Complete Hausa Novels

Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel

Reading file: Da_Izzata_Part_1_Complete_Hausa_Novel.txt

Chapter 87 of 89

Page 130

Ganin yadda Aslam ya kafe shi da jajayen idanun shi yana huci kamar wani mayunwacin zaki, sai da ya firgita , amma dake riƙƙeƙen ɗan duniya ne daure wa yayi ko a fuska bai nuna ya razana ba sai ma ci gaba yayi da cewa"Ba da kai nake magana ba fitsararre ka zuba min wasu kwala kwalan idanun ka makar na kwadi, nace dan uban uban ka ka kyale min ɗiya ta." Bai dauke idanu akan shi ba kuma bai kyale tan ba, "OK baza ka kyale ta ba ko? To ina zuwa a kwai wadanda zasu shiga tsakani na da kai, zaka gane ƙaramin ɗan iska ne kai." Yana gama faɗin haka ya juya da sauri fuuu kamar zai tashi sama ya fice daga gidan, abu biyu ne ya saka shi fice wa ba tare da zee ba, na farko dan ya gujewa wannan kallon da Aslam ke mishi dan har ga Allah ya tsora ta da yanayin shi, yasan bai da ƙarfi yin dambe da Aslam koda hakan ta kama sai dai a nakasa shi a banza, na biyu kuwa dan ya kwaso police suzo su tafi da Aslam, dan wannan karon yayi alkawarin sai ya wulakan ta shi, don idan ya kulle shi a wannan karon, in ba wani ikon Allah ba sai dai ya kare rayuwar shi a gidan maza. Har ya fice daga get ɗin Aslam bai ɗauke kanshi daga kallon shiba , ba komai ne ya hana shi haɗa ma Dad jini da majina ba, sai dan darajar mutum biyu masu daraja a gareshi na farko little na biyu kuwa ita ce zee, duk lalacewar Dad mahaifin ta ne, Kuma su iyaye komai munin halin su ba'a kin su tana son uban ta sosai kamar yadda shima yake son ta, idan ya mishi wani abu makamancin duka ko zagi tabbas idan ta farka baza ta ji daɗi ba, ga kuma little da sauran ƴaƴan da zasu haifa nan gaba tare da ita, idan har ya duki Dad zai zama abin gori ne a gare su kuma ma ai shi yana da ilmi idan ya biye mishi sun zama ɗaya kenan.

Da'ker ta samu ta lallaba ta lalubi jikin kujera ta dafa ta mike, tana jin ta tsaye kan ƙafafun ta take duk abin da ke faruwa ya shiga dawo mata da gudu ta nufi waje tana kwala kiran anty zee hango sun da tayi yasa ta nufo su, ganin zee kwance a hannun Aslam bata numfashi yasa ta sauri duƙewa cikin tashin hankalin da tsinkewar zuciya ta shiga jijjjgata tana kiran sunan ta, shiru babu ko alamar zata motsa, dago hannun ta da zata yi da nufin ta tashi taje ta kawo ruwa a yayyafa mata sai ganin hannun tayi caɓal da jini, hankalin ta ne ya kara tashi cikin kuka tace "innalillahi wainnailaihi rajiun,shike nan ya Aslam ya kashe mana ita." Sai lokacin ya lura da hannun Asmah shima hankalin shi ba karamin tashi yayi ba yunkurawa yayi ya miƙe da ita sai ga jina faca faca ya na bin jikin ta, a guje ya nufi mota da ita ya buɗe bayan ya kwantar da ita, itama Asmah rufa mai baya tayi ta buɗe gefen me zaman banza ta shi a haukace ya figi motar ya fice daga gidan, sunzo dai dai fita kwanar gidan wanda zai hau da su babban titi suka ga cincirundon mutanen a tsatstsaye tun daga nisa ya din ga danna horn, ganin yadda yake mugun gudu yana danna horn yasa tun kofin su karaso wajen mutanen suka dare suka basu hanya, bai tsaya bi ko tambayar meke faruwa ba ya harba kan babban titi ya dauki hanyar wani babban private hospital, yana shiga aka karbe ta akayi emergency room da ita, likitoci kusan uku suka rufa akan ta domin ceto rayuwar ta abin ka da asibitin masu kumbar susa

