Complete Hausa Novels

A Sanadin Son Ki Complete Hausa Novel

Reading file: A_Sanadin_Son_Ki_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 64 of 67

*PAGE 112*

Washe gari tun safe da wuri Aunty Aliyah ta kammala abin karin safe ta aikawa da Baban su Aliyu, har Aliyu ya fita schl bata ji motsin Suhaima ba, ganin ta gama komai ne ya sanya ta zura hijab ta d'auki Ameer suka tafi gidan su don gaida Baba Umaru.

Suhaima wadda tsabar gajiyar da tayi ya hanata tashi da wuri tun sallahr asuba da tayi ta koma bacci ko shima Sabeer yana dawowa daga masallaci ya rungume kayar shi suka cigaba da baccin su hankali kwance.

Suna tsaka da baccin su mai dad'i ne Jiddah ta k'araso gidan cikin d'oki da zumud'i take rafka sallama, kamar a mafarki Suhaima taji muryar Jiddah na sallama don haka da sauri ta sauko daga gadon ta fito zuwa waje, had'a ido suka yi da juna wani ihun murna suka saki tare da nufar juna da gudu suka rungume junan su cikin farinciki kamar wad'anda suka shekara basu ga junan su ba.

Ihun sune ya farkar da Sabeer daga baccin da yake gane muryar Jiddah ne ya sanya shi jan d'an k'aramin tsaki yasan yanzu zata zo ta dame su bayan yau yana son kasance wa da Babyn shi kusa dashi, don ba k'aramin kewarta yake ba wannan Jiddah duk zata 6ata mishi planning d'in shi tashi yayi ya shiga toilet don yin wanka.

Sakin junan su sukayi tare da k'urawa junan su ido na tsayin mintuna can Suhaima tace
"Jiddah kin k'ara k'iba da kyau ko dai an samu k'anin Islam ne? "

Dariya Jiddah ta saki tare da cewa
"Tabbb lallai yarinya don bakisan wahalar haihuwar bane ai sai na huta sosai kafin na sake, ke dai muna jiran naki nan da 'yan watanni "

Murmishi Suhaima tayi tare da juya eye's ball d'in ta tace
"Ni dai yanzu amarci muke ci sai mun gama tukunna "

Kama ha6a Jiddah tayi tare da cewa
"Iyyyyeee! Lallai yarinyar nan naga alama Yah Sabeer ya koya miki rashin kunyar shi "

Murmishi kawai Suhaima ta sake yi kan tace
"Ina zamu zauna d'aki ko waje? "
"Kaiii bari nasha iska a waje tukunna ina Aunty Aliyah da Yah Aliyu, hala ma yanzu kika tashi daga bacci? "

Kallon kanta Suhaima tayi sai yqnzu ta tuna da sleeping dress d'in da yake jikinta don ma cotton ce kuma doguwa,

"Sallamar ki ce ta tashe ni fah, Aunty Aliyah ina tunanin ta fita Yah Aliyu kuma schl ya tafi"

"Yah Aliyu ya koma makaranta ne? "

"Eh an d'an jima ma da komawar shi, wai ni ina Islam ne? "

Dariya Jiddah tayi kafin tace
"Zamu shigo kenan muka had'u da Babaa Lantana ta dawo daga wata barka shine ta kar6e ta "

"Okay na d'auka baki zo da ita ba nace nayi fushi dake "

"Haba ni na isa Besty na, na taho miki da ita "

Murmishi Suhaima tayi tana cewa
"Kin kyautawa kanki ba don haka ba da sai dai ki koma gida "

Suna tsaka da hirar su Sabeer ya fito daga d'aki yayi wankan shi ya sanya wata T-shirt yellow da jeans black, suna had'a ido da Jiddah ya watsa mata harara abin sai ya bata dariya aikuwa ta kwashe da dariya tare da cewa

"Ohh ni Yah Sabeer me nayi haka daga zuwa na sai harara "

Kallon Suhaima yayi tare da cewa
"Baby nah tashi kije ki wanka ki rabu da wannan mai zuwan sassafe gidan mutane "

Murmishi Suhaima tayi ta tashi tare da wuce wa d'aki, sai da ta fara gyara d'akin tsaf sannan ta wuce toilet ta wanke shi sannan ta fara wanka.

