma dad yace ta bari ma kawai se Gobe, Dan haka da sassafe Ta tashi tai abun da zatai Ta gyara ko Ina, sannan tai wanka tasa kaya tai kyau sosai cos yanzu gaskiya ta kara girma masha Allah..

___Riga da siket tasa ta dakko hijab dinta har kasa tai kyau sosai sosai, sannan ta fito, Wani yarone a neighbours dinsu ya fito dan haka ta sama damar ai kenshi gidan su ismail akan yaje ya kirashi, Yaron na shiga yace ana kiran ismail a waje, yace to kace ganinan, ya fito ya sanar da ita tace tagode, ismail kam ya shirya dan sunyi da wani frnd dinshi zasuje wani waje yana shama Shine, fitowar da zaiyi kawai yaga Xeexee,

"""wani farin ciki yaji aranshi amma yadan Fuske yace ur welcome ma, Da fatan kundawo lafiya ya baki shugo cikiba, Xeexeee tace uhm Ba komai ai mun girma yanzu,

"ismail yai dariya yace hajiya xee rigima but anyway masha Allah tunda kin girma, Allah ya kara girma da daukaka ranki ya dade,

Xee ma dariya tayi tace bansan iyaye fa, hope kana lfiya ya missing dina, Yace lolz kedai zan tambaya ya missing dina

Tace uhm aikam Munsha missing, Mum na cikine yace yeah tace alright mu shiga na gaidata, Yace ok, yana tafe tana binshi a baya har suka isa pallon ta shiga ta gaisheta, Mum ismail Tace Ki gaida hajiyarki inanan Shugowa,

Xeexee tace ok zataji tai fitowarta, waje suka koma da ismail nan dai sukai hira a tsartsaye Har ta Nuna mai New phone din da dad dinta ya Siyo mata, Congrats Yai Mata ya amsa phone din yasa numbernshi Yace da wani Suna zanyi saving Tace Kasa da ​Sweet special​ nan take yai mata flashing Numbern shi yai appearing a screen din itama tai saving da ​Sweet special​

"Tace ok zan tafi Gida Yace tun yanzu Tace eh wlhi; nan sukai sallama... Har ta shiga gidan shi yana tsaye yana cewa ikon Allah Xee tayi hankali sosai da dane seta shugo. Yace masha Allah....

Tana shiga ta tino tsarabar da ta kawomai Dialing numbernshi tayi tace Kananan ko ka fitane yace yananan, nan ta dakko kayan niki nike tana kawo mai tace gashinan tsarabanka,

Kasama magana yayi dan murna dan son da xee kemai ya wuce misali, godiya yai mata sosai tace no ba haka atsakaninsu, ya dauka kayan ya nunawa mamanshi tace Allah sarki yar albarka, Allah dai ya saka da alheri Yace ameen.

Daki ya shige yai mata text kamar haka ​Naga kaya ina mai kara godiya Allah ya hadaki da mafificin Alheri ya baki miji nagari, thanks Once again my pretty​

tana karantawa ta turo da reply tace Never mind My Sweet #ANA TARE...

Ummiey_Xeey
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & WRITTEN BY```
*Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*LIKES AND DROP YOUR COMMENT*
FB... #https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*😍

*WANNAN SHAFIN NAKINE MY DEAR UMMY KHADIJA..DEENAR HAMMA*
_May your memories today be awesome, your dreams become a reality, your joy last forever. Have a wonderful birthday._🎂🎂🎂🎂

*📄 PAGE 25___26*

Haka Rayuwar su ta Kasance cikin Jin dadi da walwala, ALHAJI abdullahi Ya kara gyara gidanshi kamar Ba shiba, Anyi painting ko ina idan ka gani idan baka saniba Zakace sabon Gida ne, Duk Saboda HALIMA ya Gyara Dan Next month ne watan haihuwarta...

"Alhaji Abdullahi Yasai komai na haihuwa hatta kayan da Maijego zata ran suna Ya siya, Su Zee kam ba a magana dan kaya ya sai musu bama a nan Ba, na Gani na fada kowa jiran Ranar nan Yakeyi, Akwana a atashi asarar mai Rai, YAU hajiya Halima Ta tashi da Wani Ciwon ciki da Baya da alamun nakuda Takeyi, Kwallawa Hajiya sa'adatu kira Tayi akan tazo ta temaketa, Hajiya na zuwa taganta cikin halin naguda

"Hajiya sa'adatu dariyan mugunta tayi ahaha, wani far da ido tayi tace Yauwa Yaranki basanan sun tafi school. Alhaji ma bayanan inaso in fada miki cewa Halima kashinki ya bushe, Yauce ranar da zaki numfashi na karshe,
Yauce ranar da na tanada ban taba fadawa kowa sirrin nan ba, Ahahah.