A fusace Dad ya bar gidan Aslam da nufin ya nufi police headquarter ya debo ƴan sanda ya biya manyan su kudi dan suzo suci mutumin Aslam sumai dukan tsiya sannu su tafi dashi su kulle shi kuma ya dauki yar shi ya tafi da ita, yana tafe yana sambatu yana zage zage kamar wani taɓɓaɓe gaba daya hankalin shi baya jikin shi burin shi kawai ya ganshi a police station, yazo tsalleke titin domin ya koma hannu da zai samu taxi cikin rashin sani wani tsohon Sharon ya shararo da gudu birke ya tsinke mai tun daga nesa yake ta danna ma Dad horn amma ina baiji ba hankalin shi baya jikin shi idanunshi sun rufe kunnuwan shi sun ɗoɗe tsabar bala'in dake cin zuciyar, aikuwa cikin hukuncin ubangiji mai Sharon ɗinnan yayi sama da Dad kuma ganin ba kowa abin ka da unguwan yan gayu yasa mai Sharon dinnan fece wa ya bar Dad nan kwance rai a hannun Allah, me gadin dake farkon Layin ne ya fito da nufin yin wani uzirin sai ganin mutum yayi kwance cikin jini shine fa yayi kururuwa mutane suka dan fiffito yawancin su ma masu gadin gidajen unguwan ne, koda suka fiffito tsayawa suka yinyi cirko cirko ana shawara an rasa wa zai taimaka mai zuwa asibiti, suna cikin wannan tsayuwar ne motar Aslam tazo ta wuce su da mugun gudu, kasancewar cikin tashin hankali yake yasa bai kula da abin da ke faruwa ba, wani he ya bada shawara a shiga gidajen dake kusa a gaya musu suzo su duba ko dan uwan su ne moto ya buge dan ga dukkan alamu daga cikin wannan unguwar ya fito, da wannan shawaran suka fara bi gidanjen da ke kusa cikin haka ne suka zo gidan Aslam, me gadi dake nan duk cikin shi ya duri ruwa ya kasa zaune ya kasa tsaye don duk abin da ke faruwa akan idanun shi ne abin da yafi daga mai hankalin shine yadda yaga Aslam ya figi mota a tsiya ce , ya tarbi mutum biyu da suka yi sallama a kofar gidan , jin abin da ke tafe dasu kuwa baiyi kasa a gwuiwa ba yace suje ya gani duk da ko kusa bai kawo tunanin Dad bane yama fi ba cewa to ko Aslam ne ya buge mutumin tunda yaga ba cikin hayyacin shi ya figi motar ba. Ko da suka je kawai sai yaga mutum da ya fita a gidan su mintuna ƙalilin da suka wuce mutumin da ya mare shi yanzu yanzu ba tare da ya mishi komai ba, "Allahu Akbar." ya furta lallai dan Adam ba'a bakin komai yake ba yanzu wannan bawan Allah idan da yasan zai shiga cikin wannan mawuayacin halin nan da yan mintuna me zai kai shi aikata abin daya gama aika ta wa yanzu yanzu. Zuciyar musulumci take yaji tausayin Dad ya kama shi, dan kuwa duk wani mai imana idan yaga Dad dole ya tausaya mishi bai yi kasa a gwuiwa ba wurin cewa bai san shi b, amma ya bada shawaran a taro napep akai shi asibiti in yaso su likitocin saji dashi, take fa yawa suka amince da zance, ya samo me napep akayi general hospital da Dad kafafuwa na lilo alama

