Complete Hausa Novels

A Sanadin Son Ki Complete Hausa Novel

Reading file: A_Sanadin_Son_Ki_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 63 of 67

*PAGE 111*

Cikin tsananin mamaki da razani Aliyu ya sake furta
"Baba me ya kawo ka wajen mu kuma yanzu?"

Dattijon ya fashe da wani irin kuka yana cewa
"D'ana kayi hak'uri ku yafe min abubuwan da nayi kuma ciki har da tafiyar da nayi na barku sama da shekaru masu yawa ban waiwaye ku ba "

Ran Aliyu ne ya k'ara 6aci da ya tuna saboda bak'incikin shi mahaifiyar su ta rasu da irin wulak'ancin da ya dunga yi musu, sam bazai ta6a yafe mishi akan abubuwan da ya aikata a gare su, don haka ya bud'e baki cikin rawar murya yace

"Baba ni da k'anwata bama buk'atar sake ganin ka kamar yanda mu ma ka gudu ka barmu don haka kawai ka kyale mu zamu k'arasa rayuwar mu babu uba "

Yana gama fad'in haka ya juya zai koma gida, yayin da Baba yake faman kuka yana furta
"Ku yafe min Aliyu hakk'in ku ne yake bibiyata ku yafe min ko na ji dad'in rayuwata "

Amman ina Aliyu bai saurare shi ba ya wuce gida tare da rufe k'ofar ya jingina bayan shi kan k'ofar duk dauriya irinta Aliyu sai da ya kasa rik'e kukan shi ya fashe da wani irin kuka mai ban tausayi har yanzu yana jin amon murya Baban nashi yana furta su yafe mishi.

"Lafiya kake kuka? "
Yaji saukar muryar Sabeer kusa dashi yana mai rik'e shi hankalin shi a tashe don a iya sanin shi Aliyu jarumi ne ba kamar shi ba dole akwai wani babban abu da ya d'aga mishi hankali.

Girgiza kanshi yake kawai ya kasa magana, suna cikin haka Suhaima da Aunty Aliyah suka shigo zauren jin kamar sautin kuka, hankalin su ba k'aramin tashi yayi ba ganin yanda Aliyu yake kuka, nan take suka fara kukan ita Aliyah zuciyar ta ce ta bata Baban ta ko Babaar tane wani daga cikin su ya rasu.

Da sauri Suhaima ta k'arasa wajen Yah Aliyu ta shige jikin shi tana kuka tace
"Yaya me.... me ya faru kake kuka? "

Ganin yanda hankalin su ne ya tashi sosai ya sanya shi bud'e baki dakyar cikin muryar kuka a shak'e yace

"Suhaima Bab..... Baban mu ne ya dawo "

Awani firgice Suhaima ta d'ago kanta ta kalli Yah Aliyu cikin tsananin tashin hankali da rud'ani kafin ta rushe da kuka tace
"Yaya don Allah kace ya tafi ina tsoran shi wallahi kada ya kashe mu kamar yanda ya fad'a, Yaya zai dawo yana dukan mu da zagin mu ina tsoran shi..... "

Ganin abin nata ya had'ar mata da tsoro, firgici da kuma sumbatu har ta rasa me zata ce ya sanya Sabeer ya janyo ta jikin shi ya rungume ta yana bubbuga bayan ta alamar rarrashi yayin da Aliyah ma ta k'arasa wajen mijinta tana bashi baki da ya bud'e k'ofar duk da kuwa da irin kallon da yake wurgata, gashi sai wani sauke huci yake kamar wani tsohon zaki.

Suna tsaka da haka ne suka ji ana bubbuga k'ofar cikin sauri Aliyah ta sanya hannu zata bud'e k'ofar amman kafin ta bud'e Aliyu ya sakar mata wata harara bashiri ta hakura kawai ta zubawa mijin nata ido yanda ya rikid'a ya koma mata wani daban kamar ba Aliyun ta ba.

"Aliyu, Aliyah, Suhaima, Sabeer ku bud'e k'ofar nan nasan kuna jin na"
Suka jiyo amon muryar Baba Adamu yana kwalla musu kira, Sabeer ne yayi kok'arin janye Suhaima daga jikin shi ya samu ya bud'e k'ofar, yana bud'e wa Baba Adamu da Babaa Lantana suka shigo bayan su kuma mahaifin su Aliyu ne yana dogara sanda.

