A Sanadin Son Ki Complete Hausa Novel
Reading file: A_Sanadin_Son_Ki_Complete_Hausa_Novel.txt
Chapter 52 of 67
*PAGE 97-98*
Jiddah ta dad'e tana kuka anan sosai Babaa Lantana ce da Baba Adamu suke rarrashin ta don Yah Aliyu yak'i tsayawa ya saurare shi ranshi a 6aci yake sosai da abin da akayi wa k'anwar shi.
"Babaa Lantana Baba Adamu ku taimaka min ku fahimtar da Yaya Aliyu wallahi ba had'in hannuna cikin abin da akayi wa Suhaima ni kaina yanzu binciken da nake yi kenan don gane gaskiya amman bai kamata Yaya Aliyu yayi min haka ba? "
Ta k'arasa maganar tana goge hawaye.
"Yanzu dai yanda Aliyu ya d'auki zafin nan ki bari har zuwa lokacin da ya huce don yanzu bazai tsaya sauraren komai ba ranshi ba k'aramin 6ace yake ba "
Cewar Baba Adamu kenan.
"Kiyi hak'uri Jiddah ki koma gida duk lokacin da ya huci zan sanya Aliyah ta kirawo ki awaya sai kizo "
Gid'a kanta Jiddah ta iyayi kawai daga nan ta shiga mota driver ya jata, wani tsanar familyn su ya d'arsu cikin zuciyar ta yanzu da ba don sun aikata haka ba da tuni Suhaima tana tare da masoyin ta Yah Sabeer, dole zanyi iya yi na do ganin an kama wanda ya aikata haka bazan iya jure rashin Suhaima kusa da ni ba ina sonta, lallai Yah Sabeer ba k'aramin ganganci yayi ba na korar Suhaima don koda zata dawo gidan shi sai yasha wahala ba k'arama.
Tun daga lokacin abubuwa suka fara canjawa don Sabeer sai da yayi wajen sati biyu a hospital kan a sallame shi, yayi wani irin ramewa sosai ko abinci baya iya ci sosai sai an matsa mishi ga wata k'asumba da ya tara yak'i yarda yaje aski agyara mishi ita sannan Mumy ma tayi kok'arin cire mishi ita da kanta amman yak'i yarda, gaba d'aya Sabeer ya canja ya koma wani iri kamar bashi ba yana zuwa aiki office amman daya dawo fah idan ya k'unshe kanshi a d'aki baya sake fitowa sai dai idan sallah zai tafi masallaci.
Ya fara zama mafad'aci abu kad'an zai fara fad'a baya shiga harkar family d'in shi kamar da, har wani lokacin ita kanta Mumy tsoron kulashi take tana mai mamakin me ya canja mata d'anta lokaci d'aya haka, idan ya sake da wani suna hira har da murmishin shi to Daddy ne kawai don ko Dr Ahmad d'an fillo baya sake musu kamar da, sosai abin yake damun su a ransu Jiddah ma baya kulata sosai kamar da sai gaisuwa ce kadai ke tsakanin su idan ma har sun had'u, ita kanta Jiddah duk yanda take da son Sabeer tana jin haushin shi.
Duk yanda yaso da ya fitar da Suhaima daga zuciyar ya kasa ji yake kamar ma k'ara mishi sonta yake, baya iya bacci kullum sai yaga pic's d'in ta, yayi kukan sosai wani lokacin ji yake daman zai iya cire zuciyar shi ya fito da ita ya goge son Suhaima aciki ko ya huta da abin da yake ji cikin zuciyar shi.
Ta 6angaren Suhaima itama kusan haka al'amarin suke sai dai ita ta cigaba da zuwa makarantar islamia kullum da yamma duk da tayi saukar alqur'an but tana sake fad'ad'a karantun ta da sauran litattafai, gashi bata yi rama kamar yanda Sabeer yayi ba don ita sosai tana kok'arin yakice shi cikin ranta ga kuma yanda Yah Aliyu suke tsananin bata kulawa duk da har yanzu son Sabeer na mak'ale cikin zuciyar ta, kullum idan tayi sallah tana addu'ar Allah ya toni asirin wanda yayi mata wannan sharrin, har a makaranta tana fad'a wa Malamai su sanya ana mata addu'a Allah ya yaye mata abin da yake damunta, sai dai kuma tana shan zund'e akauyen shi don tasha surutai don ma Yah Aliyu yayi musu kyakkyawa warning duk wanda ya k'ara nuna k'anwar shi da hannu yana aibatata sai ya sanya an d'aure shi da wannan warning da yayi musu suka samun sauk'in abun don Yah Aliyu yana da arzik'i duk ta sanadiyyar noma da kiwon da ya rik'e hannu bibbiyu.