Likitoci sun sha matukar fama sosai kafin su samu su tsaida jinin daya barke mata da'ker suka ceto rayuwar ta, Aslam da Asmah kam sunan nan a kofar emergency room din Asmah sai kuka take yi Aslam yayi rarrashi har ya gaji ya kyale ta, shi karan kanshi karfin hali kawai yake yi, dan ya kasa zaune ya kasa tsaye, sai safa da marwa yake yi, lokacin da daya daga cikin likitocin dake duƙufe akan zee ya fito har rice rige sukeyi da Asmah wajen tambayar shi halin da take ciki, be basu amsa anan ba sai cewa da yayi su biyo shi office, bayan sun zauna file din ta ya bude ya shiga dan rubuce rubuce, Asmah kam ta kosa taji wani hali zee ke ciki hakan yasa tace "Dr pls wani hali take cike meya samu yar uwata." kallon su yayi tare da gyara zaman siririn farin glass din dake idanun shi yace "patient din da kuka kawo mana wato zainab Abdus-salam, ta samu miscarriage sakamokon wani tashin hankali da firgici data shiga na lokaci daya." Kamar saukar aradu haka Aslam yaji saukar maganar Dr a zuciyar shi Asmah kam tuni ta rushe da wani irin kuka kwace ce mata akayi zee din ta rasu, Aslam kam innalillahi wainnailaihi rajiun ya shiga furtawa a zuciyar shi, Dr ne y shiga rarrashin ta yana kwantar mata da hankali, dan Aslam bashi da karfin halin iya rarrashin ta a halin da yake ciki, ji yayi zuciyar ta kara daukar zafi,rintse idanu yayi yana jin tsanar Dad na kara baibaiye lungu da sako na zuciya shi, alkawari ya dauka tare da lasar takobin wannan karon bazai bari mahaifin zee ya shashi silla ba shari'a zai yi dashi bakin rai bakin fama daga nan har kotun koli na duniya sai anbi mishi hakkin shi akan Dad koda duk abin da ya mallaka zasu kare, jajayen idanu shi bude akan Dr cikin murya mai dauke da tsananin bacin rai yace "Dr wani hali matata take." Shi karan kanshi Dr abin ya bashi mamaki amma ya dauka duk bakin cikin rasa cikin ne yasa yake mai magana a haka, cikin muryar rarrashi Dr yace " matar ka tana lafiya munyi duk abin da ya kama ta muyi, harta wankin ciki duka munyi mata, yanzu haka barci take yi allura muka mata nan da awa 4 zata farka, ku kwantar da hankalin ku, babu wani wani matsala zata farka lafiya insha Allah." Rubutu ya ɗanyi a jikin wani dan paper ya mika wa Aslam gashi wannan magunguna ne zaka siyo mata na jini sunfi yawa aciki wanda zata din ga sha ba sai mun mata Karin jini ba idan tasha wadannan magungunan amsa Aslam yayi suka yi ma Dr godiya sannan suka fito Asmah ta shiga dakin da aka kwantar da zee shi kuma ya tafi pharmacy dan siyo magunguna.

Bayan ya dawo ya samu Asmah zaune a kan kujera hannunta cikin na zee dake ta sharar barci, ajiyar zuciya ya sauke ganin ta dawo daga suman da tayi yanzu barci take sai lokacin tunanin kiran su mummy ya fado mai, take kuwa ya lalubi waya ya kira Mami, kan kace kwabo asibiti ya cika da yan uwa, sai bayan isha'e zee ta farka kuma alhmdllh jikin da sauki sai dai Dr yace bazai sallame ta ba sai zuwa gobe, Mami da Asmah ne suka kwana a Asibiti, shi kuma Aslam ya tafi gida a gurin mai gadi ya samu little har ma yayi barci abin shi cikin net a kan dan karamin gadon dake dakin mai gadi, me gadi kamar ya gaya mai halin da dad ke ciki sai kuma kawai ya share,

