A Sanadin Son Ki Complete Hausa Novel
Reading file: A_Sanadin_Son_Ki_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 36 of 67
*PAGE 67-68*
Wata sassanyar ajiyar zuciya Sabeer ya sauke a lokacin da driven taxi yayi parking a k'ofar get d'in D'AN FILLO FAMILY kallon gidan yake tamkar yau ya fara sanin shi, fitowa yayi daga cikin motar tare da rataya jakar laptop d'in shi a kafad'a sannan ya kalli d'an taxi yace
"Malam nawa ne kud'in ka? "
D'an taxi murmishi yayi kafin yace
"Yalla6ai ai wanda ya rako ka d'in nan ya biya ni kud'ina "
D'an zaro ido kad'an Sabeer yayi tare da cewa
"Da gaske ne maganar ka"
"Kwarai kuwa ya bani"
Cikim tabbatar wa driven taxi d'in ya fad'a, gid'a kai Sabeer yayi cikin zuciyar shi kuwa wani son Suhaima da Yayan ta ne ya Kara ji sun shiga zuciyar shi gaskiya Aliyu yana karamci, amman duk da haka sai da Sabeer ya k'arasa d'an taxi d'in kud'i.
Nan yayi ta godiya tamkar bakin shi ya tsinke saboda godiya yasan yau koda gida ya koma zai samu abin ciyar da iyalan shi na kwana biyu daga k'arshe yaja motar yayi gaba.
Knocking d'in k'ofar gate yayi nan gateman ya bud'e, duk da ramar da bak'in da Sabeer yayi hakan bai hana shi gane d'an lelen family d'in D'an fillo ba ne ya dawo, washe baki yayi tare da bud'e k'ofar yana yiwa Sabeer sannu da zuwa, da D'an murmishi akan face nashi ya amsa mishi kafin ya wuce zuwa part d'in su.
Yana shiga part d'in ya tarar Mumy bata nan haka ma Daddy don haka kawai ya wuce bedroom nashi, bude shi yayi ya tarar da ko'ina tsaf sai kamshin air freshener yake tamkar yana gidan, sai duhun da d'akin ya d'an yi sannan yayi zafi don haka k'arasa wa yayi ya kunna ac da fanka tare da kunna light d'in d'akin, ajiye jakar yayi saman sofa sannan ya hau cire kayan jikin shi.
Yana gama cirewa toilet ya fad'a ya jima yana wanke jikin shi sosai a bathroom sannan ya d'aura alwala ya fito, lotion ya shafa tare da sanya white 3quater and T-shirt red colour mara hannu yayi kyau don kayan sun amshe shi, perfumes ya fesa different colours bayan ya taje kwantaccen gashin kanshi ya shafe shi da mayukan gyaran gashi tamkar wata mace.
Bayan ya kammala gyara jikin shi tukunna ya shimfid'a abin sallah, nan ya gabatar da sallahr la'asar bayan ya idar ne yayi en addu'o'in shi sannan ya fito zuwa parlor.
Tun daga kan steps d'in stairs ya hango Mumy zaune a saman dining table tana cin abinci, d'an girgiza kai yayi don ganin yanda Mumyn shi ta d'an rame alamar akwai abin da yake damunta cikin zuciyar ta, cikin tafiyar sand'a ya zagaya ta bayan ta ya sanya hannun shi dukka biyun ya rufe mata idonta yana murmishi.
Mumy na cikin cin abinci taji an rufe mata ido da farko ta tsorata amman da taji wani kamshin turaren tilon d'anta sai ta d'an nutsu don fuskantar wane, don tasan dai Sabeer baya gidan sai dai ko Daddyn shine yake son zolayar ta sai ta sanya hannun ta saman hannun wanda ya rufe mata idon tana kok'arin zame hannun shi, amman ta kasa zame hannun sai kok'arin cirewa take but Sabeer yak'i bud'e idonta yana yin wata dariya k'asa k'asa.
Cikin mak'e murya Sabeer yace "canki ko wane sai na bud'e miki ido "
Jin muryar Sabeer tayi ta rikid'e mata kamar muryar Daddy don haka tace
"My dear bud'e min ido please na ganka daman yau throughout ban ganka ba "
A hankali Sabeer ya zame hannun shi a eye's nata ya jingina bayan shi da jikin bango yana sakin murmishi, juyawa Mumy tayi da nufin ganin Daddy sai eye's nata suka hango mata tilon d'anta, tsabar mamaki ne ya hanata gasgata abin da ta gani sai da ta mutsutstsuke idonta sannan tace
"Sabeer! "
Da mamaki da kuma rud'ewa da ganin shi ta sake ambatar sunan shi kafin wasu hawaye su fara zubowa daga idanun ta kallon shi take tamkar yau ta fara ganin shi.
