Complete Hausa Novels

Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Zuma Saida Wuta Part 1 Complete Hausa Novel.txt

Chapter 25 of 41

Sai da gari yayi haske Mom da Daddy suka shirya fita asibiti gurin Salma, har sun shiga mota yan'uwan Baba nayaro suka kira Daddy suka fadimai rasuwar, hankalinsa sosai ya tashi fasa zuwa asibitin yayi ya nufi Gidan taaziya, Mom kam asibiti ta wuto nan ta iske Hajiya da Jafar na jiranta a haraban gurin, shiga sukayi wards din, sukayi saan police daya ke gurin wanda ya iso da safe baisan da order din Mujahid ba yabar Jaafar ya shiga, Mom da Hajiya sun tsaya suna magana awaje.

Bacci Salma take ya karasa ya zauna kusa da ita, kallonta yake cike da so da kauna, shafan pretty face dinta yayi har zuwa kan lips dinta yana admiring dinta, dan motsawa tayi yayi sauri cire hannusa, bude ido tayi ahankalin ta dubesa, atunaninta Mujahid ne, tace "ina abinci ? Can kasan makoshinta tayi maganar.
Murmushi yayi yace "yanxu xaa kawo, how are you feeling ?
Sai sannan tagane ba Mujahid bane, yunkurowa zaune tayi kokarin yi, yayi sauri temaka mata.
Kallan shi tayi ayayinda shima kallon ta yake, murya kasa kasa tace "thank you"
"For what" ya fada hade da rike hannuta mai sakale da handcuff, haushi ne sosai yakama shi yasan aikin Mujahid ne.
Murmushi tayi, jikin sanyi voice tace "kaman nasanka wani wuri kafin ranar da kayi saving dina?
Dariya yayi wanda ya kara fiddo kyau shi,
aranta tace "so cute dashi, ba kaman banzan nan ba kullum fuska daure"
Magana zaiyi Mom ta shigo dakin, Hajiya abayanta, da sauri Mom ta karasa gurin Jafar ya mike tsaye ya matsa gefe, kuka Salma ta fashe dashi ganin Mom, nan take ta susuce tahau rarrashi, dakyar Salma tayi shuru tace "Mom yunwa nakeji, kuma acire min wannan abun" turo baki tayi tanai mata nuni da cuffs din hannuta.
"Mun shige su" Mom ta fada cike da mamaki, kallon Hajiya tayi tace "amma babu azzalimi kaman Officer nan, ji mugunta dan Allah.."
Sai sannan Salma ta lura da Hajiya dake kallon su jiki sanyaye, shuru Hajiya tayi sanin cewa d'anta ne azzalimun da Mom ta ambata.
Maida dubanta Salma tayi ga Mom, murya kasa kasa tace "Mom matar nan kaman Hajiyar Ummata"
"Itace, tare da d'anta daya taimake ki" nuna jaafar Mom tayi,
Farin ciki ne ya mamaye Salma, duk sai taji Jafar ya kara kwanta mata, ashe dai jinin tane shiyasa ya ceceta.
"Hajiya.." Salma ta fada tana kallon Hajiya, murmushi hajiya tayi ta mike ta karasa gareta tana fadin "aina dauka bazaki gane niba" rugume juna sukayi, Salma na kukan farin ciki.

Daddy na zuwa gidan Baba nayaro taaziya yayi masu, bai samu janaizar saba, abun tausayi dayaji sanadin Mutuwarsa, tashin hankali biyu ne suka hade mai, jiki babu kwari ya wuce NPF (HQ) gurin head of police, sir Ahmad.
Kara tattauna abunda ke faruwa sukayi, Sir Ahmad yace tabbas yasan da case din saidai baisan diyar shice major suspect ba, atake ya tura department dinsu Mujahid kiran sa, baa same shiba ya aika a kira mai Mubarak sanin cewa su biyu ne witness aranar da abun yafaru.
Mubarak na zuwa, Sir Ahmad yahau shi da tambayo yi, bai boye komai ba ya zayyane masu labarin salma da mujahid tun farkon haduwar su har zuwa ranar da abunda ya faru, ya kuma jajjada wa sir Ahmad lailai Mujahid baya cikin hankalin sa, So da kiyyaya sun rufe mai ido.
Zufa Daddy yahau yi, gano cewa duk case dun revovle around Baba nayaro, "amma yaron nan ya cika dan iska, yan'uwan marigayi basu pressing charges ba saikai dan kawai wata manufarka daban zaka tsangwama d'iyata" azuci Daddy yayi maganan.
Sir Ahmad yace "zaancen banza kenan, wato personal feeling dinsa yake hadawa da aikinsa dan cimma burinsa, dan bashi da kunya kuma harda aika gawa asibiti ayi autopsy alhalin yasa ko kyankyaso yarinya bata iya kashewa"
"Kaga Mubarak, nemi wani ya amso mana autopsy din mugani"
Ba musu Mubarak ya mike ya fice, police din daya kai gawar asibiti ya tura ya amso, Doctor kam zuciya daya yabada atunaninsa Mujahid ne ya aiko.