A cen general hospital kuwa bayan sun kai Dad asibiti, cikin gaggawa a kayi cikin emergency dashi aka bashi gado,wadan da suka kawo shi wucewa suka yi bayan sun sanar wa likitocin cewa tsintar shi suka yi yayi accident a bakin hanya da alama mota ce ta buge shi kuma mai motar ya gudu.jin haka yasa akayi banza dashi tun da babu wanda zai tsaya mishi, sai bayan isha'e daker dai aka samu wani likita mai dan tausayi ya kula shi, jikin shi aka duba cikin sa'a aka samu wayar shi, a kulle wayar take hakan yasa aka cire daya daga cikin sim uku dake wayar aka saka a wani wayar take lambobi guda uku suka bayyana. Daughter, wife, Brother, ganin, haka yasa suka San duk wadannan makusantan shi ne, wani je ya bada shawaran a kira Brother saboda shi namiji ne zaifi matan saurin fahimtar lamari, Alhaji Abdur-rahman na zaune a falon shi yana hutawa shida matar shi kira ya shigo wayar shi, sunan daya gani ya matukar bashi mamaki kwarai sanin irin bakin zuciya na kanin nashi yasan sarai a yadda suka yi rabuwan baran baran karya ne ya neme shi nan kusa sai dai idan shine ya gaji ya neme shi, ajiye mamakin shi a gefe yayi ya daga wayar, maimakon ya tsinkayi muryar ƙanin nashi kamar yadda ya sakankance zai ji sai ya tsinkayi muryar wannan Dr , a gurguje ya sanar dashi abin da ke faruwa da me wannan lambar Alhaji Abdur-rahman yasha mamakin jin cewa a Nigeria ne ƙanin nashi yayi hatsari har ake neman shi a general hospital, jiki a sanyaye ya amsa wa Dr da cewa gashi nan zuwa nan da 20 minutes, suna ajiye wayar Mom ya kira yake tambayar ta ina Dad nan take ce mashi rabon da shi tun jiya, take ya sanar mata da abinda ke faruwa aiko dai hankali ba karamin tashi yayi ba nan ta fashe mashi da kuka a waya, daker ya dan rarrashe ta sama sama ya tashi ya kamo hanyar asibiti, sai da Alhaji Abdur-rahman ya iso ya bude ma Dad file yayi duk abin da ya kamata yayi sannan Dr din suka taba shi.