Suna had'a ido da Suhaima ta wani saki k'ara mai rud'ewa wanda sauran kad'an ta wuntsila tsabar firgita da tsoran shi da sauri Sabeer ya taro ta ya rik'e ta k'am itama rik'eshi tashi sosai suka shige cikin gidan jikinta na 6ari don masifar tsoron shi take.

Daman tabarmar da suka karya akanta tana nan a shimfid'e zama suka yi dukkanin su ban da Suhaima da ta gudu d'aki tana kuka sai Yah Aliyu da yake tsaye ya kasa zama.

Tashi Sabeer yayi ya nufi d'akin ya tarar da Suhaima tana kwance a ruf da ciki tana kuka sosai, cikin sanyin jiki Sabeer ya k'arasa inda take ya zauna tare da janyota jikin shi ya d'orata saman k'afafun shi share mata hawayen face nata yake yi cikin sanyin murya yake rarrashin ta, dakyar ya samu tayi shiru sannan ya d'auko ruwa ya bata tasha, kad'an ta iya sha sannan yace

"Baby nah ki nutsu mu je, amman na rok'e ki kada kiyi kuka ji yanda idanun ki da fuskar ki suka yi ja gashi sun kumbura saboda kukan da kika yi"

Cikin sanyin jiki ta d'aga kanta alamar toh daga haka yaja hannunta suka fito zuwa tsakar gidan inda suke zaune jugum jugum kamar gidan makoki sautin kukan Baban su Suhaima ne kawai yake tashi, damk'e hannun Sabeer Suhaima tayi jikinta ya fara rawa don masifar tsoron Mahaifin ta take kallonta Sabeer yayi cikin zuciyar shi yana tunanin mai Mahaifin su yayi musu da har Suhaima take jin tsoron shi haka gashi ya karanto tsananin tsanar shi kan fuskar Aliyu da Suhaima.

Gefe suka samu suka zauna sannan Baba Adamu yayi gyaran murya tare da cewa

"Alhamdullilah dukkan godiya sun tabbata ga Allah subhanahu wata'ala da ya bamu aron rai har zuwa wannan lokacin da ya sanya ni ganin wai Umaru ne ya dawo gida"

Baba Adamu ya k'arasa maganar tashi cikin tsananin mamaki da jimamin yanayin da suka ganshi aciki, cikin sanyin murya da tsantsar nadama Baban su Aliyu yace

"Bani da bakin kare kaina a wajen ku don hak'ik'a na cika azzalumi mara imani kuma butulu a wajen iyalina, nayi nadama dana sani mara adadi nasan na cika mara tausayi wajen mata ta Fatima da yarana Aliyu da Suhaima, bansan ta inda zan fara neman gafarar ku ba ku tausaya min duk wani jin dad'i na rayuwa bana jin shi kuma nasan duk hakk'in ku ne ku yafe min 'ya'ya n........ "

Bai k'arasa fad'in maganar ba saboda wani kuka da ya kubce mishi na nadama, duk wajen shiru akayi ana sauraren shi sai da ya tsayar da kukan dakyar yace
"Ina Fatima ku kaini inda take na nemi yafiyar ta don Allah, Aliyu Suhaima ku yafe min ba don ni ba don girman Allah "

Baba Adamu ne yace
"Umaru sai dai kayi hak'uri amman Allah yayi wa Fatima rasuwa tun washegarin da ka tafi cikin ma dake jikinta shima ya rasu "

Neman mik'ewa yake amman jikin shi babu k'arfi ya k'asa tashi sai kawai ya fashe da kuka yana cewa
"Na shiga uku yanzu ya zanyi da d'unbin tarin hakk'in Fatima da yake kaina me yasa ma na tafi na barku Fatima ki yafe min "

Babaa Lantana tana zubar da hawaye tace
"Umaru ka godewa Allah kafin Fatima ta rasu ta yafe maka duk abin da kayi mata"

Kallon Babaa Lantana yayi tare da kura mata ido kamar yau ya fara ganin ta yace
"Da gaske kike Fatima ta yafe min? "

"Tabbas Umman mu ta yafe maka don ita ba macuciya bace kuma ba azzaluma bace ta kasance mai hak'uri da yafe wa mutanen da suka zalunce ta komai girman laifin da suka yi mata "
Cewar Aliyu kenan a fusace, matsowa kusa dashi yayi kan ya sanya hannun shi yana kok'arin rik'e Aliyu da sauri Aliyu yayi baya yana girgiza mishi kai tare da wurga mishi wani kallo yace

"Kada ka sake ka ta6a ni "
"Ka yafe min d'ana 'yata ki yafe ni "

Ya k'arasa maganar yana kallon Suhaima kauda kanta tayi daga kallon shi sai dai zuciyar ta ta fara rauni tausayin mahaifin nata ya fara shiga cikin zuciyar ta amman tana tsoron kallonshi balle tayi mishi magana.

