Complete Hausa Novels

Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 20 of 41

Bayan la'asar Salma ta farka bacci da matsananci ciwon kai, dakyar ta yunkuro zaune taji kafar tai mata nauyi, wani irin juwa take ji, sauka tayi kan gadon ta rarrafa zuwa bandaki ta dauro alwala ta fito tayi sallah zaune sannan ta koma gado ta kwanta, daukar wayarta tayi taga kiran shi, da sauri tayi dailing no dinsa.
Kaman jira yake, yayi azaman dauka yace "kina Ina ?
Murya ciki ciki, kaman mai shirin kuka tace "ina gida, tuna dazu nadawo saidai bana jin dadi"
Bata rai yayi.
"Mike damun ki ?
Shuru tayi, tanason cemai kafar ta ke ciwo tana tsoron ya tambayeta sanadi, ga kuma kanta na ciwo, wahalalliyar ajiyar zuciya ta sauke sannan tace "kaina ke ciwo".
So yage ya gasgata zancen Salim, yace "deme kuma ?
Zuciya daya bakinta ya furta "cikina"
Baice komai ba kuma bai jira abunda zata kuma cewa ba ya katse wayar, bata kawo komai aranta ba ta ajiye wayar hade da gyara kwanciyar ta.
Kasa gasgata zance Mujahid yayi, yanaso ya yadda da abunda Salim yace ya kasa, kalllon wayarsa yayi dake rike hannusa jiran ko zata kira shi yaji shuru.. Jiki sanyaye ya ajiye wayar aranshi yana fadin "Tabbas Biri yayi kama da mutum....

Masu korafin basu san ma'anar zuma sai da wuta, bara na maku bayani dalla dalla.

Shi sak'ar zuma baa iya daukan shi saboda Zuma🐝🐝 dake makale jikin sakar, komin yadda zaki ki kori Zuma bazata koru ba tsananin yadda take da taurin kai da kafiya maganin ta daya ce wato Wuta...kinasa mata wuta zata saduda ta gudu tabar sak'arta ba tare da bata lokaci ba.

Shiyasa hausawa sukace Zuma Sai da wuta.

Shin acikin
Mujahid
Salma
Salim
Jaafar
Da
Junaina waye Zuman waye wutan ??

Ina jiran Amsar ku....
[9/7, 12:37 AM] Xarah Bukar: Zuma Sai Da Wuta

~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ
(Aunty Cute)
®NWA

Vote me on Wattpad @Cutexarah

xarahbukar.wordpress.com

52

Da Magrib Mom ta lek'a d'akinta kansacewar taji shigowarta tun rana, ganin bata da niyyah fitowa ya sanya ta bibiyar ta, kwance ta ganta can k'arshe gado akudundune, k'arasa wa gurin tayi tahau tashin ta, bude ido salma tayi, jikinta gabad'aya k'yamar yake tsabar yadda zazzab'i mai zafin gaske ya cafketa, hankali mom ne ya tashi ganin yanayi ta, ba tare da b'ata lokaci ba ta taimaka mata tasa kaya suka fita waje, kiran Salim tayi yaxo yaja su zuwa asibiti, a mota sai faman yi mata sannu yake tamkar ba shine sanadi ba, bata iya amsa shiba har suka isa asibiti aka bata gado.
Koda Mujahid ya koma gida kasa zaune yayi, kalaman Salim ke yawo a kwakwalwan kansa. Kamar wani tab'abb'e yahau girgiza kansa yana fadin it cant be possible, yana son Salma kuma yayi trusting dinta, ba zai tab'a yadda da zance salim ba" wayarsa dake ajiye kan 3 sitter yadau hade da mik'ewa tsaya yayi dailing no din Salma, har kusan sau biyar bata dauka ba, nan take wani mugun haushin ta ya dirar mai, cilla wayar yayi kam kujerar sannan ya zauna kasa hade da dafe kansa. Atakaice dai ranar dakyar ya iya runtsawa, da safe bayan yayi shirin sa na office fita yayi, bai zarce ko ina ba sai gidan su Salma, ya jima yana horn daga bisani mai Gadi ya iske shi ya sanar mai babu kowa agidan sai Salim, hajiya da diyarta kuma suna asibiti, Alhaji dama baya gari.
Komawa Mota Mujahid yayi ran sa bak'in k'irin, zuciyar sa kuwa ta gama gasgatar mai da gaskian lamarin, wani irin haushi kanshi yake ji da tun farko yayi sake har Salma ta shigo mai rayuwa, yana son salma, she's the only gal da yasan he can die for, saidai bazai taba yadda ta raina mai hankali ba much less tayi deceiving dinsa with her cute innocent face, nambarta dake wayar sa yayi deleting hade da kunna motan, kallan gate din gidan yayi yace you're dead to me" afusace yaja motar sa yayi gaba.

