A Sanadin Son Ki Complete Hausa Novel
Reading file: A_Sanadin_Son_Ki_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 62 of 67
*PAGE 110*
Tana zaune a palourn tana wannan tunanin tunanin ga hawaye kaca kaca a face nata Daddy ya shigo parlourn kallo d'aya yayi mata ya d'auke kanshi kada ta karya mishi gwiwa don kwanakin biyun nan tana bashi tausayi ta sanya damuwa akanta saboda rashin jin muryar d'an nata, duk ta rame ta fara zama silent sosai, kok'arin hawa steps na bene yake yaji muryar ta na cewa
"Daddyn Sabeer ina son magana da kai please "
Ko kallonta Daddy bai yi ba ya fara hawa steps don har yanzu bai ga tayi laushi sosai ba na yanda zai sanar mata inda Sabeer yake.
Ganin Daddy ya shareta ne ya sanya ta tashi da sauri ta bi bayan shi, har zai shiga side d'in shi tayi saurin rik'o hannun shi cikin muryar kuka tace
"Don girman Allah Dear ka fad'a min inda Son yake? "
Hannun shi ya sanya wanda bata rik'e nashin ba ya zame nata hannun yayi gaba kawai ya shige side d'in shi, nan Mumy aka durk'ushe tare da sakin kuka na tashin hankali.
Daddy jingina bayan shi yayi da bayan door tare da runtse eyes nashi tausayin ta ne yake neman rinjayar zuciyar shi don yasan yana son Dr Faridah so bana kad'an ba, ba k'aramin wahala yake sha ba na wannan zaman da suke yi tare amman bashi da yanda za yi dole ya nuna mata kuskurenta na zubar mishi da en jikokin shi da tayi so yake tayu nadama sosai yanda a lokacin zai sanar mata da inda d'anta yake, amman fah kukan ta yana ta6a mishi zuciya sosai.
Sai da tasha kukanta ta more sannan ta mik'e ta wuce side d'in ta hawaye na zuba a eyes nata, kamar wata mahaukaciya sabon kamu take faman gwada kiran number's d'in Sabeer na dukkan k'asar da tasan yake zuwa har da ta gida Nigeria amman dukka abu d'aya nau'ora take sanar da ita a kashe suke, zaman tayi kan bed tare da rafka tagumi dole ta fara binciken inda Sabeer ya tafi bazata zauna ba batasan halin da Sabeer yake ciki ba.
***********
Zaune Suhaima take kusa da Aunty Aliyah suna aikin girki na dare suna er hirar su cikin nishad'i, Yah Aliyu ya fito daga palon Aunty Aliyah hannun shi rik'e da phone nashi kallon su yayi tare da girgiza kai kullum haka suke kamar abokanan juna ya fad'i hakan cikin zuciyar shi, mik'awa Suhaima wayar yayi ba tare da yace mata komai ba ya juya zuwa cikin palon.
Da kallo ta bishi cikin mamaki wane yake kiranta haka, kawai sai ta sanya wayar a kunnen ta jin ana magana, wani zabura tayi tare da tashi tsaye ta buga tsalle da ihu murna tana furta
"Jiddahhhh"
Sabeer da yake kwance kan bed cikin d'akin Suhaima da sauri ya taso jin muryar Suhaima tana ihu, turus yaja ya tsaya da yaji ta ambaci sunan Jiddah, tsayawa yayi bai k'arasa fitowa ba daga d'akin tare da hard'e hannun shi dukka biyun yana kallonta yanda take tsallen murna, murmishi ya saki cikin zuciyar shi yana cewa
"Baby nah har yanzu yarinta na damun ki halin nan yana nan bai canja ba "
Ya fad'i hakan cikin zuciyar shi yana kok'arin komawa cikin d'akin suka had'a ido da ita hura mata kiss yayi sannan ya shige cikin d'akin.
Murmishi Suhaima tayi da taga abin da Sabeer yayi mata nan ta cigaba da waya da Jiddah cikin farinciki taji dad'in sakkowar Yah Aliyu sosai kodan kewar Jiddah tayi sosai, bayan sun sha hirar su Jidda cikin d'oki take fad'a mata gobe zata zo daga k'arshe suka yi sallama cikin kewar junan su.
Aunty Aliyah na zaune tana kallon ta murmishi kawai take ganin yanda Suhaima suke waya cikin d'oki, zama tayi tana cewa
"Wallahi Aunty nayi kewar Jiddah sosai naji dad'in yanda Yah Aliyu shi ya kirawo ta da kanshi ya had'a mu "
"Nima kaina naji dad'in hakan Suhaima Allah ya bar wannan kauna dai"
"Amin Aunty, gobe ma tace zata zo "
"Allah ya kaimu sai kiyi shirin yin dambu ko d'an wake don nasan halin Jiddah da son cin su idan tazo gashi an kwana 2 bata zo nan ba "
Cikin murmishi Suhaima tace
"Haka ne kuwa Aunty nah kin ma tuna min gobe da wuri zan tashi na fara hidimar taryan ta kinsan Jiddah da d'oki da wuri zaki ganta"
D'an hararar wasa tayi mata kan tace
"Wanne tashi wuri kuma kimsan dai mijin ki na nan gashi baya jin dad'i zama zaki ki kula dashi naji da hidimar Jiddah "
Kwa6e fuska Suhaima tayi tare da shagwa6e wa har da karyar da wuya tace
"Kaiii Aunty bayan ya warke kuma gaskiya ni zan yi "
Girgiza kai Aunty tayi kafin tace
"A'a Suhaima ki bawa mijin ki kulawa yafi koma ni zanji da komai"
Bata son yin musa da ita don haka tace
"Toh Aunty "
"Yawwa tawan dad'i na dake bakya jayayya Allah ya bamu jikoki twins "
Wata kunya ce ta rufe Suhaima musamman da taji Yah Aliyu ya amsa da
"Amin Mata ta "
Wanda ya fito zai fita yaji Aunty Aliyah tana wannan addu'ar, da gudu Suhaima ta mik'e ta wuce cikin d'aki kunya sosai ta rufe ta kamar ta nutse, yayin da Yah Aliyu da Aunty Aliyah suka sanya dariya har da tafawa da hannun su.