Shima wasu hawayen tausayin Mumyn tashi ne suka zubo mishi cikin sassarfa ya k'arasa ya tsugunna agabanta ya dire gwiwar shi a k'asa sannan ya d'ora kanshi saman cinyar ta, hannun ta take saman lallausan gashin kanshi tana shafawa ta kasa magana ma gaba d'aya.
Muryar shi na rawa hawaye na zuba yace
"Mumy baki yi murnar ganina ba koh, saboda ba'a son ranki na tafi ba, kina fushi da ni ne?"
Girgiza kai take yi lokacin da yake magana, cikin sanyin murya tace
"Bazan iya fushi da kai ba Son"
"To gashi kin sanya damuwa a ranki kin rame ba"
D'an murmishi tayi kafin tace "tunanin halin da d'ana yake ciki ne ya sanya ni ramewa da shiga tashin hankali,amman yanzu tun da nagan shi a gabana zan kwantar da hankali na "
"Mumy kenan, nayi kewar ku ke da Daddy wai yana ina ne? "
"I missed U too Son, Daddyn ka yana office bai dawo ba, yaushe ka dawo, zo kaci abinci "
Duk ta rud'e da ganin tilon d'an nata sai faman tambaya take watsa mishi akan lafiyar shi don ta d'an razana da ramar shi da ta gani da duhun da D'an yi, hannun ta ya kamo yana kallon ta kafin yace
"Mumy ki nutsu ni ina cikin lafiya sosai "
"Okay zo kaci abinci, me zan zuba maka? "
D'an shiru yayi kafin yace "ki ban duk abin da kika ci"
Cikin farinciki tace "okay Son taso ka zauna "
Haka ta kamo hannun shi ta zaunar dashi kusa da ita, kafin ta mik'e tsaye ta fara zuba mishi abincin, da kanta take bashi tana faman kallon shi tamkar wata sabon halitta a gabanta, ita kanta tasan tayi kewar d'an nata da yawa duk saboda matsiyar yarinyar nan d'anta yayi mata nisa.
"Mumy tunanin me kike ne ba gashi na dawo ba"
Da murmushi kan face nata tace
"Son kawai ina tunanin irin wacce wahalar kayi a k'auyen da ko wutar nepa babu "
"Haba Mum aikuwa suna da wuta sai dai ba'a fiye samu sosai ba"
D'an ta6e bakin ta tayi sannan tace "kuma kana iyacin abincin su naga duk ka rame kayi bak'i "
"Mum kibar wad'annan tambayoyin please "
"Shikenan Son na bari "
Tana gama bashi abincin suka koma parlor tana rik'e da hannun shi gane take tamkar zai sake guduwa ya barta, basu dad'e da zama ba Daddy ya dawo agajiye sosai yake, amman had'a ido da Sabeer yasa shi neman gajiyar tashi ya rasa nan suka yi hugging d'in junan su cikin tsananin k'aunar junan su.
Nan babu dad'e wa Family d'in D'an fillo dashi kanshi Dr Ahmad d'an fillo da Hajjah Hauwaa suka samu labarin dawowar Sabeer, nan suka dunga shigowa ganin Sabeer kusan dukkanin su sunyi farincikin ganin shi, musammam Alhj Ahmad d'an fillo da Hajjah don rungume shi sukayi tamkar zasu mayar dashi cikin jikin su saboda tsabar son da suke mishi.
Jiddah wadda agidan ta wuni ta d'ago kanta suka had'a ido da Sabeer wanda yake ta zuba musu shagwa6a su kuma sun shashance da lalla6a shi, dariya take son fashewa da ita amman ganin hararar ta da yake yi ne ya sanya ta kunshe dariyar ta, daga k'arshe sai ta faki idon shi tana mishi video don ta nunawa Suhaima ta shirya zama da shagwa6a66en miji.....
Aishat A Muh'd âœðŸ»
[3/14, 5:17 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'É– âœðŸ»: *A SANADIN SON KI*
Written by
Aishat A Muh'd
Dedicated to my Sadeey SaNaz
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.