"Wai yaushe hakan ta faru bansani ba" acewar Mom, zaune take gefe gadon da Salma ke kwance, kafar mai targade daure da farin gyalle, Yunkurowa Salma tayi ta jingine jikinta a karfan gado, Magana zatayi Salim ya shigo rike da flask da Mom ta aikeshi gida ya dauko, Harara Salma takai mai, yace "sannu sister, ya jikin ?
Atakaice tace "lapia" duban Mom tayi tace "ina tafiya nayi missing steps na fadi"
Mom tace "tsautsayi kenan baya wuce ranar sa, Allah ya tsare gaba, ya ciwon Kan ?
Da sauki" Salma ta amsa, tashi Mom tayi ta fita gurin Doctor, kusa da ita Salim ya karaso hade da marairece fiska yace "sis am sorry, duk nina jaza maki"
Tabe baki tayi
"Ba komai ya wuce, ni yanzu kawai gida nakeson komawa, nabar wayata kan gado" kaman zatayi kuka ta karashe zance, Mujahid ne aranta, tana son fadimai tana asibiti karya jita shuru.
Mom ce tadawo dakin tana waya da Daddy ya mike ya fice, mikewa Salma wayan tayi ta amsa yiwa Daddy magana.

K'ashe gari likita ya sallame su, suna isowa gidan wayarta tadau ka taga miss call dinsa, farin ciki ne ya ziyar ceta ganin yadda ya damu da ita, kiran sa tahauyi fuskar ta dauke da murmushi.

Alokacin Mujahid zaune yake office yana danna laptop dake gabansa, fuskar sa babu annuri, shi kadai yasan yadda yake jin zafi azuciyar sa, yana ganin kiran nambarta yaki dauka, har kusan sau goma takira bai dauka ba, karshen ma wulla nambarta yayi a reject list ya cigaba da aikin gabansa yana huci.