"Allah Yaya kana tak'ura min yanzu fah 11:50 kace nayi zuwan sassafe "

Rage murya yayi kafin yace
"Saboda zaki hanani hutawa da mata ta ne na tsayin yini guda "

"Tabbb Yaya yanda nayi missing d'in Suhaima dasu Aunty Aliyah ai kwana zanyi anan sai dai ka koma kwanan zaure har na tafi "

Ta k'arasa maganar da tsokana tana dariya, harara ya dalla mata kafin ya murd'e 'yan yatsun ta kad'an yana cewa

"Kin fah rainani yarinyar nan amman zan sanya Khaleel yi miki kishiya ko zaki yi hankali "

"lallai ma Yayan nan an fad'a maka ina tsoron kishiya ne tazo mana ba'a kaina zata zauna ba "

Hirar su nan suka cigaba dayi har yana fad'a mata dawowar Baban su Suhaima tayi murna sosai da farinciki, da haka Suhaima ta fito har tayi wanka ta shirya cikin wata doguwar riga ta atampha tayi kyau sosai sai tashin k'amshi take, tun da ta fito Sabeer ya kafeta da eyes, cikin dariya Jiddah tace

"Yah Sabeer irin wannan kallo ai sai kasa ta fad'i "

Murmishi kawai yayi indai Jiddah ce bakin ta baya shiru idan taga abu, zama tayi nan kusa dasu bayan ta d'auko musu abin karyawar su anan take taya Suhaima murnar dawowar mahaifin su, murmishi kawai Suhaima tayi tare da cewa nagode, nan suka karya bayan sun gama ne Sabeer ya fita bai dad'e da fita ba Aunty Aliyah ta dawo da Islam a hannun ta d'ayan hannun kuma Ameer ne ta rik'e mishi hannu da yake ya fara tafiya, kar6ar Islam Suhaima tayi tana fad'in Masha Allah ganin yanda tayi 6ul6ul da ita gwanin sha'awa, cikin jin dad'i Aliyah suke gaisawa da Jiddah, suna gama gaisawa ne Aunty Aliyah da Jiddah suka fara kok'arin girkin rana yayin da Suhaima ta baiwa hankalin ta kan su Islam da Ameer tana musu wasa suna dariya.

Sunsha hira sosai tsayin yini guda don tun da suka ci abincin rana akayi sallahr azahar suka k'ule a d'aki suna fama zuba hira, sai wajen biyar driven Jiddah ya k'araso suka yi sallama dasu Suhaima ta tafi gida ko had'uwa da Yah Aliyu bata yi ba.

AFTER 3 MONTH'S

Acikin wad'annan watannin abubuwa da d'an dama sun faru daga cikin abubuwan da suka faru akwai warkewar mahaifin su daga lalurar da ta same shi da kuma samun cikin da Suhaima tayi, sosai Sabeer yayi matuk'ar farinciki da wannan cikin tsabar murna har kuka sai da tayi don yana masifar son yara, sai dai kuma wannan cikin akwai shi da laulayi fiye da na baya sosai Suhaima take shan wahalar shi duk ta rame tayi fari koda yaushe cikin amai abinci kuwa sai ta kusan yini batasa komai a bakin ta ba, duk abin da tayi sha'awar ci Yah Aliyu da Sabeer suna kok'arin nema mata shi kulawa sosai take samu daga mijinta, Yayanta da Aunty Aliyah ga su Babaa Lantana nan har Baban ta ma kullum sai ya shigo dubata kuma sai ya taho mata da d'an abin kwad'ayi gaba d'aya yayi wani sanyi kamar ba Umaru ba, Jiddah tayi farinciki sosai da albishir d'in da Sabeer yayi mata na Suhaima tana da ciki.

"Baby nah yau me zaki ce ne? "
Sabeer ya tambaye ta yana sanya kaya fitowar shi daga wanka kenan.

Kallon shi tayi idanun ta tap da kwalla tace
"Ni bana sha'awar cin komai "
K'arasa sanya kayan yayi sannan ya zauna kusa da ita tare da d'ago ta ya d'aura ta kan k'afafun shi, kallon ta yake cikin tausayi yace
"Bazan barki baki ci komai ba Baby ki fad'a min please "

Shiru tayi na d'an mintuna kafin tace
"Zan sha fruits toh sun ishe ni "

D'an murmishi yayi kan yace
"Yawwa Baby nah haka nake son ji bari naje na samo miki "

Kwantar da ita yayi saboda jikin ba k'arfi, ya bud'e mata curtains d'in window da na k'ofa don ta samu iska tana shigowa, sannan ya dawo yayi kissing nata a goshi ya fita, ya dad'e tsaye a k'ofar gida yana tunani don duk kud'in da yazo dasu sun k'are ragowar d'ari biyar ce dashi yanzu ya siyowa Suhaima fruit's da ita sun k'are, gashi gobe ko anjima idan tana son wani abu baisan yanda zai yi ba kuma shi bazai ta6a neman kud'i wajen Aliyu ba wanda shima fama yake da hidimar karatu ga d'aukan ciyar su abin da yawa gaskiya gashi duk master card d'in shi da atm card's nashi duk suna gida bai taho dasu ba da wannan tunanin ya tafi.