"Haba Aliyu kada ka zama mutum mara yafiya, nasan ka da zuciya mai kyau kayi hak'uri ka yafe mishi mahaifin ka ne baka da kamar shi duk duniyar nan, Allah yana son masu yafiya idan an zalunce su, kayi duba ma da halin da yake ciki wannan kadai ma ya ishe shi "

Nan Baba Adamu da Babaa Lantana suka dunga yi musu nasiha tare da nuna musu mahimmanci mahaifi agare su koda wanne laifi ya aikata a wajen ka yana nan matsayin mahaifi ba'a ta6a canja shi k'addara ce da son zuciya suka rinjaye shi ya aikata hakan, nan Sabeer ma ya fara ya fara lalla6a su akan suyi hak'uri su yafe mishi haka Aunty Aliyah ma ta sanya baki akan maganar dakyar da sud'in goshi Aliyu da Suhaima suka yafe wa mahaifin su saboda ganin girman mutanen da suka sanya baki cikin maganar.

Yana kuka yana gode musu tare da sanya musu albarka Yah Aliyu dai tashi yayi kawai ya shiga d'aki baya tunanin ko makaranta zai iya zuwa yau wani abu ne yake nuk'urk'usar cikin zuciyar shi kwanciya yayi yak'i fitowa sai da yaji muryar Baba Adamu yana kira shi sannan ya fito idanun shi jawur ya samu waje ya zauna.

Cikin kuka Umaru ya fara basu tak'aitaccen labarin shi bayan barin shi gidan.....

"Tun da na d'auki jaka ta na tafi ban tsaya ko'ina ba sai cikin kaduna anan na tsaya cikin kasuwa ina buge buge na, na neman aiki ni ne dako da duk wani aikin k'arfi don kawai na samu kud'i na tara naji dad'in rayuwa ta,amman sai naga ko nayi aikin kud'in basa yi min albarka sai dai uban wahalar da nake sha da haka dai na samu dakyar na samu d'an rumfa ina siyar dasu kayan miya, ba laifi ina d'an ciniki akusa da inda rumfa ta take ne akwai wata mai siyar da abinci sunan ta Ladidi mai abinci 'yar duniya ce sosai awajen ta nake siyan abinci kullum, mun gaisuwar mutunci da ita gashi wani lokacin kyauta zata zuba min abinci ta aiko min shi har rumfata da haka muka d'auki tsayin lokaci ashe sona take sai daga baya take sanar min, da fari nak'i yarda ganin yanda idanun ta suke a bud'e sosai amman daga k'arshe ta shawo kaina na amince da ita, nan muka shirya yin aure nace mata banda iyaye ni maraya ne sai kawai na samu limamin unguwa ya zama wakili na ya d'aura mana aure daman agidan ta zamu zauna tun da tana da gida, farkon zaman namu munyi shi cikin kwanciyar hankali da jin dad'i amman da muka fara d'aukan shekaru komai ya canja ta fara yi min rashin mutunci kala kala na yau daban na gobe daban, gashi yanzu kasuwa taja baya d'an kayan miyar da nake siyarwa jarin ya karye mun cinye shi a abinci, daga nan fah wulak'anci take min kala kala har takai zaman gidan ya gagare ni saboda masifar ta duk wani hakk'i nawa na kanta bata sauke min na zama kamar matar ita mijin tunda ita take ciyar dani amman da sharad'in sai nayi mata aikace aikacen gidan ".

Kallon shi Yah Aliyu yayi ya tuna lokacin da Umman su idan bata gama abinci ba da wuri zagi kala kala zai yi mata har da duka kuma ya dunga ball da duk abin da ya ci karo dashi agidan yana kiranta k'azama abubuwa dai kala kala babu irin wanda bai yiwa Umman su ba lallai Allah ne ya nuna mishi ishara akan zaluntar su da yayi.