Hajiya halima Kuka ta fara, ga zafin nakuda ga Maganganun da kishiyarta Taji tana fadi anya hankalinta Daya kuwa? Hajiya halima da karfin hali tace yaya bangane me kike nufiba da Yau zanyi nunfashi na karshe, Dan Allah ki kaini asibiti,

"Sa'adatu tace tabdijam ba inda zan kaiki barima ki Gani, Nan take ta Kira aminiyarta Hajiya Yalwa take sanar da ita, tai maza tazo gidanta Yau abun da Suka dade suna shiryawa ya tabbata Hajiya halima na nakuda,

"Yalwa wata shewa tayi tace kai naji Dadi ganinan zuwa, ba Ai minti Biyar ba se gatan Tazo, Sa'adatu bude mata gate tayi dan dama tuni ta aike masu aikin Gidan dukansu ba kowa se ita kadai a gidan, Hajiya halima kam kuka takeyi dan ta gane manufarsu kasheta sukeyi suyi _subhanallah_

Nakuda yazo gadan gadan Amma Cikin ikon Allah Yaro yaki fitowa, da sukaga Time na tashin Su Xeey ya kusa Nan suka danneta, tun tana numfashi har ya fara slow...

Halima Kam ba abun da takeyi Se addua da Allah ya tsare mata yaranta bayan Ranta, inama zata Gansu, se hawaye take tayi tana ayyana wa A zuciya Shikkenan Nata Ya Kara *A DALILIN MATAR UBAN* Yaranta Gashinan yau Zatabar duniya, Subhanallah,

Nan dai suka matseta da karfi rai yai halinsa, *INNALILLAHI WA INNA ILAIHI RAJIUN* se da sukaga bata numfashi ta mutu sannan suka Kyaleta,

_Readers kuyi hakuri nasa hAlima ta mutu nov din zaifi da dine haka, tnx kuci gaba da biyoni_

dan kar asirinsu ya tono ne, Sa'adatu ta fita makwabta tana kuka Tana sanar dasu cewa Halima ta rasu wajen Haihuwa, Ismail kam yanaji ba wanda ya tausayawa sai Xee, kan kace meye har an taru a kofar gidan,

"Sa'adatu ta dauka waya ta kira Alhaji Abdullahi mijinsu take sanar da shi cewa Halima ta rasu wajen haihuwa seta fashe da kukan munafunci,

"Alhaji ABDULLAHI meeting sukeyi nan take ya fadi yana Fadin Innalillahi wa inna ilaihi Rajiun, Matata Ta Rasu, nan fa abokanshi sukeyo kanshi se bashi baki sukeyi Akan yayi hakuri kowa be wuce ranarsa, dakyar dai ya tashi sukayi zuga Se gidan Mutuwan,

"kowa ya zauna jigum jigum an shiga mata wanka kenan, Sega driver ya Sauke su Zainab suna ganin mutane jikinsu yai sanyi duk daukansu mamansuce ta haihu dan ya Rasu,

Xee na shiga mummy ta fara kira subhanallah taji kowa yai shuru ismail kam na hangota duk yaji wani tausayi ya kamashi, yanzu wazai ce mata Mamantane ta Rasu, "Anga ma mata sutura Wasu dan dattijai suka fito sukace ina Yaranta su shugo sui mata addua, Zee najin haka tace innalillahi wa inna ilaihi rajiun, mummy has gone kenan Hawaye ya cika a idonta dan tsabar Kunci ta rasa mema Zatai tana tunkarar dakin taga Gawan mummy nan take ta fadi sumammiya ansa mata ruwa dan ta farfado ina...

__Da sauri Dad yace akaita asibiti....Allah sarki mutuwa me raba soyayya.... _Allah yaji kan dukkanin Musulman duniya wanda suka rigamu gidan Gskiya tun daga zamanin annabi adam Har izuwa yanzu, Mu kuma intamo tazo Allah yasa mu cika dakyau da imani....Ameen_

*NASIHA* _please mu gyara haleyanmu dan Allah badan Kowa ba, walhi mutuwa akwai daukan Hankali, bamusan yaushe zamu mutuba, kuma mutuwa bata da tabbas ko yaushe tazo daukanka Zatayi, idan ka mutu shikkenan sedai Masu sonka ne kadai zasu dinga maka addua dan Haka mu yawaita aikin lada da sadaka_

Ummiey_xeey
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & WRITTEN BY```
*Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*LIKES AND DROP YOUR COMMENTS*
FB.. https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Forum-E-W-F-1922297541423276/

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*😍

🎂 *hip hip hip hurry* 🎂
_Your birthday only comes once a year, so make sure this is the most memorable one ever and have a colourful day._
*H.B.D BABY XAHRAH*💘

*📄PAGE 27___28*

Bayan An dawo daga kaitane, Kowa ya zauna abun tausayi ballema *Abba* Daddy janyoshi yayi yana sharemai hawaye yana cewa addua zakai mata ba kuka ba kaji dan baba, Abba yace ok