Dad ya nakasa iya nasaka dan gaba daya kafafun shi sun samu karaya bibbiyu ga kuma hannun shi na dama, banda uban ciwukan daya jijji ga kanshi daya fashe , fuskar shi ta canja kamanni lokaci guda haƙora ukun sama dana kasa duk sun zube sai wawakeken giɓi, su karan Kansu litocin sun tausaya mai kuma sun jinjina ma taurin ranshi da bai mutu ba duk da tarin ciwukan daya ji. Abinka da harkar nera suna gaya wa Alhaji Abdur-rahman akwai karaya za'ayi gyara yace a bashi Dad ya zai canza mai asibitin ba bata lokaci kuwa akayi cike ciken komai aka saka shi a. Ambulance sai asibitin da zee ke kwance.A cikin daren aka yi ma Dad ɗauri dan tsananin azaba harda su kashi a wando suma kuwa yayi yafi so uku yana farfaɗowa, gashi baisan ya kira Allah ba, sai tsala ihu yake yi kamar wani Arne, ranar gaba ɗaya asibitin sai da akasan da zaman Dad masu tausayi nayi masu dariya nayi, su Asmah da Mami ma sun sami labari duk da basu san ko wanene bane kwarai sun tausaya mai, Alhaji Abdur-rahman ne kaiɗai yake ta kai kawo akan shi har zuwa safe, sai da yaga komai ya daidai ta har barcin azaba ya kwashe Dad sannan ya yi sallama da likitoci da niyar zai je gida ya huta, zuwa anjima zai dawo, da safe wuraren karfe 7 Aslam ya iso asibiti,kusa da motar Alhaji Abdur-rahman yayi fakin ba tare da sani cewa motar shi bace, fito wa yayi ya zagayo ya buɗe ɗaya gefen ya dauki little juyowan da zai yi daidai lokacin Alhaji Abdur-rahman ya iso wajen fakin din domin shiga ɗaukar motarshi, kallon mamaki suka shiga bin juna da shi, Aslam na tunanin to waya gaya mishi zee na asibiti don shi a tunanin shi zee yazo dubawa, shi kuma yana tunanin ya akayi Aslam yasan Dad na asibitin nan to ko shima Dr ya kira shi, Aslam ya ƙarasa ya bashi hannu sukayi musabaha, Dad yace "Ya mukaji da wannan iftila'il kuma." Ba tare da ya fahimci komai ba yace "Sai godiyan Allah, amma jikin da sauƙi sosai Alhaji don Dr ma yace yau zai bamu sallama." Alhaji Abdur-rahman cikin mamaki "sallama Kuma! wa za'a ba sallama?" Aslam yace "Ita mana." "Ita wa?" Ya tambaya, Aslam shima abin ya fara ɗaure mishi kai dan haka yace " Ita Zainab ɗin." Zaro ido Alhaji Abdur-rahman yayi cikin kaɗuwa yace "kana nufin kace min Zainab na kwance a wannan asibitin ita ma?" Aslam yace "eh Alhaji ai na dauka ma ita kazo duba wa." Maimakon ya bashi amsa sai "innalillahi wainnailaihi rajiun ya shiga maimaita wa." Can kuma yace "Muje ka kaini wajen ta na duba ta meye ya same ta." Suna tafe Aslam ke gaya mishi ai ta samu miscarriage ne, Alhaji yace "subhanallahi garin yaya." Shiru ya danyi kamar bazai gaya mishi ba sai kuma wata zuciyar ta umarce shi daya faɗa domin barin kashi a ciki baya maganin yunwa, tuno kawai abin da ya faru don faɗawa Alhaji sai da yaji zuciyar shi ta dauki zafi dan sanyin data ɗan yi tuni ya gushe. Bai yi ƙasa a gwuiwa ya kwashe komai ya shiga gaya mishi, tunkan Aslam ya kai karshe Alhaji wata uwar burki ya taka tare da juyowa hankali tashe yace "Kana nufin Abdus-salam yaje gidan ka ajiya har yayi sanadin zubewar cikin jikin Zainab." Kasa bashi amsa Aslam yayi dan wani irin tukukin bakin ciki yake ji a ranshi. "Innalillahi wainnailaihi rajiun, Allah wadaran naka ya lalace, gaskiya Abdus-salam baiyi wa kanshi adalci ba dama na gaya mishi wani rabon karfi gareshi kisa yake, to shi Allah ma yaso shi bai mutu ba amma kuma da wannan halin daya shiga ai gara mutuwa." Kallon rashin fahimta Aslam ya shiga binshi dashi, ganin haka yasa ya kwashe duk abin da ke faruwa tun da ga daren jiya da aka kira shi a waya daga general hospital zuwa wayewar garin yau, ko ɗar Aslam baiji a ranshi sai ma cewa da yayi "Allah kyauta Allah ya kiyaye na gaba." Sun tarad da su jugum jugum kamar wa'inda aka aikowa da saƙon mutuwa, Asmah da Mami na zaune a bakin daya extra bed ɗin dake ɗakin, zee kuma na zaune a bakin nata bed din rike da cup din tea a hannun ta idanunta sunyi jajur alamar taci kuka ta ba uku lada, ganin wan mahaifin nata yasa ta sake fashewa da kukan da da'ker su Mami suka samu tayi shiru, shima