Ya cigaba da cewa
"Haka nake yi mata aikin don kawai ta ban abinci, gashi tana tara maza agidan musamman 'yan daudu, ashe Ladidi 'yar bariki ce ta k'arshe daga baya nake jin labari har shaye shaye take agabana babu abin da na isa nayi k'arshe sai ta ware min d'aki a zaure aciki nake kwana azaba da wahala nasha shi kala kala nayi bak'i na rame sosai nayi nadama sosai gashi kullum cikin mafarkin Fatima nake da yara na, ita kuwa Ladidi bata haihuwa kwata kwata gashi na rasa me ya sanya na zauna nake bauta mata duk zafin zuciya ta kuwa gaba d'aya nayi sanyi kamar ba ni ba ni kaina nasan Ladidi ba haka ta bar ni ba don tana bin malamai sosai, da haka muka kwashe shekaru da ita ina cikin wannan wahalar, nan na fara rashin lafiya sosai dakyar nake iya tashi amman ko kud'in da zan siyi magana ban dashi, daga k'arshe dai Ladidi ta kamu da cutar HIV ban san tana da ita sai kawai........ "

Wani kuka ne ya kubce mishi na tsananin bak'inciki da takaici, yayin da gaban Aliyu da Suhaima yayi mummunar fad'uwa kada Ladidi ta shafawa mahaifin su ciwon, kallon shi suke a tsorace don jin mai zai ce haka su Baba Adamu da Babaa Lantana, Aliyah da Sabeer suka tsorata suna addu'ar Allah ya sanya bata sanya mishi ba.

Cikin kukan ya cigaba da cewa
"Sai kawai ta yanke shawarar bazata mutu ita kadai ba sai ta goga min ciwon nata, bansan hawa ba ban san sauka ba wata rana kwatsam naga tana faman gyara gidan ta shirya lafiyayyen abinci ta kawo min amman ban iya ci ba saboda lokacin jikina babu sauk'i, na tashi zan shiga bandak'i ne naji tana magana da wata kawar ta a waya ashe abincin nan da ta kawo min duk sai da ta zuba musu jinin jikinta saboda yanzu ban da k'arfin da zan sauke mata buk'atar ta sai ta 6ullo ta wannan hanyar, ban k'arasa jin zancen ba na zube k'asa a sume don nayi matuk'ar kad'uwa da jin wannan maganar ta"

Wata ajiyar zuciya Aliyu da Suhaima tare da sauran mutanen wajen suka saki jin bata yi nasara akan shi ba lallai Ladidi ta cika macuciya kuma muguwa, share hawayen fuskar shi yayi kafin ya k'arasa da cewa

"Daga nan sa farkawa nayi naji ni agadon asibiti sai dai na had'u da lalurar shanyewar 6arin jiki wato paralyzed,nayi kuka nayi nadama sosai alokacin kullum cikin addu'a nake akan Allah kada ya d'auki rayuwata sai nazo na nemi yafiyar ku kullum da ku nake bacci nake tashi ina tsananin son naga na dawo wajen ku, naji ma ina jinya kafin na samu na 6arin jikina ya fara motsi da taimakon wannan liman d'in da ya d'aura ma aure da Ladidi da yake d'an shi likita ne, bayan na d'an fara magana ne na saki Ladidi saki uku wadda itama alokacin ciwon yaci k'arfin ta har ta kwanta, daga nan liman ya taimaka min da kud'in mota na taho gida na nemi afuwar ku don nasan hakk'in ku ne yake bibiyar ta dakyar na iya kawo kaina garin nan wannan shine tak'aitaccen labarina tun bayan bari na gida, ina sake neman afuwar ku 'ya'yana ".

Suhaima kuka take sosai najin irin azabar da mahaifin su yasha a hannun muguwar matar nan, Cikin rad'a Sabeer yace
"Baby ba kuka zaki yi ba godewa Allah zakiyi da ya tseratar da Baba daga hannun ta "

Nan Aliyu ya dad'a saukowa daga fushin da yake da mahaifin shi jin irin azabar da yasha, sosai Baba Adamu ya dad'a yi musu nasiha kafin kuma ya nunawa Baba surukin shi wato Sabeer da kuma surukar shi Aliyah sosai Baba yaji dad'i da ganin yanda yaranshi suka dace da samun abokanan rayuwa nagari, bakin shi yak'i rafuwa saboda jin dad'in yanda su Baba Adamu da Babaa Lantana suka rik'e mishi yaran shi godiya sosai yayi musu da addu'o'i sun sha shi a wajen shi, daga k'arshe Baba Adamu yace

"Idan Allah ya kaimu gobe Aliyu ya kamata ka kaishi asibitin birni ya dad'a ganin likita sannan kuma tunda babu d'aki anan wanda zai na kwana sai ya koma gidan mu tunda muna da d'akuna ya zauna aciki kafin ya warware asan abin yi "

Kowa ya aminta da abin da Baba Adamu yace Aliyu da Suhaima sun rasa wace irin godiya zasu yi wa bayin Allahn nan tun suna yara suke d'awainiya dasu gashi har girman su basu kyale su ba, daga haka Baba Adamu ya tashi suka tafi don Mahaifin su Suhaima yaje ya kwanta ya huta.