Mamaki ne yakama Salma alamun da wayarta ya nuna mata nambarta is rejected, zama tayi tana tunanin lapia kuwa, bata saduda ba daddare tahau kokarin kirasan still abu daya yake nuna mata, hankalinta ne ya tashi, duk atunaninta ko wani mugun abune ya faru dashi. Kasa runtsawa tayi har garin Allah ya waye, da safe shiryawa tayi ta shiga motarta taja zuwa office dinsa, tana isa daga main entrance gate din wasu polisawa suka hanata shiga, mamaki ne yakamata dan kuwa sun santa duk zuwanta barinta suke, rokon su tahau yi da magiya, fir suka hanata shiga karshe ma ce mata sukai Ogan su yace karsu barta ta shigo.
Jiki sabule ta koma gida, kwata kwata batama san miya faru hakan ke faruwa ba, batai kasa a gwiwwaba saida tayi kwana uku tana zuwa basa barinta ta shiga, hankalinta sosai ya tashi, a kwana na hud'un ne ta kuma komawa, tana cikin rokonsu Mujahid ya iso gurin cikin motarsa zai shiga, ajiyar zuciya ta sauke ta nufesa da sauri, saidai mi, ko kallanta bai yiba yakara baiwa motan wuta ya shige ciki yabarta nan tsaye cikin tsananin tashin hankali marar mitsaltuwa, nan take zuciyar ta ya fadi mata somthing is not right, kai komo tahau yi agurin tana tunanin. Horn taji bayanta da azama ta juwa, tagane shi, Mubarak ne da take gani office din mujahid, karasa gurinsa tayi hade da gaidashi, yace "mai kikeyi anan, ki shiga mana".
Kai ta girgiza, tace "Mujahid ya basu order karsu bari na shiga, dan Allah ka taimaka ni, i need to talk to him".
Tausayi sosai tabashi, saidai yasan Mujahid da kafiya koda ya shigar da Salma bazai yadda ta shigar mai office ba tunda har yasa doka a entrance kar abari tashigo, ko miya hadusu kuma, duk axuci yake zancen.
Yace "why not ki hakura da ganinshi ki tafi gida, i dont tink zai kulaki"
Kaman zatayi kuka ta marairace fuska tace "dan Allah ka tamakeni, yaki kulani for d past 4 dayx, i need to talk to him, inason sanin miyasa yake ignoring dina all of a sudden"
Shuru Mubarak yayi yana naiman mafitan yadda hakan zai yuyu, ajiyar zuciya ya sauke yace "kinga abu daya zan iya maki, ki fadi inda kikeso ku hadu, ni kuma na maki alkwarin kawo maki Mujahid"
Nisawa Salma ayi, taji dadin abunda yace, hakan kadai zaisa ta hadu da Mujahid harya saurareta.
Risinawa tayi tace "nagode sosai"
Dariya yayi
"Baki fadi inda zan kawo miki shi ba"
Murmushi tayi tana tunanin peaceful gurin da yakamata su hadu, can ta tuna da plantation garden na Daddy, gurin nada matikar girma, kyau da shaawa uwa uba akwai flawowi da mayan bishiyoyi gwanin shawaa.
Tace "kasan A & M gardens na hanyar Dikkoh ?
Yace "uhhm nasan gurin, can kike so ku hadu".
Cike da farin ciki tace eh, dariya yayi yace ba matsala gobe by 4.30 zaki ganmu"
Godiya sosai tamai sannan ya wuce, motarta taja ta wuce Garden din.
Tana isa Baba nayaro ta iske, mai kula da shuke shuke gurin, gaidashi tayi aladabce ya amsa cike da fara'a, suna shiri sosai da Salma kasancewar yawanci idan damuwa tayi mata yawa gurin take zuwa shan iska.
Gurin da pink da yellow flowers suka fi yawa nan Salma tacemai ya gyara gurin yayi kyau dan tana da bako, so take idan yazo duk wata bakin cikin sa ya yaye, shikam Baba nayaro dariya sosai tabashi yahau zolayan ta yayi sirki.... Sun dan jima suna magana daga bisani Salma tamai sallama ta koma gida..
Salim ta tadda ya fito daga motar sa, da alamun shigowar sa gidan kenan, "Salma daga ina kike da yamma haka ? Ya fada cikin salon kulawa kaman gaske, deep down kuma so yake yasan ina taje dan kwana biyu baya ganin ta a office din Mujahid.
Ganin yadda yake mata kirki kwana biu yasa ta saki fuska tace "ya salim Ogan ka naban Tough tym, kwata kwata nakasa gane kanshi, yanxu baya kulani"
Murmushi yayi wanda shi kadai yasan maanar sa yace "kin manta The boss is always d boss, fadin Sakon ki saina kaimai".
Tabe baki tayi "no need gobe zamu hadu a Garden din Daddy by 4pm suprised visit zamu ma juna.."
Ware ido yayi in shocked, "yasan Garden dinne ?
Dariya tayi, tayi gaba tana fadin "a'a, gobe zai sani" tafiyar ta tayi..
Tsaye Salim yayi zuciyar shi na kuna, aranshi yace "muje zuwa, mahaukaci yahau kura", naushin iska yayi ya wuce part dinsa.

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.