"Hajiya sa'adatu Kuwa se amsan gaisuwar takeyi amma kwata kwata gabanta in banda dukan uku uku da yakeyi ba abun da yakeyi, Dan wannan ne 1st term din da tabayin kisa *Aishan Umma* _Tace ya subhanallah, meya kaiki, kema barin duniyan zaki wata rana, ya Allah ka cika mana xuciyoyinmu da imani... *Meelat Ahk* tace ameen_

"Bangeren Xeeyxeey Kuwa Tun time din da aka kaita asibiti bata farfado ba, *Mariam Tijjani* da ismail ke jinyarta, "Mariam tijjani tace Hmm Allah yajikan ki da rahama ke kuma xeey ya Allah ya baki Lafiya, Ismail Yace Ameen,

"mariam tijjani dai tana taso ta fadamai magana amma setai shuru, chan dai da maganar ta ciyota tace Ismail wallahi ni jikina yana Bani Haj Sa'adatu da Kashe Anty Halima, Dan rannan da sukazo da wata kawarta naga take takensu

"Ismail yace ohh Dear please kiyi shuru, inma itace zataje inda taje, kuma kinga yanzu idan mukace zamui bincike bamu da cikakkiyar hujja, please let Us keep this secret between me and You.... Indai da rai da lafiya wata rana gskiya Zatai halinta,

"mariam tijjani smile tayi tace tabbas kanada gaskiya ismail nagode yace ba komai Muna Tare Allah dai yajikan mumy, yace Ameen, Yace bari Yaje Yai sallah tace okay....

Bayan fitan ismail ne xeey ta dan motsa hade da fadin Innalillahi wa inna ilaihi Rajiun... Tuni mariam Tijjani tayo kanta, xeey hannunta ta rike Gam amma idonta a rufe Tana cewa Ina mummy, ina mummy yayi daidai da shuguwar Ismail, da sauri ya karaso yana sannu Sweet special,

"Xeey kam kara cewa tayi ina mummy, Dukansu idonsu cikowa yayi da hawaye Ismail yace XEEY sedai muyi hakuri Mummy ta rigamu gidan Gaskiya....Innalillahi ta kara fadawa daganan bata kara cewa komai ba,

"ismail ne yace Ya Salam Rayuwa kenan nan dai na barsu se dan tinani da hirar mutuwa sukeyi....

""Su dad kuma bazai iya xuwa ba dan cikar mutanan dake wajen, Wani kanin dad ne zaizo gaishe da Xeey din ya hadoshi da Abba yazo yaga yar uwarshi... Su abba suna zuwa yaga xeey akwance Da gudu yaje wajenta ya kwanta a kusa da ita ya fara Kuka, Jin kuka me tsananine ya farkar da xeey, firgigit ta tashi taga bro dinta nan ta rumgumeshi Suka fara kuka me tsuma Xuciya,

KANIN dad tausayine ya kamashi, Ismail Kam saboda tausayi irin nashi kasa jurewa yayi fita yayi ya sama wani waje kuka yai sosai, mariam tijjani da kanin dad kam hakuri suke ta Basu har yar nasihohi da wa'azi yai musu sannan suka dan rage Damuwa, yace kuma ba kuka zasu tsayawa mahaifiyarsu ba Yanzu ma take da bukatar addua Sosai,

Xeey tace ta dena kuka insha Allah yace yauwa my daughter.

__2days tayi a asibiti suka dawo gida. Sa'adatu kam saboda tsoro da fargaba kasa kallon Xee tayi dan Tana ganin kamar zata gane ita ta kashe mahaifiyarsu... Hahah Ashema kina tsoro

BAYAN TA DAWONE, taje tai wa mahaifinta gaisuwa dan tun ranar basa haduba, Yace yagode Allah ya gafarta mata, nan ya raftahuwa yayanshi adduo'i Sosai....

3days After rasuwan kowa yai gidanshi dan ba zaman sadakar 7 za ai ba sedai ai addua a masallaci, bayan kowa ya waste ne aka rarraba gado, Nan Alhaji Abdullahi
Yace wa sa'adatu Ga yaranshi nan ya bata amana, Beso wani abu ya tabasu, kuma kome suke bukata Tai musu

"Hajiya sa'adatu Tai kasa kasa da murya alamun mara gaskiya tace Alhaji indan wannan ne karka sama damuwa, ai yaranane, Nan kuma ta barke da kukan munafunci, Tana cewa Allah yajikan Hajiya halima, Alhaji yace ameen, Ikon Allah xee da Abba sukai dauriya, Dad ma Haka hakuri ya bata yace duk kukan nan bafa shi bane, Addua Zamui mata, Tace hakane:......

Nan ta rungumo su Xeey

*kuci gaba da kasancewa Dani taku a kullun*

*Ummiey Xeey Ce*
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & WRITTEN BY```
*Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*LIKES AND DROP YOUR COMMENTS*
F B... #https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Forum-E-W-F-1922297541423276/

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*😍

*Dedicated to All MASOYAN ADALILIN MATAR UBA*❤

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.