Wajen 30 minute's da fitar shi ya dawo lokacin Aunty Aliyah ta shiga duba ta kuma tana tambayar ta abin da zata ci, d'auko wani bowl na silver yayi da wuk'a bayan ya wanke fruits d'in zama yayi saman carpet din d'akin zai fara yanka mata Aunty Aliyah tace

"Sabeer kawo na yanka mana "

Murmishi yayi yana cewa
"Mamin Ameer ki barni aiki nane kije ki huta kawai "
Itama murmishi tayi kafin ta wuce ta fita, Suhaima na kallon shi har ya gama yanka rabi iya yanda zata iya sha anjima sai ya yanka mata sauran.

Kusa da ita ya dawo tare da tashin ta zaune ya jingina bayanta da pillow ya fara bata fruit d'in a hankali take bud'e bakin yake bata, duk da Sabeer yana iyakar d'auke damuwa akan fuskar shi ta rashin kud'i da kewar iyayen shi da 'yan uwan shi ga kuma rashin lafiyar Suhaima duk dashi wannan laulayi ne sai anyi hak'uri na d'an wani lokaci amman lalurar ta tsaya mishi a rai har wani d'an rame wa yayi amman duk da haka sai da Suhaima ta gane akwai wani abin da yake damun shi koda ta tambaye shi baya sanar da ita abin da ke damunshi sai dai ya fad'a mata rashin lafiyar tace take damunshi kyale shi kawai tayi amman tasan da wani abin sai dai ta dage da addu'a Allah ya yaye mishi koma mene.

Bayan ya gama bata ta shanye shi gaba d'aya cikin tausayin ta ya kalle ta tare da cewa
"Na k'ara miki wani? "
Murmishin yak'e tayi kafin ta girgiza kanta kawai.
"Okay ni zan fita Baby zamu fita da Ashiru amman bazan dad'e ba"

Cikin sanyin murya irin ta mara lafiya tace
"Allah ya kiyaye hanya ya dawo min da kai lafiya "
Cikin murmishi yace
"Amin Sweetie nah "
Ya k'arasa maganar yana bata peck a kumatu itama tayi mishi a saman lips d'in shi daga haka ya fita daga d'akin Suhaima tabi shi da kallon tausayi.

Haka lokaci ya cigaba da tafiy har aka shiga watan ramadan zuwa wannan lokacin jikin Suhaima ya d'an warware zata ci kowann abinci sai dai har idan ita zata dafa da kanta ba zata iya ci ba, kulawa babu irin wadda bata samu, har azumin ma tun da aka fara take jarumtar yinshi batason tasha, Sabeer kam matsalar kud'i ta yi mishi sauk'i don Daddyn shi ya sanya Jiddah kawo mishi atm card nash duk lokacin da yake buk'ata zai je ya cira amman sai dai idan ya kasance muhimmiya ce saboda yana ganin Aliyu bazai ji dad'i ba zai yi tunanin ya raina duk kulawar da yake bashi.

Da haka suka cinye wata ramadan aka shiga hidimar sallah, Yah Aliyu yayi matuk'ar kok'arin yi musu d'inkunan sallah haka aka cinye bikin sallah lafia, sosai cikin Suhaima yake girma zama dakyar tashi dakyar sosai cikin yake da girma.

Sabeer ba k'aramin tausayin ta yake ji ba haka da dare zai sanya ta a gaba yana faman kallonta tare da shafa cikin kafin ya tashi ya d'aura alwala yana kai kukan shi gun mai dukka akan ya sauki Suhaima lafiya, har wata rama yayi ta fargaba idan ya tuna yasha jin labarin haihuwa akwai wahala, daman tana zuwa awo amman a asibitin cikin gari duk ranar awo shi yake kaita ya jira ta gama su shiga adaidaita sahu ko taxi su dawo gida.

Cikin haka cikin Suhaima ya shiga watan haihuwar shi sai zuba ido ake ana jiran haihuwa shiru, yayin da Jiddah da siyo duk wani abin daya danganci kayan jariri unisex da duk wani abin buk'ata Sabeer ya bata atm card nashi taje ta ciri kud'i ta siyo, duk an gama shirin komai sai jiran haihuwa duk wani masoyin Suhaima yana mata addu'a ta Allah ya rabata lafiya da abin da yake cikinta saboda girman cikin kadai ya isa firgita mutum duk ta wani kumbura tayi wani iri kamar ba ita ba kaya sai dai ta zura dogowar riga saboda riga da siket ko da zani bata jin dad'in amfani dasu dogowar rigar ma irin buba nan mara shape, Baba Adamu kullum cikin yi mata rubutu yake na sauk'in nakuda tana sha.