direct gareta ya isa ya zauna a kusan da ita tare da kamo hannayenta ya rike cikin nashi, yana bin ta da wani irin kallon tausaya wa, cikin tsananin kuka tace "Abba dan Allah ka gaya min gaskiya da gaske Dad shine mahaifina shiya haifeni, Abba Dad kullum ikirarin shi yana sona yafi kowa sona a duniya amma wlh ni soyayyar shi ni batai mini rana ba, tun da har ya kasa bani farin ciki, ya kasa barina na zauna da mijina domin na sami Aljannahta aƙarƙashinsa, Abba Dad yayi sanadin da cikin jiki na ya fita, shin wannan wane irin sone?." Ta karashe da wani irin matsanancin kuka, jikinshi ya jawota ya rungume, Asmah da Mami tuni zuciyar su ta daɗa karyewa ji suka kamar su taya ta kuka, Aslam kam taɓe baki yayi ya dauke idanunshi daga garesu, daker Alhaji Abdur-rahman ya samu ya lallɓa zee ya samu ta tsagaita kukan ta, cikin kwantar da hankali yace "Kiyi hakuri Zainab ko wani bawa da kalar jarabtar da ubangiji yake mishi a rayuwar shi ta duniya, ke da mahaifin ki jarabtar ku iri ɗaya ne, shi kece jarabtarshi, kema shine jarabtar ki, kiyi hakuri ki daina jin kamar cewa ba shi ya haife ki ba, tabbas shi ya haifeki, amma Allah ya jarabce shi da wani irin makauniyar soyayya akan ki, wanda a karshe shine yayi sanadin nakasan shi." Nan kuma ya kwashe duk abin da ke faruwa da Dad ya sanar mata, kan kace kwabo ta kara birkicewa, sai kuka take tana kiran dadin ta, karshe ma ta tsige Karin ruwan dake hannunta tace ita gurin dadin ta zata tafi, wai a haka ma Alhaji Abdur-rahman bai gaya musu irin raunukar daya samu ba daga ita har Aslam ɗin kawai ce musu yayi, yayi hatsari, ba shiri Alhaji yasa aka kira Dr ya duba ta, a take ya rubuta mata sallama ma gaba ɗaya kawai, Alhaji Abdur-rahman yace Aslam ya kaita gida, aiko ta ƙeƙashe ƙasa babu inda zata je sai taga dadin ta, dan dole suka dunguma zuwa ɗakin da aka kwantar dashi,da taimakin wani dr abokin Aslma don ɗakin ba'a bari a shiga Aslam baiyi niyar zuwa ba kawai dan yana jin nauyin Alhaji Abdur-rahman ne amma ba dan Allah yaje ba dan ko kaɗan baiji tausayin Dad ba kwata kwata mutumin ya sire mai, gani yake ma alhakin su ne ya kama shi na zuwa da yayi bagatatan ya musu asarar ciki. Alhaji Abdur-rahman ne gaba yana rike da hannun zee sai Aslam dasu Mami biye dashi, dukkannin su saida zuciyar su ta girgiza da ganin yadda Dad ya koma cikin abin da baifi awa ashirin da huɗu ba, wani gigitaccen ƙara zee ta saki tare da durkushe wa a gaban bed ɗin da Dad ke kwance, Asmah ma tuni ta fashe da kuka hankalin ta ba ƙaramin tashi yayi ba, wai mutumin daya zo jiya ya nemi wulakansu haka, lallai Allah ba abin wasa bane, Mami ma sai dauke kwalla takeyi, na tausayin zee da mahaifin ta, Aslam kam take idanunshi suka kala sukayi jajur, duk yadda yake jin haushin Dad a zuciyar shi sai da ya tausaya mai, lallai ɗan Adam ba'a bakin komai yake ba, ganin yadda zee ke kururwa tana kuka, yasa Dr saurin basu umarnin su fita su bar mara lafiya shi kaiɗai kar su bata musu aiki, daƙer Aslam ya janyeta daga ɗakin, koda suka fito yace tazo ya kaita gida tayi wanka ƙin yarda tayi ta tafi, Asmah ma sarkin tausayi cewa tayi zata zauna tare da zee, ya kada dambu taliya amma suka ƙi bin shi, karshe shi da Mami ne kawai suka bar asibitin mami ta wuce da little can family hause dan zaman asibiti bai kamace shi ba. A nan suka wuni tare a asibiti sallah kawai ke tada su, daga inda suke zaune, sai bayan la'asa Alhaji Abdur-rahman ya musu abinci daga gida sa, , daga ita har Asmah babu wanda ya kalli inda abincin yake, saidai nan kuma Dad ya farka daga alluran barcin da aka mishi, sun so shiga su ganshi amma Dr ya hana ganin sun matsa yasa da'ker ya bar Alhaji Abdur-rahman ya shiga, ya samu Dad idanunshi a bude harass sai dai hawaye kawai yake zirararwa, ya tausaya mai amma hakan bai hana shi rufeshi da fada ba ya kuma sanar dashi abin da zuwan shi gidan Aslam a jiya ya janyo, karshe kuma ya daura da nasiha,daga yadda Dad ke kuka yana Neman gafarar shi,shi kamshi ya tabbatar yayi nadama sosai harda cewa a kira zee da Aslam