Bayan sun tafi ne Jiddah take kiran Yah Aliyu a waya bazata samu damar zuwa yau ba sai gobe, sun d'an ta6a hira da Suhaima duk da ba'a cikin nutsuwar ta take ba, kiran sallahr azahar ne ya tashe su daga nan kowa ya fara kok'arin haramar yin sallah.

Bayan sallahr ishsha ne hadari ya had'u a garin sosai dole ta sanya Suhaima d'aukan abincin su ta shigo dashi d'aki saboda yau babu zaman waje ruwa daf yake da ya sakko, agurguje ta dafa ruwan wankan su ta d'ura wani a flaks ragowar kuma ta zuba a bokiti mai murfi ta wuce d'aki, cikin toilet takai ta ajiye sanann ta koma d'akin Aunty Aliyah wadda take zaune tana sanyawa Ameer kayan sanyi saboda yanda garin iska take kad'awa, zama Suhaima tayi tana jan kumatun Ameer shi kuma yana yi mata dariya.

Hirar su suke yi inda Aunty Aliyah take taya Suhaima murnar dawowar mahaifin su, bayan ta gama sanya mishi kayan Suhaima ta d'auke shi tana mishi wasa, Aunty Aliyah ta mik'e ta shiga cikin bedroom d'in ta bata dad'e ba ta fito hannun ta rik'e da wata roba da abu aciki sai wani cup kuma a hannun ta, zama tayi kusa da Suhaima tana cewa

"Kin ga tun safe na had'a zan baki amman dawowar Baba yasa na mance kinsan dama baki k'arasa sha ba koh? "
Ta fad'i tana kallon Suhaima wadda ta ta6e fuska take son yin shagwa6a tace
"Kaiii Aunty wallahi ni nagaji da shan irin wad'annan abubuwan fah? "

'Yar dariya Aunty Aliyah tayi kan tace
"Yarinya yanzu kika fara sha kuwa wani abin ma sai kin haihu kuma ba abu ne wanda zai cutar da ke ba "

Tana gama fad'in haka ta bata na cup d'in ta shanye sannan ta tsiyaya mata na robar ta shanye daman ragowar cup biyu ne dakyar ta k'arasa shan kamar zatayi kuka ita dai Aunty Aliyah dariya tayi cikin zuciyar ta tana cewa da kanki zaki dawo neman shi yarinya.

Ganin an fara yayyafi ne yasa Aunty Aliyah fad'a mata ta tafi d'akin ta, haka ta tashi tare da yi mata sai da safe ta wuce d'akin ta, tana shiga d'akin aka saki wata tsawa batasan lokacin da ta fad'a kan bed ba ta tukunkune jikin ta na 6ari saboda tsorata.

"Washhh Allah nah! Baby kin karya ni "
Taji an fad'a a kusa da ita da wata irin murya da ta sanya Suhaima k'ara rikicewa ga d'akin da duhu, tana kok'arin sauka daga kan gadon taji an sanya hannun an kamota tare da janyo ta jikin shi, bud'e baki tayi zata saki ihu taji an rufe mata da bakinta ashe Sabeer ne ya dawo batasani ba lokacin tana d'akin Aunty Aliyah.