Sai da cikin Suhaima ya shiga wata goma cif cikin wata safiya ta monday ta tashi da azababben ciwon nakuda Allah yaso Yah Aliyu da Sabeer duk suna gida basu fita ba nan da nan aka samo taxi suka tafi asibitin da take zuwa awo, suna zuwa aka kar6eta cikin gaggawa suka wuce da ita labour room Sabeer ji yake kamar ya bita ciki amman Yah Aliyu ya rik'e shi gam ganin yanda jikin shi yake rawa yace
"Sabeer addu'a kawa zaka yi mata "
Nan ya zube akan benci kawai yana faman yin addu'ar duk wadda tazo cikin bakin shi.

Suhaima kuwa abin ba'a cewa komai iyakar wahala tasha ta kamar bazata iya haihuwa da kanta ba ma, tasha kukan har hawayen suka daina fita daga idonta saboda azaba addu'a kowacce yin ta take tana fatan Allah ya rabata da cikin nan lafiya, tun safe ake abu d'aya har zuwa k'arfe 9 na dare sannan wahalar ta tazo k'arshe inda ta haifi kyawawa yaran ta guda biyu duk maza wanda suka kasance lafiyayyu masu koshin lafiya, tana gama haihuwar su da taja wani numfashi sai ta zube nan nurse suka yi kok'arin wajen farfad'owar ta sannan suka gyara mata jikinta tsaf bayan sun gama suka sanya mata drip na k'ara k'arfin jiki da kuma allurar bacci don ta samu ta huta sosai don ta wajugu ba kad'an ba.

Sai da aka gyara Baby's d'in tsaf suka sanya musu kaya sannan suka duba lafiyar su, su kansu nurse's d'in yaran sun matuk'ar birgesu da basu sha'awa gasu identical twins ne masu kama da junan su sosai.

Sabeer kusan suman tsaye yayi tsabar farinciki a lokacin da aka mik'a mishi yaran shi, kallon su yake cikin wani irin masifar kaunar su d'in nan had'e su yayi ya rungume su cikin kirjin shi yana jin wani irin farinciki da shaukin son yaran shi addu'a yayi musu kafin ya bawa su Yah Aliyu da Aunty Aliyah yaran.

Room d'in da aka canjawa Suhaima ya nufa zama yayi kusa da gadon yana kallon fuskar ta yanda ta wani rame ta k'ara haske sosai, hannun shi ya sanya yana shafa face d'in ta wani irin kaunar ta ne yake ratsa mishi heart din shi, ta gama yi mishi komai tunda ta haifa mishi yara har biyu masu matuk'ar kama dashi da me zai sakawa Suhaima saboda farincikin da ta sanya shi, daren ranar Sabeer kasa bacci yayi idan yaran suka yi kuka ya d'auki wannan ya d'auki wannan Yah Aliyu ne kadai ya koma gida don Aunty Aliyah zama tayi saboda taimaka mishi da rik'o ln yaran.

Sai wurin asuba Suhaima ta farka lokacin Sabeer ya tafi masallacin asibitin, nan Aunty Aliyah ta taimaka mata ta gyara jikinta sannan ta zauna kan bed wata mahaukaciyar yunwa ce take kwakwular cikinta kamar wanda aka kwashewa kayan ciki gaba d'aya, sai da Aunty Aliyah ta mik'a mata Baby's d'in nan sannan ta had'a mata tea tana firfita mata don ya huce.

Kallon su take hawaye na zuba daga idonta suna d'iga kan fuskar yaran godiya take yiwa Allah da ya bata wannan kyautar da babu wani d'an adam da ya isa yayi maka ita, hakika ko a mafarki Suhaima bata ta6a tunanin zata haifi twince ba duk wannan wahalar ta haihuwar ta mance da ita ta rungume yaranta cikin tsantsar kaunar su.

Duk abin da take Sabeer na jingine a bakin kofa yana kallonta cikin wani irin kaunar ta sun bashi sha'awa, a hankali yayi tattaki ya k'arasa kusa da ita ko kunyar Aunty Aliyah bai ji ba ya rungume ta yana faman yi mata godiya kok'arin had'a lips d'in shi yake da nata ta tuna mishi da Aunty Aliyah a room d'in dole ya hakura da abin da yayi niyya, kar6ar tea d'in yayi yana bata a hankali a baki har ta shanye shi tas sai wurin 10 na safe Doctor ya salllame su bayan ya dad'a duba su an tabbatar basu da matsala sannan suka taho gida har da Aliyu wanda zuwan shi kenan ya tsaya kar6ar kayan abin karyawar da Babaa Lantana tana bashi ya kawo musu.

