Complete Hausa Novels

Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Da_Izzata_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 19 of 89

Page35 & 36

Kamal da yayi mutuwar zaune tun lokacin da amir ya fara magana akan Asma'unshi, jiki ba kwari ya miqe ya shige room d'inshi, ba abinda yafi tsaya mai arai irin cewa da amir yayi , (wlh bada don nayiwa kaina wani tanadi ba. da ba abinda zai hana nayi wuff da ita kuma ko yanzu ma bata baci ba") ya maimaita wannan kalman a fili da zuciyarshi yafi sau hamsin

Me hakan ke nufi karfa ya tsaya sanya ya sake rasa Asmah a karo na biyu , karfa yayi saken da zai kuma rasa second Chance d'inshi,
Tunawa yayi har yanzu fa Asmah bata bashi gamsasshiyar amsa game da maganar su ta rannan ba , a fili ya furta "ya zama dole ki bani amsata a gobe goben nan, ya zama dole nasan matsayi na a gareki, ya zama dole manyan mu Susan da maganar nan, Susan da zamana kar na zauna kallon ruwa kwado yamun qafa, a haka ya kwanta barci yanata tuna ni da'ker bacci barawo ya dauke shi...

Asmah anata bangaren ta riga ta gama shawara tsakanin ta da zuciyarta , ta karbi soyayyar ya kamal da hannu bibbiyu ko dan kyauta tawanshi gareta, ina laifin masoyinka. Ita kam dai ta amince da kamal indai har zai mata alfarmar barinta tayi karatun ta lpy ba tare da manya sunsan da maganar ba ,

Washe gari ummi ta iso daga abuja ita da yan biyun ta maza kannan amir, wadan da qanana ne baza su wuce shekara takwas ba, don bayan haihuwar amir ta dade kafin ta sake haihuwa har an cire rai ma, ta sauka a d'akinta dake part din hajiya mama Wanda in tazo anan take sauka , yau yan matan mummy ummin su tazo, suna can part din hajiya mama acan suka wuni sai surutu suke zuba mata , ita kuma tana biye musu taji mastalolinsu, tana basu shawarwari inna bada shawaran ne , don tun basu kai haka ba ta basu wannna daman na duk abinda ke damun susanar mata , kar su yarda su sanar ma wani a waje damuwarasu,ta jasu a jiki sosai ta maida su tamkar qawayenta,

Ranar yan matan mummy part din hajiya mama suka wuni kwana ne kawai basuyi can ba , don sai wuraren goma suka dawo part dinsu lokacin na mummy na sashen daddy,don haka dakinsu suka wuce suka kwanta sai bacci.

Washe gari juma'a ma haka suka tashi cikin hada hada don gida yadan cika, duk da ba'ayi gayyata ba saida mutane suka zo,

Zahra da Asmah sallama suka wa mummy zasuje amso dinkin su don tailorn ya kirasu ya gama , su biyu zasuje don amira da batool na sashen mami suna taya ta wasu aiyukan, cikon kud'in d'inkin mummy ta basu suka nufo parking lot da niyyar bello ya kaisu, nan suka tarar bello naya nan wai Aslam ya aike shi , juyawa sukayi da niyyar komawa ciki su jira shi, mai gadi ya wangale get motar yaya kamal ya kunno kai cikin gidan , zahra na ganin shi ta fara murna tace "yawwa ga ya kamal nan ma bar in roqeshi ya kaimu" Asmah dai shiru ta mata, da sauri zahra ta nufi motar kamal daya paker ko fitowa bai kaigayi ba , ta window tadan duqa tace "sannu da dawowa ya kamal " d'agowa yayi jin magana ta window ganin zahra ce yasa shi sakin murmushi sannan yace"yawwa zahra'u ya gida ". tace "lpy qlau, don Allah ya kamal ka kaimu tunga road mu amso dinkin mu na biki da zamusa gobe , munzo bello ya kaimu wai baya nan ya Aslam ya aikeshi" kamal yace "kai zahra na gaji fah bakiga dawowa na kenan daga gurin aiki ba gashi lokacin masallaci ya kusa "marairaice fuska tayi tace "don Allah ya kamal, tana hade hannayenta alamar roqo🙏,

dagowa yayi ya kalleta ganin yadda ta marairaice yace"dondai kece fa sis zahra, da batool ce da ba inda zanje, shiga muje na kaiki"tsallen murna tayi tana jin dadi tace "nida Asmah ne " daga murya tayi tace "Asmah zo muje ya kamal ya kaimu" bude gaban mota tayi ta shiga ,Asmah tazo ta bude baya itama ta zauna sannan tace "sannu da dawowa ya kamal ya aiki" ta cikin madubi ya kalleta kafin ya amsa mata da "lpy qlau my Asmah" Rivas yayi da motar mai gadi ya bude musu get suka fice daga gidan,