Had'e lips d'in shi yayi da nata yana wani irin passionate kiss jikin Suhaima rawa yake sosai don ta tsorata walk'iya akayi wanda har haskenta ya ratso ta window d'in d'akin nan Suhaima taga ashe Sabeer wata ajiyar zuciya ta sauke kafin ta kwace bakinta ta d'auki pillow tana bugun shi na wasa cikin kukan shagwa6a take cewa

"Shine ka tsorata ni koh?, sai na rama nima"

Kare dukan yake yana dariya yace
"Haba sweetie nah sai dai ki rame kuwa "

Gajiya tayi ta ajiye pillow tare da cewa
"Bazan ma kwana a d'akin ba komawa zanyi d'akin su Yah Aliyu "

Kok'arin tashi take ya sake janyo ta jikin shi ya rungume ta yana cewa
"Ke yanzu aka ce kije sai ki tafi? "
"Eh mana bama sai ance naje ba "
"Lallai Baby da sauran yarinta akan ki, sai ki tafi ki bar mijin ki anan suma tak'ura musu zaki yi babba dake ki wani tafi d'akin su "

Har ta bud'e baki zata sake magana ya sanya hannu ya rufe tare da cewa
"Yunwa nake ji Baby "
Sai lokacin ta tuna ko abincin rana bai ci ba saboda baccin da ya d'auke shi sai daf da la'asar ya tafi kuma ya tafi masallaci bai dawo ba sai yanzu gashi daman a makare aka gama abincin ranar.

Hannun shi ta kamo ta zaunar dashi kan carpet sanann ta zuba mishi tuwon shinkafa miyar bushashshen ku6ewa tare da manshanu ga yajin daddawa mai dad'i agefe, langa6e wa yayi a baki zata bashi bata da yanda zata yi ta fara bashi da hannun ta shima yana bata, kad'an suka iya ci ya 6ata lokaci yana lashe 'yan yatsun nan nata dakyar ya saki ta bashi tea mai lemon tsamin da ta dafa mishi ya sha, kwashe kwanukan tayi ta ajiye su waje d'aya ba damar fita kai su kitchen saboda ruwan da yayi k'arfi, rufe k'ofar d'akin tayi tare da sanya key sannan ta saki labulen window bayan ta gama ta wuce toilet don wanke hannun ta sannan ta had'a mishi ruwan wanka.

Tana tsaka da had'a ruwan ne ya shigo cikin bathroom d'in da sauri Suhaima ta juya taga Sabeer ne ya cire kayan shi sai k'aramin towel nata da ya d'aura a kugun shi wanda dakyar ya ritsa shi, hannu ya sa ya matsar da ita ya had'a musu ruwan dukka su biyun kafin ta ankara ya janyota jikin shi ya fara cire mata kaya zata yi magana kenan ya girgiza mata kai idonshi cikin nata, sunkuyar da kanta tayi kawai tana jinshi ya cire mata kayan nata tsaf.

Bayan sunyi wankan ne sukayi brush sannan suka fito daga bathroom d'in, Suhaima ta shirya cikin wata doguwar riga ta bacci mai siririn hannu cotton ce ta shafa perfume da humrah ta had'e gashin ta cikin ribbon tayi parking d'in a gefe don kada ya hanata bacci, Sabeer kuwa yana sanye da boxer d'in shi duk abin da take yana bin ta da kallo jira kawa yake ta gama shiryawa yaji ta a cikin jikin shi.

Kasa jira yayi ta gama shirin ya tashi ya d'auko ta saman bed ya sauke ta tare da kashe fitilar d'akin wadda take amfani da batir, kafin Suhaima ta fara yi mishi korafi ya had'e lips d'in su waje d'aya, nan fah Suhaima ta fara kuka tana zame jikinta aikuwa Sabeer ya rikice mata sosai wasu zafafan sak'onni yake turata mata wanda ya sanya Suhaima sakin jikinta ta biye mishi ba tare da ta sani ba.

Wannan daren sun faranta shi ya zame musu tamkar daren su na farko, Sabeer ya nuna mata tsantsar son da yake mata yana kuka yana rokanta kada ta rabu dashi, bayan komai ya kammalu ne ta fara zum6ura baki tana k'unk'uni, abin ma dariya ya bashi sosai nan ya 6ige da aikin rarrashi kan su wuce suyi wanka suna kwanciya bacci mai dad'i yayi awon gaba dasu, zuciyar kowa fes da farinciki ga kuma yanayin garin da yayi dad'i suna rungume da junan su suka yi bacci............

Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻
[5/4, 2:18 PM] Aıʂɧąɬ A Mųɧ'ɖ ✍🏻: *A SANADIN SON KI*

Wྂrྂiྂtྂtྂeྂnྂ bྂyྂ
Aྂıʂɧąɬ Aྂ Mྂųɧ'ɖ

ɖɛɖı¢ąɬɛɖ ɬơ ɱყ ʂąɖɛɛყ ʂąŋąʑ

♻ *єχ¢ℓυѕινє ωяιтєя'ѕ fσяυм*

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.