Bayan ta yana jingine a bayan k'ofa eyes nata a lumshe tana murmishi bata ankara ba taji saukar kissing a wuyan wanda ya haddasa mata sauke ajiyar zuciya tare da bud'e idonta sauke su tayi kan na Sabeer wanda daman kallonta yake.
Da sauri tayi niyyar wuce wa cikin d'akin ya sanya hannu tare da rik'e nata kafin kuma ya janyo ta gaba d'ayan ta jikinshi ya rungume ta tsam, wata wawiyar ajiyar zuciya ya sauke cikin kunnen ta ya rad'a mata
" i luv U Baby nah "
Murmishin jin dad'i tayi bata ankara ba taji ya d'auke ta gaba d'ayan ta bai ajiye ta ko'ina ba sai saman bed kwanciya a jikinta yayi hannun ta yana saman kanshi tana wasa da gashin yayin da shi kuma yake fad'a mata irin matsayin da take cikin zuciyar shi yana bayyana sirrin zuciyar shi wanda wasu abubuwan baza su fad'u a baki tsakanin shi da DANGARTAKAR ZUCIN shi ne wanda yana godiya ga Allah da bai sanya YAYI SAKEN sakin Suhaima ba wanda yasan sai ya fad'a kogin tsantsar nadama amman Allah ya takaita mishi K'ARSHEN WAHALAR shi, zai kasance mai godewa Allah har karshen rayuwar shi akan bashi Suhaima da yayi kamilar mace wadda ta had'a komai kuma wadda kowanne namiji yake fatan ajiye irinta a gida, yasan yasha wahala duk A SANADIN SON ta amman gashi komai ya wuce K'ARSHEN WAHALAR shi yazo yana fatan insha Allah babu abin da zai sake rabashi da Babyn shi sai mutuwa.
Kiran sallahr mangarib ne ya katse su Sabeer ya tashi yayi alwala ya wuce masjid ya bar Suhaima na kok'arin shiga toilet don yin alwala.
Bayan ta idar da sallahr ne ta tsaya karatun Qur'an har zuwa sallahr ishsha bayan tayi addu'o'in ta ne sannan ta sake gyara d'akin sosai ta fita ta sami garwashi ta kunna turaren wuta, sannan ta koma wajen Aunty Aliyah suna d'an ta6a hira duk da har yanzu tana jin kunyar ta akan maganar d'azu.
Sai wurin 9 na dare suka shigo gidan Yah Aliyu da Sabeer nan inda suke zaune a saman tabarma suka zauna kowanne kusa da matar shi, nan Suhaima ta zuba abincin aka fara ci bayan an gama ci aka zauna er hira zuwa 10 na dare suka yi sallama kowa yaja matar shi suka wuce d'akin su.
Duk yanda Sabeer ya so kasancewa da Babyn shi tak'i bashi had'in kai saboda tak'i mance ya tsane ta da ya furta mata, k'arshe da zai takura mata ta sakar mishi kuka dole ya hakura ya fara lalla6a ta har ya samu bacci ya d'auke ta, zuba mata ido yayi bayan bacci ya d'auke ta Baby rigima ya furta hakan kan ya sake rungume ta ajikin shi wani sonta na sake ratsa mishi cikin zuciya da haka shima bacci yayi awon gaba dashi.
*_WASHE GARI DA SAFE_*
Suna zaune gaba d'ayan su a tsakar gidan suna breakfast da yake Yah Aliyu sai da rana yake da lecture sai hira suke cikin jin dad'i da annushuwa.
Sallama suka ji ana yi lokaci d'aya gaban Aliyu da Suhaima yayi mugun fad'uwa wanda har ya kasa yunkurar tashi don yaga wane, sai da aka kuma yi har sau biyu amman ya kasa tashi har sai da Sabeer yace
"Babban Yaya ko naje na duba? "
Da sauri Aliyu ya mik'e tare da cewa
"Barshi bari naje "
Fita yayi jikin shi a matuk'ar sanyaye, yana bud'e k'ofa ya fita ras ras gaban shi ya fad'i ganin wani tsohon mutum duk kanshi da gemun shi furfura ta mamaye su gashi kamar ka hure shi ya fad'i d'an siriri dashi duk yayi bak'i ya zama wani kala gashi yana rik'e da sanda da ita yake dogarawa kallo d'aya zaka yi mishi kasan bai dad'e da tashi daga wannan muguwar cutar ba ta paralyzed ba, jiyowa mutumin yayi suka had'a ido da Aliyu lokaci d'aya Aliyu ya d'ago hannun shi yana nuna shi bakin shi na rawa dakyar bakin shi ya iya had'a kalmar
"Ba... Bab..... Babaaaa! "
Sorry Fan's na kusan gama muku ku cigaba da yi min uxiri.
Aıʂɧąɬ A Mųɧ'É– âœðŸ»
[5/1, 7:52 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'É– âœðŸ»: *A SANADIN SON KI*
Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ
ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ
â™» *єχ¢ℓυѕινє ωÑιтєÑ'Ñ• fσÑυм*
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.