Kamal ta cikin madubi yake Satan kallon Asmah dake zaune a bayan mota duk d'agowan da zatayi kuwa sai sun hada ido

Dai dai zasuhau kan babban titin da zai kaisu tunga road suka gifta motar Dr bash, shida Aslam da amir ne acikin motar, zasuje gida ne donyin shirin sallan juma'a, kasancewar motar Dr bash mai duhun gilashi ne , kuma basu San motar shi ba balle Susan ko sune aciki, suko su Amir rass suka gane su,sboda dukkan su sunsan motar kamal kuma glass d'inshi fari ne ana iya ganin na cikin motar,

Bash dake tuqi ya kalli Amir dake gefen shi yace "wai dan Allah Amir na tambayeka mana" Amir yace"inajinka Allah yasa na sani" bash yace "yammatan da na gani a motar kamal yanzu su waye" Amir yace" meyasa kake tambaya " bash yace "kaga wannan na bayan motar" Amir yace "eh Asmah kenan" Dr bash yace "tun ranar dana fara ganinta washe garin ranar dana dawo 9ja wlh zuciyata ta kamu da sonta ko baccin kirki bana iyayi saboda tinaninta, amma kullum nama Aslam maganar ta saiya shareni kokuma yace min shi bai ganeta ba, alhali ranar muna tare na fara ganinta ta fito daga part din mummy" Amir ya juyo ya kalli Dr bash yace"da gaske kakeyi bashir " bash yace "na taba maka irin wasan nan ne"Amir yace"aiko zan shige maka gaba indai da gaske kake don wlh yarinyace na tsattsatsiya mai hankali, duk Wanda ya samu daman aurenta kuma ya saki yayi babban asara," ya qarashe maganar yana kallon Aslam ta madubi, bash yace"to wacece ita a gare ku". Amir yace "kanwarmu ce, jikan alhaji Mallam cefa ba kasan shi ba babban malamin nan aminin alhaji baba, kasan shi ai" bash yace "sani kai, da muna yara har kwana na tabayi a gidan shi da mukaje da Aslam ruwan sama ya tare mu sai muka kwana, tsohon kirkine wlh" Amir yace " to jikan shice ta wurin danshi na fari alhaji aminu mai rasuwa. marainiyace iyayenta sun rasu tun tana qarama a gidanmu ta tashi, sunanta Asma'u". Bash yace "Allah sarki Allah ya jiqansu, to ita wacce ta zauna a front sit dinnan fa" Amir yace yan biyu ne fa baka ganeta bane zahra ce fa". bash yace "haba don Allah" amir yace "Allah kuwa" bash yace "eh lallai girman mace ba wuya yan biyu ne suka girma haka , Allah mai iko, to amira fa?' bash ya sake tambaya murmushi Amir ya sake ganin an ambaci sanyin idayanshi yace"tana nan lpy itama ta zama ammata, ko Aslam,?" Ya fada yana dan juyowa ya kalli Aslam ,

Aslam da tun dazu ranshi ke tafasa jin abinda suke fad'a ya watsawa Amir mugun kallo ya dauke kai, ranshi in yayi dubu ya baci, kwata kwata a rayuwarsa baya son raini da qasakanci, amma ya lura bash da Amir suna Neman ja mishi raini a gurin qananan yaran daya goya a bayan shi, yaran da yake kallo har yanzu a mastayin jarirai, daidai lokacin mai gadi ya bude musu get suka shiga gidan don yin shirin masallaci.....

Har qofar shagon dinkin kamal ya kaisu, ya kuma biya cikon kudin dinkin, basu wani tsattsaya ba ,suka dawo gida domin lokacin sallah ya kusa, kamal dimma inbaiyi sauri ba da'ker ya samu sallah,

Don haka yana sauke su zahra ta dauki ledan kayan ta fara yin gaban ,tana cewa"ya kamal mun gode Allah ya saka maka da alheri,' ta shige ciki, Asmah ma godiya ta masa ita ma, ta fito zata wuce tanama zahra qorafin bata jirata ba,
Kamal ya kira sunanta , juyowa tayi ta sauke mishi wadannan dara darn idanun nata daya sashi jin wani yarrr ajikin shi ,murmushi ya sakar mata tare da cewa " I hope kin gama tunanin ko", shiru tayi , yace "well ki shirya anjima zanzo naji amsata " gyada mai kai kawai tayi , yace "OK barin je masallaci saina dawo ' to kawai tace mishi tayi gaba, shima motar ya koma yayi Rivas ya fice daga gidan don zuwa masallaci.......

Oum ummeetarh
07041130088

Share
and
comment
fi sabilillah🙏

Date: Oct 15, 2022

💖DAMA TA BIYU💖

BY

~AYSHA NALADO~

FREE BOOK

{nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rada mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu}

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.