Tun kafin su k'arasa gidan Jiddah ta ruga su zuwa suna shigowa ta nufi wajen Suhaima da gudu ta rungume ta cikin farinciki har Sabeer na hararar ta yana cewa kada ta k'arasa mishi mata, kar6ar yaran tayi ji take kamar ta had'iye su don so gaba d'aya ta kidime sai taji tana son itama ta haifi twince sun bata sha'awa sosai.

"Suhaima don Allah kika yaye su zaki bar min su "
Fad'in Jiddah kenan harara Sabeer ya sake dalla mata tare da cewa
"Yarinya kada ma kisa a ranki bazan baki yara na ba "
"Kaiii Yah Sabeer kasan gaba nawa Allah zai baka watakila ma twince da twinkle zata yi ta haifa "

"Innallilahi Jiddah rufa min asiri idan ba mutuwa kike so nayi ba wannan ma sun ishe ni rayuwa "

Dariya aka kwashe da ita ganin yanda Suhaima gaba d'aya ta firgice, wanka Aunty Aliyah ta fara yiwa yaran yayin da Babaa Lantana kuma ta kama Suhaima tana kuka tana yi mata wankan ganye da tafasasshen ruwan zafi Suhaima ansha kuka fatar nan taji ja saboda dokan ganye jikinta, Sabeer kamar yayi kuka ganin yanda ake wahalar da Babyn shi.

Sai da aka gama gyara su tsaf sannan Baban su Aliyu yazo ganin jikokin nashi yayi musu addu'a sosai, daga nan ya tashi ya tafi sai yamma lik'is Jiddah ta tafi kamar bazata tafi ba haka take ji a wayar ta Sabeer ya kirawo Daddy yake fad'a mishi Daddy tsabar murna kamar yayi tsintsuwa ya taho har da hawayen shi na farinciki daman yana addu'ar Allah ya sanya Sabeer ya haifi yara masu yawa saboda shi kadai ne gare su sai gashi haihuwar farko da biyu Allah ya fara basu.

Washe gari kuwa sai ga Daddy yazo da kanshi saboda tsabar murna rungume Suhaima yayi yana mata godiya sosai har sai da taji kunya sosai nan ya d'auki yaran yana kallon su ya rasa ina zai sanya kanshi saboda murna.

A lokacin Sabeer yake musu hud'uba Hassan yaci sunan Dr Ahmad d'an fillo kamar yanda Daddy yace ya sanya Hussein kuma sunan Baban su Suhaima aka sanya mishi Omar dakyar Daddy ya iya tafiya har yana tafiyar Sabeer yaushe zasu gidan su don ya sanya an gyara gidan an canja komai hatta da fentin gidan sai da aka canja.

"Daddy sai lokacin da Suhaima taso dawowa har yanzu tsoron Mumy yana nan cikin zuciyar ta "
Gid'a kai Daddy yayi tausayin d'an nashi fal cikin zuciyar shi kafin suyi sallama ya tafi. Suhaima da Aliyu tare da Mahaifin su sunyi matuk'ar murna da jin sunan shi aka sanyawa Hussein har kukan farinciki yayi sosai.

Ranar suna anyi taron suna dai dai gwargwado Suhaima ta samu kyautittika tun daga kan uban gayya wato Sabeer, Yah Aliyu, Aunty Aliyah, Jiddah da mijinta Khaleel, Baba Adamu, Babaa Lantana, Baba Umaru, Ashiru abokin Sabeer na kauye, Daddy da kuma Musaddiq da matar shi wanda sai lokacin yake fad'a mishi komai da ya faru, kowannen su yayi mata kyauta daidai k'arfin shi anyi suna lafiya an gama lafiya, raguna 2 da sa 2 Sabeer da Daddy suka yanka duk wannan abin da yake faruwa babu wanda ya sani cikin family d'in d'an fillo sai da Daddy da Jiddah kawai, haka su Suhaima suka cigaba da yin wanka cikin kwanciyar hankali gashi Na'eem da Shaheed suka cigaba da girma kamannin su da Baban su na k'ara fitowa da haka har sukayi arba'in...........

Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻
[5/4, 9:12 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*

Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ

ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ

♻ *єχ¢ℓυѕινє ωяιтєя'ѕ fσяυм*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.