Ko zancen Sabeer ba'a k'ara tayar dashi ba agidan ba kowa yabar abun cikin zuciyar shi, duk wani kyautata wa Yah Aliyu yana kok'arin yiwa Suhaima duk abin jin dad'i yana kok'arin bata shi.
Ya sanya anyi gyaran gidan sosai ya kashe kud'i sosai agyaran, ginin zamani na dai dai talaka mai rufin asiri ya sanya akayi mishi, sai gidan Baba Adamu suka koma akayi gyaran, inda Suhaima ta samu yalwataccen d'aki babba guda d'aya har da toilet aciki ya sanya akayi mata, sai kuma palo babba da akayi da 2 bedrooms wanda ya kasance na Aunty Aliyah da nashi sai kitchen da toilet a waje, amman filin tsakar gidan ya ragu sosai gashi ko'ina yasha sumunti dak'unan tiles ya sanya aciki, hatta furnitures sababbin ya sanya na dai dai mai rufin asiri ban da kayan kallon da ya had'a musu duk wannan abin Yah Aliyu yayi shine don kawai faranta ran Suhaima saboda yana ganin tayi rayuwa ta cikin kud'i tsayin wasu watanni ta fara sabawa da jin dad'i shine dalilin da ya sanya yayi haka duk da ya san bai kai rabin rabin kyan da gidanta na da yake dashi.
Suhaima taji dad'in abin da Yayan nata yayi mata kawai don ganin farincikin ta, nuna mishi farincikin ta da yayi ne a lokacin ya sanya shi cikin jin dad'i da walwala wanda rabon da ya kasance cikin haka tun kafin Suhaima ta dawo gida, acikin wannan lokacin ne yaje ya zana wec and neco a wata secondary ta gaba da kauyen su don makarantar ma ta shiga cikin gari sosai, Suhaima ba k'aramin jin dad'i tayi ba na komawar da Yayanta makaranta da zai yi, shima yace mata ta kwantar da hankalin ta zai nema mata wata university d'in ta d'ora karatun ta sai ya cikawa mahaifiyar su burinta insha Allah na ganin sun samu ilimi sosai, saboda jin dad'in wannan maganar Yah Aliyu sai da Suhaima tayi kuka ashe daman zata cikawa kanta buri na ganin tayi karatu mai zurfi.
Bayan exam d'in su Yah Aliyu ta fito ne dakyar da sod'in goshi ya samu gurbin karatu a jami'ar Buk da taimakon wani Alhaji da yake kai mishi kwai da kaji duk karshen wata gidan shi a birni, duk da kyan da takardun Yah Aliyu sukayi inda zai yi karatun Mass com inda Allah ya taimake shi ma yana da machine d'in hawa sai dai cacar kud'in mai da haka ya fara karatun shi cikin nasara da kwanciyar hankali.
***********
_*AFTER 7 MONTHS*_
Sabeer ne na hango yana fitowa daga side d'in shi duk yayi wani tamkar ba Sabeer d'an gayu d'an kwalisa ba yana sanye cikin wani jallabiya milk mai yankakken hannu, tafiya yake kamar zai fad'i saboda yanda jikin babu kwari, bedroom d'in Mumy ya nufa yana son fad'a mata yana son shan coffee a dafa mishi.
Har ya d'ora hannun shi kan handle d'in bud'e k'ofar zai murd'a yaji muryar Mumy tana cewa
"Ga wannan kud'in na sallame ki daga yau ki koma kauyen ku yanzu yanzun nan don na fahimci sosai Daddyn Sabeer ke zargin ki kuma naga yana sanya miki ido a duk wani motsin ki nasan idan ya cigaba da hakan asirin mu ne yake daf da tonuwa, tunda kinyi nasarar raba wannan shegiyar matsiyaciyar da d'ana aikin ki ya gama, idan kuwa kika yi kok'arin tona min asiri kinsan zan iya sanya wa a kulle ki har karshen rayuwar ki ko a 6atar min da ke "
Cikin rawar jiki mai aikin tace
"Wallahi Hajia bazan ta6a tona miki asiri ba baza ki k'ara ganina ba ma har abada "
Wani murmishi Dr Faridah ta saki kafin tace
"Good da ya fiye miki alkhairi kuwa tashi maza ki had'a kayan ki ina son yau kibar gidan nan "
"Toh toh Hajia yanzu ma kuwa "
Ta kwashe kud'in mai yawa da Dr Faridah ta bata ta fito zata fita daga d'akin. Jikin Sabeer wanda ke rawa kamar mai yin rawar sanyi yayi hanzarin barin bakin k'ofar ya 6uya a wani corridor yana kallon ta ta wuce can part d'in su na masu aiki.