Mujahid na Tuki ya dunga ganin call daga office, asibiti zaije amsan autopsy ya fasa ya wuce Office, yana isa aka sanar mai Sir Ahmad na kiran shi, hankali kwance ya shiga office din, wani mugun Harara Daddy yakai mai, shan jinin jikinsa yayi ya dake ya karasa gurin Sir Ahmad.
Sir Ahmad yace "yanxu M. Abdulsalam ka kyauta da abunda kayi, kaida kake daya daga cikin wanda suka san aikinsu, miyasa kakeso yin injustice ?
Kallon bangane ba Mujahid yamai, police ne ya shigo da autopsy result ya mikawa Sir Ahmad, Mujahid kaman yayi ihu.
Budewa Sir Ahmad yayi ya karanta sanna ya dubesa yace "the deceased was beating with severe blows before stab to death, yanxu gayamin ita buduwarta ka da kakejin haushi itace tamai dukan kafin ta kashe shi ko kuwa she is stupid dazata kashe shi kuma ta tsaya yimai kuka ba tare data gudu ba"
Shuru Mujahid yayi yana kallom Mubarak da wutsiyan ido, sarai yasan shiya tona komai..
Sir Ahmad yace "ka godewa Allah Mahaifin yarinya baiyi pressing charges akan attempting kashe diyar sa dakayi ba, daga yanxu nayi closing case dinnan, kai kuna you're suspended till further notice".
Mugun Kallon Mujahid yakaiwa Sir Ahmad, afusace ya ciro bage, Id da bingidar ya zubarsu kan table dinsa, hade da ficewa afusace yanai huci, mikewa Mubarak yayi yabi bayansa..
Daddy yace "hukuncin yayi tsauri da yawa.
Sir Ahmad yace "Barni dashi, so nake yagano bambancin sentimental feelings dinsa da aikinsa".

Mubarak na kwalla mai kira ko kallan sa baiyi ba,
Ya shige motarsa yaja afusace, gurin abinci ya nufa ya siya take away sannan yaja zuwa asibiti gurin Salma..
Tundaga nesa ya hangi babu police gurin, haushi ne yakamasa, yana shiga dakin mutanan daya gani yasa shi daskarewa gurin, Hajiya da Mom zaune gefe suna hira, Jafar zaune kusa da Salma yana bata tea abakin tana zuba mai shagwaban ta koshi, sai wani lallabata yake.
"Kai kuma fah, daga ina ? Mom tafada fuska ba annuri ganinsa sanyen da kayan yan sanda.
Afusace Hajiya ta mike ta kwashe shi da marin da saidai Salma ta saki ihu tsabar razana.
Bai damu da marin ba banda jafar dayake watsawa mugun kallo.
"Dan ubanka bani mukullin Handcuffs din.." Hajiya ta fada cikin karaji.
Karamin mukullin ya mikata ta amsa ta jefawa jafar ya cabe yayi sauri bude handcuffs din, mikewa yayi yabawa hajiya, "ungo tsiyar ka, kuma ka fice anan" hajiya ta fadi hade dajan haunnsa ta dunkule mai Handcuffs din ciki, Mujahid baice komai ba yayi kokarin ajiye abincin, tsawa Hajiya tamai tace ya wuce da abinci baa bukata, zuciyarsa na tafasa ya juya ya fice.

Mom tace "dan banxan yaro, waishi police, kinyi maganin shege"
Mugun Kallo Salma takai mata ba tare data lura ba, aranta adduaa take Allah yasa Mujahid ba d'an Hajiya bane, idan kuwa hakan ya tabbata she won't forgive him da boyemata shi dan uwan tane da yayi.

Mujahid na Fitowa ya Hadu da Daddy zai wuce ciki, kawar dakai yayi gefe ya wuce ranshi na kuna.
Dariya Daddy yayi yace "kaji da rashin aikin ka, Salma kuwa tama nisa".

Wayyo su oooo anyi 2 zero 😂
[9/7, 12:37 AM] Xarah Bukar: Zuma Sai Da Wuta

~na~
©ҳaɾaɧ bųkaɾ
(Aunty Cute)

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.