ya nemi gafarar su, Alhaji Abdur-rahman ya hana tare da cewa taya bari ya kara samun sauki tukun, daga karshe ya koma barci saboda karfin magungunan da aka bashi yanzu bayan farkawanshi. Bayan isha'e Aslam da Abba da Alhaji baba suka zo asibe ko za a basuyi ba Alhaji Abdur-rahman shima ya dawo da ta masallaci . Mami ne data koma gida ta labarta wa Abba abun da ke faruwa shine fa ya sanar wa su daddy da Alhaji baba sun tausaya matuka duk da sunji tsiyar daya tafka Allah ya kama shi. Bayan sun gaggaisa Alhaji Abdur-rahman yace bari yaje yaji daga bakin Dr ko zasu iya shiga su ganshi dan ɗazu jikin da sauƙi, kafin ma ya kai ga tafiya wata nurse ta nufosu da sauri tana haki, dukkan su ido suka zuba mata zuciyoyin su na tsistsin kewa, tace "wacece zee da Alhaji Abdur-rahman da Aslam da karima a cikin ku." Zabura zee dake rungume jikin Asmah tayi ta mike, Aslam ne ya bata amsa da "gamu nan duka." Tace "Dr yace kuzo maza patient ɗin ku yana son ganin ku da gaggawa." Da sauri kuwa suka rufa mata baya dukkansu zuwa ɗakin, Dr ɗaya suka samu da nurse ɗaya akan Dad suna faman bashi taimakon da zasu iya, kimanin mintuna ashirin kenan da farkawanshi, tunda ya farka jikin shi ya ƙara rikice gaba ɗaya sai dai bakin shi bai mutu ba sunan zee da Aslam, Alhaji Abdur-rahman da karima, kawai yake kira a wahalce, ganin yanayin da yake ciki ne kawai yasa Dr ya zare mai karin ruwan da jini da duk wani na'ura dake jikin sa dan jikin shi ha bashi wannan mutumin kam da'ker zai kai labari, hakan daya gani yasa ya aikin nurse dinnan ta kira mutanen da yake nema watakila wasiyya zai bayar, da gudu zee ta karasa gaban shi tana wani irin kuka, mai ban tausayi, da'ker yace "Zainab mutuwa zanyi, ki yafe min." Ciki kuka tace "dadi na baza ka mutu ba in sha Allah zaka warke zafin ciwo ne yasa kake ganin kamar ajalin ka yazo." Murmushi yayi wanda ba kowa bane zai fahimci hakan saboda yadda fuskar shi tayi dameji, yace "mutuwa zanyi Zainab ni nasan abin da na hango, ina mijin ki yake." Aslam dake tsaye daga can baya idanunshi jajur ya karaso gaban Dad, kallon shi Dad yayi ya mika hannunshi guda mai lafiya ya kama hannun Aslam ya manna dana zee dake tsaye kusa da shi cikin maganar shi irin ta marasa lafiya sosai wanda sai mutum ya kasa kunne yake iya gane mai yake fada yace "Aslam kayafe min, nasan na cutar da kai na yi sanadin da ka rasa gudan jikin ka, amma dan Allah karka kulla ceni komai nakeyi akan soyayyar Zainab ce, itace jarabtata duniya tunda na haifeta nake bata wa mutane da yawa rai akan ta indai ita zatai dariya, Allah ya rarabceni da makahon so akan Zainab, kuma har yanzu dana ke kan gabar barin duniya daidai da kwayar zarra banji ɗigo na sonta ya ragu a zuciya ta, ga amanar Zainab nan na bar maka Aslam, duk duniya babu wanda take so sama da kai dan Allah ka kula min da ita ko bayan rai na, dan Allah badan halina ba." kafin ya samu daman kara cewa wani abu tuni harshen shi ya karye sai magana yake yi amma babu mai fahimtar shi, tuni zee ta ƙara ruɗewa tare da fashe da wani irin kuka ta faɗa jikin shi ganin haka yasa Aslam janyeta da karfi tana fisgewa ya fice da ita daga ɗakin, Asmah ma dake kuka Abba ya rike hannun ta ya fice da ita waje,Alhaji Abdur-rahman ne ya masto gare shi yana sharar kwallah ya kama hannun shi ya rike gam yana cewa "dan uwana insha Allah baza ka mutu ba, zaka tashin akan kafafun ka zafin ciwo ne." Alhaji baba dake tsaye gefe yana kallon yanayin Dad ya tabbatar wannan kam yana kan gaba, matsowa yayi gare shi ya shiga laƙaba mishi Kalmar shahada, Allah sarki Dad kasa.kamawa yayi sai ya bude baki zai kama kuma maganar ya sarƙe, karshe idanun shi ya shiga kafewa kumfa na fitowa daga bakin shi, take kuma jikin shi ya fara sakewa a hankali kuma kanshi ya karye gefe.............

Oum Ummeetarh
07041130088
💖DAMA TA BIYU💖

BY

~AYSHA NALADO~

FREE BOOK

{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya,Allah kajiqan iyayen}

Chapter Navigation

Use this section to move to any chapter without going back to the top.