Cikin zafin nama Sabeer ya bita a baya da sauri aikuwa yayi nasarar ritsata zata shiga d'akin, kallon Sabeer take tuni cikinta ya d'auki k'ara yana hautsinawa ganin yanda ya rikid'a kamar wani zaki.
Bata ankara ba ya dalla mata mari har guda biyu zata yi ihu yayi saurin sanya hannun shi d'aya a baki alamar tayi shiru yana zare mata ido wad'anda suka yi ja jikin shi yana rawa sosai, ba shiri ta mayar da bakin nata ta rufe shi k'am har da d'ora hannu ta damk'e bakin nata.
Kafin ta ankara wani fitsari mai zafi ya kubce mata yana tsiyaya sai faman matse kafa take da sauri Sabeer yaja baya kafin yana yarfe hannu tare da duba jikin shi ko ta 6ata shi, belt d'in jikin shi ya cire ya fara zuba mata, sai rawar disco take gashi ba damar yin ihu, gani yayi belt d'in kamar bata shigarta sai kawai ya yar da ita ya nufe ta ya shak'e mata kamar zai kashe ta tuni idanun ta sun firfito kamar zasu zazzago ga dakyar take sauke numfashin ta, Allah ne ya kawo Daddy hanyar wajen zai tafi garden yaji kakari awajen ya nufo wajen, ganin abin da d'an nashi yake kok'arin aikatawa da sauri ya nufi wajen dakyar ya 6am6are ta daga hannun shi sai wani huci yake fuskar nan tashi tayi ja.
Yana sakin ta ta zube tana jan numfashi cikin rud'ewa Daddy yake girgiza Sabeer yana cewa
"Son me kake shirin aikatawa ne me tayi maka iyeeeee? ""
Cikin rawar murya Sabeer yake nuna ta da hannu yana cewa
"Dad.... Daddy kace ta tayi magana ita... itace ta... take zubar wa da Suhaima ciki "
"What! "
Cewar Daddy da sauri.
"Keee fad'a mana uban da ya sanya ki aikata hakan? "
Cewar Daddy a fusace, cikin rawar murya tace
"Don Allah kuyi hak'uri wallahi sanya ni akayi "
"Wane ya sanya ki? "
Murya na rawa da jiki na 6ari ta kasa magana sai da Sabeer ya daka mata wata razananniyar tsawa sannan ta bud'e baki dakyar tace
"Wallahi Hajiya ce ta sanya ni ba laifi na bane "
"Wacce Hajia? "
Cewar Daddy cikin zak'uwa.
"Hajiya Faridah ce wallahi take sanya ni zubawa Suhaima maganai a abu tasha sai cikin ya zube "
"What!? "
Cewar Daddy da Sabeer a lokaci d'aya suka furta hakan cikin matuk'ar razana tare da firgita da jin abin da tace, sulalewa Sabeer yayi a k'asa tare da d'ora hannun akai shikenan Mumy ta cuce shi ta gama dashi wayyo Allah nah Suhaima daman ba laifin ki bane yanzu ta ina zan iya dawo da Suhaima a rayuwa ta.
Wata zabura da yayi sai da ya firgita Daddy cikin tsananin fusata ya nufi cikin palo yana kwallawa Mumy kira, yayin da Daddy ya tura Larai cikin d'aki ya sanya key ya 6ame k'ofar don baza'a barta ta gudu a banza ba sai ta fuskanci hukunci dai dai da abin da ta aikata, kafin ya bu bayan Sabeer don yau za'a yi tashin hankali..............
Aıʂɧąɬ A Mųɧ'É– âœðŸ»
[4/14, 9:08 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'É– âœðŸ»: *A̺͆ S̺͆A̺͆N̺͆A̺͆D̺͆I̺͆N̺͆ S̺͆O̺͆N̺͆ K̺͆I̺͆*
Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ
ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ
â™» *єχ¢ℓυѕινє ωÑιтєÑ'Ñ• fσÑυм*
Chapter Navigation
Use this section to move to any chapter without going back to the top.